Showing 66001 words to 69000 words out of 72709 words

Chapter 23 - AUREN HADI COMPLETE DOCUMENT WRITING Samira Haruna.txt

yamutse tace "wallahi La Mama zazzab'i ne ga ciwon kai ya takura min sosai, sai amai da nake fama dashi tun jiya da dare."


Abun mamaki kallon juna sukayi tare da murmusawa kafin Mama tace "to Allah ubangiji yasa rashin lafiyar alkairi ce, yanzu kije ciki ki samu wuri ki kwanta kafin ta shigo."


Da k'yar ta tashi tana shiga falo tayi karo da wasu 'yan uwan sunata hira, ciki ciki ta gaishesu da "sannunku da hira."


Wucewa taje tayi d'akin mai bikin sai muryar Sumayya taji ta bayanta tana fad'in "aikin banza aikin wofi, wai har mu za'a ma d'aukar kai, da bamu san asalin balbela ba da sai tace mana daga misra take, wai dan iyayi da ganin kinfi kowa ace sai yanzu kika zo bikin 'yar uwarki, mtssss."ta k'arashe da jan dogon tsaki.


Cikin yanayi marar dad'i Ummi ta jiyo tana kallonta tace "aunty Soumayya lafiyarki k'alau, meya faru?"


Wani tsaki ta kuma ja kafin tace "asibiti ce a kaina iyakar rashin lafiya, ko nima ci mun mutumci za kiyi ne?"


Cikin dakakkiyar murya Ummi tace "bari har narar da ki kayi shi, in yaso saina ci."


Ciki da hassala tace "ranar da nayi me?"


"Wai dan Allah miye haka, shigowata fa kenan me yake damunki ne haka?"


Cikin gadara Soumayya tace "bikin 'yar uwarki ake fa, amma ace sai yanzu ana kiran sallah azahar zaki zo, saboda ke kina tunanin yanzu kin zama wata tsiya mijinki ma haka shi yasa kike yanda ki kaga dama."


Saida Ummi ta gyara tsayuwarta cikin rashin jin dad'i tace "uhum, to kinji dai maganar nan yanzu ta fito fili, amma ba saboda na jima bane kike wannan abun, naga akwai dayawa wanda har yanzu suma basu zo ba, sannan tsawon sati d'aya nayi ina zarya gidan nan, sannan kina ina daren jiya dana kusan raba dare a gidan nan.?


Cikin b'acin rai tace "miye ke raina to?gaskiya ce na fad'a danni ban iya b'oye b'oye ba, danni bana jin tsoronki kamar yanda sauran 'yan uwa da sarakuwarki da kuma shi mijin tacen suke tsoronki."


Cikin zafin nama Ummi taci kwalar rigarta tana fad'in "Mamana kike fad'a ma haka da mijina?"


Itama cikin zafin rai ta fincike rigarta tana fad'in "dallah sakeni malama, kinji wani d'aurin duniya wai Mamana da mijina, to an fad'a d'in ko k'arya nayi basa tsoronki, kije ki tambayesu kiji shin basa damuwa da rashin haihuwarki ne, amma saboda an riga an gama dasu yasa ko idon tuhuma babu wanda ya tab'a kallonki dasu duk sunja bakinsu sunyi shiru."


D'orawa tayi da fad'in "duk kunbi kun mallake mutane ke da 'yar uwarki da kuma uwar taku sai yanda ku kaga damar yi dasu, shi yasa tun yanzu nake ma d'an uwana (Abdul) kallon k'arshe dan tunda akace za'a hadashi da tsatsonku Islam da namu tsatson nasan nan da d'an lokaci kad'an zamu daina ganinshi."


Ummi da tuni hawaye suka wanke mata fuska bata iya cewa k'ala ba sai kallonta da take, da k'yar tace "tun yaushe kika fara jin haushina, tun yaushe kika fara hassada damu, tun yaushe kika fara bak'in ciki dani?"


D'orawa tayi da "koda yake babu amfanin sanin wannan d'in, dan nasan ba zai rasa nasaba da d'aya daga cikin biyun nan ba, kodai rashin auren da Allah bai nufa ba tsakanin mijina da 'yar uwarki, ko kuma rufin asirin da yayi mana, hakane ko?" ta tambayeta.


"Haushin me zanji, Allah ya kiyaye wallahi nafi k'arfin sama dukiyarki ido, domin ni Allah ya bani abinda ke kuma ba kida shi, wato haihuwa."


Wani murmushin takaici Ummi tayi tace "ai kinji aikin jahilci, gashi kuma ki kace abinda Allah ya baki wato haihuwa, hakan na nufin kenan kinsan da shine ke bayarwa, sannan kince abinda ni kuma banda shi amma sai ba kice abinda Allah bai min ba, dan Allah da tsayawa kina sawa rayuwar wasu ido da makaranta kika koma ki sake karatun tauhidinki dan akwai gyara a ciki."


Cike da jin zafin abinda ta fad'a mata tace "an fad'a maki bamu san komai bane, ai mata irinku 'yan neman duniya ido rufe kuna sadaukar da mahaifarku ne wa bokayenku da aljanu, kinga kuwa rashin haihuwarki ba zamu dan gantashi da All...."bata k'arasa ba taji wawan mari har guda uku a kumatunta.


Wa zamu gani in ba Salman ba da Islam ta kirashi a k'ofar gida saboda gani da tayi abin yak'i k'arewa, idonshi ne suka kad'a sukayi ja sai huci yake, cikin tsananin b'acin rai ya fara magana "dan ubanki waya aikeki fad'a mata haka, an fad'a maki kowa kece shi yasa har kike tunanin ta sadaukar da mahaifarta, to naji ta sadaukar saime ai buk'atarta ta kuma biya tunda ta samu abinda take so."


D'an yatsa ya nuna mata yace "wallahi daga yau sai yau kar na sake ji ko ganin ki tareta da makamanciyar wannan maganar, in dai har bake ke bayar da haihuwar nan ba ba kuma uban wani yake bayarwa ba to ku rabu da ita kinji na fad'a maki."


Juyawa yayi ya kalli Ummi data dafe kanta yace "kije ki samu wuri ki kwanta, karki sake kula duk wani da zai d'aga maki hankali."


Kallonshi tayi sai dai gani tayi ya rabu kusan gida hud'u sai gaba d'aya d'akin taga yana juya mata saboda jiri, hannunta ta mik'a mashi kamar makauniya dan ba ida yake ta mik'a hannun ba, kamo hannun yayi yace "lafiyarki k'alau kuwa?"


Ba tare da maganarta ta fito ba tace "kaini gida, ba zan iya...." luuuu tayi baya zata fad'i Salman yayi saurin tallabota, Kareema ce ta shigo dan haka Salman ya d'auketa suka kaita d'akin yaran Nadiya suka kwantar da ita anan ta fara dubata.


Gaba d'aya iyaye da kakanni fad'a sosai suka ma Soumayya, hakan yasa ta bar gidan cikin b'acin rai ta koma gidanta, su Jawahir ma haka ransu ya b'ace sosai kuma sunyi mamakin yanda Ummi bata kaima Soumayya bugu ba, dan ita bata juriyar magana har k'wara kaji hannu a maimakon bakinta.


Tunda Kareema ta tambayeta yaushe rabonta da ganin aladarta tace wata biyu, tun nan ta fara jiyo k'amshin alkairi amma saida tasa aka siyo jeux test ta gwada fitsarinta sannan ta tabbatar, wai da gudu ta fito daga d'akin tana k'walla kiran "yaya Salman, yaya Salman."


Su Jawahir dasu Mama ne a k'ofar d'akin dan haka suka tambayeta lafiya, bud'ar bakinta cewa tayi "Mama, La Mama ba zan fad'a ba sai kun ban goron albishir?"


Cikin rashin fahimta suka ce "goron me kuma, meya faru da Ummi ne?"


Cike da tsantsar farin ciki ta rumgume La Mama tana fad'in "wallahi juna biyu ne da ita har wata biyu."


_Tab', farin ciki fassara irin wanda akayi ma b'ata lokaci ne da kuma b'annan ruwan birona 😎 ah to._


Sujuda Salman bai san adadin da yayi ba ta godiya ga ubangiji, Ummi ta zubar da hawaye na farin ciki tare da godiya ga Allah, anan aka tayar da abinda ya faru tsakaninta da Soumayya ana mai k'ara girmama al'amuran ubangiji, shi yasa babu kyau shishigi ga al'amarin Allah, gashi dai ta bud'e baki tana fad'a akan wai ta jima har take goranta mata akan rashin haihuwa, ashe ma rashin lafiyar d'aukan cikin ne ya tsayar da ita.




Daga wannan rana daga wannan lokaci Ummi ta fara rainon cikinta tare da taimakon duk wani d'an uwa makusancinta mai k'aunarta, haka kuma daga wannan lokaci sai Ummi ta dinga taka tsantsan da kowa in ba 'yan uwanta kuma aminanta ba, sosai take samun kulawa daga wajen danginta da kuma oga Salman dan yanzu ko goyonta ya daina yi haka kuma duk wani abu da yasan idan yayi zaisa tayi gudu, to ya daina duk dan kula da lafiyar abinda yake cikinta, Ummi kam yanzu in banda hutu da motsa jiki babu abinda take, dama dai mutuniyar mutane ce kama daga mak'ota 'yan uwa abokan arziki kowa na baibaye da ita, hakan ne yasa idan Salman ma ya fita baya da damuwa yasan akwai masu kula mashi da ita.




Idan kuma sukayi tafiya tare, to tana wajen mak'otansu in zai fita dan sun saba dasu an zama kamar 'yan uwa na jini, gasu da kulawa da kirki mutanen shi yasa Ummi ke jin dad'in zama dasu.


Cikinta na wata biyar lokacin kuma suna Cotonou, gashi lokacin ana sanyi sosai kullum cikin kayan sanyi take duk abin ya isheta, ranar tana zaune a gidansu Sara sunata hira abinsu tana kallonsu sunata kai da kawo, Salman ne ya kirata a waya tazo gashi ya dawo gida da gudu ta tashi ta shiga gidan.


Tun kafin ta shiga d'akin Salman ya taso da gudu ya rik'eta yana fad'in "miye haka kuma Ummi? gudu fa kike sai kin fad'i ki jamin bala'i."


Cikin shagwab'a tace "kuyi hak'uri, na daina."


Bai tankata ba sai zif d'in rigarta daya cire mata tare da aje rigar gefe, ta d'auka buk'atar tane yake amma sai taga ya cire mata kayan sanyin ya saka mata wanda suka fisu girma da nauyi, hular sanyi ya saka mata da cash coux tare da siririn glass fari sannan ya duk'a ya saka mata takalma k'afa ciki sannan ya mik'e tsaye ya kalleta daga k'asa har sama sannan yace "yah, haka yayi ba?"


Turo baki tayi tace "to wannan so kuke na mutu ko, ni gaskiya ku mayar dani gida wallahi na gaji da saka kayan nan kullum."


Dariya yayi yace "to muje dama ciren ticket d'in zamu je ki raka ni."


Cike da farin ciki ta nufeshi da k'arfi da nufin ta rumgemeshi, hannun ya d'aga mata tare da fad'in "tsaya tsaya, dan Allah ki dinga yi a hankali kinji saboda abinda ke cikinki."


Kukan shagwab'a tasa tana fad'in "ni wallahi ku mayar dani gidanmu wajen Mamana tunda yanzu kun bar sona tunda na samu ciki sai shi kuke so."


Janyota yayi ya rumgume yace "haba Mamar 'yan biyuna, ni na isa na daina sonki ai sai dai in babu numfashi na."


Kafin tayi magana yayi sama da ita suka fita daga d'akin sannan ya ajeta ya rufe d'akin suka wuce, sosai Ummi taji dad'in fitar dan yawo sukayi sosai har bakin ruwa saida ya kaita, sunyi farin ciki sosai saida yamma sannan suka hau taxi suka ciro ticket sannan suka dawo gidan hannun Ummi d'auke da ice cream da bonbon mai tsike, dan kuka ta saka mashi da yak'i ya siya mata ice cream d'in, amma gashi har yanzu bata ko lasa ba bare tasha.




Tunda ciki ya shiga wata na shida sai laulayi ya dawo mata sabo pil a leda, cikin wata shida kamar na wata takwas sosai yayi girma, haka ta dinga fama kullum da abinda zata ji sabo ga nauyin jiki kasala duk ta hargitse kamar ba ita ba, duk wani abu na jikinta bata san tab'ashi hakan yasa kanta ta daina kitso yankan farata kuma Salman ne ke mata dan bata iyawa, wanka kawai take da k'ok'arin yin saboda bata so mijinta yaji wani odeur daba k'amshi ba a jikinta, shima babu sabulu sai dai tayi tsaye ta kunna panpo ruwa na zuba in ta gaji ta kashe ta fito ta shafa turare, Salman ne ke mata da sabulu in zaiyi, kaya kam ko kad'an yanzu ko atamfa ta daina sawa bare less ko shadda kullum cikin dogayen riguna take na kantie marasa nauyi.


```CIKI SAYIN MATA```




Kwana tashi a wajen Allah babu wuya, haka har cikin Ummi ya shiga wata na *TARA* daga lokacin kuma Mama ta hana tafiya tare da suke tunda lokacin haihuwarta ya kusa, shi ma kuma tunda ta shiga watan haihuwarta ya tsaida duk wasu harkoki da zasu sa saiya bar gari ya maida hankalinshi akan jaririyarshi.


Masha Allah cikin Ummi shine rigani kwana, dan yanzu kam idan ta zauna to sai an had'a da addu'a take tashi tsaye, sosai sosai cikinta yayi girma ga tsini k'afafu kam sukace ja bani wuri saboda kumburi kai kace iska ne aka busa mata, amma duk da haka sai cikin yasa tayi kyau a fuska ga haske kamar wacce bata da jini a jiki, Mama da Salman tausayinta suke kullum haka suka duk'ufa wajen rok'on Allah ya sauketa lafiya, kuma har yau Salman Mamar 'yan biyu yake kiranta dashi.


Koda taje likita aka fad'a mata nan da sati biyu zata iya tsammanin jiran haihuwa, koda tazo gida ta tada hankalin Salman saiya kaita gida ta haihu acan, bai mata gardama ba ya kaita gida wajen La Mama, daga ranar suka tare can da zama har Salman d'in, yau ta kama asabar d'in k'arshen wata ana reunion gidan Alhaji, amma La Mama ta hanata tafiya saboda ganin yanda tayi wata iri da ita kamar dai ace mata ta haihu kuma ta haihun.


Haka akayi rΓ©union Ummi kuma bata damu ba dan ita tasan abinda take ji, ana sallah la'asar su Jawahir Nadiya Khairat Hafsat suka zo wajen Ummi anan suke fad'a mata wani sabon tsari da taji dad'inshi sosai, wai Alhaji ya dakatar da auren Islam da Abdul dan yaji abinda Soumayya ta fad'a watak'ila kuma maganar daga manyanta taji shi yasa ta fad'a ita ma, Abdul kam yana son Islam sosai hakan yasa baiji dad'i ba yaji kuma Soumayya ta bashi haushi, abin mamakin ma shine cewa da Alhaji yayi idan Islam d'in tana da wanda take so ta fito dashi tunda babu wani matashin saurayi daya isa aure, hakan ba k'aramin k'ara b'atama wasu rai yayi ba dan a ganinsu yanzu ma shige da ficen ne akayi shi yasa haka ta faru.


Sun jima suna tattaunawa kafin suka tafi La Mama kuma ta shigo, tunda taga Ummi tasan lokaci ya kusa tunda dama kwana goma sha d'aya kenan a cikin sati biyun da aka bata, kallonta kawai take tana yamutsar fuska tare da cije leb'e amma ba tace mata komai ba, har bayan sallah isha Salman ya shigo gidan ya zauna kusanta ya mik'e k'afafu yana kallonta cike da tausayawa, ganin yanda zufa keta keto mata har ta kai fitowa take, ko uffam ta kasa cewa sai jujjuya kai take yi haka har La Mama ta kawo masu dafaffen naman kai data dafa.


Gashi dai Ummi tana so ta ci amma ina ta kasa, a hankali Salman ya dinga dib'a yana sa mata baki, amma koda ta karb'a sau uku bata k'ara na hud'u ba, cikin rarrashi yace "haba Mamar 'yan biyuna ki k'ara mana ko kad'an ne."


Kamar za tayi kuka tace "La Mama ki fad'a masu su daina cemin Mamar 'yan biyu."


Bud'ar bakin La Mama cewa tayi "haba Ummi wannan girman ciki naki masha Allah in baki haifi 'yan uku ba ko yan hud'u, ai dai kya haifi 'yan biyu."


Salman bushewa yayi da dariya yace "ahan, kinga ashe La Mama ma kallon Maman 'yan uku da hud'u take maki."


Ba tayi magana ba Islam ta shigo hannunta rik'e da Ihsan autar Sa'ada, wajen Ummi ta zauna tana mata magana amma ko jinta ba tayi, Salman ne yace "Ihsan ki rabu da auntynki bata lafiya nak'udar 'yan biyu take." ya fad'a yana shek'ewa da dariya.


Cikin d'umin yara Ihsan tace "eh tonton, ai kasan aunty 'yan biyu zata haifa ko?"


Cike da fara'a yace "ashe kema kin sani, to waya fad'a maki?"


"Wallahi ko tonton 'yan biyu ne ni da kaina na gani."


Dariya La Mama tayi tace "shi kenan ya tabbata 'yan biyu zaki haifa insha Allah, sai dai fatan Allah ya sauke ki lafiya sannan muga mi zaki haifa."




Tun Salman na hira da Abba ya lura da Ummi bata jin dad'i sosai, haka ma Abba yana kallonta duk saiya ji tausayinta ganin yanda ta canja k'afafu a mik'e ko motsin kirki bata iya yi, ai kam sai nak'uda tace salamu alaiki Ummi gadan gadan ta taso mata, tuni suka d'auketa sai asibiti yayin da Mama dasu Hajiyoyin Alhaji suka biyo bayansu, 22:30 suka je asibiti amma cikin ikon Allah da addu'o'in iyaye sai ga santalen santalen kyawawan yara maza guda biyu an fito ma dangi dasu waje su gani da misalin k'arfe 23:40.


πŸ’ƒπŸ’ƒπŸ’ƒπŸ’ƒπŸ’ƒπŸ’ƒπŸ’ƒπŸ’ƒπŸ’ƒπŸ’ƒ


```FARIN CIKI KENAN```


'Yan biyun farko kenan a cikin famillyn Alhaji Manu mai dala (tsoho mai ran karfe), irin farin ciki da walima tare da kyaututtukan da 'yan biyu suka samu basa misaltuwa, mahaifin yara bakinshi ya kasa rufuwa komai siyowa yake wa yara da mai jego, ya bawa Ummi kyautar yaran dukansu saboda bai san me zai bata ba, amma matsayinshi na uba yayi alk'awarin kula dasu, haka aka gudanar da suna aka kashe kud'i sosai Ummi ma tayi bajinta dan ba komai take cewa Salman yayi ba ita ma nata kawai take yi da guminta.


Yara sun samu suna ```MOHAMED TAUFIK' da ```MOHAMED RAFIK', Allah ya rayaku akan sunna.


Kwana biyu da biki Inna da aunty Fateema suna shirin tafiya, Salman ya shigo d'auke da ledoji biyu d'ayar ya bawa su Inna d'ayar kuma ya mik'awa Ummi wai na 'yan biyu ne, tana bud'awa kayan yara ta kuma gani kuma abin dariyar kowane iri hud'u hud'u, cikin jin haushi Mama tace,


"Wai kai miye haka, abu kamar hauka ina ma laifin ka siyo kala biyu, amma saika siyo kowane har hud'u hud'u, duk me za ayi dasu ka duba kaga gudan tarin tilin kayan da yaran nan suka samu fa."


"Ayi hak'uri Mama, ai sai a aje ko wasu an bawa idan anyi haihuwa." cewar Ummi da taji babu dad'i kalaman da Mama ke fad'ama jarumin nata.


Haka suka dinga tafiyar da sabuwar rayuwarsu tare da yaransu masu kama da mhaifinsu sai dai kumatunsu suna lotsawa ko murmushi sukayi kamar dai mahaifiyarsu haka kuma jikin mahaifiyarsu dan 'yan lukutayene yaran, Islam da Momy ne suka zauna gidan bayan tafiyar mai tsaronta suke tayata kula da yaran, gashi har yanzu bata iya masu wanka ba sai Salman keyi masu, nono kad'ai ke had'ata dasu da sunsha su Momy zasu karb'e su suyita jagula sai in sunyi bacci kawai, idan kuma babansu ya dawo to suna hannunshi dan ko bacci sai dai ya d'orasu akan k'irjinshi yana shafasu har suyi bacci.




```Muje zuwa```πŸ˜πŸ˜πŸ˜πŸ’‹
29/03/2019 Γ  20:22 - Mamar LatifπŸ’ƒ: πŸ’‘AUREN HA'DI πŸ’‘


_Samira Harouna_




*FIN*
```{k'arshe}```




πŸ‡ΈπŸ‡¦ *ZAMAN AMANA WRITER'S*
_(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_πŸ€œπŸ€›


*Page*


9⃣9⃣-1⃣0⃣0⃣


πŸ’ƒπŸ’ƒπŸ’ƒπŸ’ƒπŸ’ƒπŸ’ƒπŸ’ƒπŸ’ƒ


Salman ne zaune k'asa ya mik'e k'afafu yasa robar wankan yara tsakiyar k'afafunshi da Taufik' a hannunshi yana masa wanka sai

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login