Showing 42001 words to 45000 words out of 72709 words

Chapter 15 - AUREN HADI COMPLETE DOCUMENT WRITING Samira Haruna.txt

tsaye za tace masa cas.


Amma tana mayar masa da yace zaiyi amarya kuma zata fara bashi hak'uri, haka Salman ya samu yana wasa da Ummi son ransa ta hanyar k'ara aure, kullum soyayyar junansu ce ke k'ara k'aruwa a tsakaninku sai dai har yanzu kowa baya yarda d'an uwansa ya fahimta, haka suke zaune sai dai wani lokaci daga kallon da suke aikawa junansu ya kan tona sirrin zuciyoyinsu.


Salman yayi niyyar ba zai fara fad'awa Ummi kalmar so ba,saboda sanin Ummi da yayi zata iya watsa masa k'asa a ido idan ya fad'a mata, shi kuma a yanda yake jinta a zuciyarshi dama sauran sassan jikinshi baya tunanin zai iya jurar rasata ko jin rashin amincewarta daga bakinta.


Ummi ma haka ta zab'i ta b'oye ta barwa kanta ita kad'ai ba tare data fad'a masa ba, tunda ta fahimci bata gabansa ko kad'an shi yasa ma zata ci gaba da b'oyewa har lokacin da shima zai fara jin irin abinda take ji sannan ya fad'a mata.






A haka kuma warin auren su Ummi suke ci gaba da kula da cikinsu, Khairat, Nadiya suna fama da laulayi mai tsanani su Jawahir kuma alhamdulillah za'a ce.


Har yau har gobe idan Ummi ta kira La Mama dan su gaisa, sai La Mama ta k'ara jaddada mata akan ta kula da mijinta sannan saita fad'a mata wani abu da zata k'aru da shi ko dan rayuwar gaba.


*WATA BIYU*


A lokacin ne su Jawahir suka fara shirye shiryen komawa makaranta, in da Ummi ita ma ta nemi izinin Salman akan ya barta ta koma makaranta, sam Salman yak'i amincewa yace sai tayi hankali sannan zata fara fita ma daga gidan.




Ummi tayi kuka tayi magiya tayi rarrashi amma sam yak'i yarda, dole Ummi ta hak'ura ta shafa ma kanta lafiya, yayin da su Jawahir suka fara karatu sai dai suma suna kewar Ummi sosai duk da tana gaba dasu a ajin, amma dai koba komai zasu dinga had'uwa.


Tun lokacin sai Ummi ta sauya gaba d'aya ta daina walwala ba kamar da ba, yanzu duk abinda Salman zai mata bata kula shi sai dai ta bishi da ido kawai, hakan ba k'aramin tab'a Salman yayi ba dan kuwa farin cikinta shine nashi, amma yanzu gashi ta daina gaba d'aya, dole Salman ya nemi mafita daga matsalar dan a ganinshi koda ace ba abinda yake da iko a kanshi bane ai zaiyi k'ok'arin ganin ya sata farin ciki, bare kuma yana da iko.




Ummi na zaune a falo tana kallo tare da uban tagumin data rabka Salman ya shigo da sallama, kallo d'aya ta masa ta kau da kanta tana amsa sallamar, zaune yayi kusanta yana kallonta, ledar dake hannunsa ya mik'a mata ta karb'a tana kallonsa ta aje ledar dan a tunaninta irin kayan k'walam d'in da yake siyo mata ne.


Kallonta yayi yace "miye haka kuma? ya za'a baki abu amma ba zaki duba ba ki gani, kawai saiki aje."


Ko kallonshi ba tayi ba ta d'auki ledar ta fara dubawa, take farin ciki ya lullub'eta saboda ganin d'inkakken tenue (uniform) da sauran kayan makaranta da duk abun da d'an makaranta zai buk'ata.


Fiddo kayan tayi ta mik'e tsaye tana gwadasu a jikinta bak'ak'e (tenue 'yan lycée ne na moufida), riga iya gwiwa wacce ta bud'e sosai da gajerun hannuwa sai dogon wando mai forme d'in slim da kuma hijab daya wuce rigar, sannan da nik'ab, cikin mamaki tace,


"Wannan fa yaya Salman na miye?"


Murmushi yayi yana kallon tsantsar farin cikin dake kan fuskarta yace "naki ne"


Bud'a baki tayi cike da farin ciki tace "wow, yaya Salman amma naji dad'i sosai, hakan kenan na nufin zan koma makaranta nima?"


Da ido kawai ya mata alamar Eh, cike da farin ciki ta k'araso wajenshi ta zube k'asa tana fad'in,


"Kai amma yaya Salman naji dad'i sosai, Allah ya saka maka da alkairi, Allah ya k'ara bud'i na alkairi, Allah bar min kai, Allah ya saka maka son...."shiru tayi ta kasa k'arasawa.


Mamaki ne ya bayyana a fuskarshi tare da fad'in "ya saka min son mi?" kai kawai ta girgiza alamar ba komai, mik'ewa yayi ya nufi d'akinshi ita ma haka, suna kaiwa k'ofar d'akin Ummi tace,


"Yaya Salman yaushe zan fara tafiya?"


"Gobe mana"ya fad'a yana bud'a d'akinshi, murmushi tayi wanda ya bayyana hak'oranta tare da dinple d'inta sosai, Salman dake k'ok'arin shiga d'akinshi ne tsaya tare da dawowa yana kallonta, a hankali yasa d'an yatsarshi akan dinple d'inta ya latsa, ita kam k'ura mashi ido tayi tana kallo yayin da shi kuma kasa had'a ido da ita saboda tartsatsin da yake ji idan yana kallon idonta ma abota girma da fari.


Bai bar latsa kumatunta ba yace "Ummi na barki ki koma makaranta ne saboda tabbacin da nake da akan ki, na san zaki kula da kanki sannan zaki karemin mutunci na dama mutuncinki."


Ajiyar zuciya ta sauke tana kallon cikin idonshi tace "insha Allah yayana, ba zan tab'a baka kunya ba, sannan ba zanyi abinda zai shafi mutuncin ku ba, zanyi iya bakin k'ok'arina wajen ganin na kare maku hakk'inku da yake kaina musamman ma kai."


Murmushin jin dad'i yayi yace "me yasa musamman ma ni?"


K'asa tayi da idonta cikin jin kunya tace "saboda kai mijina ne." tana fad'a ta k'arasa shigewa d'aki tana dariya, Salman ma haka d'aki ya shiga yana jin wani sanyi na ratsashi yana ji ina ma ace Ummi ta fad'a mashi kalmar so a matsayin godiyar abinda ya mata.




Tun asuba Ummi da tayi sallah bata kwanta ba, tana gama had'a abinda kari ta d'an gyara abinda zata gyara a d'akinta da falo dama cuisine, tana kammalawa ta shiga wanka tana fitowa tsaf ta shirya cikin tenue d'inta.


Jakarta ta d'auko da hijab da nik'ab ta fito falo ta ajesu saman kujera sannan ta nufi d'akin Salman dan ta tashe shi, da sallama ta shiga amma shiru bai amsa ba alamar bacci yake, saida ta k'arasa har gabanshi ta k'ura mashi ido tana kallo yana baccinshi cikin kwanciyar hankali.


Rumgume hannayenta tayi a bayanta a hankali tace "ina sonka yaya Salman, sai dai ba zan iya fad'a maka ba, dan na san kai baka sona kuma ba zaka soni ba, amma zan ci gaba da jiran lokaci na san zai zo."


Lek'a fuskarshi tayi taga sosai yake baccinshi dan haka ta sunkuya daf da k'eyarshi ta sumbata, mik'ewa tayi tare da zura hannunta ta rufe hancinshi, da sauri ya juyo da kanshi yana bud'a idonshi yana ganin Ummi ya tashi zaune yana ci gaba da kallonta, murmushi kawai take masa kafin yace,


"Wannnan kuma wane irin tayar da mutum daga bacci ne?"


D'aga kafad'u tayi tare da d'aga gira sama alamar ba magana, saukowa yayi daga kan gadon yana fad'in "saina ji kamar an sumbace ni a kaina ko?"


Bud'e baki tayi cike da mamaki, lokaci d'aya kuma tayi k'asa da kanta tana wuru wuru da ido, gaf da ita ya matso yace "kece ko, ko dai akwai abinda kike b'oyewa ne ban sani ba?"


D'ago ido tayi suka kalli juna, ja tayi da baya tana fad'in "haba dai sumbata fa? sai kace wani jariri."


Toilet ya nufa yana fad'in "banyi mamaki ba dan kince haka, amma ki sani wani lokacin ma miji yafi jariri buk'atar kulawa."


Kallonshi tayi tace "to, ni dai na san ana cewa namiji kamar k'aramin yaro ne, duk in da kayi dashi can zaiyi."


Tsaye yayi yana kallonta kafin yace "kuma ke kin yarda da abinda aka fad'a d'in?"


Murmushi tayi tace "me zai hana ko, tunda mune ke jan ragamar."


Ganin ya tun karota yasa tayi saurin ja da baya tana fad'in "dan Allah ni dai kaje ka shirya kar nayi late a zuwan farko."


Sai lokacin ya lura da kayan dake jikinta dan haka yace "oh, hakane fa, ok ki bani 5 minute ina zuwa."


Kallon agogon dake gefe gadon tayi tace "ah bon, 5 minute? Ok je t'atend."


Ciki ya shige ita kuma ta dawo falo ta zauna jiranshi, kallon agogo take lokaci na tafiya amma Salman shiru bai fito ba, ido Ummi ta fiddo tare da mik'ewa tsaye tana dafe da k'irjinta ganin 07:45, kukan shagwab'a ta saka tana fad'in,


"Shikenan zuwan farko zan fara da late."


Hijabinta ta saka ta goya jakarta ta d'aura nik'ab, d'akin Salman ta nufa sai kuma suka ci karo da juna, ido ya fiddo waje yana k'are mata kallo sama da k'asa kafin ya nunata da hannu yace "ke kuma wannan shiga haka bak'a k'irin kamar wata 'yar wuta."


Turo baki tayi duk da baya gani sannan tace "yaya Salman ka dubi lokaci fa ya wuce, wallahi nayi retard."


Lokaci ya duba ya k'ara zaro ido yana fad'in "kai kai kai, lallai kam, to wuce muje ina fatan dai kin karya?"


"Ni ban karya ba, kawai idan naje naci wani abu."


Wucewa sukayi bayan ta rufe d'akin, tunda suka kama hanya tayi shiru tana kallon gari, Salman ne ya kalleta yace "ina fatan dai ba zaki cire nik'ab d'innan ba idan kinje can?"


"Haba yaya Salman dole zan cire mana dan nasha iska, lokacin zafi ne gashi yanzu ba'a ruwa sosai."


Hararanta yayi yace "bana so, karki bud'e fuskarki kowa ya gani."


"Amma yaya Salman akwai takura fa, kai baka san nik'ab ba wallahi tana hana mutum kyakyawan shed'a."


Kallonta yayi irin ba wasanan yace "wallahi idan naji labarin kin cireta, to daga ranar bake ba k'ara komawa makaranta."


Cikin shagwab'a tace "to yayana idan zan ci abinci kuma fa?"


"To na yarda ki d'aga idan zaki ci abinci, amma da kin ida ki mayar."


Hararan gefen ido ta watsa masa a ranta tace "sai kace wani sona yake da yake takura min haka"


Kallonshi tayi tace "wai yaya Salman ta yaya ka sama min gurbin karatu anan ne cikin sauri haka?"


Ba tare daya kalleta ba yace "to miye na wahala a ciki, dama anan kike karatu kuma sun baki gurbi in da zaki ci gaba, kawai baki zo da wuri bane har anyi karatun wata biyu babu ke."


Cikin tsoro Ummi tace "to yanzu idan suka tambayeni ya zance masu?"


"Na gama da wannan ma, dan na fad'a masu kinyi aure kuma yanzu ba kida lafiya."


Wani kallo ta masa tace "to me kace masu yake damuna?"


Wani kallon raini ya mata yace "na fad'a masu kina fama da laulayi ne."


A firgice ta kalleshi tace "laulayi, na ciki ko na me?"


"Ke wanne kika sani?"


Kallon gabanta tayi tace "na san na ciki."


Shima ba tare daya kalleta ba yace "to shi nake nufi."


Wani lallausan murmushi tayi tare da dafe cikin tace "wai ciki, Ummi da ciki, babbar magana."


Kallonta yayi yace "kina sonshi kenan?"


"Ina so sosai, Allah ya nuna min na samu nima."


Kallon ba kida hankali ya mata yace "keda ko hanyar daya bi baki bi ba, kuma a hakan kike neman shi."


Bata kalleshi ba tace "to miye a ciki? ai abun rabone kura ta haifi akuya."


Kallonta yayi yace "lallai kam, amma ki sani wanna kura za tasha dukan tsiya idan ta haifi akuya."


"Lallai kam, watak'ila kuma ba zata sha ba." fad'ar haka yayi daidai da zuwansu ecole d'in, bud'a k'ofar tayi zata fita tace "sai anjima."


"Idan kun tashi ki kira ni." ya fad'a yana kallonta, har zata fita ta tsaya tare da tara masa hannu tace "kud'in abinci na."


Hannu yasa aljihu ya fito da kud'i yana tambayar ta "nawa zan baki?kin san ni ba d'a gareni ba bare na san nawa ake bayarwa, kuma ma ke har wani kud'i za'a baki da girmanki."


"To ina girman yake? har yanzu fa ban wuce jaririya ba."


Kallonta yayi sosai yace "a hakan, uwar wasu kakar wasu?"


Cikin shagwab'a tace "nifa yarinya ce, har yanzu a wanke nake babu datti."


"Allah ya shirya min ke 'yan matana, ni fad'a min nawa zan baki."


Dariya tayi tace "ameen yaya Salman, kawai ka kimanta sai ka bani."


Kafin su ankara suka ji k'arar k'araurawa (sonner) lokacin shiga aji yayi.


Cikin hanzari tace "kawai ka lissafa nawa ake baka da kana kamar ni."


"Ni ai ina kamar ki kud'in makaranta ma ni na biyawa kaina."


Cike da k'aguwa Ummi tace "to kawai ka ban 1000f ta isheni."


Dubawa yayi sai dai babu wacce ta buk'ata, dan haka ya bata 5000f tana karb'a ta fita tana fad'in "zan aje maka canjinka, sai kazo."


Kallonta yayi sai gudu take har ta shige ciki, kai girgiza yaja motar yana fad'in "kaji gudun da take kamar yarinya, ba zata yi hankali ba wannan har saina saita ta."


Yaji dad'i sosai ganin yanda kayan suka mata d'as da ita, gashi duk sun rufe jikinta sai idanunta kawai da hannayenta ne a waje, dan takalman data saka ma k'afa ciki ne maras tudu(valerine) bak'ak'e.








```SAM```😍
11/03/2019 à 17:51 - Mamar Latif💃: 💑AUREN HA'DI 💑


_Samira Harouna_


🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITER'S*
_(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_🤜🤛


*Page*




7⃣9⃣-8⃣0⃣




Haka zaman nasu yake tafiya ba yabo ba fallasa, har yanzu babu abinda ya canja daga zaman nasu sai dai abu d'aya shine yanzu Ummi tana yin duk abinda Salman ya sakata, har yanzu Ummi ba tada sarau dan kuwa ko yanzu Salman yace mata kule to kai tsaye za tace masa cas.


Amma tana mayar masa da yace zaiyi amarya kuma zata fara bashi hak'uri, haka Salman ya samu yana wasa da Ummi son ransa ta hanyar k'ara aure, kullum soyayyar junansu ce ke k'ara k'aruwa a tsakaninku sai dai har yanzu kowa baya yarda d'an uwansa ya fahimta, haka suke zaune sai dai wani lokaci daga kallon da suke aikawa junansu ya kan tona sirrin zuciyoyinsu.


Salman yayi niyyar ba zai fara fad'awa Ummi kalmar so ba,saboda sanin Ummi da yayi zata iya watsa masa k'asa a ido idan ya fad'a mata, shi kuma a yanda yake jinta a zuciyarshi dama sauran sassan jikinshi baya tunanin zai iya jurar rasata ko jin rashin amincewarta daga bakinta.


Ummi ma haka ta zab'i ta b'oye ta barwa kanta ita kad'ai ba tare data fad'a masa ba, tunda ta fahimci bata gabansa ko kad'an shi yasa ma zata ci gaba da b'oyewa har lokacin da shima zai fara jin irin abinda take ji sannan ya fad'a mata.






A haka kuma warin auren su Ummi suke ci gaba da kula da cikinsu, Khairat, Nadiya suna fama da laulayi mai tsanani su Jawahir kuma alhamdulillah za'a ce.


Har yau har gobe idan Ummi ta kira La Mama dan su gaisa, sai La Mama ta k'ara jaddada mata akan ta kula da mijinta sannan saita fad'a mata wani abu da zata k'aru da shi ko dan rayuwar gaba.


*WATA BIYU*


A lokacin ne su Jawahir suka fara shirye shiryen komawa makaranta, in da Ummi ita ma ta nemi izinin Salman akan ya barta ta koma makaranta, sam Salman yak'i amincewa yace sai tayi hankali sannan zata fara fita ma daga gidan.




Ummi tayi kuka tayi magiya tayi rarrashi amma sam yak'i yarda, dole Ummi ta hak'ura ta shafa ma kanta lafiya, yayin da su Jawahir suka fara karatu sai dai suma suna kewar Ummi sosai duk da tana gaba dasu a ajin, amma dai koba komai zasu dinga had'uwa.


Tun lokacin sai Ummi ta sauya gaba d'aya ta daina walwala ba kamar da ba, yanzu duk abinda Salman zai mata bata kula shi sai dai ta bishi da ido kawai, hakan ba k'aramin tab'a Salman yayi ba dan kuwa farin cikinta shine nashi, amma yanzu gashi ta daina gaba d'aya, dole Salman ya nemi mafita daga matsalar dan a ganinshi koda ace ba abinda yake da iko a kanshi bane ai zaiyi k'ok'arin ganin ya sata farin ciki, bare kuma yana da iko.




Ummi na zaune a falo tana kallo tare da uban tagumin data rabka Salman ya shigo da sallama, kallo d'aya ta masa ta kau da kanta tana amsa sallamar, zaune yayi kusanta yana kallonta, ledar dake hannunsa ya mik'a mata ta karb'a tana kallonsa ta aje ledar dan a tunaninta irin kayan k'walam d'in da yake siyo mata ne.


Kallonta yayi yace "miye haka kuma? ya za'a baki abu amma ba zaki duba ba ki gani, kawai saiki aje."


Ko kallonshi ba tayi ba ta d'auki ledar ta fara dubawa, take farin ciki ya lullub'eta saboda ganin d'inkakken tenue (uniform) da sauran kayan makaranta da duk abun da d'an makaranta zai buk'ata.


Fiddo kayan tayi ta mik'e tsaye tana gwadasu a jikinta bak'ak'e (tenue 'yan lycée ne na moufida), riga iya gwiwa wacce ta bud'e sosai da gajerun hannuwa sai dogon wando mai forme d'in slim da kuma hijab daya wuce rigar, sannan da nik'ab, cikin mamaki tace,


"Wannan fa yaya Salman na miye?"


Murmushi yayi yana kallon tsantsar farin cikin dake kan fuskarta yace "naki ne"


Bud'a baki tayi cike da farin ciki tace "wow, yaya Salman amma naji dad'i sosai, hakan kenan na nufin zan koma makaranta nima?"


Da ido kawai ya mata alamar Eh, cike da farin ciki ta k'araso wajenshi ta zube k'asa tana fad'in,


"Kai amma yaya Salman naji dad'i sosai, Allah ya saka maka da alkairi, Allah ya k'ara bud'i na alkairi, Allah bar min kai, Allah ya saka maka son...."shiru tayi ta kasa k'arasawa.


Mamaki ne ya bayyana a fuskarshi tare da fad'in "ya saka min son mi?" kai kawai ta girgiza alamar ba komai, mik'ewa yayi ya nufi d'akinshi ita ma haka, suna kaiwa k'ofar d'akin Ummi tace,


"Yaya Salman yaushe zan fara tafiya?"


"Gobe mana"ya fad'a yana bud'a d'akinshi, murmushi tayi wanda ya bayyana hak'oranta tare da dinple d'inta sosai, Salman dake k'ok'arin shiga d'akinshi ne tsaya tare da dawowa yana kallonta, a hankali yasa d'an yatsarshi akan dinple d'inta ya latsa, ita kam k'ura mashi ido tayi tana kallo yayin da shi kuma kasa had'a ido da ita saboda tartsatsin da yake ji idan yana kallon idonta ma abota girma da fari.


Bai bar latsa kumatunta ba yace "Ummi na barki ki koma makaranta ne saboda tabbacin da nake da akan ki, na san zaki kula da kanki sannan zaki karemin mutunci na dama mutuncinki."


Ajiyar zuciya ta sauke tana kallon cikin idonshi tace "insha Allah yayana, ba zan tab'a baka kunya ba, sannan ba zanyi abinda zai shafi mutuncin ku ba, zanyi iya bakin k'ok'arina wajen ganin na kare maku hakk'inku da yake kaina musamman ma kai."


Murmushin jin dad'i yayi yace "me yasa musamman

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login