Showing 39001 words to 42000 words out of 72709 words
Chapter 14 - AUREN HADI COMPLETE DOCUMENT WRITING Samira Haruna.txt
dan yanzu kam ya fahimci abinda ke cikin zuciyarta ne ya fito fili, lallai har yanzu tana kishi da shi to amma me yasa.?
D'akinshi ya koma yana tunani akan abinda ta fad'a har bacci ya d'aukeshi, ita ma bacci ne yayi gaba da ita.
ππππππππ
05/03/2019 Γ 17:33 - Mamar Latifπ: π AUREN HA'DI π
_Samira Harouna_
πΈπ¦ *ZAMAN AMANA WRITER'S*
_(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_π€π€
*Page*
7β£5β£-7β£6β£
Tunda safe Ummi ta tashi ta had'a abin karyawa iya bakinta ta ci, tana kammalawa tayi wanka ta komo falo ta zauna tana kallo, Salman ne ya fito daga d'akinshi singlet da dogon wando da alama sport zai je.
Ko kallonshi Ummi ba tayi ba haka ta zauna har ya dawo saidai baiyi gumi ba saboda ansha ruwa jiya, d'aki ya shiga kai tsaye ya shiga toilet dan yin wanka, yana fitowa ya shirya cikin k'ananan kaya sannan ya fito falon.
Ba tare daya kalleta ba yace "tunda har yanzu ba kiyi wayon gaida mutane ba, to ki kawo min abinci na."
Bata kalleshi itama tace "iya bakina kawai na dafa kuma na cinye."
Wani kallo ya watso mata kafin yace "Ummi karki saka ni abinda banyi niyya ba, ki kawo min abinci na kafin ranki ya b'ace."
Saida ta watsa masa harara ta murgud'a baki sannan tace "kaji min mutum dan Allah, to wallahi ba zai yiwu ba haka kawai ni da ciyar da kai kuma wata da morarka, kaje mana amaryarka ta baka abincin."
Dariya ce ta sub'uce masa bai shirya ba, sosai yake dariya har da rik'e ciki yake, Ummi kam ta gama cika dan haushi kawai sai taja dogon tsaki, shiru Salman yayi yana kallonta kafin ya mik'e tsaye yasa hannuwa aljihu yace,
"Ok zan tafi naci a waje, amma fa karki manta Salman d'an dangi ne, iya gidansu Khamis ma kad'ai zan iya cika ciki na har saina ture."
Yana shirin ficewa Ummi tayi karaf ta rik'e hannunshi tana fad'in "a'a dan Allah kayi hak'uri to zan dafa maka abinda kake so."
Kallonta yayi ya kalli hannun data rik'e yace "sake min hannu malama"
"Dan Allah kayi hak'uri wallahi zan yi." ta fad'a kamar mai shirin fashewa da kuka, dawowa yayi ya zauna bisa kujera har yanzu tana rik'e da hannunshi, kallonta yayi sosai kamar yana so ya fahimci wani abu a tare da ita kafin yace,
"Mi amarya ta ta miki ne haka? tun jiya kike masifa a kanta."
Dama kamar jira take sai kawai ta fara kuka kamar an k'wak'wale mata ido, Salman kam shiru yayi yana sauraranta har ta gama, kusan minti shabiyar tayi tana kuka kafin ta bawa kanta hak'uri ta share hawaye ta kalleshi tace,
"Yaya Salman wai da gaske aure zaka k'ara?"
Cike da gamsarwa yace "e aure zanyi, miya faru?"
Shan majina ta fara tare da saukowa daga kan kujera ta zube akan gwiwoyinta biyu ta had'e hannayenta biyu alamar rok'o tace "yaya Salman dan Allah kayi hak'uri karka k'ara aure, wallahi ni kuma nayi maka alk'warin zan canja zan zama yanda kake so kuma zanyi duk abinda kake so."
Hannayenshi ya d'ora akan gwiwoyinshi yana kallonta cikin mamaki yace "Ummi me yasa ba kya so, miye matsalarki idan na k'ara aure?"
Kuka take sosai tace "ban sani ba nima yaya Salman, kawai dai bana jin dad'i idan kace zaka k'ara aure zafi nake ji a cikin nan da k'unci." ta fad'a tare da d'ora hannu a k'irjinta b'angaren zuciyarta.
Wani irin murmushi Salman yayi najin dad'i yayin da yake fad'a a zuciyarsa "lallai wannan so ne kuma Ummi tayi nisa, kawai dai ta kasa fad'a kamar yanda nima na kasa fad'an komai."
Da hannu ya mata alama ta zauna kusa dashi, tana zaunawa ya kalleta yace "Ummi da gaske kike fad'an maganar nan?"
Cikin kuka tace "wallahi da gaske nake yaya Salman, ba zan sake maka rashin kunya ba."
Shi kam kamar yayi dariya amma ya rik'e, cewa yayi "ok tunda kince haka na yarda, amma a bisa wani sharad'i."
"Na yarda koma wane iri ne in dai zai hana ka k'ara aure."
"Ok ba zan k'ara aure ba in dai zaki dinga jin magana ta, amma ki sani duk sanda kika min ba daidai ba to tabbas a satin nan k'anwarki zata shigo gidan nan a matsayin amaryarki."
Saida ta harareshi ta gefen ido tace "na yarda, kuma wallahi idan nayi abinda kake so kuma kace zaka k'ara aure to wallahi...." mik'ewa tayi danta had'a mashi abin karin, da sauri ya rik'e hannunta yace,
"Wallahi me?"
Saida ta nuna shi da yatsa tace "saina kashe ka, dan ba zan had'u ni da wata a kanka ba." Fak'at π³
Wucewa tayi Salman ya bita da ido "anya yarinyar nan ba zata kashe ni ba kuwa in ina maganar auren nan?"
_Ah to koma dai miye ni dai ina daga nan_
Haka ta wuni ita d'aya a gidan jikinta yayi sauk'i sosai shi yasa ma babu wanda yazo gidan dubata saidai kiranta a waya kawai, har dare haka ta kammala 'yan aikace aikacenta kafin Salman ya shigo gidan, kai tsaye d'akinshi ya shiga yayi wanka yana fitowa ya shafa mai, tsaye yayi yana kallon kayan da zaisa kafin daga bisani ya yanke wata shawara.
"Abule, Abule, wai Abu bata jine?" Salman ne fa ke kiran Ummi haka, Ummi dake zaune falo tun kiran farko taji tasowa tayi tana fad'in "haba wallahi saina maka rashin mutunci in kana kirana da wannan sunan."
"Gani" ta fad'a a tsaye, kallonta yayi dan bai san da shigowarta ba hankalinshi na kan sak'on daya shigo wayarshi yanzu, ba tare daya kalleta ba yace "fiddo min kayan da zansa."
Kallon ba kada hankali ta bishi dashi har ta bud'a wadrob d'in ta d'auko wasu bleue noir rigar kamar singlet saidai hannuwan suna da fad'i sai dogon wando.
Aje masa tayi tana kallon wayar dake hannunshi, tashi yayi ya aje wayar dan yasa kaya, sai kawai idonta ya sauka kan chart d'in da suke da mai wannan sunan *Reine*, da sauri ta d'auki wayar tana kar'ema photon Nuseiba kallo wanda ga dukan alama yanzu ta aiko shi, a k'asa kuma ta rubuta,
__kana da girma a wajena yaya Salman, ba zan iya had'a ido da kai ba koda a photona ne._"
Jin hawaye sun taho mata ne yasa ta aje wayar tana kallonshi, kallonta yake shima kafin yace "ya dai lafiya?"
"Allah zai saka min in har kaci amana ta, kuma wallahi zanje na samu Nuseiba har gida sai naji dalilin da yasa take kula ka, azzalumai macuta kawai."
Zata fita ya rik'o hannunta tare da fad'in "ke kina hauka ne, wai mi yake damunki ne?"
Cikin b'acin rai ta fizge hannunta tace "lΓ’che moi (sake ni)"
Tana fita d'akinta ta shiga ta fad'a saman gado ta fashe da wani kuka mai cin rai da ban tausayi.
*Kishi kenan, zama da kishiya sai dole amma idan a kayi hak'uri to komai ya kan zo ya wuce kamar bai faru ba, mu dinga saka hak'uri tare da tausar zuciyar mu da kuma addu'a, dan ba kowace mace bace zata iya hak'urin ganin ta had'a miji da wata.* _Allah kasa muyi kishi mai tsabta irin na matan Annabi (S A W)_
Yana saka kaya ya d'auki wayar yana kallon Nuseiba kafin yace "kiyi hak'uri ba zan iya juran ganin hawayenta ba, in dai har a kanki ne take shiga k'unci to daga yau ba zata sake b'ata ranta ba, ina son aurenki ne saboda kashe wata matsalata, amma idan maganar so ake to Ummi ce a cikin zuciyata dama birnin raina, bana jin wata ko wani abu kamar yanda nake jinta a cikin zuciyata dan haka daga yau komai ya k'are, ba wai zumuncin mu ba saidai daga yanzu ba zan sake maki kallon wacce nake so na aura ba, daga yanzu kin koma k'anwata kamar yanda kike a da, Ummi kuma zan ci gaba da k'ok'arin sakata farin ciki da yardar Allah."
"Dole na guji b'acin ranta in dai har a kaina take kishi haka, ban san me take ji ba amma da zan iya kwatantashi da abinda naji jiya lokacin da tace min wannan likitan ya rik'eta, to tabbas ba k'aramin b'acin rai da tashin hankali take ciki ba."
Yana fad'a ya canja sunan Nuseiba daga Reine zuwa Cousine Nuseiba kamar yanda yake a sauran numbobin 'yan uwa, d'akin Ummi ya shiga sosai ta bashi tausayi ganin ta dage tana kuka dan taji sauk'in abinda ke damunta.
Zaune yayi tare da d'agota ya d'ora kanta a k'irjinshi yana fad'in "haba Ummi duk wannan kuka dan kinga photon Nuseiba ne? amma ai ni na maki alk'awarin na fasa ko?"
D'agawa tayi daga jikinshi cikin kuka tace "yaya Salman me yasa, me yasa nake jin haka? wallahi ji nake na tsani 'yar uwata? "
Kai ya girgiza mata ya k'ara janyota ya rumgume yana cewa "shhhh, kiyi shiru kinji ya wuce ba zan sake ba"
Cewa tayi "yaya Salman ba wai na hana ka k'ara aure bane, ni kawai bana so ne ka auri kowace mace, ina ji da ina da iko a kanka to dana hana ka auren kowace mace a duniya, yafi muyi zaman mu haka koda ma za kayi ta duka na wallahi ba zan gaji ba."
Ji yayi duk ya k'ara jin haushin kanshi in dai har tana jin haka a kanshi, to miye zaisa ba zai zauna da ita ba ya kuma k'ara sonta fiye da yanda ita take sonshi.
Rarrashinta yayi tayi har tayi shiru kafin suka komo falo ta bashi abinci yaci, dare nayi kowa ya kama hanyar d'akinshi, suna kaiwa k'ofar d'akunan suka kalli juna Salman ne yayi murmushi yace,
"Kiyi bacci ba sai kin kawo min tea ba."
Shiru tayi tana kallonshi dan haka yace " kina buk'atar wani abu ne?"
Nan ma babu amsa dan haka ya matso kusa da ita yace "ko zaki kwana d'akina ne?"
Tana jin haka ta bud'a d'akinta ta shige, dariya yayi ya shiga d'akinshi shima yana fad'in "tsoro kamar farar kura, ko taya zata fuskanci daren farkonta.?"
```Wannan aiki kuma ai ya rage naka ```π
05/03/2019 Γ 19:30 - Mamar Latifπ: πAUREN HA'DI π
_Samira Harouna_
_'YAN K'UNGIYATA INA JI DAKU_
```MY HEENAT, MY BK, MY SEEYA, K'AWALLIYA CEYMER, HAPSY, QUEEN BK, MY LISSA```πβ€π
πΈπ¦ *ZAMAN AMANA WRITER'S*
_(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_π€π€
*Page*
7β£7β£_7β£8β£
Yau Ummi ita d'aya tayi break dan yau alhamis Salman na azumi, tana kammalawa ta fara sharar falo da goge goge tana cikin goge dinning Salman ya fito cikin bleue shadda, d'inki ya masa kyau sosai gashi sun dace da k'irar shi, tsaye yayi yana k'arewa Ummi kallo data sha dogon wando da k'aramar riga, sun kamata sosai kayan gashi kuwa Ummi dama dai bata da kyau na nunawa amma k'ira kam ko a mujjala za'a iya bugata, tsaf rigar ta tsaya a k'ugunta daram wata hula ce a kanta irin mai maganin sanyi sai dai tsakiyar kanta ta tsaya sai gashinta daya kwanta a bayanta.
Daf da ita ya matso yana ci gaba da kallonta, k'amshin turarenshi da Ummi taji ne yasa tayi saurin juyowa karaf idonsu suka had'u, k'asa tayi da kanta tace "ina kwana"
Yanda rabin k'irjinta ke waje wuyanta hannayenta gaba d'aya sun d'auki hankalinshi, hannunshi yasa a hankali ya shafi wuyanta har damtsenta, jin yanda yake wani latsa fatarta yasa tayi saurin janye jikinta tana kallonshi, kallon idonta yayi da suka fara tona asirin abinda ke zuciyarshi cikin wata irin murya yace,
"Ummi bana so ki sake saka irin wannan kayan a gidan nan."
Kallonshi tayi cikin mamaki tace "saboda me, me yasa zan daina? naga ko a gidan mu ina saka kayan da raina ke so bare kuma gidana."
Cikin mamaki shima ya kalleta yace "gidanki fa ki kace? inama laifin kice gidan mijinki."
"E mana gidana, domin kuwa in da babu ni ba za'ace danan gida ba, haka da baka da ni da ba za'a kiraka mai gida ba."
Gaf da ita ya matso yana mata wani shu'umin kallo yace "amma ai a zahiri ne mutane ke ganin haka, amma a bad'ini har yanzu ke k'aramar yarinya ce baki cika cikakkiyar mace ba."
Ummi kam kallon jikinta ta fara tun daga sama har k'asa sai dai bata fahimci komai ba, kallonshi tayi tace "a hakan ne ban cika cikakkiyar mace ba? ina haka dani?"
"Murmushin gefen labb'a yayi yace "cikakkiyar mace bawai tana nufin mai k'iba ko kyau ko ilimi ko iya gayunta da sauransu ba."
Rik'e k'ugu tayi tace "to kenan me yake nufi?"
Gashinta ya janyo yana wasa dashi kafin yace "zan fad'a maki ranar da kika cika babbar mace, amma ba yanzu ba dan ba zaki fahimce ni ba."
"Ka fad'a zan gane ina da fahimta sosai."
Sakin gashinta yayi ya nufi hanyar fita, da sauri Ummi tace "in dai ban cika cikakkiyar mace ba, to kaima baka cika ba..." shiru tayi saboda yanda ya juyo yana kallonta, saida ya matso kusanta yace "ban cika namiji ba kike so kice?"
Shiru tayi tana kallonshi dan haka yace "ok muje na nuna maki ni namiji ne kuma na gaske."
Hannunta ya kama zuwa cikin d'akinta, tana ganin sun doshi d'akin ta fara k'ok'arin kwace hannunta, rik'eta yayi sosai yace "muje saina nuna maki"
Zubewa tayi k'asa tana bille bille tana kuka tana fad'in "a'a wallahi bana so dan Allah kayi hak'uri wallahi kai namiji k'arya nake dama."
Ganin zata b'ata masa lokaci yasa ya kimkimeta sai d'akinta ya zubdata akan gado, ganin yanda take kuka tana bashi hak'uri yasa ya rik'e dariyarshi wutar d'akin ya kashe tare da dawowa wajenta yana kallonta yana cire ma b'allan rigarshi yana fad'in "to wai miye na kukan? naga ke zaki zama babbar mace ni kuma zan zama babban yaro."
Cikin kuka Ummi tace "ni d'in banza wallahi bana son na zama dan Allah ka k'yaleni wallahi cikina ke ciwo ga baya na ma rik'ewa yake, ko kana so olcerta ta tashi ne?
Baya ya bata dan ya samu damar dariya tare da cire rigarshi har da singlet d'in duka ya aje a gefen gado sannan ya mik'a mata hannu yana fad'in "zo nan"
Da gudu ta nufi toilet dan neman tsira, da hanzarinshi shima ya bita tare da rik'ota, baiyi wata wata ba wajen wurgata saman gado yayo kanta gadan gadan, runfa ya mata da k'irjinshi yana k'ok'arin had'a bakinsu waje d'aya, ganin idon Ummi duk sun canja bakinta bud'e tana k'ok'arin maida numfashi amma ta kasa dan ji take kamar ya danne mata ma shak'ar iska ne.
D'agata yayi ya koma gefe ya kwanta yana dariya yana fad'in "matsoraciyar kawai, ashe bakinki na rufuwa, ashe akwai lokacin da kike rasa abin fad'a.?"
Ummi na tashi k'ofa ta nufa ta kunna wutar d'akin, juyowa tayi tana kallonshi tsaki ta masa tana shirin fita yace "zo nan."
Daga jin amon muryarsa babu wasa dan haka ta dawo tayi tsaye tana kallonshi har yanzu kuma kwance yake, "wa kike wa tsaki?"
Shiru tayi ta kasa magana dan haka yace "ok kimin tsaki san ranki kafin amaryata ta shigo gidan."
Tana jin haka ta zube k'asa tace "dan Allah kayi hak'uri wallahi ba zan sake ba daga yau."
Ba tare daya kalleta ba yace "to naji, tashi ki fita ki barni zan kwanta a nan."
Tab'e baki tayi ta yunk'ura zata tashi idonta suka sauka akan wani abu, gabanta ne ya fad'i sosai mik'ewa tayi tare da nuna wajen tace "yaya Salman miye wannan, meya ji maka ciwo anan wurin?"
Da sauri ya dafe wurin tare da tashi zaune amma bai tanka taba, a hankali Ummi tace "yaya Salman dan Allah miya ji maka ciwo a wurin nan mai hatsari, ko kaima kayi k'in ji irin na yara?"
"Ke bana san wannan tambayar kinji ko,wuce kije in da zaki"
Wucewa tayi jiki a sanyaye tana tunanin wannan wane irin ganganci ne ciwo a kusa da mara ko tsoro ma baya ji, to wai mima yaji masa ciwon ne?"
Tashi yayi yaje gaban madubi yana k'ara kallon ciwon dake k'asan cibiyarshi wanda shekara d'aya kenan daya same shi, kayanshi yasa ya fito daga d'akin tana zaune yace "saina dawo."
"A dawo lafiya" ta fad'a a takaice shi kuma ya fice daga gidan.
Tana zaune rana ta fito sosai taji ana bubbuga k'ofar gida, cike da mamaki ta saka hijab ta fito ta bud'e tana kallon mai buga k'ofar mamaki k'arara a fuskarta, MANNIR ne tare da Alhaji gefe ta matsa tana fad'in "ku shigo ciki".
Ciki suka shiga Ummi har yanzu jikinta a sanyaye yake dan bata san da wacce Alhaji ya zo ba, wuri suka samu suka zauna saida suka gaisa da Mannir sannan ta kalli Alhaji a tsorace tace "ina kwana"
"Lafiya lau, kun tashi lafiya?"
"Lafiya lau muke, yasu Hajia suna lafiya?"
"Lafiya lau suke, amma basu san zan zo nan ba"
Shiru Ummi tayi tana sauraran abinda zai fad'a, shiru ne ya ratsa wajen na dak'ik'u shabiyar kafin Alhaji yayi gyaran murya yace "Ummi na san kinyi mamakin ganina a gidan nan ko?"
Cike da ladabi ta jinjina kai dan haka yace "ba abun mamaki bane, nazo ne dan naga jikinki nima, sannan na shaida maki na daina fushi dake yanzu."
Murmushi ne ya bayyana a fuskarta tana fad'in "na gode sosai Kakana"
Da hannu ya mata alama ta matso kusa dashi tana zuwa kanta ta d'ora akan gwiwarshi tana hawaye tace "Alhaji ka yafe min, wallahi ranar ma babu abinda ya faru kawai dai...." bai bari ta k'arasa ba yace "ya isa haka Ummi, nima nayi kuskure matakin dana d'auka akan ki bai kamata ba ko kad'an, domin kuwa na sanki farin sani dan rayuwar da ki kayi a gidana, tafi wacce ki kayi a gidanku yawa kiyi hak'uri kinji ko."
Haka suka jima suna hira kafin suka tashi tafiya Alhaji ya k'ara mata nasiha akan ta kula da mijinta sannan ta zama mai ladabi da biyayya ga mijinta.
Ummi taji dad'in yinin nan fiye da sauran yinin da 'yan uwa ke zuwa mata, haka ta wuni cikin farin ciki da annashuwa.
*A GURGUJE*
11/03/2019 Γ 17:51 - Mamar Latifπ: πAUREN HA'DI π
_Samira Harouna_
πΈπ¦ *ZAMAN AMANA WRITER'S*
_(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_π€π€
*Page*
7β£9β£-8β£0β£
Haka zaman nasu yake tafiya ba yabo ba fallasa, har yanzu babu abinda ya canja daga zaman nasu sai dai abu d'aya shine yanzu Ummi tana yin duk abinda Salman ya sakata, har yanzu Ummi ba tada sarau dan kuwa ko yanzu Salman yace mata kule to kai