Showing 45001 words to 48000 words out of 72709 words
Chapter 16 - AUREN HADI COMPLETE DOCUMENT WRITING Samira Haruna.txt
ma ni?"
K'asa tayi da idonta cikin jin kunya tace "saboda kai mijina ne." tana fad'a ta k'arasa shigewa d'aki tana dariya, Salman ma haka d'aki ya shiga yana jin wani sanyi na ratsashi yana ji ina ma ace Ummi ta fad'a mashi kalmar so a matsayin godiyar abinda ya mata.
Tun asuba Ummi da tayi sallah bata kwanta ba, tana gama had'a abinda kari ta d'an gyara abinda zata gyara a d'akinta da falo dama cuisine, tana kammalawa ta shiga wanka tana fitowa tsaf ta shirya cikin tenue d'inta.
Jakarta ta d'auko da hijab da nik'ab ta fito falo ta ajesu saman kujera sannan ta nufi d'akin Salman dan ta tashe shi, da sallama ta shiga amma shiru bai amsa ba alamar bacci yake, saida ta k'arasa har gabanshi ta k'ura mashi ido tana kallo yana baccinshi cikin kwanciyar hankali.
Rumgume hannayenta tayi a bayanta a hankali tace "ina sonka yaya Salman, sai dai ba zan iya fad'a maka ba, dan na san kai baka sona kuma ba zaka soni ba, amma zan ci gaba da jiran lokaci na san zai zo."
Lek'a fuskarshi tayi taga sosai yake baccinshi dan haka ta sunkuya daf da k'eyarshi ta sumbata, mik'ewa tayi tare da zura hannunta ta rufe hancinshi, da sauri ya juyo da kanshi yana bud'a idonshi yana ganin Ummi ya tashi zaune yana ci gaba da kallonta, murmushi kawai take masa kafin yace,
"Wannnan kuma wane irin tayar da mutum daga bacci ne?"
D'aga kafad'u tayi tare da d'aga gira sama alamar ba magana, saukowa yayi daga kan gadon yana fad'in "saina ji kamar an sumbace ni a kaina ko?"
Bud'e baki tayi cike da mamaki, lokaci d'aya kuma tayi k'asa da kanta tana wuru wuru da ido, gaf da ita ya matso yace "kece ko, ko dai akwai abinda kike b'oyewa ne ban sani ba?"
D'ago ido tayi suka kalli juna, ja tayi da baya tana fad'in "haba dai sumbata fa? sai kace wani jariri."
Toilet ya nufa yana fad'in "banyi mamaki ba dan kince haka, amma ki sani wani lokacin ma miji yafi jariri buk'atar kulawa."
Kallonshi tayi tace "to, ni dai na san ana cewa namiji kamar k'aramin yaro ne, duk in da kayi dashi can zaiyi."
Tsaye yayi yana kallonta kafin yace "kuma ke kin yarda da abinda aka fad'a d'in?"
Murmushi tayi tace "me zai hana ko, tunda mune ke jan ragamar."
Ganin ya tun karota yasa tayi saurin ja da baya tana fad'in "dan Allah ni dai kaje ka shirya kar nayi late a zuwan farko."
Sai lokacin ya lura da kayan dake jikinta dan haka yace "oh, hakane fa, ok ki bani 5 minute ina zuwa."
Kallon agogon dake gefe gadon tayi tace "ah bon, 5 minute? Ok je t'atend."
Ciki ya shige ita kuma ta dawo falo ta zauna jiranshi, kallon agogo take lokaci na tafiya amma Salman shiru bai fito ba, ido Ummi ta fiddo tare da mik'ewa tsaye tana dafe da k'irjinta ganin 07:45, kukan shagwab'a ta saka tana fad'in,
"Shikenan zuwan farko zan fara da late."
Hijabinta ta saka ta goya jakarta ta d'aura nik'ab, d'akin Salman ta nufa sai kuma suka ci karo da juna, ido ya fiddo waje yana k'are mata kallo sama da k'asa kafin ya nunata da hannu yace "ke kuma wannan shiga haka bak'a k'irin kamar wata 'yar wuta."
Turo baki tayi duk da baya gani sannan tace "yaya Salman ka dubi lokaci fa ya wuce, wallahi nayi retard."
Lokaci ya duba ya k'ara zaro ido yana fad'in "kai kai kai, lallai kam, to wuce muje ina fatan dai kin karya?"
"Ni ban karya ba, kawai idan naje naci wani abu."
Wucewa sukayi bayan ta rufe d'akin, tunda suka kama hanya tayi shiru tana kallon gari, Salman ne ya kalleta yace "ina fatan dai ba zaki cire nik'ab d'innan ba idan kinje can?"
"Haba yaya Salman dole zan cire mana dan nasha iska, lokacin zafi ne gashi yanzu ba'a ruwa sosai."
Hararanta yayi yace "bana so, karki bud'e fuskarki kowa ya gani."
"Amma yaya Salman akwai takura fa, kai baka san nik'ab ba wallahi tana hana mutum kyakyawan shed'a."
Kallonta yayi irin ba wasanan yace "wallahi idan naji labarin kin cireta, to daga ranar bake ba k'ara komawa makaranta."
Cikin shagwab'a tace "to yayana idan zan ci abinci kuma fa?"
"To na yarda ki d'aga idan zaki ci abinci, amma da kin ida ki mayar."
Hararan gefen ido ta watsa masa a ranta tace "sai kace wani sona yake da yake takura min haka"
Kallonshi tayi tace "wai yaya Salman ta yaya ka sama min gurbin karatu anan ne cikin sauri haka?"
Ba tare daya kalleta ba yace "to miye na wahala a ciki, dama anan kike karatu kuma sun baki gurbi in da zaki ci gaba, kawai baki zo da wuri bane har anyi karatun wata biyu babu ke."
Cikin tsoro Ummi tace "to yanzu idan suka tambayeni ya zance masu?"
"Na gama da wannan ma, dan na fad'a masu kinyi aure kuma yanzu ba kida lafiya."
Wani kallo ta masa tace "to me kace masu yake damuna?"
Wani kallon raini ya mata yace "na fad'a masu kina fama da laulayi ne."
A firgice ta kalleshi tace "laulayi, na ciki ko na me?"
"Ke wanne kika sani?"
Kallon gabanta tayi tace "na san na ciki."
Shima ba tare daya kalleta ba yace "to shi nake nufi."
Wani lallausan murmushi tayi tare da dafe cikin tace "wai ciki, Ummi da ciki, babbar magana."
Kallonta yayi yace "kina sonshi kenan?"
"Ina so sosai, Allah ya nuna min na samu nima."
Kallon ba kida hankali ya mata yace "keda ko hanyar daya bi baki bi ba, kuma a hakan kike neman shi."
Bata kalleshi ba tace "to miye a ciki? ai abun rabone kura ta haifi akuya."
Kallonta yayi yace "lallai kam, amma ki sani wanna kura za tasha dukan tsiya idan ta haifi akuya."
"Lallai kam, watak'ila kuma ba zata sha ba." fad'ar haka yayi daidai da zuwansu ecole d'in, bud'a k'ofar tayi zata fita tace "sai anjima."
"Idan kun tashi ki kira ni." ya fad'a yana kallonta, har zata fita ta tsaya tare da tara masa hannu tace "kud'in abinci na."
Hannu yasa aljihu ya fito da kud'i yana tambayar ta "nawa zan baki?kin san ni ba d'a gareni ba bare na san nawa ake bayarwa, kuma ma ke har wani kud'i za'a baki da girmanki."
"To ina girman yake? har yanzu fa ban wuce jaririya ba."
Kallonta yayi sosai yace "a hakan, uwar wasu kakar wasu?"
Cikin shagwab'a tace "nifa yarinya ce, har yanzu a wanke nake babu datti."
"Allah ya shirya min ke 'yan matana, ni fad'a min nawa zan baki."
Dariya tayi tace "ameen yaya Salman, kawai ka kimanta sai ka bani."
Kafin su ankara suka ji k'arar k'araurawa (sonner) lokacin shiga aji yayi.
Cikin hanzari tace "kawai ka lissafa nawa ake baka da kana kamar ni."
"Ni ai ina kamar ki kud'in makaranta ma ni na biyawa kaina."
Cike da k'aguwa Ummi tace "to kawai ka ban 1000f ta isheni."
Dubawa yayi sai dai babu wacce ta buk'ata, dan haka ya bata 5000f tana karb'a ta fita tana fad'in "zan aje maka canjinka, sai kazo."
Kallonta yayi sai gudu take har ta shige ciki, kai ya girgiza yaja motar yana fad'in "kaji gudun da take kamar yarinya, ba zata yi hankali ba wannan har saina saita ta."
Yaji dad'i sosai ganin yanda kayan suka mata d'as da ita, gashi duk sun rufe jikinta sai idanunta kawai da hannayenta ne a waje, dan takalman data saka ma k'afa ciki ne maras tudu(valerine) bak'ak'e.
```SAM```😍
11/03/2019 à 17:51 - Mamar Latif💃: 💑AUREN HA'DI 💑
_Samira Harouna_
*HASBUNALLAH WANI'IMAL WAKIL*
🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITER'S*
_(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_🤜🤛
*Page*
8⃣1⃣_8⃣2⃣
Su Jawahir sunyi farin ciki sosai ganin Ummi a makaranta ba zato ba tsammani, haka suka kasance tare har lokacin tashi yayi Ummi ta kira Salman yazo ya d'auketa.
Sosai su Jawahir suka birge Ummi ganinsu da tayi kowace da d'an k'aramin cikinta tana turawa, babban abinda yafi shiga ranta shine, ganin yanda suka canja lokaci d'aya duk sun canja abincin cinsu, abinda waccen take ci yanzu bata ko san k'amshinsa, haka abinda wata bata ci a da yanzu kuma tana cinshi sosai, wannan canjin ya birge Ummi sosai.
```ALLAH YA KAWO MAI ALBARKA```
Suna shiga gida ta cire nik'ab da hijab da jakarta ta yab'a akan kujerar falo ita kuma tayi ciki, Salman kam ruwa ya d'auko a fridge ya zauna yana sha, ya jima zauna yana jiran ta fito ta fad'a mashi abinda zata ci dan ya siyo mata amma shiru, mik'ewa yayi ya nufi d'akin, k'ofar kawai ya bud'a ba tare daya shiga ba.
Da k'yar ya had'e wasu yawu da suka tarar masa sannan ya kau da kansa gefe yana satar kallonta yana tambayarta "amm, dama na zone naji abinda zaki ci na siyo maki?"
Ummi dake ci gaba da shafa manta d'aure da d'an k'aramin towel d'in da ko cinya bai k'arasa rufe mata ba, sannan duk ta barbaza manyan kitsonta a bayanta ya kwanta, cike da karsashi tace masa,
"A'a yaya Salman ina zuwa yanzu saina dafa mana abinda zamu ci, saurin da nake kenan dama."
Cikin satar kallonta yace "kefa yanzu kika dawo kina buk'atar hutu, kawai ki fad'amin me zaki ci."
Juyowa tayi ta nufi wadrob ta bud'a tana duba kayan da zata d'auka tana fad'in "a'a yaya Salman zan dafa da kaina, a cikin kwana shida na karatu, kwana hud'u duk zan dinga tasowa k'arfe 13:30 , kaga idan nace zaka dinga siyomin abinci ai ban kyauta ba, dan haka ka barshi yanzu zan fito na d'ora mana yafi ace munyi latin cin abinci amma ba siyowa ba, kuma ma naga ai daga ni sai kaine a gidan."
Murmushi yayi tare da kallonta yace "sai kin fito."
Sai lokacin ta kalleshi taga yanata wani sunkuye kai, a hankali ta tako tazo gabanshi ta tsaya, hannunshi ta kama kamar yaro ta d'ora a gefen fuskarta tace "kace Allah ya min albarka, kamar yanda Abba yake min."
Duburburcewa yayi ya rasa me zai fad'a, gaba d'aya ya rasa network d'inshi take idonshi suka sauya suka fara canja launi, Ummi kam tsoro ne ya rufeta dan haka taja da baya tana fad'in "ina zuwa yanzu."
Kamar zai tashi sama haka ya fita daga d'akin ya shiga nashi, gado ya fad'a ruf da ciki yana taro abinda k'wak'walwarshi ta gane mashi hakan yasa kuma ciwonshi ya k'ara tunzura yana dad'a gaba.
Maganinshi ya d'auko ya b'alla yasha tare da mai sa bacci yasha, lokaci k'alilan bacci yayi gaba dashi ba dan ciwon ya bari ba.
Ummi na fitowa cuisine ta shiga ta fara had'a abincin rana mai sauk'in sarafawa, 14:40 ta kammala d'akin Salman ta shiga ta tashe shi daga bacci, yana fitowa tare suka ci abinci suna idawa ta d'auke kwanukan ta mayar cuisine ta wanke ta goge duk inda ta b'ata.
Tana fitowa Salman ta gani da jakar makarantar ta ya fiddo litattafanta yana dubawa, k'arasowa tayi tana kallonshi ta zauna, kallonta yayi yace "kin gane darasin da aka maki yau?"
Gyara zama tayi tace " taya zan gane da zuwa d'aya, dole ina buk'atar na samu mai koyamin idan na dawo gida."
Cike da raha Salman yace "to in hakane ki dinga biyana duk
wata saina dinga koya maki."
Matsowa tayi kusa dashi tace "da gaske yaya Salman? to ka fad'i nawa kake so na baka?"
Cike da fara'a yace " ki fad'a da kanki me zaki iya bayarwa duk wata."
"Duk wata?" ta tambayeshi, kai ya d'aga mata alamar Eh, dan haka tace "ok, to ka koyamin, ni kuma duk wata zan biyaka ta hanyar haifa maka kyakyawan yaro ko yarinya masu kama da kai."
Salman bai san lokacin daya fashe da dariya ba yana fad'in "yara dai, duk wata? ba kida dama Abu."
Turo baki tayi gaba cike da shagwab'a tace "Eh mana, miye a ciki?"
Da k'yar ya tsagaita da dariyar yana kallonta yace "to amma me yasa sai masu kama dani, me yasa ba kya san ki haifi masu kama dake?"
K'asa tayi da kanta tace "to ai ka fini kyau ne shi yasa."
Ya mutsa fuska yayi yace "Ummi waya fad'a maki ba kya da kyau?"
Kallon idonshi tayi tace "kasha fad'amin haka sau da dama, har wani lokaci ma ka kan kwatantani da mage ko aljana."
K'asa yayi da kanshi dan bai tab'a tunanin abin yana cikin ranta ba har yanzu, kallonta yayi yace "Abu karki damu da wannan, kawai ina fad'a ne amma ba wai yana nufin ke mummuna bace, kina da abinda ba kowa keda shi ba."
Hararan wasa ta masa tace "hmm, kamar me kenan?"
Kallonta yayi sosai kafin yace "kamar idonki masu abin al'ajabi, wanda basa kalluwa ga ragon namiji bare kuma mace, sannan kina da dinple wanda yake k'ara maki kyau idan kina dariya ko murmushi ke har ma da kuka idan kina yi."
Wai dad'i kashe Ummi, yau Salman d'inta ne ke yabanta haka, farin ciki ne ya k'umeta yasa tayi fari da ido cikin kissa tace "hmm, to ni dai naji muyi karatun."
*A kwana a tashi* lokaci na tafiya al'amura na faruwa da dama daga rayuwar Salman da Ummi, tun lokacin Salman kema Ummi lesson ba dare ba rana in dai har yana gida, shak'uwa sosai ta k'ara shiga tsakaninsu a wani b'angaren kuma suna k'ara zurfafa soyayyar da sukewa junansu.
*Sati uku* da fara karatunta Salman ya sake tafiya Cotonou, da k'yar ya iya kwana goma a cikin sati biyun daya d'iba zaiyi, dan kuwa babu abinda yake daya wuce tunanin Ummi da kewarta.
Haka ma a wajen Ummi, dan kuwa ko abinci ta daina ci sosai dan yanzu ta saba da cin abinci tare da Salman, kafin ya tafi saida ya d'auko Islam tare da Momy (autar su Salman) ya kawosu dan su tayata bacci, hakanne yake rage mata damuwa da tunani da kuma k'arfafa gwiwar da Salman yake mata akan karatu duk lokacin da sukayi waya.
Tunda safe Salman ya kan kirata yaji ya suka tashi, kasancewar yana da jadawalin lokacin karatunta (emploi du temps) yasa tana fitowa daga aji kiran Salman zai shigo wayarta, da dare haka zasu sha hira abinsu har dama karatu yana k'ara kwatanta mata a waya.
*Ranar* da Salman ya dawo, ya dawo da k'udirin sauke hakk'in dake kanshi, yayi niyyar kusantar Ummi ta hanyar data dace bawai ko ta halin yaya ba.
Rashin sa'a a ranar daya zo, a ranar bak'on Ummi yazo (period), bayan wannan kuma gashi suna shirin shiga satin jarabawa, hakan yasa Ummi ta zama busy sosai bata da lokacin komai har lokacin kanta, hak'uri kawai Salman yayi amma ba dan haka yaso ba.
*Litinin* Ummi suka shiga zana jarabawa, kwana uku sukayi kuma a kwana ukun nan Ummi ko abinci bata san ci sai Salman ya matsa mata lamba sannan, hasali ma ba ita ke dafa abincin ba siyowa Salman keyi, ririta ta kawai yake dan shirin shi shine suna gama jarabawa tofa shima dole ya shiga hq dan tashi jarabawar.
*A kullum d'an Adam na nashi ne, Allah ma yana nashi, mutum baya da ikon tsarawa kansa rayuwa sai yanda Allah ya tsara masa* su Ummi na fitowa daga aji aka fara ruwa kamar da bakin k'warya, zuwan Salman dan ya d'auketa yasa Ummi fitowa daga mafakarta ta k'arasa in da yake, ruwa sun jik'ata sosai hakan yasa tana shiga mota ta cire hijab d'inta da jakarta, suna zuwa gida ma haka suka tsaya suna kallon juna ganin yanda ruwan ke sauka da k'arfi.
Cike da shagwab'a Ummi tace "to yaya Salman kaine namiji kuma mai hakk'in kula dani, dan haka ka rufeni saimu shige ciki."
Hararanta Salman yayi yace "ahan, kenan yau kin tuna haka ko?"
Turo baki tayi gaba tace "to ni dai wallahi idan na shiga ruwan nan zan iya mura, dama gashi na riga dana jik'e."
"To shikenan, ki shirya zan fita yanzu kema saiki fito."
Fita yayi ya zagaya ma zauninta ya kamo hannayenta ta fito, rumgumota yayi a jikinshi ya matseta a hankali ya d'agata ya d'ora k'afafunta akan nashi sannan ya d'auko hijab d'inta ya masu runfa dashi, a hankali ya fara takawa saboda tana bisa k'afafunshi ne kamar ya d'auketa ne, idon Ummi na kan k'irjin Salman data d'ora hannayenta ta kasa had'a ido da shi, shi kam fuskarta kawai yake kallo tare da k'ara matse kunkuminta da duka hannayenshi biyu.
Suna shiga falo ta zame jikinta daga nashi, sai dai duk da haka saida suka jik'e da ruwa take jikin Ummi ya fara rawar d'ari, kallonta Salman yayi lokacin da yake cire takalmanshi k'afa ciki, saida ya gama cirewa ya d'ago yana b'alle ma b'allan rigarshi yace,
"Ya dai malama?"
Bud'ar baki tayi zatayi magana ji kake "hatshimmm." ta b'arzo wata atshiwa, ja baya Salman yayi yana fad'in "kai, haba ke kuwa atshiwa ba sanarwa kawai saiki fyace ni."
Wata maganar taje tayi amma ina sai wata atshiwar tare da fitowar majina a hancinta, ajiyar zuciya Salman ya sauke cike da tausayawa ya matso kusa da ita yana kallon fuskarta, kallabinta ya cire ya jefar a kujera haka ma ribom (chouchou) d'inta take gashinta marar kitso ya zube a bayanta wanda ya jik'e da ruwa sai k'amshin man kai yake *(BLACK QUEEN {COCONUT OIL} )*.
A hankali ya had'ata da k'irjinshi ya zura hannayenshi a bayanta ya zuge zif d'in rigarta, tana kallonshi har ya rabata da rigarta yayi saura bras d'inta fara, sunkuyawa yayi yana shirin zame wandonta daga jikinta tayi saurin ja da baya tana fad'in "a'a ya isa haka....atshimm." ta k'arasa maganar tana k'ara atshaweshi.
Tissue ya ciro a aljihunshi ya matso kusanta yasa ya goge mata majina har da cewa "fyato" kallonshi tayi sai dai ba tayi magana saboda ya rufe mata hanci da tissue, bud'e mata ido yayi ya sake cewa "fyato"
Tsaf Ummi ta fyato ya goge mata, juyawa tayi ta bud'e d'akinta ta shige tana ci gaba da atshiwar, shi kam binta yayi da kallo kafin shi ma ya nufi nashi d'akin.
Zuwa dare Ummi ta galabaita sosai dan mura bata mata da dad'i dama in dai ta damk'eta abinka ga jar fata duk ta fita hayyacinta ta sukurkurce, tun doguwar rigar data saka dawowarta har yanzu ita ce a jikinta, kanta duk ya yamutse saboda kwanci da take hancinta har yayi ja saboda goge majina, idonta banda ruwa ba abinda sukeyi ko magana bata ji sosai dan kunnuwanta sun d'ume, haka gaba d'aya mak'oshinta ciwo yake ga bala'in ciwon kai, duk ta rikita Salman da kukan shagwab'ar da take bata tab'a