Showing 93001 words to 93806 words out of 93806 words
din gaba Daya anyi anyi taqi farfadowa dole Akai asibiti da ita itama aka jere su kowa da dakinsa Babu Wanda yasan inda kansa yake tsakanin ita da Dad da Dadah ga su Babbah da sai yanda hali yayi Suma.
Ahmed Daya Dan samu kansa cikin karfin hali ya sanar da Aunt Didi ayi gaggawan shirin fitar da Omar zuwa gurin dangin Didi din Dake Angola sbd jinyarsu acan tinda shi baida lafiyan basa kariya ko jinyarsa Dan haka su tattara su tafi can hankalinsa zaifi Kwanciya sbd zaa iya tinanin qarasa Omar din daga Nan tinda Yariga ya shige coma shi da Babbah sai yanda Allah yayi dasu.
Mum Nur Daman Batada niyar barin mijinta a Nigeria din ayi jinyarsa sbd ko zai tashi dukkaninsu sunsan ba yanzu ba ko duba da yanayin niqan da mota tai masa Dan haka a take washe garin ranar suka hada komai suka bar Lagos zuwa Abuja sbd acan zaa tashi.
Kaman abin da ake Jira qanqanin lokaci aka rufe mansion din suka tafiyarsu batareda sun tafi da Babbah ba kaman yanda Ahmed yaso sedai Shima ba qaramin Jin jiki yakeyiba tinda ya Bada umarnin tafiyar Bai sake sanin inda kansa yake ba shima har suka bar qasar.
Jamaal Neman haukacewa yakeyi a Nigeria din sbd duk yanda yaso wucewa yabar qasar da Ameenatou lamarin ya gagara sbd Babu abinda take dashi na barin qasar hakama acan kiransa akeyi mahaifiyarsa na tsananin buqatansa da gaggawa sbd tsoron sukeyi wani abu ya faru Jamaal din Baya kusa sunsan bazai taba yafewa kowa ba..Dan haka Jamaal din yake cikin tsananin mawuyacin hali da Neman mafitan yanda zai Hana su Dad taba ko farcen Ameenatou din Tako ina.
Washe gari da wucewansu JDENS Dad dinsa ya farfado Dan haka ya sake Jin kansa ya dauki zafin da Bai taba dauka ba Dan haka Kai tsaye karfe biyun Rana ana fitowa sallahn azahar aka daura Aurensa da Ameenatou wadda ita Kuma karfe biyu da rabi ta farka sedai abinda bai taba tinanin zaiwa wani ba a rayuwarsa shine juyar Maka da hankali shine abinda yasan kadai mafita a garesa kafin yaje ya dawo ya tafi din sbd matiqar tana cikin cikakkiyar hankalinta Koda igiyoyin aurensa Dake kanta bazasu Bata cikakkiyar tsira daga su Dad da Lameenu ba sai Hakan,
Kasancewanta mara cikakkiyar hankali a yanzu shine kadai zai Hanasu mallakar ko tsintsiya daga dukiyar Omar kaf datake kasar duka sun bari daga gareta,
Babu maganar kudi ko wani gado tinda Omar yana raye ayanzu Amma sbd tsoron Omar din zai iya rasa rayuwarsa daga can ya sakashi yin Hakan sbd alluran duka duka wata Daya zatayi tana mata aiki zata dawo daidai Wanda yake Saka ran kafin can ya dawo gareta.
Siddeeq kuka yakeyi sosai jikinsa na cira sbd tausayin kansa,Dana Ameenatou din Dana Jamaal din Wanda ya kasance a tsaka me wuyar gaske gashi ya kasa yadda da kowa akan Ameenatou tinda wainda ya yadda dasu gasucan a kwance asibiti Babu Wanda yasan ranar tashinsu.
Hankalin lameenu tashi yayi mummunan yi da samun labarin juyewan kan Ameenatoun Daya fara Jin farin ciki da tsananin Jin dadin an tafi anbarta a hannunsu sune iyayenta sune sukeda cikakkiyar ikonta da dukiyarta.
Bai shiga Mummunan tashin hankalin Daya Sakasa faduwa ba Saida akayo asibitin dashi Shima Saida yaji AN DAURA AUREN JAMAAL DIN DA ITA,
AMEENATOU OMAR JEEDEN SEELAH DIN A YANZU CIKAKKIYAR MATAR JAMAAL SEELAH DINCE HALAK MALAK...... Innalillahi wainna ilaihirrajiun.
Dad ma da farfafowansa kenan zancen girgiza yayi har Saida Shima jikin ya sake Neman rikicewa.
Sunaji suna Gani Jamaal ya dauke Ameenatou din ya Kaita wani tsadaddiyar asibitin masu matsalan kwakwalwa na wani abokin aikinsa acan Poland kwararre Shima ya Bada Amanarta gasu da wani irin tsananin tsaron gaske a asibitin wanda acan ne kadai zai samu nutsuwan barinta,
Hakama radadi da tashin hankalin da zatai ta shiga akan rasuwarsu Haroon da Babbah datake tinanin shine ya rasu bazasu taba dawo mata ba sbd bazata taba tinawa ba sai ta dawo daidai zasuyi mata saukin gaske.
Da zai tafi haka ta zaune a dakinta da Babu abinda ya rasa tana kallonsa da fararen idanuwanta da suka rame lokaci Daya harya fice aka rufe mata dakin.
A ranar jirginsa yabar kasar bayan yabarwa siddeeq komai da zai kula dasu Babbah da Hafiz harma da Dadah da umma ke dawainiya da ita.
END OF PART 1
DAN ALLAH DUK INDA NAHI KUSKURE A DAUKESA A MANTUWA KO AJIZANCI,
Insha Allah bayan sallah zamu Dora part 2
Allah ya bamu ikon ibada cikin aminci da yardar Allah
Allah Kuma ya nuna mana kaman yanda mukaje hutun Nan ayau lafiya mun dawo lafiya.
##MAMUH
#AMEENATOU JDEN SEELAH
#JAMAAL SEELAH
#BABY ARFAT SEELAH
#LOVE
#DEEP
#ROMANCE
#THE SELAHS
#WARISCOMING
#ZAFAFA BIYAR
*_ZAFAFA BIYAR_*
1 *_Ameenatou!!_*
_Mamuhgee_
2 *_Tsutsar Nama!!_*
_Billyn Abdull_
3 *_Gudun Kaddara!!_*
_Safiya huguma_
4 *_Kwankwason Jimina!!_*
_Miss xoxo_
Guda Daya 400
Guda biyu 700
Guda uku 1k
Guda hudun 1200
*_6019473875 MUSAA ABDULLAH SAFIYAH keystone bank_*
*_ATURA SHEDA ZUWA 09166221261_*
*_MTN/VTU 09134848107_*
_*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din 09033181070*_
*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*