Showing 84001 words to 87000 words out of 93806 words
har ta cikin kansa da kunnuwansa Dan haka ya zare hular kansa yayi wurgi da ita Yana cewa
"Omar me nake ji?
Me yake faruwa?
Menene yake Kuma Shirin faruwa?
Shin balain ne ya dawo da masifar kokuwa wace balain ce take Shirin dawowa??
Meye hadinka da SEELAHs???
Kallansu yakeyi Daya bayan Daya a rude Yana Neman Karin bayani Dan kansa Neman Juyewa yakeyi da tashin hankali da tsoron abinda zai iya faruwa idan wani abu ya samu Ameenatou dinsa.
Omar ne ya dago tareda tashi tsaye Yana fuskantar babban idanuwansa jajir yace
"SEELAHs shine Nima nawa asalin sunan ba Jden ba?
Mamman seelah, Lameenu seelah, Omar seelah da Yan uwanmu biyu da suka rasu kasim da jamilu seelah Yan uwan jini muke,
Dukiya itace ta lalata jinin dayake yawo a jikin kowannenmu na alkawarin tsira tare mu mutu tare,
jinin yan uwanmu ne Daya zuba akan dukiyar ya gurbata dukiyar ta Saka mu samun Kanmu a mummunan halinda muke ciki a yanzu na bibiyan rayuwar Yan uwanmu Amma ka sani har abada bazan iya rabuwa da yata ba a yanzu kaman yanda nayi alkawarin Bata kariyar da ban samu bawa mahaifiyarta ba,
Ameenatou a yanzu itace babban abinda duk wani maqiyana yake Neman samu,
Ameenatou itace mukullin dayake riqe da duk wani abinda Dana mallaka,
Ameenatou itace mamallakiyar dukkanin tarin dukiyar Jden a rubuce Dan haka samunta a shine mafi farin cikin cikan burinsu,
Sanin wacece Ameenatou shine babbar hatsari da tashin hankalin da dukkaninmu zamu fuskanta Dan haka Babu maganar aurenta a goben Dan har abada bazasu taba Dena Neman ba har sai ranarda suka samu sanin waye magajin dukiyar jdens gaba dayanta.
A rubuce dukkanin dukiyata da abinda na mallaka nata ne,
Ahmed ya sani ayau Kai da Jamaal inason Kuma ku sheda Hakan sedai ku sani barin asan wacece ita shine karshen komai.
Kallan babbah Daya gama jiqewa da zufan gaske hankali tashi yayi kafin ya Kalli Ahmed ya zaune dashi ahankali ya fara zayyano masa asalin tarihinsu da komai tin daga barowansu gaban iyayensu har zuwa yanzu da suke maganar.
Kuka wiwiwi Babbah keyi dukkanin jikinsa na rawa sbd shiga tashin hankali da tsoron rayuwar dasuka samu kansu dumi dumi aciki ta masifar da Bai taba ji ba...
Jamaal ma kusan silalewa yayi kan kujera wannan Karan da hannuwansa biyu ya Saka Yana rintse idanuwansa sbd kansa Dake Neman bugawa tareda zuciyarsa....
Ahmed ma da tinda yake da Omar din baisan asalin asalin mafarin komaiba sai yau din sbd kaf duniya yanzu Babu Wanda yasan ba uwa Daya Uba Daya SEELAHs suke ba sai yau din,
Ko Jamaal da Haroon dasuke yayan cikinsu da matayensu Basu taba sanin wannan sirrin ba sai yau din da Omar yake fada musu da bakinsa cewan ba uwa Daya Uba Daya suke ba...
Dukkaninsu Dake palon silalewa sukai qasa kowa kafafunsu na kasa daukansu,
Duk tsananin jarumta da karfin halin Jamaal Hawaye ne suka ciko jajayen idanuwansa yanajin wani abu me nauyin gaske ya tsaya ya tokare kirjinsa sbd baqin ciki da radadi tareda kunyar abinda ake fada mahaifinsa na ciki,
Makashi ne ya haifesa?
Makashin Yan uwansa da wainda Basu da hakkinsu na komai shine mahaifin Daya haifesa,
Mahaifinsa shine makashin kakanninsa da macen da harya mutu bazai taba Dena Sonta ba.....
innalillahi wainna ilaihirrajiun,
Innalillahi wainna ilaihirrajiun
Babbah kuka yakeyi sosai hankalinsa da gashin jikinsa duka suna tashi,
Shi kansa Omar da sai yaune ya Bude Baki ya iya furta abinda yake ransa qunshe tsawon shekarun Nan Bai taba maganar dayake cin zuciyarsa Yana saukar masa da radadi mafi ciwo na yanda shi da Yan uwansa suka kasance,
Tin suna Shan nonon iyayensu suke tareda juna a guri Daya aka haifesu suka taso tare batareda ko a takalman sakawa iyayensu sun banbantasu sbd kauna junan datake yawo a jininsu tin
A iyayensu take acan ta samo asalinta har a nasu jinin,
Sun tashi da kauna me karfin gaske a tsakaninsu Amma yau rayuwar junansu suke nema,
Wannan abin ne yake Saka Omar baqin cikin Daya zauna zuciyarsa yake cinsa akowace daqiqan rayuwarsa Dan haka yau Daya samu furta sirrinsu hawayen ne suka gangaro masa a Karan farko sbd a yanzu bayan su ukun dasuke gabansa Babu Wanda ya yadda dashi Akan yarsa,
Su uku sune wainda yasan zasu tayasa bata kariya da rayuwarsu Dan haka ya juyo da idanuwansa akan Jamaal Wanda shi kadai ne Seelah Daya dayake Jinsa har cikin ransa Kuma ya yadda dashi fiyeda rayuwarsa kaman Ahmed a Sanyaye yace
"My son Ina tsananin baqin cikin hanawa Dan uwansa wannan auren sbd ba Kai bane,
Kai kadai ne namijin dana yarda na bawa aurenta na jefata cikin SEELAHs batareda naji shakka ko tsoron Hakan ba,
Kaine Wanda zan bawa amanarta ko Bada aure ba Amma kwata kwata zuciyata Bazata taba samun nutsuwa ko Kwanciyar hankalin bawa Haroon aurenta ba Badan komai sai Dan rauninsa ga mahaifinsa Wanda ba ita kadaina akanta shi kansa tasa rayuwar a hadari take.....
Dago jajayen idanuwansa Jamaal yayi ya zubawa Dad Omar din tareda girgiza masa Kai bakinsa na sake daukan nauyi sbd tsananin son da Dan uwansa yakewa Ameenatou din idan aka rabasa da ita matsalar ciwonsa zata iya Maidasa cikakken mahaukacin dayake tsananin tsoron ya koma,
Bazai iya kallan Rabin jikinsa Haroon din ya koma Hakan ba,
Zai iya sadaukar da rayuwarsa akan lafiyan Haroon da Kuma samar masa macen dayake so fiyeda nasa ran Dan haka ya Bude Baki bakin cikin muryansa Daya shaqe sbd tsananin tashin hankali da baqin ciki harma da shock yace
"Dad Dan Allah Karka Hana Haroon auren Ameenatou,
Ameenatou itace farin Daya Kuma nutsuwa Daya rak Datake riqe da rayuwar Haroon,
Hana masa aurenta tamkar rabasa da lafiyarsa ne gaba Daya,.
Haroon Yana yimata tsananin son da bazai taba barin komai ya faru da ita ba Koda hakan na nufin zai gitta tasa rayuwar".
Kuka Babbah ya sake fashewa dashi sbd gano gaba Daya su rayuwarsu acikin seelahs din da aurenma gaba Daya a duhu suke Babu Abu Daya dayake gaskia sai soyayyar da Ameenatou dinsa takewa Haroon sbd Jamaal da Haroon dai mutum biyu n mabambamta da suka ringa wasa da zuciyar Ameenatoun,
Tayaya zai bari Ameenatou tayi aure a cikin wainnan mutanen da yanzu ma tsoro suke tsananin basa bayan Omar din da Ahmed sai Jamaal din Wanda yaji yamafi samun nutsuwa dashi.
"Bazan taba bawa Haroon ko Daya daga cikin zuriar seelahs din auren Ameenatou ba gaba Daya har abada" babban ya fada Yana dagowa jajayen idanuwansa Yana kasa kallan Jamaal Daya cike masa ido har lokacin Hawaye ne ke zubowa daga idanuwansa.....
#MAMUH#
#THE SEELAHS
#THE JDENS
#LOVERS
#MARRIAGE
#AMEENATOU JDEN SEELAH
*_ZAFAFA BIYAR_*
1 *_Ameenatou!!_*
_Mamuhgee_
2 *_Tsutsar Nama!!_*
_Billyn Abdull_
3 *_Gudun Kaddara!!_*
_Safiya huguma_
4 *_Kwankwason Jimina!!_*
_Miss xoxo_
Guda Daya 400
Guda biyu 700
Guda uku 1k
Guda hudun 1200
*_6019473875 MUSAA ABDULLAH SAFIYAH keystone bank_*
*_ATURA SHEDA ZUWA 09166221261_*
*_MTN/VTU 09134848107_*
_*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din 09033181070*_
*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_**_AMEENATOUH_*
_Mamuhgee_
#Arewabooks@Mamuhgee
#ZafafaBiyar
#BestLove
53
Maimaicin fasa aura masa Ameenatou da akeyi ne ya Saka kansa kasa dauka hannuwansa suka fara rawa hakama kafafunsa,
Toshewa kirjinsa yakeyi Yana Jin kaman bazai iya Jan numfashi ba ga idanuwansa da suka fara ganin babbiyu Dan haka yafara bin Bango Baya Gani sosai ya juya Yana dafe gefen kansa da hannu Daya Yana kokarin Bude idanuwansa dakyau da basa Gani sosai bayan gasu a buden.
Tsananta rawa jikinsa yakeyi sosai,
Mummunan faduwa yayi Yana gap da Isa motarsa sbd tsananin da jikinsa yayi Dan haka da rarrafe ya nufi kofar ficewa ya fice yabar Motarsa a gurin Yana rarrafawa duhun gaske Yana qara rufe idanuwansa.
BB dayake nesa sosai daga gidan sbd bayan ya koma Mam sakashi dawowa yayi akan ya tabbatarda ya riqe tsawon lokacin da suka dauka a tare Dan haka ya dawo batareda ya tabbatarda su waye da waye a cikin gidan ba gashi Kuma Yana shakkar Isa gurin sosai ko shiga a samu matsala Dan baisan takun Jamaal ba.
Idanuwansa akan gidan da duk motsin dazai fito cikinsa yake Dan haka Yana hango motsi ya fito daga maboyarsa ahankali tareda Dan biyu duhun ya iso gurin daidai lokacinda Haroon yake fara buga kansa a Kan titin dayake tsit Babu kowa ko motsin komai..
Tareda yayi da sauri tareda rufe masa Baki ya janyesa da sauri daga gurin yayi cikin duhu dashi Yana Jin kirjinsa na harbawa Yana leqa hanyar gidan baiga ko motsin kowaba dazai fito daga ciki.
Sunkutar Haroon yayi gaba Dayansa duk girmansa sbd shi kansa BB din ba qaramin Mai qarfin gaske bane sbd a Bude yake kaman basamude.
Gurin motarsa Dake nesa da gidan ya nufa dashi ya Bude ya Sakasa ciki tareda rufe motar yana juyawa yaga har lokacin Babu kowa yaja motar yabar gurin da sauri sbd Baya buqatan cigaba da jiran indai Haroon daga ciki yake tareda su Omar din yasan me zai masa duk abinda suka tattauno zasuji koma Menene adaren Nan.
****Jamaal irin roko da tabbaci tareda alkawarin da yayiwa Dad da Babbah akan auren ya Saka jikinsu sanyi Jin irin halinda Haroon yake ciki da ciwon dayake cin kansa batareda shi kansa ya sani ba,
Sanar dasu yayi alkwarine ya dauka ana auren zai tafi tareda Haroon din da Ameenatou gurin mum dinsu acan zasu zauna duk wannan yaqin batareda ko dayansu cikin su biyun ba zaayisa wanna alkwarine yayi musu.
Kallansa Dad Omar da idanuwansa sukai jajir yayi sbd Babu abinda Jamaal zai rokesa a rayuwarsa yaji bazai iya basa ba Amma kuma yanzu ana magana ne akan 'yarsa da Bai hadata da kowaba hakama tafi komai na duniyar Nan Daya mallaka mahimmanci da daraja Mai girman gaske a zuciyarsa.
Babbah a nasa bangaren farin cikin Ameenatou ne kadai abinda yake tsaye a ransa,
Tsananin Son da Ameenatou kewa Haroon shine babbar matsalar Dake tayar da hankalinsa Dan kuwa Babu wani abu komai girmansa da zai ciresa daga zuciyarta...
Omar kuwa Jamaal Dayake cikin tsaka me wuyar gaske akan Dan uwansa ya kalla Yana Jin abubuwa da yawa a zuciyarsa gameda auren Wanda zaifi farin ciki da Jin dadin tareda samun cikakkiyar nutsuwa ko bayan mutuwa ace Jamaal ne igiyoyin auren 'yarsa suke hannunsa,
Auren Ameenatou tamkar wani babban nauyin da mutum baisan dashine ba zai dauka Dan kuwa dukiyarta gaba Daya nauyinta akansa zasu sauka,
Haroon bazai taba iyawaba sedai Kuma so yayi gaggawan shiga lamarin nasa da Ameenatou Amma Kuma aurenta ba abune Mai saukin gaske ba garesa,
"Jamaal kayi mun alkawarin zaka tsaya ka tsayu ka zama kariya ga 'yata?
Ka mun alkawarin zaka Hana duk wani cuta tarwatsa rayuwanta?
Kamun alkwarin ko Dan uwanka zaka tsayu gabansa ka zama katangar karfenta idan ya kasa Bata kariya da tsaron Daya kamata,
Idan na bawa Haroon auren 'yata ka sani shi auren na basa Amma Kaine na bawa Amanarta ta har abada,
Ni amatsayin mahaifin Daya haifeta Kaine na bawa aurenta da kaina kaikuma ka karbanwa Dan uwanka Dan haka idan har ka Aminta shi ka bawa auren tabbas bazan Hanaka ba sedai Kasani har abada ni Amanar 'yata na baka Kaine ka aura mata Dan uwan naka.
Jajayen idanuwan Jamaal ya dago Babbah ya fara kalla Wanda Shima shi yake kalla zuciyarsa na rawa hakama jikinsa amsarsa suke Jira Dan dai shi Kam Babbah bayajin zai aminta da auren sedai kafin yayi magana Jamaal ya fadawa Dad maganganun da suka hatta jikin Babbah yin sanyi baisan lokacinda Hawaye suka sake gangaro masa ba sbd yanajin tabbas Shima ya amince a aurawa Haroon din Ameenatou sbd Jamaal ya kashe musu jiki da alkawarin Daya dauka tareda Amanar Ameenatou Daya tabbatarwa dad din idan har su Dad dinsa sun samu damar taba ko suturar jikin Ameenatou da dukiyarta to bayan ransa ne Inshallah.
Ahmed Daya kasa riqe kansa akan tsananin kaunar dayakewa Jamaal rungumesa yayi sbd Daman yasan Jamaal namijin gaske ne ko Dad Omar baice komaiba jininsa yafi karfin ganin cutatarwa indai Jamaal Yana sane,
Kaunar datake tsakanin Jamaal da Omar kaunace irin ta asalin 'da da uban da suka hada jini,
Yanda yake Jin Dad Omar ko mahaifinsa Baya jinsa a cikin ransa Hakan,
Shi kansa Omar yanda yakejin Jamaal ko ransa ko cewa Yayi yaje da kansa ya sanarwa su Mamman waye yarsa zaiyi sbd yasan bazasu iya komai Dan itaba.
Rungumesa Ahmed yayi Yana Jin nauyin dayake zuciya da kansa sun rage na alkwarin bawa Omar da 'yarsa kariya Koda da rayuwarsa ne.
Har lokacin Jamaal zuciyarsa wani irin nauyi da daci ne danne da ita Dan haka Dad Omar ma dayake Jin nauyi da tsananin dacin zuciya rungumesa yayi sai alokacin hawayen Jamaal din suka gangaro daga idanuwansa Shima Dad Omar sai alokacin nasa suka gangaro Dan Bai taba zubda Hawaye ga rabuwarsa da Yan uwansa ba sai yau din Badan abin Baya cin zuciya da ruhinsa ba sai Dan baisamu Wanda daidai irin radadin ne aransaba sai yau din Dan yasan radadin dayake ransa shine yake ran Jamaal.
A cikin daren Omar ya sanar dashi komai daya Dade a rubuce na sunan AMEENATOU dayake kan komai na Abinda ya mallaka Dan haka Babbah yaji hankalinsa ya sake tashi Dan kaman sun sake nutso ne shida iyalansu da Ameenatou din cikin wutar qaddarar da zata kona kowa Dan haka take yaji zazzabi da ciwon kirji na rufesa,
Jamaal ma ciwon kan ne tareda zazzabin gaske ya rufesa sbd kirjinsa Daya toshe Dan haka cikin karfin hali ya fito kusan su babban da Dad Omar na bayansa suka fito gurin sedai babban tashin hankalin da suka tarar a wajen ne ya Saka jiri diban Dad Omar da Jamaal lokaci Daya sbd tabbatarda motar Haroon ce a gurin pake.
Ahmed ma dayake cikin shock saurin tare Omar yayi Yana kallan motar da tashin hankali yace
"Haroon Yana gurin Nan??
Babbah na Jin Hakan jiri ya zubar dashi jikin motar Omar Dake gurin Yana ambatar "Qalu innalillahi wainna ilaihirrajiun.
Jamaal Daya ji kansa na sake daukan masifaffiyar zafi da sauri ya nufi motar yaganta a rufe
Ahmed da Shima cikin tashin hankalin ya zagaya Baya ya zagayo koina gidan baiga Haroon dinba ya dawo saiga key din motarsa a kasa gurin yashe.
Babbah na ganin Hakan yayi zaman Yan bori a gurin Yana cewa
"Shikenan haukarsa ta motsa zaije ya sanar WA mahaifinsa"
Zabura yayi da sauri ya nufi Omar Yana cewa
"Wallahi tinda baida cikakkiyar lafiya tsaf zai iya sanarwa ubansa,ku yi wani abu Akai ko wlh tallahi a cikin Daren Nan na tattara iyalina ku nememu ku rasa wlh ko zaka sake ganina sai qiyama idan mun hadu gaban Allah."
Dad Omar da Baya ma gane me Babbahn ke fada motarsa ya nufa Dan sauri Shima Jamaal tasa ya nufa Ahmed ne yasamu karfin halin Jan Babbah ya jefa mota ya rufe suka tayarda motacinsu kaman masu wasan tsere cikin mugun gudun Daya Saka Babbah sake shiga tashin hankali suka hau titi su sukai kudi shi yayi arewa kowannensu Yana Saka Kiran wayar Haroon din ba kakkautawa.
Jamaal kaman zai tashi sama haka ya figi motar Yana Saka Kiran Haroon din idanuwansa na rikidewa gaba Daya Dan kuwa kowannensu tsoronsa kada Haroon din ya nufi su Dad Dan haka tabbas yaji wani abu shiyasa ya bar gurin a halinda basuda tabbacinsa tinda ga key din motarsa yashe a gurin.
#MAMUH#
#JAMAAL JEEY SEELAH
#AMEENATOU JDEN SEELAH
#OMAR JDEN SEELAH
#MAM SEEELAH
#LAMS SEELAH
#THE SEELAHS
#WAR
*_ZAFAFA BIYAR_*
1 *_Ameenatou!!_*
_Mamuhgee_
2 *_Tsutsar Nama!!_*
_Billyn Abdull_
3 *_Gudun Kaddara!!_*
_Safiya huguma_
4 *_Kwankwason Jimina!!_*
_Miss xoxo_
Guda Daya 400
Guda biyu 700
Guda uku 1k
Guda hudun 1200
*_6019473875 MUSAA ABDULLAH SAFIYAH keystone bank_*
*_ATURA SHEDA ZUWA 09166221261_*
*_MTN/VTU 09134848107_*
_*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din 09033181070*_
*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_**_AMEENATOU_*
_Mamuhgee_
#Arewabooks@Mamuhgee
#ZafafaBiyar
#BestLove
54
BB kuwa Kai tsaye gidansa ya nufa Dan Haroon din Kuma harya Isa Bai Hadu da wata matsala ta jamian tsaro ba Dan haka Yana Isa yayi parking motarsa a harabar gidansa ya Bude ya fito ya zagayo ya Bude motar ya dauko Haroon din Wanda ciwonsa yakai kololuwan tashi sai fizga yakeyi Yana jijjiga kansa Yana buga kan a jikin hannuwansa idanuwansa a rintse.
Kai tsaye Dayan dakinsa yakaisa ya zubar a kasa tareda juyawa ya fice daga dakin Yana Ciro wayarsa ya Saka Kiran babban yaransa.
Yana daukan wayar Kai tsaye BB yace
"Killer ka kawomin Ps biyu yanzun Nan"
"Yes oga" killer ya fada daga bangarensa Yana kashe wayar tareda ture macen datake kansa tana lashesa kaman sweet har Saida kanta ya bugu da Bango ko a jikinsa ya miqe tsaye Yana kama dadar kansa datake a watse ya Saka Roba ya daureta tsakiyar Kai Yana nufar toilet ya wanko jikinsa ya fito,
Underwear yafara sakawa kafin ya Saka Jean Akai ya Saka shirt ya dauki wayarsa da key din motarsa yafice bayan ya shiga dayar dakinsa da mugayen kwayoyin rayuwa suke ciki ya dauko wadda ogan ya buqata.
Koda killer ya iso gidan BB ya tube yayo wanka dagashi sai underwear Wanda kusan Babu abinda na jikinsa da baka Gani.
Dakin suka nufa Yana miqawa killer hannu ya amsa fitinanniyar kwayar wadda take hade da ruwan alluran ta,
Tsananin karfi da balain dayake tattareda ita uku ake tanata asha Daya alluran Kuma tafi komai balai da masifa Dan hadda tsananin azabar gaske ne da ita Dan haka suna shiga dakin ya daga allurar Bai tsaya wata wata ba ya kama wuyan Haroon ya soka masa ita tareda dure masa ruwanta gabaki Daya Wanda yayi daidai da budewan idanuwansa cikin tsananin azabar da Bai taba samun kansa aciki ba take ya qame kaman Sanda kafin jikinsa ya saki gaba Daya Hawaye na gangaro gefen Idanuwansa da sukai duhu gaba Daya Baya ganin komai.
Sakin kansa BB yayi gaba Daya ya yanke jiki agurin ya zube kansa na bugawa da bakin table Dake gurin gashinsa na fashewa jini na fitowa ahankali ya lumshe idanuwansa Yana Jin jijiyan jikinsa kaman suna tsinkewan hakama jinin dayake jikinsa yana konewa cikin wata sanyayyar azaba Mai radadin gaske ga ganinsa gaba Daya ya dauke Baya ganin komai Baya Jin komai.
Dad Lameenu ne da BB ya kira tin Yana hanya ya shigo dakin bayan BB ya Bude masa kofar Yana kallansa tareda basa tabbacin Haroon din bayaji Baya ganin Komai.
Tsayuwa Dad Lameenu din yayi akansa tareda kallan BB Wanda Shima killer ya kalla aka Ciro kwayar killer na kokarin rabawa uku BB yace ya basa a Hakan.
Cikin tsananin firgici da tashin hankali killer din duk rashin imaninsa ya Kalli BB din sbd ko ukun idan aka ranata akasha ba qaramin Neman kashe mutum takeyiba bare duka Kuma har gida biyu.
Karban kwayoyin Yan kanana dasu BB yayi baiyi wata wata ba ya Bude bakin Haroon dayake kwance kaman gawan data rasa gatan suturtawa ya zuba masa su duka tareda karban ruwan da Alh Lameenu yake miqa