Showing 54001 words to 57000 words out of 93806 words

Chapter 19 - Ameenatou Book Original Complete Book .txt

25 Nov 2024

4041

zasu fara Neman Dan uwan matar Omar Wanda a yanzu sukeda cikakkiyar tabbacin 'dan Omar Yana hannunsa.


Lameenu da hankalinsa yafi na Mam tashi sbd yanada labarin project dinsu ba lallai yakai labari ba Dan kuwa komai Baya tafiya yanda akeso,
Idan Mam yaji Hakan abun sake lalacewa zeyi Dan shi Kam ya gaji da Mam Yana sake bawa Haroon Daman shikuma Yana sake rusa su sbd bazai taba zaba me amfanin da sukeso ba Babu amfanin basa damammakin da ake basa,


Shi a nasa son su cire Haroon daga komai nasu Dan baida amfani kawai su bazama Neman magajin Omar Dan kuwa Babu abinda zasuyi yanzu dukiyar ta dawo yanda take koma fiye da yanda suke tsammani bayan su mallaki dukiyarsu ta Omar Dake ransu tin shekara da shekaru.


Mam ma a cikin ransa kusan tinanin ne a ransa Dan kuwa idan ba bazama sukai suka haukace gurin Neman magajin Omar ba faduwansu zai Sakasa yiwa dansa abinda baitaba tsammata yi din ba Dan kuwa ya tabbatarda Haroon yafi kowanne 'da rashin amfani,
Ya rasa wane irin Kai ne dashi gashi tsaban rashin basira ya kasa roko ko rarrashin Jamaal ya dawo musu,


Ba komai ya sakashi sakar masa pressure da nuna masa hantara da rashin kauna ba sai Dan ya rufe ido ya dage ya Saka Jamaal dawowa garesu ba Dan yasan duk duniya Haroon ne kadai zai iya Saka Haroon dawo musu Dan kuwa duk Wanda yasansa yasan Haroon ne abinda yafi komai so da kauna fiyeda komai bayan mahaifiyarsa Dan haka suke zafafawa Haroon komai Dan Jamaal ya dawo musu Amma Haroon din kaman kansa Babu komai a ciki Se iska,


Duk maganin da suka Saka masa a drink suna susuta kwakwalwansa Dan ya zama abin tausayin da zai Saka Jamaal ya dawo garesa abin ya gagara sbd yasan duk abinda Haroon zai koma bazai taba zabar barinsaba Koda Jamaal da mum dinsa sunso daukesa bazai taba binsu ba Dan haka yakeda tabbacin Jamaal zai dawo sbd Dan uwansa.


Suna Isa gida kowa mansion dinsa ya shige batareda tsayawa office nasu Dan tattaunawa ba Dan kowannensu Yana buqatan kadaicewa Dan dawowa daidai.


Mum Atee na ganinsa da yanayinsa bayan shigowansa tasan akwai damuwa me girma Dan haka tabarwa Ayesha zaban kayan datakeyi a waya ta bisa zuwa sama tana fatan ba matsalar Haroon bane da itama zuwa yanzu lamarinsa yafara isarta Dan itace kullum me zuba maganin da suke basa a drink dinsa na cin abinci sai kuma ta tabbatarda yasha cikin kulawa da dadin Baki Wanda ahankali ahankali yake yiwa kwakwalwansa illa harma da kuzarinsa batareda sanin Dad dinba Dan abinda yasaka ta ringa basa daban da abinda take basa din.




******Barr Haroon seelah a yanzu ba zaman Nasarawa ne ke basa nutsuwa da farin ciki ba ganin Ameenatou ne da rayuwar ahalinta da yanzu ya zamar musu tamkar Dan uwa,


Ayanzu Daya sabu da zamanta a cikin zuciyarsa Babu ranar da Baya zuwa gidan duk yanda zai gaji da ayyuka kuwa saiyaje gidan da daddare acan yake fira cikinsu sai dare sosai yake komawa masauki.


Babbah da dukkaninsu har zuciyarsu sun basa matsayi me kyau da kauna me sanyi kallansa sukeyi a Dan uwa duk da tsananin tazarar datake tsakaninsu Dan kuwa idan ya zauna cikinsu kaman saika wanke hannu zaka tabasa Dan yanda yake fita daban kaman wata acikin taurari.


Ameenatou sosai suka shaku cikin qanqanin lokaci Kuma a bayyane yake yanzu tsananin son dayake mata duk da itama tana sonsa sosai sedai hakanan wasu lokutan sai takejin kaman irin son datakewa su Yaya Hafiz take masa Amma Kuma tace bazata auri kowa ba sai shi Dan Hakan ne ma yakejin samunta a rayuwarsa zai samu nutsuwa da Kwanciyar hankalin Daya rasa tareda kadaicin rayuwar dayake ciki.


Bai taba sanin wannan son dayake a cikin kirjinsa yanzu ba shine abinda Dan uwansa Jamaal yake ji a lokacinda fadilansa tana raye ba,
Baitaba dauka zaiso mace irin son da Jamaal yayiwa fadila ba sai yanzu dayake Jin Ameenatou har cikin jininsa da ruhinsa Dan kuwa akanta ne yafara Jin Koda Dad dinsa zai yafesa idan har zata zama cikin rayuwarsa zai iya fuskantar Hakan.


Dukkaninsu Babbah sun San so me tsanani yakewa Ameenatoun Dan haka yake sake matsayi sosai a zuciyoyinsu musamman Hafiz dayake Jin farin cikin Ameenatoun zata samu rayuwar da zata zufafa iliminta Dan sunada burin tayi karatu me zurfin da zata dogara da kanta tinda bazata zauna karkashinsuba har abada.


Aikin Daya kawosa fara lalacewa yayi matsaloli suka fara bayyana sbd gabaki Daya hankalinsa da nutsuwan dayake samu a gurin Ameenatou suna can,
Idan ciwonsa yafara tasowa na damuwa Baya gane komai Baya ganin komai idan ba gidansu Ameenatou ya taho ba ya zauna ya zuba mata idanuwansa tana magana yana sauraronta Kokuma Idan tana tareda su Babbah tana zuba sangartanta son ranta batareda damuwa da Yana gurinba Dan matiqar tana taredasu Bata duba kowa duk abinda takeso zatayi Abinta shi Kuma Hakan yake sake kashesa akanta musamman idan tana fadan shi kadai ne zai zama mijinta Babbah zai aura masa ita.


Wannan kalman itace kalman da ayanzu take fin komai Sakasa farin cikin Da bayada shi kwata kwata a rayuwarsa.


Siddeeq hankalinsa yafara tashi sosai da irin son da Haroon yakewa Ameenatou Dan karfinsa yafara Sakasa shakkar lafiyansa ga Kuma bangare Daya aikin dayake gabansu fa Babu haske ko kadan kullum sabuwar matsala ake samu Dan haka yake cikin tashin hankalin.


Ranar dasu Dad suka zauna da turawan da suke cikin aikin suka fara samun barazanar janyewa daga hadin gwiwan kwata kwata jinin Mam Hawa yayi sosai Saida aka kira likitoci gida suka dubasa aka basa magani hadda su ruwa.


Mum Atee hankalinta tashi yayi Dan haka ta dagawa Haroon hankali da kuka Saida ya dawo Lagos a ranar cikin mummunan tashin hankalin abinda ya samu Dad dinsa.


Dad Lameenu kuwa kusan zaucewa yafara kokarin yi Dan ganin Mam a halinda yake ciki yasan balain Da yakai Mam kwance ba qaramin balain da zai kawo karshensu ba kwata kwata ne ba Dan haka ya kira BB ya Bude musu wuta akan tsananta bincikensu ko Wanda ya taba sanin dangin Aminatu ne aka samu a kamosa a kawosa.
#MAMUH




*_ZAFAFA BIYAR_*


1 *_Ameenatou!!_*
_Mamuhgee_


2 *_Tsutsar Nama!!_*
_Billyn Abdull_


3 *_Gudun Kaddara!!_*
_Safiya huguma_


4 *_Kwankwason Jimina!!_*
_Miss xoxo_


Guda Daya 400
Guda biyu 700
Guda uku 1k
Guda hudun 1200


*_6019473875 MUSAA ABDULLAH SAFIYAH keystone bank_*


*_ATURA SHEDA ZUWA 09166221261_*


*_MTN/VTU 09134848107_*


_*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din 09033181070*_


*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_**_Arewabooks@Mamuhgee_*
35
Tinda Haroon ya dawo Dad dinsa ya Hanasa ganinsa Dan Baya buqatan ganin ko fuskan Haroon din.


Mum Atee ce ta ringa lallaba Haroon din da duk inda hankalinsa yake ya tashi da wannan hukuncin na Dad dinsa.


Kusan Shima kwantawa yayi ciwon sbd hukuncin Dad dinsa na qin barin ya gansa.


Da wannan damar mum Atee tayi amfani ta ringa shayar dashi kwayar da suke Banka masa Dan haka sai yafara rikicewa ahankali ahankali sbd fushin Dad din da Kuma kansa da suke Neman juyar masa.


Siddeeq Daya fahimci yanayin Haroon din ya sauya sosai ya fara tsananta sosai daukesa yayi suka koma Nasarawa Koda lamarin zaiyi sauki idan Yana ganin Ameenatou wadda itama kullum take cikeda kewansa da damun su Babbah akan kada fa yaje ya auri wata acan Lagos yabarta anan ita tana jiransa.




Dawowansu Nasarawa ciwonsa tsananta yayi gashi basa ganin likita a bayyane a boye suke Gani sbd kada Yan jarida su ji Barr Haroon seelah magajin SEELAHs yana fama da matsalar data shafi damuwa da kwakwalwa.


Su Babbah Jin baida lafiya sosai suka shiga damuwa da tausaya masa sbd kaunar da suke masa ta wuce ta ogan Hafiz da Kuma Mai son Ameenatou.


Babbah da Yaya Abdul da kansu suka takurawa Haroon din da siddeeq suka Kaisa asibiti da kansu suna zuwa aka basa gado a dakin da Babu Wanda zaisan waye a asibitin.


Kwanciyarsa asibiti ya Sakasa sake tabbatarda bazai iya rayuwa Babu Ameenatou ba Dan kuwa kauna da kulawan da Bai taba tinanin ana samu daga ahali ba sune ya samu Dan kuwa Hafiz ne ma kusan yake kwana ya tashi dashi a asibitin babbah da Abdul ma kullum anan suke kusan wuni dadah da Heartbeat dinsa kuwa kullum sai sunzo da daddare su koma tareda su Babbah gaba dayansu.


Ameenatou duk narkewa tayi ganin yanda ciwon kwana biyu ya mayar dashi Dan haka tausayinsa ya Saka sonsa Data kasa ganewa da tantancewa cike dukkanin zuciyarta.


Kwanansa biyu aka sallamesa batareda ance musu komaiba kawai dai wai ciwon Kai da bp dinsa ne ya hau sbd damuwa da stress na aiki.


Bayan an sallamosa da kwana Daya Lagos ya tafi Dan sake dubo Dad dinsa Wanda har lokacin ko wayarsa Baya dauka.


Bayan isarsa Lagos Shima siddeeq gida ya koma Dan dubo umman fadila da yanzu Alhmdlh ta rungume kaddara tana rayuwarta cikin Kwanciyar hankali da Kuma kulawa me tsananin datake samu da kauna sosai daga siddeeq din Daya inganta rayuwarta sosai Babu abinda ta rasa saima Jin dadinta datakeyi.




******Tsayuwa Haroon yayi jikinsa na sanyi ganin Dad dinsa zaune a kan dining din cin abincinsu na dare bayan baiyi tsammanin ganinsa ba a gurin Dan kwata kwata ya Dena barin Yana ganinsa.


Mum Atee ce tayi saurin tasowa daga inda take zaune kusa da Dad din Yana washe Baki cikin kulawa da kauna sosai ta nufosa tana cewa


"Zo ka zauna yau tareda Dad Dinka zakaci abinci Inshallah duk komai ya wuce"


Kallan Dad din yayi Yana qarasowa jiki a Sanyaye zuciyarsa na sanyi hakama jikinsa na sake mutuwa sosai.


Mum Atee ce tayi saurin ja masa kujeran kusa da Dad tana cewa ya zauna ai Dad dinma yayi kewansa.


Zama yayi batareda ya dago ya Kalli Dad dinba Shima Dad din Bai kallesaba ba Saida gurin ya dauki shiru tsawon mintina kafin Haroon din ya dago ya Kalli Dad dinsa da idanuwansa dasukai wani irin ja da sanyi cikin sanyi da nutsuwa yace


"Dad barka da fitowa,
Yaya jikin?
Allah ya karo Maka afuwa da sauki."


Numfashi mata sauti Dan dumi Dad din ya sauke kafin ya amsa Kai tsaye Babu Jin dadi ko kadan a muryansa Dan kuwa ganin Haroon din kadai tafasa zuciyarsa yakeyi Dan gap yake da yafesa gwara yasan baida 'da ko Daya a gabansa Saiya fanjama mummunan aikinsa dakyau kawai ayi me yiyuwa.


Ayeesha Dake table din itama cikin kulawa ta gaida Dad din tana masa ya jiki ya amsa Yana gyada mata Kai kafin Suka fara cin abinci Babu me cewa komai.


Suna gama cin abincin mum Atee sai sake zuba masa juice din data hada masa da kanta takeyi cikin kulawa da tattalinsa kaman Dan data haifa.


Suna gama cin abincin kafin kowa ya tashi Dad sai lokacin ya dago ya Kalli Haroon cikin kamewa Babu sakewa ko kadan yace


"Ka hada komai na SSl project ka ajiye za'a rufesa gaba Daya Wanda kasan me Hakan ke nufi ai ko?"


Wani mugun zufa ne ya fara tsiyayowa daga cikin rigar Haroon ya dago idanuwansa ya Kalli Dad din cikin tsananin kwantar da Kai yace


"Dad Ina rokon ka karamin time na cike time din da aka dibarmin tin farko akan aikin nayi alkawarin zan cika Maka alkawarin dana dauka akan aikin,
Dad please Karkayi saurin rufe komai wlh Ina iya kokarina fiyeda yanda kake tsammani,
Ko yanzu rashin lfy nayi kwana biyun shiyasa aka fara samun durkushewa Amma wlh Dad nayi Maka alkawarin komai zaizo gabanka yanda kakeso....


Daga masa hannu Dad din yayi zuciyarsa na wani irin ciwo da radadi Dan har lokacin Jin yakeyi zuciyarsa Bata warkeba.


Jajir idanuwan Haroon din sukai kaman yanda na Dad din sukai jajir yanajin baisan me zai kama ba yabar Daya tsakanin 'dansa da dukiyarsu dasuke Neman rasawa.


Mum Atee datai shiru Dan muskutawa tayi tana rokon Dad din akan ya sake bawa Haroon din dama.


Ayeesha kuwa shiru tayi dukkanin jikinta yayi sanyi da tausayin Haroon Daya rasa komai akan Dad dinsa Amma Babu Wanda ya taba appreciating nasa ko kadan.


Shiru Haroon yayi zuciyarsa na nauyi me tsanani tareda nauyin Kai shima me tsananin Yana sauraran yanda mum Atee ke rokon Dad din kafin ya amince masa da sharadin ana samun matsala zai tattara ya koma Poland Shima gurin mahaifiyarsa.


Dagowa yayi da jajayen idanuwansa ya kalli Dad din tareda masa godiya kafin ya miqe jiki a mace yabar dining din Shima Dad miqewa yayi yabar dining din.


Koda ya koma dakinsa juyawa kansa yafara yi masa tin a palonsa ya zube Yana dafa Bango kaman ganinsa zai dauke Yana Jin kansa kaman zai tarwatse.


Daqyar yakai kansa dakinsa ya Isa gaban mirror Yana Neman maganinsa Amma Bai gansa ba.


Raffowa yayi Yana barin duk abinda ya fadawa harya Isa gefen gadonsa yafara janyo drawers hannuwansa na wata irin rawa Yana yamutsa kayan ciki gurin Neman maganinsa Amma kwata kwata ya kasa ganinsa.


Buga kansa yafara yi a jikin gadonsa Yana wata irin rawar jiki.


Wayarsa Dake gefen gadon ajiye ce tafara ringing Amma Sam baima San meyake ji ba bare yaji Kiran.


Ameenatou Dake kiransa Dan Jin muryansa sake Saka Kiran Tayi tana matsuwa Daya dauka Dan haka kawai zuciyarta keson jinsa Dan yanzu zuciyarta ta gama yin naam da karban sonsa fiyeda yanda tayi tinanin tana son nasa.


Cigaba da Kiran datake masa ya Sakasa dago idanuwansa da sukai wani irin mugun jajir ya Kalli wayar.


HB ya Gani rubuce kan wayar yaga itace.


Hannuwansa Dake wata irin rawa ya dago suna jijjiga ya Dora akan wayar ya dauko tareda daga wayar ya Saka handsfree ya ajiye Yana Jinta acikin dadaddiyar muryanta me sanyi da nutsuwa tana magana.


Yana jinta Amma kwata kwata Baya iya magana saima Juyewan dayake Jin kaman kansa zeyi da azabbiyar ciwo da nauyi hakama jikinsa rawa yake qarawa sosai Yana hada zufan dayake sake tsatsafo masa Tako ina har cikin tafin hannuwansa da kansa.


Sunansa ta sake kira cikin damuwan jinsa shiru tana narke masa a wayan.


Wasu hawayen azabbiyar Sonta da tausayin kansa masu tsananin zafin gaske suka gangaro masa ya rufe idanuwansa harta gama magana yanaji ta kashe wayar batareda ta sake Kiran ba.


Kuka me zafi ne ya kufce masa Yana buga kansa a jikin gadonsa da karfi har lokacin jikinsa rawa yakeyi sosai musamman hannayensa.


Ya Dade acikin wannan azabar tsawon lokaci kafin ya Dan samu sassauci ya rarrafawa ya sake dudduba maganinsa ya gansa a Palo ya dauka da sauri hannuwansa na kakkarwa ya Bude roban ya zubo guda biyu ya jefa bakinsa tareda Isa inda ruwa suke da sauri ya dauka ya shanye maganin yana sake hada zufa me yawa kafin ya silale a palon ya zauna Yana rintse idanuwansa Yana jingina bayansa jikin bayan Daya daga cikin tsadaddun kujerun palon.


Yayi mintina sosai ahakan kafin ya dawo daidai ya sauke numfashi da ajiyan zuciya tareda miqewa tsaye ya nufi bedroom dinsa gurin wayarsa Kai tsaye ya nufa ya dauka Yana kallan time yasan zuwa lokacin Ameenatou tayi bacci Dan haka Hafiz ya kira ya tambayesa ya sanar mace tayi bacci.


Sallama sukai batareda ya kirata ba Dan kaman yanda su Babbah ke lallabata haka Shima yake lallabata kaman zuciyarsa Dan haka bazai iya tadata bacci da wayarsa ba.


Ajiye wayar yayi ya miqe ya nufi bathroom ya sakarwa kansa ruwa yayo wanka ya fito daure da towel ya shirya cikin kayan bacci marasa nauyi ya kwanta Yana rufe idanuwansa jikinsa har lokacin a Sanyaye.




Washe gari tinda safe breakfast kawai yayi dasu Dad yayi musu sallama suka nufi airport suka bar Lagos din shida siddeeq.


Bayan tafiyarsa Dad Lameenu ya Saka aka bisa Dan Saka masa ido sosai akan lamarinsa kowanne irin motsinsa da komai Dan shi Kam bazai yadda suna kallo su wayi gari basuda komaiba.
#MAMUH#
#JAMAAL JEEY
#HAROON SEELAH
#AMEENATOU
#IDENTICAL TWINS




*_ZAFAFA BIYAR_*


1 *_Ameenatou!!_*
_Mamuhgee_


2 *_Tsutsar Nama!!_*
_Billyn Abdull_


3 *_Gudun Kaddara!!_*
_Safiya huguma_


4 *_Kwankwason Jimina!!_*
_Miss xoxo_


Guda Daya 400
Guda biyu 700
Guda uku 1k
Guda hudun 1200


*_6019473875 MUSAA ABDULLAH SAFIYAH keystone bank_*


*_ATURA SHEDA ZUWA 09166221261_*


*_MTN/VTU 09134848107_*


_*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din 09033181070*_


*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_**_Arewabooks@Mamuhgee_*
36
Ameenatou na islamiya ya dawo Dan haka bayan yayi Sallah abinci yaci ya kwanta Dan samun baccin da tinda yake Lagos harya baro Bai wani samuba.
Shima siddeeq hutun ya kwanta ya samu kafin yamma.


Karfe Biyar da mintina ya tashi daga babbacin na awa Daya da Yan mintina San Saida yayi laasar ya kwanta.


Wanka kawai yayi ya shirya ya karbi ke din mota daga hannun siddeeq da kansa yaja ya nufi makarantarsu Ameenatou Kai tsaye.


Yana Isa ana tayar dasu Kuma Hafiz ma Yana Isa daukota Dan haka Koda ta fito cikin doguwar hijabinta akansa idanuwanta suka fara sauka Yana tsaye jikin motarsa Yana waya ahankali kaman mara lafiya kyakkyawar fuskansa ta fada kadan gaba Daya ya juyo hankali da idanuwan duk Wanda ya fito makarantar dama masu wucewa akansa sbd ganin bature tsaye bakin makarantar tasu.


Waya yakeyi Amma Shima tinda ta fito idanuwansa na kanta yanajin jikinsa na mutuwa zuciyarsama sanyi tayi Dan baisan wane irin so ne yakewa Ameenatun ba.


Ganinsa itama ya Sakata sakin kyakkyawar murmushi tana Dan dauke idanuwanta daga kansa Dan kuwa Jin tayi ganinsa ma gaba Daya ya Sakata Jin wani farin ciki me yawa gashi tana son tayi murna sosai a fili Amma batason Yan makarantar Susan shi zata aura su fara kalle mata shi Dan gulmansu.


Nufosu tayi zata Bude Baki tayi magana Hafiz ya jefa mata wani kallan Daya sakata nutsuwa tana hadiye zancen Daya fadawa Haroon na kewan datai masa me tsanani.


Kashe wayarsa yayi Yana kallanta fuskansa daukeda murmushi Mai bayyanarda farin ciki yace


"Barka da fitowa Budurwan Babbah"


Wani sabon farin ciki taji ya rufeta sedai narke fuska tayi tana qasa qasa da murya kada Hafiz yaji tace masa


"Yanzu ba budurwan Babbah bace ai na sauya suna"


Mota ya Bude mata ya shiga ya rufe mata Saida ya zagaya ya shiga ya zauna Hafiz ma ya shigo kafin ya kalleta Yana tayar da motan yace


"Yanzu yar budurwan Barrister ce ko??


Wani sabon dadin taji Yana hararan Hafiz da Shima ita yaketa harara kaman idanuwansa zasu fado Amma taqi kallansa bare taga kwabar dayake mata ya ido sbd sakarcin Data Saba yi musu hadda Haroon din kada tayi a gaban makarantar cikin bainar jamaa.


A hanya kafin su Isa gida guri uku tana sakawa ana biyawa sbd siyan wani littafinta na islamiya da zata dashi gobe kafin suka Isa gida anata kokarin shiga sallan magrib Dan haka Haroon din Bai shiga ba alwala kawai sukai a waje suka wuce masallaci ita Kuma ta shige gida.


Saida sukai ishai suka shigo gidan anan Haroon yaci abincin Dare tareda

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login