Showing 72001 words to 75000 words out of 93806 words
fita tayi yau ita kadai a Karan farko rayuwanta taje gidan kawarta Aminiyarta Khadija Tayo mata bankwana itama Khadijan satin zaa fara bikinta shiyasa bazata samu binsu ba ayi bikin da ita Dan haka suka hakura dole da samun bikin juna.
Fitowa sukai tareda Khadija din ta rakota har kusan Rabi kafin ta koma ita Kuma ta wuce.
Dayake hanyar site ne gidansu Khadijan tana kawowa gurin hanyar site din ya hango motar Haroon ta tsaya a bakin hanyar da zatabi ta wuce bakin shago batareda an Budeba.
Glass ya saukan aka miqo masa Abu daga shagon Wanda take kyautata zaton ruwa ne sbd bayan motarsa aka Saka masa.
Wani kyakkyawar murmushi me sanyi ya sauke daga fuskanta tana kallan motar ta tabbatarda shine a ciki bayan yanzu da sukai magana cemata yayi Yana Abuja.
Motan ta nufo tana daga wayarta Dan Saka Kiransa taji me zai fada mata yanzu Kuma.
Tana isowa motar ta miqa hannunta Daya akan mabudin kofan Baya Dan tasan anan yake zama siddeeq ne me jan motar
Tana budewa daidai Yana dagowa daga abinda yake Karantawa daga iPad din hannunsa ya kalli kofan motar da aka Bude Idanuwansu suka shiga cikin na juna
Shikuma a Karan farko Daya Kalli idon wata 'ya mace rayuwansa bayan rasuwan matarsa.
Itama nata idanuwan kusan shine karanta na farko kallan cikim idan mutum Dan haka ta dauke fararen idanuwan nata tana sake wata fitinanniyar murmushi tareda shiga ta zauna Kai tsaye tana juyowa suka fuskanci juna qamshinsa na shigan hancinta Kai tsaye zuwa zuciyanta murmushinta Bai daukeba sedai yau din ta kasa kallansa sbd kunyar takusa zama matansa Kila yau takeji da wani shagwabbiyan murya ta dago ta zuba masa idanuwanta tace
"Shine kacemun kana Abuja sbd kada muyi bankwana kafin na wuce ko??"
Siddeeq Daya rasa ta inda zai fara gyaran matsalan Dake kokarin faruwa fitowa yayi da sauri daga motan ya zagayo ya rufe mata kofar Data shigo ya sake dawowa mazaunin driver da sauri ya zauna sai alokacin ya juyo ahankali ya saci kallan JEEY Daya zuba mata fararen idanuwansa Yana kallanta cikeda mamaki da shakkar ko tanada matsala ne Dan baisanta ba baima taba ganinta ba yake ganin.
Hadiye numfashi siddeeq yayi cikin Dan daidaita murya ya riqa JEEY din magana Yana washe Baki da nuna kulawa yace
"AMEENATOU,
barka da fitowa,yau ke kadai kika fita ne??
Hakan daya fada ya fada ne Dan JEEY yasan wacece din shiyasa ya ambaci sunan nata Kai tsaye Yana tada motar yaja ahankali suka bar gurin Yana juyawa Dan maidata gida.
Dauke idanuwansa JEEY yayi akanta tareda rufe iPad dinsa daidai lokacin ta sake motsowa kusa dashi tanason fada masa maganar da batason siddeeq yaji sedai tana motsowa da fuskanta Dan fada mata din Yana juyowa da tasa fuskan kadan ya rage fuskokinsu ya Hadu tayi saurin yin bayan kirjinta na bugawa ta dago ido ta kallesa Shi kuwa Kai tsaye ya Bude Baki yace siddeeq ya ajiyesa site.
Kasa magana tayi sbd kirjinta Dake bugawa har lokacin shiyasa har motan ta tsaya Bata iya cewa komaiba harya Bude motan ya fice yabarta zaune tana kallan inda ya tashi da ido fuskansa da numfashinsa Daya bugu fuskanta na dawo mata.
Gida siddeeq ya wuce ya ajiyeta Yana mata zancen aikin Dake gabansa ne duk suka Saka kansa daukan zafi shiyasa Baya cikin mood kwata kwata yau din.
Bata iya cewa komaiba ta Bude motan ta ficewanta tareda shigewa gida.
Mota ta musamman ce tazo ta daukesu guraren 2 na Rana tayi Abuja dasu daga can suna Isa airport ba Bata lokaci jirginsu ya daga zuwa Lagos.
Suna sauka Lagos Abdul ne da kansa yaje da motan Aliyah 'yar Alh Lameenu wadda tinda Taga Abdul din taji yayi mata sbd batason namiji me kudin da shine zai juyata tafison Wanda itace me kudin Kuma yar me kudin dazata ringa yanda takeso baya hanata bare ma Saka ido Dan Bata wani zama kasar itama kullum tana yawo karatun ma duk ta kasa tsayawa tayi sai yawon kasashe.
Dayake Dad ne yace yaje da motan ya daukosu shiyasa ya taho da motan ya daukosu.
Gidan Abdul din a kusa da tsadaddiyar anguwan masu shi da mansions din seelah din suke yake Dan haka daga gurin mum Atey driver ya kawo musu abinci bayan isowan nasu.
Gida ne me maana Wanda ya bawa Babbah da Hafiz mamaki sosai sbd ace anbawa sabon ma'aikaci gida irin wannan me Dan yalwa da kyau da tsari Kuma komai akwai a aciki gaskia sedai Dan zasu hada zuria ne Amma tinda a cikin kudin aikin Abdul din akace kamfani zai ringa cire kudin haya sai sukafi Jin nutsuwa da Kwanciyar hankalin sakewa da Hakan.
Daki uku ne a gidan sai Palo biyu da kitchen sai back door da store sai kowanne daki da toilet dinsa.
Kowa daki Daya ya dauka Abdul Daya,Hafiz Daya sai su Babbah Daya sbd Ameenatou tafiyanta zatai gidanta Nan da kwanaki Dan haka baa Raba dakin da ita ba Amma dai na Hafiz itace a ciki da komai nata shikuma yana kwana Palo kafin ayi bikin Amma kayansa suna dakin Yaya Abdul Wanda nasa dakin na daga gefensa daban nasu Babbah ma Yana daga gefe daban na Ameenatou dinne a tsakiya.
#MAMUH#
*_ZAFAFA BIYAR_*
1 *_Ameenatou!!_*
_Mamuhgee_
2 *_Tsutsar Nama!!_*
_Billyn Abdull_
3 *_Gudun Kaddara!!_*
_Safiya huguma_
4 *_Kwankwason Jimina!!_*
_Miss xoxo_
Guda Daya 400
Guda biyu 700
Guda uku 1k
Guda hudun 1200
*_6019473875 MUSAA ABDULLAH SAFIYAH keystone bank_*
*_ATURA SHEDA ZUWA 09166221261_*
*_MTN/VTU 09134848107_*
_*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din 09033181070*_
*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_**_Arewabooks@Mamuhgee_*
46
Haroon yanason dawowa Lagos Amma sbd kada ya zama ana ganinsa a Lagos Kuma ana ganin Jamaal a site yasakashi hakura ya zauna tareda Jamaal din Wanda Shima yafara kokarin Maida hankali ya gyara career dinsa data watse ta matsayinsa na lawyer.
A bangaren su Dad kuwa tsarin katin gayyatar Omar na musamman ne,
Duk tsawon shekarun Nan da basa tare bawai sun yanke muamala ne kwata kwata ba aa Suna waya da sauran gaisuwa a waya batareda kowannensu ya nunawa Dan uwansa komaiba,
Shi Bai taba yi musu wata maganar bare nuna wani abin daban kaman yanda suka Basu taba cewa komaiba bare nuna shakka fargaban yasan wani abin kawai dai kowa na nesa da Dan uwansa duk dubaru da nuna kaunarsu Bai Bata zuwa inda suke ba kaman yanda ya toshe hanyarsu ta zuwa inda yake iya Hulda da zumuntar waya sukeyi tareda nunawa juna kauna da kulawa a iya wayar sai yanzu da wannan kyakkyawar Daman ta taho musu wadda baida kowanne uzuri ko dalilin Badawa na qin zuwa auren Haroon Wanda sune ma ya kamata ace sinje Neman auren nasa batareda anje dashi Mam dinba Dan shine iyayensa.
*****Ta bangarensu Amarya Ameenatou kuwa suna fama da kadaici da bakuntar sabon guri Amma irin rayuwar da suka samu kansu a ciki ta wadata ta Saka bakuntar zuwan musu da sauki ga Kuma hidiman da aketa kokarin farawa gadan gadan.
Su mum Atee dasu mummy Sarat da jamaarsu sun kawo lefen auren Wanda ya amsa sunan lefen gaske na auren masu abun duniya Dan kuwa sosai dadah da umman fadila datazo tarbon lefen sbd Jamaal da siddeeq harma da Haroon din suka girgiza da tarin kayan da aka kawo din tareda wasu mahaukatan sarkokin Dalma(zinari/gwal/gold).
Da dadah da umman fadila sai Jamaar amanar dadah biyu da suka taho bikin Tim daga Nasarawa Dan lasa arzikin Suma da Kuma tabbatarda amanarsu Dan idan Basu taho auren budurwan gidan Babbah ba yar gaban goshin dadah dasu Hafiz ai basuyi komaiba.
Duk da basuda wani karfi Saida Babbah ya fidda kudi masu Dan kauri a Dan abinda suke Tarawa na bikin ya Bada tukuicin da sedai masu aikin da sukai shigo da kayan ne suka karba Amma mum Atee Sam kin karba sukai suna nuna ai ba komai bazasu karba tukuicin ba bayan a cikin ransu dukkaninsu qyanqyamin taba kudin ma sukeyi sbd Yan dari biyar biyar ne a hade dubu hamsin cif.
Su umma anan duka wuni sunata duba kayan har dare suna sake Saka albarka da adduar fatan farin ciki me dorewa a auren.
Washe gari masu gyara na musamman aka turowa Ameenatou wadda za'a fara gyarawa Tin daga satin har satin auren Wanda ya rage saura sati biyu cif.
Ranar farko da aka fara yimata gyaran ta fara sauyawa abinta sbd fatarta irin me santsin Nan ce dake karban komai da wuri,
Farin ciki da dokin datake ciki itada Haroon ya wuce duk inda ake tinani sbd karfi da yaji duk yanda Babbah da Dadah suka Kai basa ganin laifi ko illan komai datakeyi Saida suka ringa Jin kunya da mamakin irin son datake wa Haroon Wanda ya Sakasu shiga tsoro da duqufa da adduar Allah yasa irin girman son dayake mata ya tabbata a rayuwar auren nasu yakuma barsu tare har karshen rayuwarsu.
Haroon a wannan lokacin yana cikin kwanakin farin cikin rayuwarsa me tsananin gaske da Bai taba samun kansa a cikinsu ba Wanda Hakan ya sanyaya zuciyar 'dan uwansa da mahaifiyarsa akansa wadda Bata isoba har lokacin Amma ta sheda farin cikin Da Haroon dinta yake ciki Wanda takejin a matsayinta na uwa a garesa tayi missing Daman basa wannan farin cikin dasuke Gani tareda shi sedai tana Jin dadi har ranta daya samesa sanadin macen dayakeson.
Jamaal tausayin dan uwan nasa ne ya Sanyaya zuciyarsa bata cikin farin ciki ko walwala kwata kwata Dan Bai taba ganinsa a irin wanna kyakkyawar yanayinba tsawon rayuwarsu Dan haka yake tayasa farin cikin Samun abinda shi Bai samuba Dan kuwa a nasa labarin Bai taba samun farin soyayya a tareda wadda yaso din ba, duk lokacinda suka dauka a tare lafiyanta koyaushe itace abinda take gaban soyayyarsu Dan haka har suka rabu Basu taba samun kansu a cikin irin wannan farin cikin ba Dan haka baisan Menene yanayinba da yanda ake samun Kai acikinsa.
Koda yaushe a waya suke maqale da juna suna magana tana nuna masa duk abinda akai mata na gyaran Amarya Wanda kullum take sake sauyawa sosai tana fita budurwan datake cikin Hutu da gyara sosai Dan tinda suka taho Lagos din Bata sake fita ko gate ba daga gyara sai Hutu da AC datake Sha da lafiyayyar abinci me gyara jiki take ci.
Har lokacin Bai dawo ba Haroon din Yana Nasarawa n Abuja aikinsu gap yake da kammaluwa Wanda yake Jin kaman Yana Neman rasa kansa kafin gama aikin ya koma Lagos din.
******Su Dad so biyu suna turawa Omar jeden gayyatarsa a matsayin Wanda zai karbanwa Haroon din auren Amma Yana toshe buqatansu ta Hakan sai gashi hankalinsu Yana Neman tashi da Hakan Dan haka Kai tsaye Mam yayi masa maganar Amma still dai ayyukan gabansa bazasu basa Daman zuwan ba ya sake Bada uzurinsa sbd Koda suke maganar ba Baya Nan Yana Japan Dan haka Kai tsaye ya Saka Ahmed ya tura musu zunzurutun kudi a matsayin gudunmawarsa data Saka su Dad din shiga mamaki da baqin gaske me tsanani.
Tsaban kudin suka kalla suna sake shiga qyashin gaske da bakin cikin irin yanda ya debo kudi irin wannan me yawa ya Basu kusan 500m as gudunmawarsa.
Shiru Dad Lameenu yayi lokacinda suke cikin tinanin abinyi gameda baqin cikin da Omar yake Neman sakasu Dan kuwa idan har zaayi auren Nan Bai tahoba tabbas Babu amfanin yin auren babba a garesu Dan duka kudi da dukiya me yawan da aketa zubarwa ana Shirin auren da akeson duniya ta sheda auren SEELAHs duk Dan sbd Omar din yazo ne Amma Kuma komai Yana Neman lalacewa a daidai lokacinda Babu time na Neman mafita ko gyara.
Mam da hankalinsa ya rabu biyu a yanzu akan yanda komai na ayyukansu ke tafiya daidai da Kuma sauyin Haroon Daya fara Sakasa Jin so da kaunan Dan nasa me tsanani na cikeda sedai Kuma Yana shakkar Shima yazo yayi auren mace ta sauya masa shi yazo Kuma baida abinda zaiyi masa barazana dashi Dan tankwarasa Dan haka gaskia gwara ya kama dukiyan dayake son kamawa Koda yayansa sun juya masa Baya yanada abinda bazai taba Jin zafi ba.
Lameenu wani numfashi ya sake Yana dagowa ya Kalli Mam da Shima yake Nisa cikin nasa tinanin ya sauke numfashi Yana ajiye wayar hannunsa daya gama da BB akan a Turo Yan jarida gidan Babbah zasu tafi Kai masa ziyara Yana son a yada abinda ya hadasu din sbd Omar yaga abinda sukeson ya Gani.
Mam da Baisan me Lameenu ke nufi ba yace
"Kayi duk yanda zakayi Omar yazo kasar nikuma wanna Karan nayi alkawarin cike aikin komai da hannuna batareda matsala ko dayaba wannan alkawarina ne."
Murmushin Daya tsaya iya fuska lameenu ya sake Yana Jin dadin Hakan Dan yasan aikin da Mam yasaka hannunsa da kansa aciki kaman cikan alkwarine Da Baya tashi cikar wannan aikin Dan haka ya sake murmusawa Dan shi a nasa bangaren ya gama yadda da indai akwai abinda Babbah ya sani gameda Omar da abinda ya Haifa to tabbas Omar Saiya taho wannan auren idan yaga Babbah a tareda su din.
****Da yamma a gidan Babbah Dad Lameenu yayi Sallah tareda su a masallaci bayan sun Dade suna tattauna maganar daurin auren ya bawa Ameenatou kyautan motan da ita aka taho gidan wadda ta tareda katin gayyatan da aka bugo na musamman me tsadan gaske.
Yan jaridan da BB ya turo sun dauko bayanan da yiwa motar hotuna da Kuma yiwa Babbah da Alh Lameenu din hotunan da suka fito da kyau.
Babbah Bai karbi motan ba ya Saka aka mayar akan bayan auren idan Ameenatou ta dawo hannunsu an Bata acan.
Dayake ba damuwa Daman sukai da lamarin ba Yana dawowa da ita aka ajiye kawai sedai a Daren aka hada labarin dasukeson a hada dauke da hoton Babbah Dana Dad Lameenu suna dariya cikin farin ciki dayake nuna shakuwansu da kusanci sosai.
Washe gari bayan Dad Lameenu din ya gama karantawa kallan fuskanta Babbah yayi wadda ta fito da kyau akan
"mahaifin Sirikitar Seelahs Mal Nuhu babbah ya nuna farin cikinsa da Jin dadinsa ga kyautan motar da sirikansa da kansu suka kawiwa yarsa har gida amatsayin tukuicin auren dansu"
Kai tsaye tareda invitation dinsu na musamman na auren da hoton dayake dauke da wainnan bayanan ya Saka aka yada kafin kace me labarin ya fara yaduwa har inda basa zato.
********
_Greece_
Dattijo ne Dan zaka zama confused akan shekarunsa and Hutu da wayayyar ilimin data gama ratsa rayuwansa Tako wanne Sako ya koma half bature kwatakwata.
Zaune yake a cikin lafiyayyar balcony din gidansa Mai tsananin yalwa da tsari irin na masu kudin gaske dayake Shan iska Yana sanye da farin glass Daya qarawa farar fuskansa kyau sosai da qara fitarda sirrin kyau da Kwanciyar hankalin da Allah ya wadacesa dashi yana karanta mahimman bayanai a Apple iPad datake hannunsa kafarsa Daya na kan Daya hakama gabansa table ne da laptop take Akai a Bude da alama itama wani sakon ya karanta kafin daga gefe qaramin tea cup ne Daya Sha coffee yabari a gurin.
Ahmed ne da Shima ya sauya sosai kaman wani lafiyayyan dattijon bakin bature Shima Hutu da kudi sun ratsashi ya iso gurinsa Kai tsaye da tasa iPad Shima a hannunsa.
Yana isowa kafin yace komai iPad din ya jiye a gaban Omar jeden Kai tsaye Yana cewa
"Ya kamata kaga abinda yake faruwa" ya nuna masa screen din iPad din.
Idanuwa Omar ya juya akan iPad din yana zare farin Glass din idanuwansa idonsa Kai tsaye akan fuskan Babbah da suketa azaban nema ya sauka a tareda Lameenu a gefensa suna dariya cikin farin ciki da shaquwa.
Hannuwansa Dake rawa ahankali yakai ya dauki iPad din a hannunsa Yana kafe hoton da ido kafin idanuwansa suka gangara akan abinda yake rubuce Wanda shine yake Saka Ahmed zufa da motsawan zuciya cikin tashin hankalin da Bai taba tinanin samun kansa ba.
Alh Omar Dayake Neman kasa gane komai saurin miqa hannu yayi Yana Neman ruwan Sha sbd yawunsa da suka qafe take.
****
SEELAHs sun shiga satin farin cikinsu Dan aikin project ya kammala an kaddamar
Fadan farin cikinsu Baya yiyuwa musamman Dad Lameenu dayake ganin sun tsallake rijiya da Baya Dan haka sune cikin farin ciki sosai.
Haroon sosai ya samu lambar yabo da karramawa tareda burge abokan huldodinsu da yawa ciki hadda turawa da yawa da suka yaba da aikin Dan haka take SEELAHs suka ringa samun manyan proposals masu zafin gaske Daya Saka su Jin duniya ta sake dawowa hannunsu Kuma a cikin satin suka samu sabuwar babbar Hulda daga Ashalawa wadda ta sake Saka kan Lameenu gigicewa shi Kuwa Mam a yanzu alfaharin gaske yakeyi da Haroon Wanda yake cikin farin ciki Shima sosai ya ringa Jin kaunar Dan uwansa na sake kere dukkanin abinda yakeso a rayuwarsa.
Dan haka a Lagos aka shirya hadaddiyar lafiyayyar dinner da aka barar da mahaukatan kudin gaske ta kammaluwan aikin.
Kusan duk wani babba dayaci ya tayar da Kai dayake mu'amalantar seelah ko sanatayya ya halarci dinner din wadda aka sakawa matakan tsaro da securities sosai.
Karfe goma Sha biyu da kusan Rabi aka gama dinner din wadda tsarinta yake na asalin Yan boko da masu kudin da muqami sai business tycoons kowa ya watse.
A daidai wannan lokacin da aka gama dinner din seelahs a wannan lokacin ne jirgin Omar jeden ya sauka a Abuja Nigeria.
#MAMUH#
*_ZAFAFA BIYAR_*
1 *_Ameenatou!!_*
_Mamuhgee_
2 *_Tsutsar Nama!!_*
_Billyn Abdull_
3 *_Gudun Kaddara!!_*
_Safiya huguma_
4 *_Kwankwason Jimina!!_*
_Miss xoxo_
Guda Daya 400
Guda biyu 700
Guda uku 1k
Guda hudun 1200
*_6019473875 MUSAA ABDULLAH SAFIYAH keystone bank_*
*_ATURA SHEDA ZUWA 09166221261_*
*_MTN/VTU 09134848107_*
_*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din 09033181070*_
*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_**_Arewabooks@Mamuhgee_*
47
Sabon drivern da suke tareda shi tin Baya Wanda dashi kadai Ahmed ya yadda yayi contacting Tin kafin zuwansu ayau din aka tanadi lafiyayyar motan da zata daukosu daga airport har Mansion dinsa Dayake jere Dana Yan uwan nasa.
Babu amfani ko kadan ga gujewa zama gidansa dayake hade da masu tinda abinda yafi so da kauna duniyarsa fiyeda komai ta riga ta shiga hannunsu Dan haka ya yanke shawaran tinkaransu kaman yanda suka tinkaresa Dan yasan Nemansa ne sukeyi Kai tsaye shiyasa suka bayyanawa duniya fuskan Babbah Dan ya Gani duk da baida tabbacin sun gane asalin waye 'yarinyar da suke Shirin aurawa dansu din Hakan yake son tabbatarwa Dan baida ikon kowanne irin motsin da zai Saka babynsa a hadarin da zai illata masa ita sbd a yanda aka kawo sauran kwanaki ne kadai suka ragewa auren bayajin Babbah zai fahimci abinda yake son ya fahimta Amma dai Kuma