Showing 39001 words to 42000 words out of 93806 words

Chapter 14 - Ameenatou Book Original Complete Book .txt

25 Nov 2024

4027

ya raba hankalinsa kan firar da Kuma Jamaal Wanda Bai iya furta ko kalma Daya ba Dan Yana cikin nasa tinanin daban.


Abinci mum Atee ta Aiko anan bangaren aka jere musu a dining din Jamaal ta Basu Daman cin abinci a tsakaninsu da 'yayansu.


Mum da kanta ta takurawa Jamaal cikin kulawa Mai tsananin gaske yasamu yaci abincin yasha ruwa yabar dining din and magrib datai.


Yana barin gurin mum ta bisa da kallo kafin ta dawo da kallanta kan Mam Dan karantar yanayinsa sbd ko kadan batason yasan me suka gano batareda sun fitar da fadilan waje ba.


Sallan magrib sukai suna gamawa Jamaal yabar gidan da motarsa.


Dad da Haroon ne tareda Dad Lameenu suka dawo ciki.
Kai tsaye office dinsu na gida suka nufa harda Haroon suna tattauna maganar wani aikin dayake hannunsa na fito da yaran BB da tsautsayi yasaka aka kama dayansu sbd wani aikin boyen da yayi musu.


Suna gama maganar dagowa Dad yayi ya Kalli Haroon Yana karantar yanayinsa tsawon mintina kafin yace


"Meyake faruwa ne da Jamaal Bayan gobe ne daurin aurensa??
Akwai wani matsalan ne Daya kamata na sani?
Menene yake faruwa?


Dad Lameenu ma zubawa Haroon idanuwansa yayi Yana kallansa Dan Jin Abinda yake faruwa da Basu saniba.


Dagowa Haroon yayi ya Kalli dad din Yana Jin jikinsa na sanyi,
Numfashi ya sauke ahankali kafin ya sake dagowa cikin sanyin murya yace


"Jikin fadila ne yayi tsanani sosai,
Mum ma ko bayan isowanta jiyan Saida ta dubata sosai karshe ma a asibiti suka kwana akanta Amma dai angano matsalar daga oxygen data amfani dashi yayi mata mummunan illa Kuma abin tashin hankalin shine oxygen da ita kadai take amfani dashi ne aka gurbata da wani abin Amma dai mum tana kan binciken zasu gane Menene"


Dad Lameenu wani numfashi ya hadiye ya koma masa ciki kafin ya Dan juya ya Kalli Mam Wanda Babu abinda yayi
kafin yayi wata magana Mam din ya rigasa da Bude Baki a natse yace


"To shi Jamaal din yasan da Hakan?
Yasan me sakamakon ya bayar?


"No sai sauran results din sun Hadu zuwa gobe mum zata sanar masa"


Wani sanyayyar numfashi Mai hade da bayyanarda alhini da tausayi Dad Lameenu ya sake
Shikuwa Mam har lokacin Bai nuna kowanne irin yanayi ba sai shiru da yayi kafin ya sauke karamin numfashi Yana Mata fatan samun lafiya ya sallami Haroon din ya fice yabarsu.


Tinda ya fita babu Wanda yayi magana a cikinsu sbd zuwa yanzu da suka manyanta kowa yagama sanin tinanin da kowa keyi a kowanne lokaci wani abin ya taso.




Jamaal Bai dawo gida ba sai dare sosai bayan ya baro gidansu fadila jikinsa a matiqar mace Dan yau fadilan da kanta take kuka tana rokon ya mata alluran da zata rasa hankalinta Dan ta Dena Jin Abinda takeji zuwa safe.


Iyayenta kuka sukeyi da Hawaye a gabansa na tausayinta
Duk wata karfin zuciyarsa Saida kukan fadilan ya karya masa shi.


A goben da zaa daura masa aure da ita a goben Inshallah zasu bar kasar sbd komai na tafiyan ya kammala goben ne ranar tafiya.


Mum dinsa ma jikinta mutuwa tayi da yanayinsa Dan haka Bata takurasa sosai ba akan abinci,ice tea ta hada masa kadai ya Sha ya shige bedroom dinsa.


Wanka yayi ya kwanta Kai tsaye Yana rufe idanuwansa wani nauyi na karuwa a zuciyarsa.


Karfe uku na tsakar dare Haroon ya fito daga bangarensa cikin tashin hankali da damuwa me tsananin gaske ya nufo part din Jamaal da wayarsa a hannu yayi knocking.


Knocking yakeyi sosai Amma Sam Babu alaman ma suna jinsa Dan haka ya cikin tashin hankalinsa Dake karuwa ya Kalli wayarsa Dake sake ringing Kiran siddeeq Yana shigowa..


Juyawa yayi kawai da sauri ya koma dakinsa cikin gaggawa da rawar jiki ya Dora jacket babba akan sweatset din Dake jikinsa ya zari keys din motarsa ya fito.


Baiyi wata wata ba ya fada motan ya tayar cikin zafi yayi wani mugun horn dashine ya tayar da Dad dinsu da shi kansa Jamaal din harma da mum dukkaninsu a tare suka tashi zaune suna sake Jin horn din a kunnensu sosai.


Time kowannensu ya kalla cikin mamaki Mai girman gaske.


Ziro kafafunsa daga gadon Jamaal yayi tareda saukowa Yana nufar window na dakinsa ya ware curtain Yana kallan harabar gidan daidai motar Haroon din na ficewa daga gidan cikin wani irin gudu me zafin gaske.


Sakin curtain din yayi cikin tsananin mamaki tareda juyowa Yana ziro slippers a kafafunsa Shima jacket din ya Sako kan kayan baccin jikinsa ya fito Palo Kai tsaye Yana nufar kofar ficewa daidai Nan mum itama ta fito tana cewa


"Lafiya kuwa?
Meyake faruwa?


Batareda ya juyowa ba yace ta koma daki zai dubo meyake faruwa.


Yana fitowa harabar gidan Dad ma Yana fitowa cikin mamaki da shakkar abinda ya fidda Haroon a lokacin.


Securities din gidan ma duka suna tsaye a harabar gidan


Dad da mamaki yace


"Meyake faruwa?
Waye ya fita da motan Haroon din?


Jamaal kuwa Yana isowa Kai tsaye yace


"Wats going on here?"
Waye ya fita?
Ina Haroon?


Daya daga cikin securities dinne ya Kalli Dad yace


"Sir,sir Haroon ne ya fita Amma security Daya yabisa sbd dare ne sosai Kuma baima tsaya mukasan meye matsalan ba ya....


Jamaal da kallo Daya yayiwa gate din da Haroon ya fice Bai tsaya Jin sauran zancen ba ya juya ya koma Kai tsaye key ya dauko da wayarsa Daya kunna Yana kokarin Kiran numbern Haroon.


Dad na ganin fitowansa da key cikin mamaki da tashin hankali yace Maza securities su janyo mota su bisa Dan bazai bari yayansa duka biyu su fice a Daren ba batareda yasan meyake faruwa ba da rashin tsaro.


Mum ma hankalinta tashi yayi mummunan yi da sauri ta dauro jallabiya me girma akan kayanta ta fito Amma Jamaal yace kada Dad yabari ta biyosa.


Daukan wayar Haroon yayi daidai da isar Jamaal motarsa cikin murya Mai sautin Kai tsaye yace


"Meyake faruwa?
Meyasa zaka fita a wannan time din?
Bazaka iya sanar da kowaba kafin ka fita?
Ganinan fadamun inda kake kawai...


Shiru yayi tareda dakatawa daga Bude motan dayake kokarin yi maganar da Haroon din ke fada cewan gobara ne sosai ya kama gidansu fadila.


Wani mummunan jiri ne Mai qarfi sosai ya debesa yayi saurin daga motar
Mum ma da saurin gaske ta qaraso gurinsa itada dad tana tambayarsa Menene Amma Sam Bai ya cewa komaiba sai idanuwansa da suka sauya take ya dago ya zuba mata Saida gabanta yayi mummunan faduwa.
#MAMUH#
AMEENATOU
#ZAFIN KAI


*_ZAFAFA BIYAR_*


1 *_Ameenatou!!_*
_Mamuhgee_


2 *_Tsutsar Nama!!_*
_Billyn Abdull_


3 *_Gudun Kaddara!!_*
_Safiya huguma_


4 *_Kwankwason Jimina!!_*
_Miss xoxo_


Guda Daya 400
Guda biyu 700
Guda uku 1k
Guda hudun 1200


*_6019473875 MUSAA ABDULLAH SAFIYAH keystone bank_*


*_ATURA SHEDA ZUWA 09166221261_*


*_MTN/VTU 09134848107_*


_*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din 09033181070*_


*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_**_Arewabooks@Mamuhgee_*
25
Dad na ganin Hakan yayi saurin kallan Abdul Yana cewa Maza a fiddo mota a biyo bayansu da ita sbd yasan koma ya cewa Jamaal yayi zamansa ba zaman zeyiba Dan haka ya koma ciki Ya Sako jallabiya doguwa fara kal ya fito.


Koda ya fito tini Jamaal yabar gidan Dan haka Kai tsaye shi da mum da securities suka mara masa Baya zuciyarsa na nauyi da fatan kada komai ya samu 'yayansa a cikin wannan sililin Daren ace sun fita Babu Wanda yake tareda jamian tsaron lafiyarsa a cikinsu har gwara Haroon ance security Daya ya bisa
To Jamaal fa¿.


Mum kuwa duk a tsorace take ma kwata kwata sbd tsoron idan ba wani abin ne ya faru ba me girma ko zai faru,
Koma dai Menene itadai fatanta Allah ya tsare mata 'yayanta ya Basu kariya da kaucewa musiba da masifa kowace iri.


Dad daya kasa tantancewa ko canko Menene yake faruwa shiru yayi Yana fatan Isa ga yayansa cikin gaggawa kafin kome zai farun ya faru tukuna...


Bayan motar Jamaal suke hangowa Yana gudu sosai Wanda ya Saka jinin Dad fara Hawa Yana Jin zuciyarsa na wani irin tsalle da rawar tashin hankali Dan kuwa Jin yayi kaman zuciyarsa ne a cikin motar Jamaal din ana wannan gudun da ita.


Mum kuwa idanuwanta a rufe ma suke tana Jin alamun itama BP dinta ya haye sama a take.


Hanyar gidansu fadila da suka nufa ya Saka Dad Jin wani irin Abu me nauyi Yana saukowa daga maqoshinsa zuwa kirjinsa sbd ya tabbatarda idan ba ciwonta yayi ajalinta ba to tabbas lameenu ya aika su BB rufe aikin kwata kwata kafin asanar da Jamaal sakamakon Wanda Shima akwai tanadin da yayiwa Hakan Amma a cikin sanyi da cike aiki take batareda barin kowace alama ba.


Tin daga nesa wutar Dake cin gidan sosai suke ganinta
Take jikin mum ya dauki rawa hawayen tashin hankali na ciko idanuwanta sbd Jamaal kada yace zai shiga gidan.


Dad da Shima dukkanin jikinsa ke cirewa sbd wannan tsoron tini yace ayi parking cikin daga murya.


Ko gama parking baayiba Dad ya Bude motan ya fito yayi gurin Jamaal da sauri Yana Kiran sunansa hankalinsa tashe sedai Jamaal din Baya jin komai fadila kawai dayake buqatan Gani a hannuwansa.


Haroon da siddeeq ne suka hango zuwansa da gudu Haroon yayo gurinsa ya tareda tareda rungumesa sosai daidai isowan Dad idanuwansa kaman zasu fado sbd tashin hankali da sauri ya rungume Jamaal din ta Baya Shima Yana Jin zufa na tsinko masa.


Jamaal zare jikinsa yakeson yi Amma sun masa wata irin kyakkyawar runguma Haroon na cewa


"Fadila is safe siddeeq ya fito da ita"


Wannan kalaman ne suka Saka Jamaal din jikinsa ya saki tsawon minti Daya kafin ya dago idanuwansa jajir Yana buqatan ganin fadilan.


Ambulance ta asibitinsu ce ta iso cikin gaggawa aka dauki Fadila wadda batasan Ina kanta yake ba tareda umma wadda itama take a sume sbd hayaqin Daya bugeta.


Motan kashe gobara ce itama ta iso daidai lokacin sukuma suka bar gurin zuwa asibiti cikin gaggawa.


Siddeeq barinsa Akai tareda mutane da masu kashe gobara harma da Police da suka iso gurin cikin tashin hankali sbd baba Dake cikin gidan baa fiddosa ba,


Mum asibiti suka marawa su Jamaal Baya itada da Dad Wanda yakejin Yana dawowa hayyacinsa daidai sbd barin yayansa gurin Dan motan Haroon ne bayan ambulance din sukuma suna bin tasa motar.


Ana Isa asibiti cikin gaggawa likitoci suka amshi fadila da umma aka shige emergency dasu
Haroon kuwa da Dad Jamaal din suka zauna tareda dashi Dan basa karfin gwiwa.


Mum da ita aka shiga emergency din Dan taimakon gaggawa fadilan take buqata sbd Bata tareda oxygen nata tini ya fizge yana can.


Zaman jiran tsammani me azabar gaske sukeyi dukkaninsu tin daga Jamaal din har Dad da Haroon,


Haroon sai Kai da kawo yakeyi Yana Jin kaman ya yayewa Dan uwansa abinda yake ji.


Sai asuba likitocin suka samu shawo kan fizgo numfashin fadila aka Saka mata wani oxygen din bayan mum ta tantancesa.


Umma kuwa Daman tini ta farfado Dan Daman hayaqi ne ya sumar da ita Amma dayake mijinta da yarta ne a ranta tini ta farko cikin sanyin jiki da fargaban baba da akace Yana can tareda siddeeq ita Kuma fadila tana asibitin tareda ita.


Dad da mum ne suka koma gida bayan sallan asuba suka bar Haroon tareda Dan uwansa.


Suma bayan sallan asuba dubo fadilan yai suka dawo office dinsa anan yayi shiru Yana tinanin yanda zasuyi su sanar da umma gawar baba na asibitin.


Siddeeq ya kalla cikeda kulawa da tausayawa Dan Shima maraya ne gaba da Baya su baba dinne gatansa danginsa yanzu baba ya rasu.


Har karfe tara na safe suna asibitin Kuma Basu sanar da umma komai ba sai guraren goma suka taho dakin datake Jamaal ne Kai tsaye ya sanar da ita rasuwan baban cikin dacin zuciya da tausayi me tsanani.


Numfashi ta sauke ahankali me zafin gaske batareda ta motsa ba sbd jikinta ya Bata Hakan Kuma zuciyarta tini ta amsa Hakan ta karbi jarumta.


Dago jajayen idanuwanta dasukai jajir tayi ta Kalli siddeeq Dake Hawaye sosai zuciyarsa na tarwatsewa.


Cikin karfin hali ta Bude Baki ahankali tace


"Haka Allah ya kaddaro Kuma na amsa wannan hukuncin na ubangiji,Allah yaji qansa yayi masa Rahama ya bamu danganar rashinsa."


"Amin" dukkaninsu suka furta cikin damuwa da sanyin jiki.


Karfe goma da Rabi Akai janazah dinsa aka rufesa suka dawo.


Kaman yanda yake ayau din zaa daura aurensa da fadila baa daga ba Dan haka bayan karfe biyu na Rana aka halarci masallacin da zaa daura musu aure.


Cikin fararen kayanda suka bayyanarda kamanninsu sosai shida Haroon suka fito tareda mahaifinsu Wanda Shima fararen kayan ne a jikinsa irin na 'yayansa Wanda aka zuba kudi kaman baa San darajansu ba aka Siya kayan aka Dinka.


Qamshinsa daban yake Dana kowa Dan haka take qamshinsa ya doke nasu nasa kadai ake ji Kuma a Hakan cikin Baya tattareda walwala ko Daya sbd halinda matarsa take ciki duk da haka kawai saukin da Basu tsammata ba yazo mata da safen duk da batada karfi ko kadan har lokacin Amma ta Bude idanuwanta sosai tayi magana dashi tareda nuna masa ta samu karfinda inshallah zata iya adon aurensu da zaayi a yau din.


Karfe biyu daidai Aka daura masa aure da Fadila kaman yanda yake buri da fata ta tabbata cikakkiyar hankalinsa,matar Dr Jamaal Mamman seelah.


Bayan daurin auren Yan jarida da media da ba'ama San ya Akai suka sani ba suka karaso gurin sedai kafin su samu Daman daukan hotinansa yabar gurin batareda ya tsaya komaiba sedai Haroon ne ya tsaya a amatsayin Jamaal din yana miqa godiyarsa ga wainda suka halarta Yana amsa adduoinsu batareda ansan bashi a gurin ba Dan hatta su Dad din Basu dauka Haroon bane Jamaal ya tafi.


Siddeeq ne yake Jan motar Jamaal din har suka Isa asibiti zuciyarsa wani fayau yake jinta jikinsa na sanyi kalau batareda yasan wane irin yanayi ne yakeji a jikinsa ba.


Suna Isa asibitin kusan dukkanin wani likitan Dake asibitin Yana dakin fadila cikin tashin hankali da gaggawan cetan ranta kowa na nuna kwarewansa Dan sanin mahimmancinta Mai tsananin girma ga Dr Jamaal din.


Hatta mum dinsa tana dakin cikin nuna kwarewanta da son cetan ran sirikitarta wadda rashinta zai taba rayuwar danta fiyeda yanda suke tinani.


Ganin umma zaune bakin dakin idanuwanta jajir dukkanin jikinta a Sanyaye zuciyarta tayi wani irin nauyi da kirjinta ke Neman kasa dauka.


Dakatawa yayi cak bakin Kofar dakin ganin yanda nurses ke fitowa da gudu suna komawa cikin bawa abinda sukeyi mahimmanci me girma.


Siddeeq ma kasa motsawa yayi daga inda yake tsaye zuciyarsa na bugawa da karfi ya juya Ina Dr Jamaal din yake ya kallesa da jajayen idanuwansa Dake sauyawa da fargaban abinda suka tarar.




Kasa motsawa Dr Jamaal din yayi tsawon mintina biyu Yana Jin dukkanin wani sanyi na gauraye gangar jikinsa kafin ya daga kafafunsa ahankali ya Isa kofar dakin ya Bude ya shiga daidai kunnuwansa na dauko sautin maganar Dr zayyan.


"Time of Dead 3:06"


Innalillahi wainna ilaihirrajiun" shine abinda mum ta fada jikinta a matiqar Sanyaye zuciyarta na shiga wani irin sanyi da mutuwar jiki me tsananin gaske.


Sauran likitocin ma gaba Daya jikinsu sanyi yayi musulman ciki suna ambatar


"innalillahi wainna ilaihirrajiun da allahu Akbar"


Kafiran ciki kuwa tausayinta Dana Dr Jamaal ne yake rufesu sbd tasha wuya sosai itama a iyama lokacinda ta fara zuwa asibitin kadai bare rayuwarta ta Baya.


Ficewa likitocin suka fara ganin Dr Jamaal din a tsaye bayan sun rufeta har fuska sun gama rubuta komai a file dinta anyi signing anrufe an ajiye a gefe shikenan ita ta huta da gwagwarmayar duniya.


Mum dinsa ce kadai ta rage ta tako ahankali batareda ta iya cewa komaiba sai hawayen Daya ciko idanuwanta Yana gangarowa ta rungumesa ahankali cikin mutuwar jiki tana basa hakuri hawayenta na Kara gudu.


Fashewan kukan umma me sautin daya sake karya zuciyar kowa ne ya sauka cikin kunnuwansa take ya rintse idanuwansa dasukai wani mummunan ja yanajin dukkanin zuciyarsa na kakkaryewa tana watsewa.


Siddeeq ne ya rungume umma Yana tarota jikinsa sbd kukan datakeyi hadda na mijinta data rasa a ranar kukan Bai fitoba sai yanzu data rasa yarta taji abinda ya dunkule a zuciyarta ya fashe mata.


Wani irin kuka me cin Rai da qunci me tsanani takeyi sautinsa na karya dukkanin zuciyoyin sauran likitoci da Jamaar Dake gurin Amma Babu me iya cewa komai sbd tana buqatan yin kukan.


A ciki ma mum ce keyiwa Jamaal din kukan dashi zuciyarsa Bazata iyaba sbd Jin ma yakeyi baida sauran emotions kwata kwata bayajin komai face dutse a zuciyarsa.


Labarin na Isa gurinsu Dad da Haroon gabaki dayansu asibitin suka dungumo cikin tashin hankali musamman Haroon Dan kuwa JAMAAL ne a ransa,
Jin yakeyi rasuwar fadilan Shima tana gigita kansa da nutsuwansa dan haka a rikice ko Gani sosai bayayi suka iso asibitin.
##MAMUH




*_ZAFAFA BIYAR_*


1 *_Ameenatou!!_*
_Mamuhgee_


2 *_Tsutsar Nama!!_*
_Billyn Abdull_


3 *_Gudun Kaddara!!_*
_Safiya huguma_


4 *_Kwankwason Jimina!!_*
_Miss xoxo_


Guda Daya 400
Guda biyu 700
Guda uku 1k
Guda hudun 1200


*_6019473875 MUSAA ABDULLAH SAFIYAH keystone bank_*


*_ATURA SHEDA ZUWA 09166221261_*


*_MTN/VTU 09134848107_*


_*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din 09033181070*_


*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_**_Arewabooks@Mamuhgee_*
26
Shi kansa Dad da Dad Lameenu cikin damuwan halinda Jamaal yake ciki suke,
Mum Atee da Ayesha ma tini suka iso motansu mummy Sarat na bayan tasu Dan haka take asibitin ya cika da familyn seelahs cikin damuwa da tashin hankalin yau wace irin Rana ce?
Mahaifinta ya rasu yau,
An daura mata aure yau itama ta rasu a yau din.


Haroon na isowa kallo Daya yayiwa Dan uwansa yaji idanuwansa sun ciko da Hawaye masu tsananin zafin gaske suna gangarowa ya rungume Jamaal din.


Dad ma na isowa rungumesa yayi Yana kallan mum Dake hawaye sosai sbd tausayin fadilan da wuyar datasha tareda tausayin danta Dan shine yake cikin azabar zuciya yanzu me tsanani ta sani.


Dakin gawar suka bari suka koma office dinsa gaba dayansu familyn kowa fuskansa Babu dadi Dan tausaya masa bisa ba rashin dayayi Dan kuwa Babu Wanda Bai tabbatarda irin so da matsayin da fadila take dashi a rayuwarsaba.


Umma siddeeq ne kadai a tareda ita sai mum data koma gurinsu daga baya Dan ummanma itace abar tausayi fiyeda kowa Dan itace tayi rashinda sai me karfin Imani ne zaiyisa Rana Daya Bai zauce ba.


Ganin Halinda umman ke kokarin shiga ya Saka mum Bada umarnin a kwantar da ita cikin gaggawa Dan taimaka mata.
Bayan an kwantar da umman harma anyi mata allurai da wasu abubuwan an samu tayi bacci ta baro gurinta ta dawo gurin Jamaal Daya kebe kansa a dakin dayake cikin lafiyayyar office dinsa ta fara kokarin yi masa nasiha da basa karfin gwiwan bawa zuciyarsa hakuri.


Gida kowa ya koma sbd Shirin janazah dinta wadda zaayi a Seelahs din bisa ga umarnin Dad tinda ta riga ta zama matar dansa.


Kafin lokacin yayi Yan uwan umman su uku tini suka iso daga garinsu mata biyu namiji

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login