Showing 87001 words to 90000 words out of 93806 words

Chapter 30 - Ameenatou Book Original Complete Book .txt

25 Nov 2024

4037

masa ya zuba masa take suka wuce maqoshinsa.


Suna shiga kafin ma su fara aiki BB ya bari fuskansa da karfi tareda tayar dashi zaune duk da jikinsa asake yake Babu abinda yake Aiko a jikinsa.


Cikin tsananin mawuyacin halin da ko mara Imani Saiya zubar masa da Hawaye ya Bude bakinsa kansa na masa wani hayaqin masifa da balai yafara jijjiga Yana cewa


"Ameenatou itace 'yarka Dad Omar, Dad Omar ka auramun Ameenatou sbd mutuwa zanyi idan na rasata, Ameenatou bazan taba barin kowa yasan itace 'yar da ake nemaba ko da Hakan zaiyi sanadin Raina Dad Omar,
Babbah ku bani Ameenatou,
Jamaal ku bani Ameenatou,
Dad Omar ka taimakeni ka cika mun burin auren Ameenatou.......""


Sakinsa BB yayi tareda ja Baya da tsananin karfi jikinsa na daukan wani rawa da tashin hankalin da Bai taba tinanin shiga ba sbd Jin Abinda Haroon ke fada,


Shi kansa Lameenu Baya yayi da sauri Saida killer ya tarosa sbd firgici da shock din abinda yaji din.


Haroon kuwa sanqarewa yakeyi jini na fitowa bakinsa da hancinsa sosai sedai Bai Dena magana ba hakama jikinsa Bai Dena jijjiga ba.


Da sauri cikin masifaffen tashin hankali da tsoron abinda yake Gani da Wanda yaji Dad Lameenu ya Kalli BB Yana cewa suyi sauri su gogewa Haroon din jinin su mayar dashi inda zaa samesa kada ya mutu a hannunsu.


Suma Dake cikin tashin hankali sake shiga sabon tashin hankalin sukai sbd sanin waye Mam idan 'dansa ya mutu a hannunsu Dan haka ba Bata lokaci suka daukesa suka Kai mota
Kusan motarsu data Lameenu a tare suka fice su sukabi wata hanyar Shima yabi wata.


Tafiya sukeyi suna gudu sosai suna kallan Haroon din Wanda yake zubarda jini sosai har lokacin cikin mafi tsananin azabar rayuwarsa da Bai taba jiba.


Tafiya me tsayi sukai kafin suka Isa inda BB din ya daukosa suka ajiyesa agurin suka gudu batareda kowa ya gansu ba.


Suna barin gurin motar siddeeq da shima ya shiga layin masu tsananin Neman Haroon din sbd zautuwan da Jamaal ke Neman yi gurin Nemansa Yana Sako Kai a layin Dan sake dubawa sai gashi kuwa yayi mummunan Gani Dan halinda ya samu Haroon din saura kadan ya buga zuciyarsa,


Bazai iya barin Jamaal ya gansa a wannan mummunan halinba Dan haka hankali tashe ya daukesa tsaban shiga rikici Kai tsaye Mansion din ya nufa dashi sedai Yan Isa ganin abin yayi muni Dad ya nema Kai tsaye sbd shi kansa jijjiga jikinsa yakeyi tsaban tashin hankali.


Mam na fitowa kallo Daya yayiwa Haroon ya Yanke jiki ya Fadi sbd zuciyarsa data buga irin bugun da zai iya kamuwa da shanyewan Rabin jiki mum Atee ce tayi saurin rikesa itama jikinta na daukan rawar tsoro da firgita sbd ganin abinda yafi karfin nata rashin Imanin.


Daukansa Akai aka nufi ciki dashi Kai tsaye bangarensa Akai dashi zuwa lokacin jikinsa sake sanqarewa yakeyi Dan haka suna Isa Kai tsaye toilet siddeeq ya wuce dashi ya Saka a bathtub din dayake cike da ruwan sanyi.


Dad kasa tsayuwa yayi ya qarasa gurin Haroon din dayake sanqare acikin ruwan jini har lokacin Yana fitowa ta hancinsa.


Wani irin kukan da baisan yanada shi bane ya fashewa Dad din Yana ihun ambatar Haroon din daidai Nan Lameenu yashigo Shima kafafunsa na rawar tashin hankali da tsoron abinda zai iya biyo Baya.


Kamo Haroon din yayi Shima Yana ambatar sunansa sedai Haroon Babu abinda yake ji a lokacin.


Sosai jinin yake sake gudu Wanda ya Saka siddeeq kasa riqe kansa ya kira Jamaal Wanda yaketa bulayi a titin Lagos Yana Neman Haroon din Yanajin abinda siddeeq ya fada Kai tsaye ya juyo motarsa kaman zai tashi sama yayo mansion din.


Isowansa yayi daidai da wani tarin jinin gaske da Haroon ya feso daga bakinsa Mai yawa jikinsa na qarasa sakewa gaba Daya a jikin Dad Wanda yake rungume da Haroon din qamqam Yana Jin Abinda Bai taba ji ba na ganin zaka rasa Wanda kake tsananin so da dukkanin rayuwarka.


Ganin Dan uwansa ya Saka Jamaal karasawa kafafunsa na Neman sarewa hakama zuciyarsa koina yankewa yaji tana yi.


Dad Lameenu da sauri ya janye daga Haroon din ya bawa Jamaal guri.


Hannuwansa duka biyu yakai cikin ruwan ya kamo Dan uwansa Yana fitowa dashi sbd gaba Daya jikinsa ya lalace da jini
Bai tsaya komaiba ficewa yayi dashi daga dakin ya fita dashi Dad Wanda ya kasa motsawa daga inda yake tsaban mutuwan dayakejin duka jikinsa yayi Babu inda ke motsuwa mum Atee ce ta kamasa suka fito suma suka marawa Jamaal din Baya.


Asibiti Jamaal ya nufa dashi cikin gaggawa aka karbesa sedai hadda Jamaal din aka shiga sbd samun damun tsayar da jininsa da ya zube sosai Dan take jininsa ya fara yin qasa.


Dayake da yawan manyan doctors din asibitin sunsan Dr Jamaal Seelah din baa hanasa shigaba Dan shine ya tsayar da jinin sedai ana buqatan jinin sakawa Jamaal din da gaggawa take ya kwanta aka fara diban nasa ana sakawa haroon din Wanda ya koma daidai sedai Babu inda yake motsi a jikinsa yayi fari fayau a cikin kankanin lokaci ya koma abin tausayin da zaka dauka shekarunsa ashirin a kwance.


A waje kuwa Dad da mum Atee da siddeeq ne sai Dad Lameenu da mummy Sarat duka tsit gurin ya dauka bayan Kaida kawo Babu abinda siddeeq keyi su kuwa Dad aketa Neman Kiran likita ya dubasa sbd jininsa yayi mummunan hawan dayake buqatan maganin gaggawa Shima.
#MAMUH




*_ZAFAFA BIYAR_*


1 *_Ameenatou!!_*
_Mamuhgee_


2 *_Tsutsar Nama!!_*
_Billyn Abdull_


3 *_Gudun Kaddara!!_*
_Safiya huguma_


4 *_Kwankwason Jimina!!_*
_Miss xoxo_


Guda Daya 400
Guda biyu 700
Guda uku 1k
Guda hudun 1200


*_6019473875 MUSAA ABDULLAH SAFIYAH keystone bank_*


*_ATURA SHEDA ZUWA 09166221261_*


*_MTN/VTU 09134848107_*


_*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din 09033181070*_


*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_**_AMEENATOUH_*
_Mamuhgee_
#Arewabooks@Mamuhgee
#ZafafaBoyar






55


Dad Omar ma tin kafin a ga Haroon din jininsa yahau Shima har yana Naman zubewa dole Ahmed ya dawo dashi gida Shima aka Nemo likita.


Babbah ma a gida likitan aka Nemo sbd take ya rafke zuciya na ciwo sosai hankalin nasa Iyalin yayi mummunan tashi.




A cikin Daren abubuwa da yawa sun faru marasa dadi da tashin hankali tareda Saka hawan jinin mutane da dama,


Sai guraren asuba Haroon ya farka sedai cikin yanayin Daya Sakasa tsiyayo da Hawaye masu zafin gaske Yana kallan Dan uwansa Dake gabansa zaune Yana kallansa idanuwansa jajir
Ko baa fada ba yasan irin radadin dayake zuciyar JAMAAL bamai faduwa ne ba,


Wani numfashi Mai dumi ya sauke ahankali hawayen cikin idonsa na gangarowa yanason magana Amma ya kasa sbd baisan me zai fada ba,


Abu uku zuciyarsa a yanzu kadai take so sbd samun sanyin da sassaucin azaban dayake ji na cin jininsa,


Ganin mahaifiyarsa,ganin Ameenatou da Kuma Jamaal din Wanda shi gashinan a gabansa.


Ahankali ya Bude bakinsa cikin sanyi da karfin hali yace


"Nagode"


Sukan Jamaal kalmar tayi Dan haka ya miqe tsaye Yana kokarin danne tausayi da tsinkewan da zuciyarsa keyi tareda nauyin dayake ji a kirjinsa yace


"Ka manta yau daurin aurenka???


Murmushi Haroon din yayi Mai sanyi kafin yace


"Ban manta ba shiyasa nayi Maka Godia.


Magana yakeson yi Amma bazai iya ba sbd hakanan zuciyarsa da bakinsa basa son furta komai bayan idanuwansa Daya zubawa Jamaal din Yana kallansa jikinsa na mutuwa hakama idanuwansa sunyi jajir.


Shima Jamaal Jin yayi bakinsa da zuciyarsa sunyi nauyi sosai bazai iya cewa komaiba bayan yin shiru suna sauraron numfashin junansu.




*******Mam a cikin Daren Lameenu daya kasa zama ya kasa tsayi yasaka BB ya kawo musu rahoton abinda yake Neman zautashi tinda yaji a bakin Haroon.


BB a cikin asibitin ya sanar da Mam wacece 'yar Omar Jaden da Kuma alaqarsa da Babbah akan cewa shine da kunnensa yaji lokacinda ya bisu.


BB na gama fada Lameenu ya sauke ajiyan zuciyarsa Dake cikin balai da masifa tinda yaji zancen shi kadai,


Maganar da farko kaman a mafarki Mam ya jita Saida ya dago idanuwansa da sukai jajir ya Kalli BB
BB din ya jinjin masa Kai alamar haka zancen yake.


Da hannu Mam yayi musu alama dasu kira masa likita numfashinsa tsayawa zaiyi.


Da sauri BB ya fice ya kirawo likita Wanda y dawo dakin tareda Mum Atee da itama tana asibitin Taki tafiya.


Tsaban tashin hankalin firgitan da Mam yayi Saida aka Saka masa oxygen na wucen gadi daqyar yakai asuba sbd tinane tinane da sakawa da warwarewa.


Asubar fari yaji dukkanin ciwonsa dayake ji a jikinsa ya warke,
Bai taba sanin Kowane 'da da baiwar da Allah yayi masa ba da kalan arzikinsa sai yanzu,


Haroon ayau ya tabbatar masa da Hakan sbd zai basa abinda yayi shekaru Yana nema tin kafin ya Saka ran haihuwarsuba,
Bai taba Saka ran duk wannan tashin hankalin da sukaita fama dashina karshen dukiyar Omar a gidansa zata dawo,
Wannan auren shine babbar taskar arzikinsa Daya Dade Yana kashe kashe gurin mallaka,
Wannan auren da yace bazaiyiba ayau Yana tabbatarwa kansa idan baayi auren Nan ba to shine Baya raye Amma wallahi tallahi Babu Wanda zai Hana auren Nan dauruwa ayau kaman yanda ayau din Omar Zai bar duniyar dukiyar tashiga hannunsa da dalili....


Lameenu da Mam din ya Sakasa zuwa asibiti gurinsa tin asubar fari gama tattaunawa sukai inda kansa ya shiga wani zafi da duhu ya shiga lissafin abinda zai faru Idan auren ya tabbata.


Wannan auren idan anyi sa Ameenatou Jden ta zama matar Haroon sirikar Mam ayau Kuma idan Omar ya mutu gadonta na dukiyarsa gaba Daya zata zama a karkashin mijinta wanda dukiyar gaban dayanta zata koma ne akan yanzu gadon sirikar Mam ce ba tasu ba da zasu mallake su Raba tsakaninsu.


Jin yayi kansa na Neman kuncewa da lissafi Amma Kuma ko yayane su Raba Omar din da duniyar tukuna zasu fuskanci juna shida Mam din akan dukiyar sbd tabbas dole kasonsu me tsoka Yana cikinta.




Mam ne ya shiga dakin da Haroon yake kwance sedai idanuwansa biyu har lokacin shida Jamaal Babu me magana sai da Dad din ya shigo Jamaal ya fice ya basu guri dad din ya Kalli Haroon Wanda Shima Haroon din shi ya kalla Yana Jin tausayin mahaifin nasa akan rayuwar Daya samu kansa Dan haka yake Jin inama zai iya sauya Dad din dayayi Hakan.


Sunansa Dad ya ambata cikeda kulawa da farin ciki shimfide a fuskansa Yace


"Haroon Allah ya albarkaci rayuwar da zaka fara daga yau dinnan har ranar tashin qiyama,
Allah ya haskaka zuciyarka yanda ka haskaka tawa,
Allah yayi Maka kyakkyawar karshe ya albarkaci zuriar da zaka Haifa."


Hawaye ne kawai suka silalo daga idanuwan Haroon sbd Bai taba samun wannan kyakkyawar adduar Mai dadin sauraro daga mahaifin nasa ba Dan haka ya rintse idanuwansa jikinsa gaba Daya na yin sanyi da mutuwa ahankali ya Bude bakinsa cikin kaunar Dad dinsa da har lokacin yakeji yace


"Amin Dad nagode Allah ya Saka da Khairan,
Allah ya tsarkake Maka zuciyarka ya wanketa Dad ya Kuma baka ikon gyarawa da tubar masa"




Shima Dad din cikin farin ciki da tsananin kaunar dansa yace "Ameen Haroon"


Jamaal ne ya dawo dakin daukeda takardun Haroon din Daya karbo dasu zai tafi akwai binciken da zaiyi akansu.


Duk da rashin karfi dayake jikin Haroon din hakanan Jamaal ya daukesa daga asibiti sbd bazai taba barin a daga daurin auren ba daga ranar sbd hakanan a yanzu zuciyarsa tafi ta Haroon cika da tsoron Da baisan na Menene ba Idan ba ganin yayi igiyan auren Haroon din sun rataya akan Ameenatou ba.


Dad ma bayajin akwai abinda zai Hana wannan auren ayanzu Dan haka gida suka dawo kowa na kokarin fara Shirin daurin auren Wanda zaayi da karfe goma Sha Daya na rana.


Dad Omar ma hankalinsa kwantawa yayi Daya samu tabbacin su Mam Basu ma samu damar magana da Haroon ba tin jiyan Dan haka yasan sirrinsu Bai fita ba Dan haka ya kira Babbah Wanda Shima yake a tsinke tini ya sake yafara Shirin daurin auren shi dasu Hafiz da zuciyoyinsu suke cikin farin ciki Mai tsananin gaske.


Amarya Ameenatou kuwa da batai waya da Haroon ba sai da safen Jin tayi kaman yayi mata caji Dan haka ta sake daga sanyin jikin datake fama dashi yin jiyan zuciyarta da kirjinta na nauyi.
Dan haka ta sake Wainda suka taho shirinta ta Basu Daman shigowa inda take Dan fara shiryata sbd daurin auren ma ya kusa ga gidan nasu a cike yake sosai da Yan bikin gashi Babbah yace bayan daurin auren zai sanar da ita abinda Bai taba sanar da ita ba Mai tsananin mahimmanci Dan haka duk ta sake zaquwa da ayi daurin auren ta zama ta Haroon ya zama nata.
Wannan tinanin kadai sake narkar da zuciyarta yakeji cikin farin ciki Mai sanyin gaske.




******A yanzu kusan dukkanin seelah Babu Wanda tin daga zuciyarsa yake cikin tsananin farin ciki da wannan auren ba Dan haka sosai ake cikin annuwan gaske Dan haka tini suka kammala nufinsu da komai akan Omar Wanda Shima yake cikin nutsuwa da farin ciki Dan ana daura auren zasu tafiyarsu hadda Haroon din da Ameenatou da Jamaal shiyasa ma suka dakatar da Dr Aleena daga zuwan tinda Nan zasu taho.


Ahmed ma Yana cikin farin cikin gaske Jamaal ne kadai yake Jin kirjinsa da zuciyarsa cikin nauyin Daya hanasa ko numfashin daidai.




Karfe goma saura kusan kowa ya gama Shirin daurin auren,


Haroon Wanda Jamaal ne ya tayasa shiryawa cikin kyakkyawar farar shaddar datai masa wani irin kyau haskensa da Bai taba sanin yana dashiba bayyana sosai.


Ayau hatta turare iri Daya sukai amfani dashi sbd komai dayake jikinsu iri dayane babu banbanci abinda Basu taba yiba kenan tin suna kanana har girmansu sai yau din.


Time Haroon ya kalla yaji jikinsa ya mutu da farin cikin wannan ranar Dan haka ya Ciro wayarsa ya Saka Kiran Ameenatou wadda itama kusan ankusa gama shirinta tana dauka ajiyar zuciya kawai ya fara saukewa kafin ya ambaci sunanta Yana ce mata Yana Sonta kawai ya kashe.


Murmushi kawai tayi tana damqe wayar a hannunta tareda cigaba da shiryawa.


Jamaal tsayuwa yayi bakin window ranar aurensa na dawowa sabuwa acikin zuciyarsa Dan haka nauyin kirjinsa yake sake karuwa Yana sakashi shiga yanayin tashin tsikar jikinsa idanuwansa na Neman sauya Amma ya kasa Hana zuciyarsa shiga wani irin tsoro duk jarumtarsa.


Matsowa Haroon yayi Yana kallan time da yayi yace


"Muje ko time yayi"


Juyowa Jamaal yayi ahankali ya zuba masa idanuwansa da suka sauya sedai Bai iya cewa komaiba.


Tsoro yakeji sosai Dan haka ya Dan dauke idanuwansa daga Haroon yanayin gaba Haroon din ya biyosa yana gyara zaman babbar rigar jikinsa.


Motar Mam da securities dinsa ce ta fara barin gidan ya wuce daurin auren zuciyarsa fes,


Fitowan su Jamaal yayi daidai da fitowan Dad Omar tareda Ahmed zasu shiga mota Dan haka Kai tsaye ya kofar harabar Daya hada gidajen suna nufa suka Isa gurinsa idanuwansa na kansu Yana kallansu a tare zuciyarsa na cika da farin ganin auren yarsa Dan haka Kai tsaye rungume Jamaal yayi kafin ya rungume Haroon da yau Shima yake cikawa kowa idanuwa da kwarjini Mai sanyi.


Cikin kulawa da kauna Dad Omar ya kallo Haroon yace su shiga motarsa suje daurin auren tare.


Cikin farin cikin Hakan Haroon ya juyo ya kallo Jamaal zaice da Dan uwansa yake son zuwa daurin aurensa sai Jamaal din Wanda ya kasa samun nutsuwa ya girgiza masa Kai Yana kallan fuskansa Yace yabi Dad din kawai.


Murmushi me sanyi Haroon yayi tareda gyada Kai kaman qaramin yaro yabi dad da Ahmed dukkaninsu suna murmushi suka shige mota.


Jamaal na kallo suka tada motar suka bar harabar gidan Shima ya juya yabar harabar gidan.


Dayake sun Dade da fita kafin ya fita Kai tsaye biyawa sukai suka dauki Babbah sbd Shi Daman da Omar zasu tafi daurin auren sai gashi Kuma sunzo da Haroon sai Hakan yayiwa Babbah dadi sbd zaiso ya sake bawa Haroon amanar Ameenatou
Babbah na shiga suka tada motar suka bar gurin.




Jamaal na kama hanyar zuwa gurin daurin auren siddeeq ya kirasa kaman bazai daukaba Saiya Isa sai kuma ya dauka
Abinda siddeeq din ke sanar masa yaji Yanzu daga bakin Lameenu da BB a Mansion shine ya sakashi juya kan motarsa ya kama hanyar gidansu Ameenatou sbd bazai taba barin wani abu ya samu matar Haroon ba aranar aurensu kaman yanda Shima ranar auren ya rasa tasa matar.


Wayar Dad Omar yake kira cikin gaggawa Amma Sam Bata shiga,
Ta Ahmed ya koma kira kwata kwata Bata shiga itama,
Ta Haroon ya kira ita Kuma Saiya jita a cikin motar dayake din Dan haka yayi wurgi da wayar seat din gefensa tareda qarawa motar tsananin gudu yana nufar gidan.




Yana Isa kofar gidan Hafiz da Abdul sun fito kenan cikin Shirin wucewa ko kashe motar baiyiba ya fito da sauri Yana kallan Abdul yace


"Yi sauri karbi bayansu Dad da Babbah ka sanar musu kada su bi ta Aneyam nzki road,
Ka tabbatarda Basu bi hanyar ba yi sauri, yi sauri...


Abdul na Jin Hakan da Kuma ganin yanda Jamaal din yake a zafafe ya sakashi fadawa motar Hafiz ma ya fada suka bi bayan su Haroon din da mugun gudun gaske.


Shikuwa Kai tsaye harabar gidan ya shiga daidai fitowan Ameenatou din zata bawa Hafiz agogonsa Daya manta gurin sauri cikin mahaukacin navy blue tsadaddiyar lace din Daya fidda kayanta da kuruciyarta akansa idanuwanta akansa suka sauka ta tsaya cak daga inda take tana masa kallan Daya Sakasa qin kallan fuskanta bare gane kamanninta.




Takowa tafara yi ahankali tana nufosa cikin sanyin da duka jikinta kawai taji yayi hakama kirjinta nauyi yayi mata take me tsananin.


Gap take da isowa gurinsa wayar hannunta tayi ringing daidai Nan tasa wayar Shima tayi ringing itace ta fara daukan tata tareda kaiwa kunnenta tareda tsayawa cak daga inda take.


Daga nasa Kiran yayi da siddeeq yayi masa sedai baima gama Jin Abinda yafara fada masa ba Ameenatou ta Yanke jiki ta zube a jikinsa kaman matacciya Shima Neman zubewan yakeyi siddeeq daya iso bakin gate din gidan a haukace sbd mummunan tashin hankalin da baa Saka masa Rana ba ya shigo da mugun gudu.ya taresu gaba dayansu.
##MAMUH#*_AMEENATOUH_*
_Mamuhgee_
#Arewabook@Mamuhgee
#ZafadaBiyar






56
A jikin Jamaal gaba Dayanta Ameenatou din ta zube Dan haka baida zabin Daya wuce riqeta da hannuwansa Shima nasa kafafun na gagararsa daukansa.


Siddeeq da idanuwansa ke rikice da wani mugun ja riqesa Shima yayi Yana Kasa kallan fuskarsa data fara gaba Daya.


Umman fadila ce tareda anti zulaihat cikin mutanen dadah da suka taho daga Nasarawa biki ne suka fito daukan kaya a harabar gidan suka tarar da wanna tashin hankalin da sauri siddeeq yace umman tazo ta dauke Ameenatou daga jikin Jamaal din.


Da sauri suka qaraso tare umman ta tattaro Ameenatou din daga jikinsa tana tambayar lafiya a rude Tana raba

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login