Showing 69001 words to 72000 words out of 93806 words

Chapter 24 - Ameenatou Book Original Complete Book .txt

25 Nov 2024

4044

wayi gari sun rasu dukansu su biyu sai shi Dayan yaron nasa sun fito dashi Dan haka Babu matsala Tako ina.


Juyawa Jamaal yayi ya fito idanuwansa basa ganin gabansa sosai sbd Ja da tashin hankalin Daya tsinci kunnuwansa daji batareda ya tsaya jin sauran abubuwan da hankalinsa yake Neman kasa dauka duk da ya Dade da sanin ba imani a lamarinsu Dad bare tausayi sbd abinda sukaiwa fadila da har yanzu baida sheda ko tabbacin sune sukai Amma ayau da kunnuwansa Yana Jin abubuwan da baisan tayaya ma zaace sune suke aikatawanba,


Haroon ya San dukkanin wannan abin dayake faruwa kenan ya boye masa tinda gashi suna maganar a gabansa batareda sanin ba Haroon dinne ba.


Yana fitowa Kai tsaye mota ya nufa Yana miqawa siddeeq hannu ya basa key batareda ya Juyaba,
Kirjinsa yake Jin ya toshe masa Babu iska ko kadan Babu abinda yake buqatan so kaman ya fita daga Mansion din.


Siddeeq na ganin Hakan ya miqa masa key din motar Haroon Daya fito dashi Dan fitarsu idan sun gama.


Saida siddeeq ya nuna masa motar ya nufi inda take tin kafin ya Isa ya Budeta Yana Isa shiga kawai yayi ya tayar da reverse ya fice daga Mansion din Yana saukar da duka glasses din motar sbd iska ta shigesa.


Yana ficewa siddeeq ya Ciro wayarsa Yana shakkar abinda ya faru daga cikin office din Amma dai koma Menene Haroon Yana buqatan sani Dan dawowa sbd ansamu matsala ga dukkanin alama.


Su Dad kuwa farin ciki da zaquwan auren ne gaban Daya ya mamayesu sbd ga dukkanin alama sanadiyar auren zasu samu abubuwa da dama dasuke so suke fata,
Haroon ya fara zama abin Alfaharin da zai sake fitar da sunan seelahs da tsayuwarsu hakama dawowan Omar dasuke fata ta sanadin auren da dole zaizo ko Dan Yan jarida dazasu yada maganar auren koina da rashin zuwansa auren 'dan farko da zaayi a Seelahs din tinda na Jamaal kaman auren boye ne da ba kowa ya saniba Amma wannan da kansu zasu Kai masa gayyata ta musamman da matsayin zamansa wakilin ango da zai karba auren da hannunsa.


******Haroon dayake tareda mahaifiyarsa tana jinyarsa cikin tsananin so da kauna da kulawa tareda tattali Jin yayi zuciyarsa ta karaya Da yanda tin farko ya zabi mahaifinsa akan mahaifiyarsa,


Bata taba nuna masa banbanci tsakaninsa da Jamaal ba sedai shine Karan kansa ya zabi mahaifinsa akanta sbd sonsa dayakeji cikin ransa fiyeda komai.
#MAMUH#




*_ZAFAFA BIYAR_*


1 *_Ameenatou!!_*
_Mamuhgee_


2 *_Tsutsar Nama!!_*
_Billyn Abdull_


3 *_Gudun Kaddara!!_*
_Safiya huguma_


4 *_Kwankwason Jimina!!_*
_Miss xoxo_


Guda Daya 400
Guda biyu 700
Guda uku 1k
Guda hudun 1200


*_6019473875 MUSAA ABDULLAH SAFIYAH keystone bank_*


*_ATURA SHEDA ZUWA 09166221261_*


*_MTN/VTU 09134848107_*


_*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din 09033181070*_


*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_**_Arewabooks@Mamuhgee_*
44
Mum Aleena datake Jin batason sake rabuwa da 'danta sbd halinda yake ciki na tsananin buqatan kulawansu dan sai sunyi da gaske zasu iya rabasa da depression din Daya kamasa,


Drug kuwa da suka samu a jininsa Basu sanar masa ba itada Jamaal sbd sunason tantance shine yake Sha da kansa kokuwa sbd sun kasa yadda ko sanin tayaya zai zama Yana Shan kwayoyi irin wainnan.


Siddeeq Kuma ya tabbatar musu da Babu kwayoyi mayen ko makamancin Hakan da Haroon yake Sha Amma Kuma duba da depression dayake ciki da tsananin matsi a Hannunsu Dad zai iya samun kansa da Shan kwayoyin Dan samun fita hayyaci ya Dena Jin komai.


Tin daga ranar da Haroon din ya taho aranar ya ringa yiwa mum din kuka kaman karamin yaro cikin ciwo da tsananin buqatan again Dan uwansa akan bayason rasa Ameenatou kaman yanda ya rasa fadila,
Shi a yanzu ba yabon mahaifinsa yake nema ba Ameenatou kawai yakeso a rayuwarsa.


A gaban Mahaifiyarsu Jamaal ya Sakasa sukaiwa juna alkawari.


Idan Haroon yayi masa alkawarin dawowa ga mahaifiyarsa Dan samun lafiyansa da rayuwar nutsuwa da Kwanciyar tare Kuma da cika burin Mum dinsu na ganin yayanta duka biyu a tareda ita to shi Kuma yayi alkawarin zuwa ya gyaro dukkanin abinda Haroon yakeso Dan samun yabo daga Dad dinsa da Kuma zama abin alfaharinsa tareda tabbatar da aurensa da yarinyar Amma ana daura auren zasu taho tare.


A daidai wanna gaban Babu abinda Haroon bazai iya yiba akan samun Ameenatou da samun nutsuwan zuciyansa data Dan uwansa da mum Dan haka ya amince da dawowa cikinsu gaba Daya bayan auren take mum ta rungumesa cikin farin ciki da Jin dadi sosai tana Jin kaman tinda ta haifesa sai yanzu ne zata samu zaman datakeson yi da 'danta hakama zata kaman yanda ta kaunaci fadila take taji tana kaunan Ameenatou har cikin ranta duk da Bata taba ganinta ba Amma tayi masa alkawarin inshallah da ita zaayi aurensa.


Daman ba wani zama zasuyi a Poland dinba Nigeria zasu taho sbd bikin auren Da Haroon din kwata kwata yaji Baya son a dauko lokaci ayi kawai ya tahowansa kusada mahaifiyansa Dan haka sauki kawai sukeson ya Dan samu su taho saiga Kiran siddeeq Wanda ya sakashi shiga fargaba da tsoron abinda Jamaal yaji Dan haka shine ya dagawa mum hankalin komawansa baima jirata ba washe garin ranar ya Siya ticket dinsa ya tahowansa Dan bayason abinda zai janyo fushin Jamaal ya lalata masa komai adaidai lokacinda ake gap da samun abinda yakeso.


Jamaal kuwa a ranar Bai kwana a Lagos ba ya wuce Abuja tareda siddeeq ko su Dad din Basu saniba Dan idan Yana ganinsu zuciyarsa kasa riqe koshi waye din takeyi gwara ya tafi ya Jira zuwan Haroon Daya San duk inda yake idan har baida gaskia Yana hanyar dawowa.


Kwana Daya saiga Haroon din ya diro Amma Bai yadda ya Hadu da Jamaal din ba Kai tsaye Nasarawa ya wuce sbd bayason suyi hayaniya Kuma baisan Menene yaji bama tukuna bare yasan ta inda zai fara.


Da yamma sosai ya iso Dan haka wanka da sallah kawai yayi Bai tsaye komaiba ya wuce gidan Babbah.


Zaune suke a tsakar gidan sai lallabata dadah keyi sbd taqi Shan magani daga ciwon Kai zazzabi ya maqale kwana biyu anata fama da ita.


Zuwansa ya Saka Abdul sakin ajiyan zuciya hakama Hafiz Babbah Baya Nan
cikin sakewan fuska da nutsuwa ya qaraso Hafiz na janyo masa kujeran zama Yana masa barka da zuwa.


Yaya Abdul ya fara bawa hannu suka gaisa cikin tsananin kulawa Yana tambayarsa kwana biyu ko numbernta Baya shiga.


Murmushi ya sake Yana cewa aikin dayake gabansa ne ya sakashi kashe dukkanin wayoyinsa sbd aikin ya koma babba fiyeda yanda suke tsammani.


Gurin dadah ya Maida kallansa Yana gaidata cikeda girmamawa da kulawa kafin idanuwansa suka koma kan Ameenatoun Dake zaune sanye da Riga da wando na bacci ko hula Babu a kanta ko inda yake Bata juyo ta kalla ba maganinta take kokarin Sha tana kasawa sbd batason magani ko kadan.


Hafiz Dayafi kowa shiga damuwan bayan Ameenatou tambayarsa siddeeq yayi suna sake shiga wata firar Amma gaba Daya hankalinsa na kan Ameenatou da yayi magana tayi masa shiru kaman Bata ji ba Kuma kowa yasan ta jisa Daman sun San sai anyi Hakan.


Dadah ce ta Dan rarrasheta tana cewa


"Budurwa bakiji ana Miki ya jiki bane?
Duka fushin bana rashin kiransa da zuwan bane gashinan ai ya taho saiki sauko,
Yi masa hakuri kinji¿


Maganin ta daga duka ta Saka a bakinta tareda binsa da ruwa ta shanye batareda ma tasan tayi Hakan ba sbd fushin Daya taso mata.


Tinda ta fara zazzabin ko ruwa Se ta Saka anbata ko hulan kanta Bata iya sakawa sai an Saka mata sai gashi ta miqe tsaye da kanta ta wuce dakinta tana cewa bacci zatayi.


Hafiz ne ya Bude Baki yace


"Ke meye haka wai?
Inace Wanda ake fushi da ciwon akansa gashinan yazo,Kuma Ashe Zaki iya tashi da kanki kika ringa wahalar Dani da Dadah tin jiya ko bacci na fara saita kirani na kawo mata ruwa Ashe tsaban rashin tausayi ne to Zaki San dawa kikai."


Tana jinsa Bata ce komaiba saima hararan kofar datai tana Jin zafin abinda yayi mata ranar Yana dawo mata.


Dadah murmushi ta sake tana sake tambayarsa nasa jikin ya amsa mata sbd yasan halin mutuniyar sarai basai an tsaya basa hakurin abinda tayin ba,
Abdul ma sake tambayar jikin da aikinsa yayi kafin suka fada firar tafiyansa Lagos gobe zuwa nxt week Kuma su dadah ma zasu taho duk da ba zuwan kenan ba zadai suje suga inda Allah ya Kaisa dasu.


Duk firar dayaketa yi hankalinsa na kan kofan dakinta Amma Sam taqi yadda ko motsi tayi yaji dadi Bare fitowa.


Sallan magrib suka fita sukayo suka dawo gidan tareda Babbah daya masa ya jikin da fadan rashin Kiran tinda koyayane Daya samu ko mintina bibbiyu a wuni ya ware ya kira din zasuji dadi itama me fushin da bataiba.
Gashi tanata fushi da maimaita shariyan dayayi mata.


Hakuri ya bawa Babbah har suka shiga wata firar inda Babbah din ya sanar masa su Alh Lameenu sun kira akan maganar auren sukeson ta taso ayita kusa tinda dai ba amfanin jiran ko tsaiko.


Har cikin ransa yaji farin ciki Yana mamayesa sedai Kuma fushin da Ameenatou keyi me zafi akansa Yana cin zuciyarsa sbd yasan Jamaal ne yayi mata koma Menene Dan haka Shima take yaji Yana buqatan ganinsa Dan haka anan yayi sallar ishai yaci abinci suna gamawa harya fito Bata fito a dakinba Kuma babbah ya Hana kowa takurata fitowa saita huce da kanta taji ta hakura tukuna.


Yana fitowa da wayar hannunsa ya kira layinsa dayake hannun jamaal Amma Jamaal din yaqi dauka sbd Shima Yana sane da Haroon din ya dawo guje masa yayi.


Kiran dayake yi Jamaal yaqi dagawa ya Sakasa dawowa hayyacinsa akan abinda yake jiransa Dan haka dole ya shirya tinda safe ya nufi Abuja.


Koda ya Isa Jamaal din Yana bacci Dan haka siddeeq na ganinsa ya saki murmushi Mai hade da sakewa Yana masa barka da dawowa.


Kallan hanyar stairs na Hawa sama yayi kafin ya dawo da kallansa kan siddeeq din fuskansa a sake Shima Yana amsawa ya ajiye keys din hannunsa da wayarsa Daya ya nufi dining da aka cikesa tsaf da breakfast din Jamaal din ko zama baiyiba Yana Isa dining din Jamaal ya sauko daga saman sanyeda silk pyjamas farare Kal sai slippers dinsa masu shegen tsada da taushi a qafa kallo Daya yayiwa Haroon ya matse fuskansa datake sheqi kaman ba bacci ya taso ba Yana qarasowa ko zama beyiba Haroon ma ya Dan matse tasa sbd kada Jamaal din yayi masa fada a gaban siddeeq yace


"Meyasa nake Kiran wayanka baka dagawa tin jiya fa da daddare bayan isowana?"


Sai alokacin Jamaal ya juyo ya kallesa da idanuwansa da suka Sakasa Jin kunyar Dan uwan nasa na Abinda ya boye masa duk da haryanxu Yana shakkar idan gaskiyar abinda su Dad keyi ne yaji sbd da bazai zauna haka calm ba.


Ciki muryan dayake kokarin danne bacin ransa yace


"Ka taho ne sbd ban dauka Kiran ba kokuwa sbd kana son sanin abinda na sani gameda ainihin abinda kuke aikatawa a boye?"


Maganar tasa ta Saka Haroon kallansa Yana cewa


"A boye Kuma?
Me kenan??
Me kaji?
Kuma daga bakin wa?


"Daga bakin manyanka,Amma koma Menene baka buqatan sani
kaman yanda ka iya boye sirrinsu bana son sanin komai daga bakinka Amma dai ka fada musu taba Dad jeden shine babban Barna da kuskuren da zasu tafka sbd jinin wani karfi ne dashi baa zubar dashi a sake zama lafiya,
Wannan shawara ce da zaka sanar da daddies Dinka."


Yana fadar Hakan ya taba sa ya wuce zuwa dining din sbd yin breakfast.


Kasa motsawa Haroon yayi sbd Baisan me zai fada ba.


Yana gurin tsaye Jamaal ya gama breakfast dinsa ya koma sama yayi wanka ya shirya ya fito a shirye qamshinsa na cika iskar gidan ya fice shida siddeeq sbd sosai yake aikin dayake gabansa Dan kasar gaba Daya Jin yayi fita ransa tafiyansa yakeson yi batareda yabar Haroon din ba Koda me zaayi kuwa,
Aikin kawai yake son gamawa ayi auren su tafi Babu ranar dawowa.




A gidan suka bar Haroon yanata sakawa da kuncewa har sai dare suka shigowa gidan ya fice Dan a matse yake dayake ya duba Ameenatou tinda yanzu Kam baida aikin yi bayan zama guri Daya harsai jamaal ya dawo.


Yauma kwata kwata Bata saukoba duk rarrashinta da duka gidan suka taru sunai mata haka ya gama ya koma Amma dai gwara yau din ta zauna Bata shige dakinta ba.




********Jamaal gaba Daya Jin yakeyi kaman ana konasa aqasar Dan haka ya toshe dukkanin hanyar da zata Bata lokacinsa akan abinda ya kawosa ya dukufa sosai akan aikin Wanda tini ya dauki hanyar kammaluwa sbd sosai ake Aiko na masu zallan ilimi gadan gadan ba wasa ba shirme.


Hafiz dayake ganin sauyi sosai a Haroon din dayake Gani Gurin Aiki da safe da Kuma Wanda yake Gani gidansu da daddare sai ya Saka Hakan akan gurin aiki daban da gida Shima Saiya janye daga nuna kusancinsu da Haroon din gurin aiki saisun hade gida suke fira da gaisawa yanda ya kamata.


Jamaal kansa mamakin Haroon din yakeyi sbd yanda zuciyansa ta gama mutuwa akan yarinyar bayaji Baya Gani Baya gane komai idan bana Yarinyar ba da har lokacin shi Yama kasa tsayawa ya riqe sunan.


Fahimtar irin son dayakewa yarinyar ya Saka Jamaal din Jin bazai iya barin Haroon ya rasata ba.


Ta bangaren su Dad kuwa duk lokacinda ya buqaci ganin Haroon Jamaal ne yake zuwa sbd bayason Haroon ya sake tsayuwa a gabansu Dan kada su lalata masa aikin treatment Daya basa shida mum akan lafiyansa da suketa kokarin ganin samunta Dan kuwa shiyasa suka buqaci komawansa tareda sakashi alkawarin komawan acan Dan kuwa abinda yake Sha Wanda Basu gane Menene ba yayi masa Mummunan illan da basason ma ya sani kwata kwata.
#MAMUH#




*_ZAFAFA BIYAR_*


1 *_Ameenatou!!_*
_Mamuhgee_


2 *_Tsutsar Nama!!_*
_Billyn Abdull_


3 *_Gudun Kaddara!!_*
_Safiya huguma_


4 *_Kwankwason Jimina!!_*
_Miss xoxo_


Guda Daya 400
Guda biyu 700
Guda uku 1k
Guda hudun 1200


*_6019473875 MUSAA ABDULLAH SAFIYAH keystone bank_*


*_ATURA SHEDA ZUWA 09166221261_*


*_MTN/VTU 09134848107_*


_*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din 09033181070*_


*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_**_Arewabooks@Mamuhgee_*
45
Ranar da Abdul ya cike kwana hudu a Lagos Dan fara aiki a ranar su Dad Lameenu suka sake dawowa nasarawa maganar tsayar da aure hadda Abdul din aka taho Wanda Dad Lameenu ya jasa a jikinsa sosai yana masa kallan kaman 'dansu duk Dan sbd ya sake dasu sosai ya samu aminta dasu har zuci ya yanda komai zai taho a sauki.


Sun sake zama anyi magana an tsayar da ranar auren sati uku hudu masu Wanda daqyar dai su Babbah suka aminta da Hakan sbd kwanakin sun musu kadan duk da ba wani biki sosai akace zaayiba Tinda a Lagos zaayi komai Amma hakama sun buqaci yafiyan duk wani abu da amarya zata buqata Amma Babbah ya nuna amincewa da Hakan gaskia sbd duk fafutikan rayuwar dasukeyi shi da su Abdul na inganta rayuwarta ne su Bata gata Dan haka dole zasu wadata ta da dukiyan aure kaman kowace 'ya yar asali yar gata daidai karfinsu.


Su Dad din Basu wani ja da Hakan ba Daya dage Dan haka take suka gabatar da komai aka Yanke sukai Godia Suma su Babbah sukai godiya.


Wannan Karan harda dadah aka kirawo musu suka gaisa da ita da Ameenatou din wadda take sanye cikin doguwar Riga maroon sai veil data doro Akai.


Sun nuna yabawansu da nutsuwanta a fili sosai suka ringa sake yiwa Babbah godiya Wanda tini ya sake Jin hankalinsa ya kwanta dasu da mutuncin da suke dashi hakama Abdul ya sake tabbatar masa da mutuncin dasuke dashi harma agurin mutane Dan haka yake sake godewa Allah akan zabin da yayiwa Ameenatou dinsa Dayake ta addua da fata.




Da farko babbah baida niyar zaman Lagos din Amma a yanzu da Aure yakai 'yar budurwansa yaji bazai iya zama a nesa da inda take ba tinda harsuna da inda zasu zauna din agidan Abdul Dan haka ya aminta da komawa Lagos din gashi Daman Hafiz ma Lagos din zaibi Haroon kaman yanda yayi masa alkawarin dashi zai koma Koda aikin site ya kammalu acan zai basa aiki a kamfaninsu.


Tsayar da ranar auren ya Saka Haroon shiga lokutan farin cikin rayuwarsa Dan haka ya sake nutsuwa sosai Yana mayarda hankali cikin aikin project din da Jamaal ya tsayu akansa Dan kammalawa ya tafiyansa Dan kullum Jin yake Yana sake matsuwa da barin kasar.


Haroon ganin irin kulawa da kaunan da mahaifinsa yake nuna masa ayanzu Dayake alfahari dashi dakuma ganin abubuwa nata dawowa kan hanya sai yaji soyayyar Dad dinsa na kashe masa jiki kaman bazai iya tafiya ya barsa ba Amma Bai bar Jamaal ya fahimci Hakan ba Dan Jamaal kwata kwata ya Dena bayyana a gaban su dad din sbd yanzu kauna zalla sosai Dad yake nunawa Haroon Dan haka yabarsa ya samu kaunar dabai samu daga Dad dinba Wadda yake tsananin so da burin samu.




*****Su Babbah kuwa A nasu bangaren sosai hidiman tayi musu yawa sbd ga hidiman Shirin biki gata tashinsu duk da ba siyar da gidansa zaiyiba Yan haya aka Nemo zaa Saka Dan haka suketa shirye shiryen tafiya da siyarda abinda ba dashi zaa tafin ba.
Su mum Atee ma da zasu taho kawo kayan aure su lefe da masu gyaran amarya Babbah cewa Yayi su barshi acan tinda suma a satin zasu iso Daman sun zabi yin auren acan ne sbd kawowa kowa sauki dangin angon masu zuwa da Jamaar seelahs din da duka manyan mutane ne da manyan qasa hakama da Yan kasashen qetare sbd sosai Mam ya fito ya nunawa duniya auren dansa zaayi Kuma aure na alfarma na Manyan masu abin duniya Dan haka aketa shiri da Kuma miqa gayyatansa ga abokanan huldansu da manyan masu kudin da suke tare harma da gwamnoni.


Ita kanta amaryan Haroon Kuma budurwan Babbah farin cikinta kusan kullum Baya boyuwa sbd a kwanakin Dan kullum auren yake matsowa cikin tsakiyar ranta take sake Jin tsananin kauna da son Haroon Wanda ya tsayu tsayin daka ya tabbatarda ya dawo da sonsa sabo fil cikin ranta.


Daga shi har ita Hafiz yace ya rasa wanne yafi rawan kafar aurenba ita dai bata tanka Hafiz din sbd ta shirya masa duk abinda Bai zata ba bayan auren tinda a karkashin mijinta zaiyi aiki.


Duk hidiman auren da akeyi Jamaal Bai shiga ko dayaba sbd baida time ko kadan na batawa aiki yakeyi gadan gadan ba dare ba Rana Kuma Hakan saka su dad farin ciki yakeyi.




Ranar dasu Babbah suka gama parking zasu wuce Lagos Kuma jirgi zasubi dukkaninsu sbd murna Ameenatou har

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login