Showing 75001 words to 78000 words out of 93806 words
bayajin har abada zai iya bayarwa ko barin 'yarsa da ita kadaice jininsa Kuma Jaden daya data rage ta shiga hannunsu Mamman.
A cikin Daren su dukkanin iyalan seelahs da suka dawo suka tararda koina na wutar mansion din Jden a kunne ta haskaka koina na zagayen gidan Wanda Hakan ya tabbatar musu da an kunna switch na wutan gidan gaba Daya dayake kashe hakama securities ne na musamman koina zagaye da gidan Wanda Koda suka fita hidiman bikin Babu ko Daya a mansion din.
Babban abinda ya sake raya mansion din shine matar Ahmed da yayansa biyu dasuke tareda su duka a cikin gidan Dayake kusan tsarin Mansion dinsa na can Greece Dan haka a cikin Daren ma'aikatan da duka aka Riga aka tanadar musu suka iso gidan cikin abinda Bai wuce awanni ba aka hau aikin gyaran gidan kafin su iso shiyasa Koda suka iso komai tsaf Babu abinda yake tashi sai kamshin freshners dana manyan humidifiers dana burners dayake tashi a duk inda ka Saka kafafunka da sanyin ACs da Suma suke aiki.
Ma'aikatan kusan guda biyar ne aka kawo dukkaninsu mata sai namiji Daya da shikuma harabar Mansion din itace tasa.
Mum Noor matar Omar da har lokacin ta riga ta rasa cikakkiyar lafiyanta akan abinda ya faru Bata Gani sosai hakama Bata iya tafiya sai akan wheelchair itama hakanan suka taho sbd yazo da niyar zama ya fuskanci wainda suke son fuskantarsa Amma zuwan na yarsa ne Daya danne dukkanin abinda yake ji akanta tsawon shekarun ya nesanta da ita sbd Bata kariya da rayuwar Kwanciyar hankali batareda tsoro ko fuskantar hatsarin dayake tattareda wata dukiyar ba,
Taimako da kyakkyawar rayuwar dayaso Basu itada su Babbah duk ya danne kansa ya janye daga garesu sbd koma huldan dazaiyi dasu a boye su Mam zasu iya bibiyan Hakan su mata illa.
Yayan Ahmed ba wani shekaru ne dasu ba sbd ya Dade sosai sosai baiyi aureba har Saida ya fara manyanta ma Dan haka suke Yara daidai kusan Ameenatou din Amma tama girmesu da shekaru biyu zuwa uku haka Dan babbar kenan sai namijin Wanda duka duka yanzu yakeda 10yrs zuwa 11 Dan haka masu aiki tini suka fara kokarin kaisu dakinsu Dan taimaka musu dasu wanka da sauransu.
Mai aikin da itace kaman babba a cikinsu sunanta Zahida itace ta Kai kayan kowannensu dakinsa ta fito ta nufi dakin yar budurwan wadda batasan sunanta ba Saida taji mom dinta ta ambaci sunanta da Fatmah kafin ta kama itama.
Abincin alfarma marasa nauyi irin Wanda sukasan zasu iya ci ne dayake dukkanin masu aikin kwararri ne aka dauko wainda albashinsu ma na musamman ne suka jere a makeken dining din Wanda Babu abin buqatan ci da Sha da baa jere ba cikin tsari.
Alh Omar ne a sama gaba Daya da mum Noor
A qasa Kuma Dayan bangaren Ahmed da nasa Iyalin ne dakin Fatmah daban hakama dakin Arfat daban.
Dukkaninsu Babu Wanda zai iya cin wani abinci a Daren sbd gajiyan dasuke tattare da ita,basa wani Jin yunwa sbd sunci snacks dasu tea da sai sauransu a jirgi so basa wani Jin yunwa Hutu kawai suke buqata.
Arfat da Bai Saba da koina ba hasalima shi Bai taba zuwa Nigeria ba tinda aka haifesa Dan haka kwata kwata qin yadda masu aikin su kusantosa yayi wanka yayi abinda ya shirya cikin kayan bacci ya fito ya nufi dakin Fatmah ya kwanta tareda ita itama duk da Bata san Kwanciya dashi Amma sbd bakuntan gidan ya Sakata kyalesa bayan sunyi sallah tea me zafi ta buqata daga masu aikin kawai Tasha ta kwanta.
Duk yanda Mam suka shiga mamakin abinda yake faruwa Basu nemesa ba sbd dare yayi Suma Kuma a matiqar buqatan hutun suke sbd hidiman da aka Sha Dan haka suka bari zuwa da safe Dan tabbatarda idan Omar jden dinne ya sauka Nigeria.
******Washe garin ranar da mamaki kowa ya wayi gari da ganin dawowan Wanda baa taba tinanin Gani ko yaddar zai dawo din ba wato Alh Omar jeden seelah wadda tini labarin ya fara yaduwa.
Mam da Lameenu da kansu suka taho yi masa barka da sauka cikeda farin ciki Mai tsananin gaske da nuna yabawarsu batareda nuna komai a fuska ba,
Shima Bai nuna komaiba cikin farin ciki da nuna kewan juna ya bayyana farin cikin ganinsu.
Fira suka zauna sosai cikin kewa da murnan kasancewansu tare da juna a yau din bayan tsawon lokaci sun Hadu a matsayin brothers da aka Sansu.
Mum Noor Bata nuna komai ba sbd ba komai ma ta sani ba Dan haka sosai aka Hadu anata murna da farin ciki musamman dasu mum Atey suka shigo hakama su mummy Sarat ma duk sun shigo hadda su Aliyah anata murna harma da matar Ahmed Aunt Didi Wanda take wayayyar mace sosai Kuma ta waye ga ilimi Dan haka ta saki jikinta ta sake acikinsu.
A tare duka ahalin sukai breakfast qatuwar dining din gidan Dad Omar ana sake tattauna bayan rabuwa da Kuma murnan auren Haroon Daya sake hada auren.
Bayan breakfast shigewa su Dad suka sake yi Babu Wanda yake jinsu suna palonsa anata maganganu.
Su mum Atee ma sun jima sosai kusan a gidan aka wuni gaba Daya sai daga baya kowa ya koma masu fita Kuma irinsu Aliya tini ta qara gaba duk da Dad Omar tana yinsa sbd Yana kaunarsu sosai hakama wasu lokutan idan ta Kalli tazarar dukiya Dan rayuwan dayake da shi da 'yannansa su Dad dinta sai take Jin inama shine ya haifeta gashi a waye fiyeda Dad dinda da ilimin da kallansa kadai zakai kasan ya gama shigarsa Tako ina.
Sai dare Jamaar gidan suka samu Hutu da gidan yayi tsit sukaci abinci gaba dayansu a dining kafin kowa ya shige dakinsa yayi wanka ya kwanta Dan samun hutawa.
Washe gari Haroon ne da Bai samu zuwa ba jiyan ya taho yayiwa Dad din sannu da zuwa cikin farin ciki sosai.
Zuba masa idanuwa Dad Omar din yayi Yana karantarsa cikin nutsuwa da kulawa a matsayinsa n Wanda zai auri yarsa ta cikinsa.
Haroon sosai yake kauna da girmama Dad Omar shima Amma Kuma kusanci da kaunan Dake tsakanin Jamaal da Dad Omar din Babu Wanda zai iya shiga ko samun irinta Dan haka Shima Omar yake kaunar Haroon har ransa sbd kaunar dayakewa Jamaal da Dr Aleena Amma Badan mahaifinsa ba.
Haroon ya Jima a gidan Shima kafin ya fito Kai tsaye ya nufi ganin amaryansa.
A Daren Ahmed da Omar suka fita sedai Bai nufi gidan Babbah Kai tsaye ba Wanda suka samu bayanin komai nasa da gidansa,
Zuwa gidansa Kai tsaye yanada hadari Dan haka masallacin da babban yake sallah ya nufa Dan yin sallan ishai acan.
Babbah tareda Abdul da Hafiz suka fito daga gida suka nufi masallaci kowanne da sauran ruwan alwala a fuskansa Hafiz na latsa wayarsa Babbah na masa maganar meyasa yake zuwa da waya masallaci Hakan baida amfani tinda ba dadewa zaiyiba a masallacin.
Shiga masallacin sukai Babbah ne a gaba kafin su a bayansa suna shiga suka shiga sahu
Ana kokarin tayarwa Ahmed da Dad Omar suka shigo masallacin Kai tsaye gefen Babbah Omar ya tsaya Yana gyara tsayuwansa Dan tayarda sallan Ahmed ma gefen Omar din ya tsaya Yana gyara nasa tsayuwar.
#MAMUH#
*_ZAFAFA BIYAR_*
1 *_Ameenatou!!_*
_Mamuhgee_
2 *_Tsutsar Nama!!_*
_Billyn Abdull_
3 *_Gudun Kaddara!!_*
_Safiya huguma_
4 *_Kwankwason Jimina!!_*
_Miss xoxo_
Guda Daya 400
Guda biyu 700
Guda uku 1k
Guda hudun 1200
*_6019473875 MUSAA ABDULLAH SAFIYAH keystone bank_*
*_ATURA SHEDA ZUWA 09166221261_*
*_MTN/VTU 09134848107_*
_*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din 09033181070*_
*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_**_Arewabooks@Mamuhgee_*
48
https://chat.whatsapp.com/K3rO5UonX4GDVxtQbA5mZl
Assalamualaikum wa rahmatullahi ta'ala wa barakatuhu!!! Wannan group din dai na komai da komai ne. A taiqaice
*Farashin mu na daban ne compared to sauran Yan kasuwa
*Kaya masu kyau da quality. Abinda kika zaba shi za a Baki
* Swift delivery.watau waybill a sauqaqe da Yardar Allah
* Muna sake New Arrivals ka fin su cika Gari
* Muna iya duba maku kaya a good price ko da ba namu ba ne idan kuka Aiko da hoton kayan
Allah sa mu qaru da juna Ameen
***********
Babbah da baisan waye a gefensa ba sbd ya riga ya tayar da sallansa Dan haka hankali kwance da nutsuwa yake sallan hakama suma kowa ya natsu a cikin jam'in.
Dun Yana sallah ne Babu filin tinanin komai a zuciyarsa Amma dai Kuma ya tabbatarda ko waye a gefensa bako ne a masallacin Kokuma babban mutum ne sosai Dan qamshinsa me sanyi da nutsuwa ya tabbatarda Hakan kusan a duka sahun Babu Wanda qamshin me sanyi Baya shiga hancinsa.
Ana sallame sallar Babbah yana juyowa zai gyara zamansa idanuwansa suka sauka akan fuskan Wanda yake kusa dashi din take salatin daya debo daga bakinsa ya bace masa bat.
Juyawa gefensa Daya dasu abdul suke zaune yayi yaga hankalinsu Baya kansa adhkar kawai sukey,
Juyawa yayi bayasan yaga kowa abinda yake gabansa yakeyi da sauri ya sake dawo da kallansa gefen nasa ya sake kallan fuskan Omar ya kasa yadda da idanuwansa Gani sukeyi daidai Dan haka ya ambaci sunan Hafiz a hankali cikin nutsuwa yace
"Wannan bawan Allahn Dake gefena ka taba ganinsa a kuwa??"
Kallan Omar Dake zaune hankalinsa kwance Yana addua yayi yaga kwata kwata idanuwansa basa kansu hakama da alama lafiyayyan Mai abin duniya ne dan daga nutsuwansa da motsin jikinsa kadai zaka gane Hakan.
Girgiza Kai Hafiz yayi ahankali Yana dauke kallansa daga kan Dad Omar din Daya Burgesa Kai tsaye sbd wani sanyayyan kwarjininsa Daya cike idanuwansa dama duk Wanda ke kallansa Dan kaman kusan yakusa zama bature Dan fari ne sosai farin ma na Hutu.
Numfashi me dumi Babbah ya sake saukewa a karo na kusan biyar kafin ya juyo idanuwansa da suka sauya take ya Kalli Omar din baice komaiba Shima Omar din baice komaiba sai hannu Daya miqawa babban Yana Dan sake fuska da muryansa me Kamala yace
"Assalam alkm"
Cikin karfin hali babban ya miqa masa hannun Yana amsa sallamar Kai tsaye batareda ya kallesa ba kafin ya miqe tsaye Yana wucewa yabar masallacin.
Su Abdul cikin girmamawa sosai suka gaida Dad Omar din Wanda ya miqa musu hannu Shima Daya bayan Daya sukai musabaha Yana kallansu cikeda kauna da kulawa kafin suka bi bayan Babbah sedai suna fita suka tarar da ya bace musu da alama ya kama hanyar gida.
Hanyar gidan suka kama Hafiz na fidda wayarsa daga aljihu Dan Saka kira Abdul kuwa Kai tsaye hanyar gidan ya kama sbd zai fita da Dadah siyayyar turarukan wutan da zasuje yi itada umman fadila na MEERAH B PALACE masu fitinanniyar kamshin da duk amaryan datai amfani dashi Babu ta yanda bazata Hana zuciyar duk Wanda ya shaqa zaman lafiya ba Dan qamshine da a iya gurinta ne kadai ake iya samunsa.
Dayake washe gari ne kadai bazaa daura auren ba Dan haka Gyaran da akewa Ameenatou din ya koma so Daya a wuni maimakon so biyu sbd sauyin datai yayi yawa gaba Daya bazaka taba ganinta Kai tsaye ka dauka budurwan Babbah bace.
Babbah daga cikin masallacin Kai tsaye wani gurin ya nufa yaqi nufar gidansa Dan Bayaso abinda zai Kai Omar gidansa Kokuma abinda zai Saka a gansa da Omar ko a mafarkinsa kuwa Dan har abada baida alaqa dashi,
Alaqan Dake tsakaninsu sun Riga sun yanketa sbd shine kadai abinda ya Saka Ameenatou dinsu take raye,
Aurenta shine abinda zai sake Bata tabbatacciyar tsari daga mahaifinta da masu bibiyansa sbd zatai aure gidan arzikin da zasu Bata kariyan da duk take buqata Dan haka yaji Inama gobe ne daurin auren...
Aurenta kadai zai Hana Omar amsarta daga hannunsa duk da Shima Koda Babu auren bazai taba basa ita ba sedai bayan ransa kuwa Dan haka yaji tsananin dadin Daya kasance auren ya raba musu gardaman yaqin da zasuyi akanta.
Mema ya dawo dashi bayan tsawon shekarun da sukai Basu San inda yake ba baisan inda suke ba kowa na tasa rayuwar?
Tayaya Ameenatou zatasan bashine asalin mahaifin Daya haifetaba?bama zata San wannan gaskiyar me rugusa farin cikinta ba a yanzu datake cikin tsananin farin cikin aurenta da Wanda take mutuwan so.
Tafiya yakeyi batareda ma yasan inda yake jefa kafafunsa ba sbd tinani da tashin hankali harma da tsananin bacin ran dayake Jin Yana tasowa Yana rufe dukkanin zuciyansa na bayyanar Omar gabansa.
Tafiya Mai Nisan gaske yayi batareda yasan yayi ba har Saida yaji kafafunsa suna Neman kasawa kafin ya tsaya Yana duba inda ya kawo kansa Bai saniba.,
Kafin ya sauke numfashin zafin zuciyar Dake cinsa lafiyayyar motan dake daukan idanuwansa ta tsaya gabansa Batareda an sauke glass ba Ahmed ya Bude motar ya fito ya Bude kofar Baya inda Omar yake zaune Yana kallan Babbahn Ahmed yace
"Bismillah"
Jajir idanuwan Babbah sukai Yana yiwa Omar wani kallo abinda ya danne shekara da shekaru Yana taso masa Mai tsananin zafi da radadin gaske harma ciwo me nauyi.,
Shima Omar Babbah din yake kallan gashi anguwar tsit Babu mutane sosai Kuma akwai duhu Dan haka Babu Wanda zaisan waye suka tsaya dauka.
Ahmed ne ya sake kallan babban Kai tsaye yace
"Ko zaa taimaka Maka ne gurin shigan??"
Maganar Ahmed ta Saka Babbah dagowa ya kallesa Jan idanuwansa na karuwa sbd yasan me Hakan ke nufi,
Ahmed shine Wanda ya kawo sakon yafe Ameenatou da Omar yayi tin tana kwana Daya da haihuwa a duniya Dan haka tsana da zafin Omar Dayake ji daidai yakejinsu akan Ahmed.
Shima Ahmed a nasa bangaren zuciyarsa a shirye take da duka dangin Omar dana matarsa sbd Bai yadda da kowa ba akan Omar hakama zai iya taka kowa Babu ruwansa akansa,
Idan rayuwar Omar sukeso to tabbas saisun shirya daukanta Dan ba sauki ya shirya musu.
Abinda yake ji a zuciyarsa tsananta ta yanda ko numfashin iskan da Omar yake gurin Bazai iya shaqaba,
Hakama tayaya zasu fuskanci juna da Omar din?
Me zasu tattauna?
Meye a tsakaninsu?
Ameenatu ce Kuma ta rasu Dan haka ba sauran abinda ya rage Dan wannan Ameenatou din ya yanzu tasa ce Babu abinda zaisa ya tsaya ya sauraresa, idan ma zasuyi magana to yabari sai bayan daurin aurenta.
Takawa yayi a raba gefen Ahmed ya wuce Yana Jin kirjinsa na tsananta nauyi kaman numfashinsa ma zai toshe.
Motsawa Ahmed yayi zai bisa Omar ya dakatar dashi sbd Shima tasa zuciyar datai nauyi.
Tayarda motar sukai suka bar gurin sbd ganin kaman wata motar tafe Wanda Sam bayason asan Yama San Babbah sbd abinda ya lura ya karanta a tsakanin zuwansa zuwa yanzu shine su mamman basusan Ameenatoun itace Ameenatou Jden ba da suke tsananin nema Dan haka yanada Daman Hana auren ko dauketa kafin sanin nasu Wanda kowanne time zasu iya sanin Hakan sbd yasan sarai ana biye da takunsa da lamuransa shiyasa bayason bayyanarda sanayyarsa da Babbah.
Suna wucewa Babbah ya Nemi guri ya zauna Yana rintse idanuwansa sbd zufan Daya jiqasa me zafi,
Baisan ta inda zai fara barin Ameenatou tasan ba sune suka haifeta ba,
Idan ta sani kwata kwata bayason duniya tasan ita 'yar Omar Jaden ce sbd hatsarin da rayuwarta zata shiga me girma,
Ba Dan bayason Omar ya Hadu da 'yar tasa ne ba sai Dan barin su Hadu din asan yarsace komai zai iya lalacewa,
Ameenatou zata iya shiga hadari sbd ko bayan aurenta zata iya shiga hadarin duk da acikin masu arziki sosai zatai auren Amma Shima Omar din me kudin gasken gasken ne Amma aka tafi har cikin gidansa aka kashe Ameenatunsu tana cikin nakuda ba Dan Allah yasa Ameenatou rabo bace da yanxu baisan a wane matsayi rayuwarsa take ba Babu Ameenatunsa Babu abinda ta Haifa.
Ya jima a gurin zaune cikin tsananin damuwa da tashin hankalin da Bai Saka masa Rana ba Dan kuwa duk Jin yayi Lagos din fitar masa a Rai hankalinsa ya fara tashi matiqa.
Daqyar ya dawo da kansa gida sbd kirjinsa dayake wani irin ciwo da nauyi hakama zufa yake hadawa sosai ya kasa denawa.
Yana isowa gida ya shige daki batareda kowa yaga halinda yake ciki ba Dan sunacan sunata hayaniyar bikin da zaayi gobe Wanda Seelahs suka hada.
Omar ma yana komawa gida kusan damuwan tabasa tayi Saida likita yazo ya Danyi checking BP dinsa kafin ya shige cikeda damuwa Dan bayason nunawa Babbah karfinsa yanason ya aminta dashi suyi maganan Daya kamata kafin lokaci ya kure sbd idan ya nuna masa power kaman yaci mutuncinsa ne bayan Tsananin gata da son dayasan Yanawa 'yarsa fiyeda yanda yake son nasa yayan na cikinsa.
Ahmed dayaji shikam baida hakuri ko lokacin batawa akan lamarin Yanke shawaransa yayi Babbah dole ya saurare abinda ake son fada masa Dan Jin Wanda akeson aji daga garesa.
A cikin Daren jirgi ya sauke Jamaal tareda siddeeq a Lagos batareda sanin kowa ba Kuma a Daren yayi magana da Ahmed Wanda basusan Jamaal na qasar ba Shima Dan haka da safe siddeeq ne yaje mansion din Mam seelah ya dauko Haroon Wanda a ranar yake cikin farin cikin dayafi na kullum sbd daga ranar sai ranar daurin aurensa da mutanensa da yawa Shima suna Lagos Dan halarta daurin auren goben.
Wata lafiyayyar tsadaddiyar Lodge din da Jamaal yake siddeeq ya Kaisa Yana shiga Jamaal dayake jiransa ya fito tareda siddeeq din suka barsa acan sbd Jamaal din na buqatan ganin Dad Jden.
A rumfar hutawan Dake bayan mansion din ta gurin garden suke wadda ta hada kofofin gidajensu uku batareda saika zagayo ya gate ba kake shiga tanan Dan haka yasa familys din suke kaman a gida gade guri daga daga baya Baya gaban mansions din ba.
dukkaninsu ne a zaune su uku sai Ahmed na hudu suna zaune cikin Hutu da nutsuwan Wainda arziki da Hutu ya ratsa fira sukeyi Hakama table dayake gabansu tea ne kusan kala hudu a different tea set masu kyau da tsada sai healthy snacks na Manyan mutane sai wayoyinsu da Kuma jaridan yau.
A Jden mansion baa yadda motar kowa nene ta shigo gidan ba iya ta masu gidan ce kadai take shiga ta Kuma fita Dan haka siddeeq baima nufi gidan Kai tsaye ba mansion din Dad ya shige sbd securities ma na ganin motar Haroon ce ta dawo suka wangale gate din ya shige da ita yayi parking.
##MAMUH#
*_ZAFAFA BIYAR_*
1 *_Ameenatou!!_*
_Mamuhgee_
2 *_Tsutsar Nama!!_*
_Billyn Abdull_
3 *_Gudun Kaddara!!_*
_Safiya huguma_
4 *_Kwankwason Jimina!!_*
_Miss xoxo_
Guda Daya 400
Guda biyu 700
Guda uku 1k
Guda hudun 1200
*_6019473875 MUSAA ABDULLAH SAFIYAH keystone bank_*
*_ATURA SHEDA ZUWA 09166221261_*
*_MTN/VTU 09134848107_*
_*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din 09033181070*_
*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_**_Arewabooks@Mamuhgee_*
49
https://chat.whatsapp.com/K3rO5UonX4GDVxtQbA5mZl
Assalamualaikum wa rahmatullahi ta'ala wa barakatuhu!!! Wannan group din dai na komai da komai ne. A taiqaice
*Farashin mu na daban ne compared to sauran Yan kasuwa
*Kaya masu kyau da quality. Abinda kika