Showing 36001 words to 39000 words out of 93806 words
kaunarsa.
Ko Alh Lameenu lokuta da yawa shi kansa Yana tsoro da shakkar yanda Mam ke tsananin son Jamaal Dan haka yake gudun kada Hakan ya zama raunin Mam su samu matsala sosai me girma tinda Jamaal din kwata kwata ba page Daya suke dashi ba akan abinda suke aikatawa Dan ma Allah ya rufa musu asiri ba shine lawyer ba Haroon ne da kashinsu ya Dade da bushewa duk power dasuke riqe da ita suna juya sharia yanda suke so da sai Jamaal ya tabbatarda sun rasa komai.
A Daren ranar firan da suka jima a tsakaninsu basuyiba Saida sukai shida Dad ciki kulawa da kauna har tsawon dare kafin ya fito ya wuce part dinsa tareda Haroon da Shima ranar kaunar Yan biyunsa ta motsa a part din zai kwana.
Bedroom dinsa ya wuce Kai tsaye ya fada wanka zuciyarsa na samun nutsuwan dayake buqata wadda ya rasa a kwanakin sbd rigimansa da Dad.
Haroon ma Dayan dakin ya nufa wankan yayi ya fito Kai tsaye ya nufi bedroom din Jamaal ya Bude closet dinsa ya dauko kayan bacci black ya Saka ya fito yaje kwanta,sai a lokacin Jamaal din ya fito ya shirya cikin fararen kayan bacci ya kwanta tareda dauko wayarsa Yana Kiran fadila a natse.
*******Amincewan Dad shine babban abinda yayiwa kowa dadi da farin ciki har bangaren su fadilan wadda batada wani qwari ko kuzari Amma tayi murna sosai.
Babu Bata lokaci Jamaal ya buqaci ayi auren Dan kuwa a yanda yake sane da ciwonta yayi tsanani sosai Dan kuwa yanzu lungs dinta sunyi Nisa sosai oxygen ma Neman gagara riqesu yakeyi Dan haka yake buqatan auren zai fita da ita yaga wasu likitocin da zasu duba case dinta sosai tareda shi.
Bai sanarwa kowa ba har iyayenta matsalanta yayi muni sedai daga su har fadilan jikinsu yayi sanyi sosai Dan sosai kullum take sake zama weak numfashin ma ahankali ahankali take iya shaqarsa.
Hakanan suke lallabawa Dan asamu ayi bikin,
Fadila da kanta ta cire Rai daga rayuwa a yanzu Amma dai babban fata da burinta shine ta samu zama matar Jamaal kafin Allah ya dauki ranta,
Tanason cika masa burinsa na son ganinta a matsayin matarsa mallakinta kafin ta koma ga Allah Dan haka take fata Dan rokon Allah ya Bata qwari da qarin kwanakin da zata cika masa wannan burin.
Su kansu iyayenta duk yanda jikinsu yayi sanyi ga yanayinta a yanzu ta Basu qwarin gwiwan karban kaddararsu,
Suma a yanzu fatansu ta zama matar Jamaal kafin Allah ya dauki ranta
Idan hakan ta faru zasuyi farin ciki ko bayan ranta sbd burinta ya cika Kuma Jamaal ya zama sirikinsu baiyi musu wahalar banza a banza ba.
Jamaal kwanakin auren na sake kusantowa Amma kwata kwata kansa ya dauki zafi baida lokacin komai bayan tattaunawa da Neman yanda zaiyi ya kawowa fadilan sauki ta samu shakar numfashi me dadi da nutsuwa Dan lamarin yafara karya masa zuciya Amma Koda zaiyi yawon duniya da kasashe ne zai Nemo mata lafiya idan har Allah yayi zata warke din.
Kwanaki na sake kusantowa na auren fadila na sake zama weak sosai Dan yanzu gaba Daya tayi fayau kaman Babu jini a jikinta hakama sai qanqancewa takeyi tana rama da komawa karama.
A daidai wannan Gabar iyayenta sunyi kuka harsun godewa Allah sbd tinda take fama da ciwon tsawon shekaru Bata taba komawa Hakan ba sai yanzu gashi ita kanta wannan Karan ta fidda Rai daga rayuwa adaidai lokacinda taso ace ta rayu Dan bawa Jamaal farin ciki.
A rayuwar seelahs Babu Wanda ya taba tinanin zaa samu Jamaal a hali na fita hayyaci sbd kwallafa Rai a Abu sai yanzu.
Duk yanda su Dad suka dauki matsayi da girman yarinyar a zuciyarsa abin ya wuce Nan Dan haka hankalinsu yasake mummunan tashi akan lamarin auren.
Gaba Daya Jamaal ya aje komai ya tattara hankalinsa gaba Daya akan Neman mafitan ciwon fadila,
Kai tsaye ya ajiye komai har aikin asibiti sbd gaba Daya ta koma a kwance take rayuwa a kwanakin ga oxygen din kwata kwata kaman ya Dena mata aiko Dan haka take ya fasa jiran sauran kwanakin auren yace a daura kawai zai fita da ita waje mum dinsa ma tana Jira zasu taru da wasu likitocin su duba matsalanta Daya kasa Ganowa.
Babu Wanda yayi musu da maganar auren nasa dayace a matso dashi Dan Babu wani biki ko hidiman ma da zaayi tinda amaryan a kwance take tana Neman numfashinda zata shaqa ma ta rayu.
Haroon baitaba sani ko ganin haka asalin so yake ba sai akan Dan uwansa Wanda Bai taba Ganin abinda Jamaal yaso fiyeda komai ba bayan iyayensa dashi sai Fadila,
So ne me tsafta da karfin gaske da Allah ya jarabcesa dashi na yarinyarda ba lallai ta rayu ba Dan koshi da ba likita ba baiga alaman tashi ga fadila ba sedai kwata kwata Jamaal ya kasa yarda da fadilan bazata warke ba ta tashi ta basa 'yan biyun datai alkawarin basa Shima yayi alkawarin ita kadai ce zata zama uwar yayansa,
Ita kadai ce macen dayake son ta Haifa masa wasu Jamaal and Haroon Kokuma Mamman da Omar.
Tausayinsa sosai Haroon yakeyi tin yanzu Daya kasa gane komai ya jinginar da rayuwansa kwata kwata akan fadila da iyayenta da suka koma sune masu basa hakuri da qwarin gwiwa.
#MAMUH
#SEELAHS
#AMEENATOU BABBAH
#LOVE
#HOTLOVE
*_ZAFAFA BIYAR_*
1 *_Ameenatou!!_*
_Mamuhgee_
2 *_Tsutsar Nama!!_*
_Billyn Abdull_
3 *_Gudun Kaddara!!_*
_Safiya huguma_
4 *_Kwankwason Jimina!!_*
_Miss xoxo_
Guda Daya 400
Guda biyu 700
Guda uku 1k
Guda hudun 1200
*_6019473875 MUSAA ABDULLAH SAFIYAH keystone bank_*
*_ATURA SHEDA ZUWA 09166221261_*
*_MTN/VTU 09134848107_*
_*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din 09033181070*_
*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_**_Arewabooks@Mamuhgee_*
23
Mum dinsa ya buqaci zuwanta a kasar sbd ta tayasa duba yanayin na fadila dayake tsananin basa faduwan gaban da Bai taba samun kansa da tsoron wani abu ba sai yanzu Dan kuwa ko chances na surviving nata yaqi yadda ya duba sbd Bayason Jin ko kalaman rasawa.
Duk wani ayyuka Dake gaban Dr Aleena ajiyesu tayi tayi shirin zuwa Nigeria cikin damuwa sbd Jamaal da gaske ya Saka damuwan da tsoron matsalan fadila sosai.
A daidai gaban dayake yanzu shine ko dubata Baya iya yi da kansa saidai sauran likitoci su dubata.
Da kanta take kokarin bawa kanta kuzari da karfin hali Dan basa nutsuwan cewa tana samu sauki duk da Babu saukin datake samun saima tsananta da abin yakeyi.
Ranar da mum dinsa ta sauka Nigeria
Tareda Haroon sukaje daukota airport.
Kyakkyawar baturiyar da bazaka taba cewan itace ta haifi manyan zaratan matasan Dake tsaye suna jifanta da kallan tsananin kauna da kewa musamman jamaal da ganinta gabansa ya Saka dukkanin rauninsa Daya kasa bayyana gaban kowa bayyana a gaban mahaifiyarsa.
Itama kallansa tayi tareda zuba masa idanuwanta masu haske irin nasu tana kallansa zuciyarta na karyewa da tausayin abinda take hangowa acikin idanuwansa.
Hannuwanta ta ware daidai lokacinda ya ranqwafo yayi mata kyakkyawar runguma Yana lumshe fararen idanuwansa dasuka Dan sauya Yana Jin nauyin Dake zuciyarsa Yana rabuwa sbd ganinta
itama rungumarsa tayi dakyau tana Jin inama zata iya cire ciwon fadilan ta dawo dashi kanta Dan kawai bawa Jamaal din farin cikinsa.
Sun jima ahakan tana fada masa magana me sanyi cikin kunnuwansa tana shafa bayan kansa kafin suka saki juna ya riqe hannunta Daya Yana Jin nutsuwan Daya rasa tsawon lokaci na shigarsa kadan kadan.
Rungume Haroon tayi tana Jin kaman zata hadiyesa Shima kafin suka juya zuwa mota hannunta na cikin na Jamaal Wanda ke sanye da guntun wandon Dior da rigarsa ash sai fcap da sunglasses fuskansa Babu wani walwala sosai sai daukan ido yakeyi acikin Rana shida mum dinsa harma da Haroon da baiyi haskensu ba.
Mota suka shiga Kai tsaye Haroon ne me tuqin mum na Baya sai Jamaal din a gaba.
Kai tsaye gidansu fadila mum ya buqaci a fara zuwa tafara dubata tinda shine abinda ya kawota kasar.
Suna Isa kofar gidan babanta na waje tareda siddeeq 'dan kanwarsa data jima da rasuwa itama Yana karatu a Lagos din a hostel yake zama Amma tinda ciwon fadila yayi tsanani ya dawo gidan dole sbd baban yakai baida cikakkiyar lafiya Shima sbd zuciyarsa Dake kasa daukan rashin yarsa duk ya Tina da Hakan.
Suna ganin motar Seelahs suka San Jamaal ne.
Haroon ne yafara fitowa Dan haka suka tinkarosa siddeeq na masa barka da zuwa Saida Jamaal din ya Bude dayar kofar ya fito suka gane ba shine suka tinkara ba Haroon ne Dan haka suka juyo suka dawo bangarensa suna masa barka da zuwa.
Cikin girmamawa ya gaida baba Yana tambayar siddeeq exams dinsa Daya gama a jiya.
Fitowan Dr Aleena ne ya Saka baba da siddeeq kallanta suna tabbatarda itace mahaifiyar su Jamaal din sbd kamannin da suka hada Dan haka cikin mutuntawa da girmamawa sosai suka gaidata suna mata sannu da zuwa cikin turanci.
Amsawa tayi itama a mutunce kafin sukai cikin gida gabaki dayansu.
Umma ma tarban mutunci da girmamawa taiwa mum din da Haroon duk da Shima ya zama kaman na gida yanda Jamaal yakoma Kai tsaye Dan gidan baida shamaki da koina da komai.
Dakin fadila suka nufa tana zaune a jingine da gado an mata kariya da pillows masu taushi idanuwanta a rufe tana Jan wani kasalallen wahalallen numfashin dayake shiga lungs dinta daqyar.
Kallo Daya mum tayi mata ta juyo cikin sanyin jiki ta Kalli Jamaal Wanda yanayinta yake karanta Dan ko a Poland tana cikin manyan likitocin da ake alfahari dasu manya.
Qarasawa tayi har inda fadilan ke zaune ta Bude idanuwanta ahankali da Jin qamshinsa da shi kadai ne yake Ankarar da ita da zuwansa.
Akan mum ta sauke idanuwanta dasukai ciki sosai Bata iya budesu duka sosai sbd rashin karfi sosai.
Durqusawa mum tayi gabanta tana mata sannu cikin tsananin kulawa da nutsuwa kafin ta Kai hannuwanta biyu ta kamo hannun fadilan Daya tana gyara zamanta gefenta cikin sanyi ta tambayeta Yaya jikin.
Cikin nutsuwa da sanyin murya me tsananin taushi ta amsa tareda yi mata sannu da zuwa sbd karfin hali.
Tsit dakin yayi kowannensu na tsaye daga waje daga Jamaal din Se mum ne kadai a dakin tafara dubata tana Jin shakkar abinda tafara tinanin matsalan take.
Kallansa tayi lokacinda ta zare oxygen din hancin fadilan takai hancinta tana shaqa kadan tana Dan rufe idanuwanta Dan shaqarsa cikin relaxing komai nata.
Numfashin fadilan ne yafara sama sama Dan haka ta mayar mata dashi ahankali tareda sake kamo hannunta tana Jin pulse nata.
Cikin abinda Bai gaza mintina arbain na zuwa hamshin ta kusan gama karance matsalan fadilan ta gangan jikinta.
Kallan Jamaal tayi Wanda gaba Daya ya tashi daga likita a lokacin ya koma kaman me jiran sakamako.
Numfashi ta sauke tareda miqewa tsaye ta dawo gefensa ta tsaya a natse tace
"Ina buqatan ganin file nata yanzu a fito dashi daga asibiti a kawomin"
Kallan fadilan yayi tareda kamo hannunta Daya acikin nasa yayi mata sannu kafin ya Kalli mum cikin Dan sassauta murya Yana baro gurin fadilan yace
"Mum asibitin zaa tafi da ita yanzu ai sbd acan ne zatafi samun cikakkiyar time da kulawa da duk abinda ma zamuyi..."
Kallan fadilan itama mum tayi cikin sanyi da tausayi kafin ta dawo da kallanta kansa tace
"Abarta a gida zan dubata anan tareda duk abinda nakeson tantancewa sbd Ina tinanin koma Menene matsalan daga oxygen data shaqa ne yayiwa lungs nata mummunan illa a yanda na karanci numfashinta da kyau da yanda kirjinta yake amsa zuwa lungs din but Ina buqatan sabon oxygen akawo daga wani gurin daban bana asibitinku ba."
Manyan idanuwansa da suka mum din kallansa tana Jin sanyin jiki ya zuba mata Yana Jin gefen kansa na sarawa sbd tinanin oxygen nata nada matsala shine abinda Bai taba shigowa kansa da bincikensu ba sbd daga asibitinsu ake Bata shi Dan haka ma ne Bai taba tinanin Koda bugun iska wai zaa samu matsala a oxygen din datake shaqa ba,.
Hakan ne ya hanasa Gano asalin matsalan Dena shigarda da numfashi keyi dakyau kenan duk qwarewansa a aikinsa ko me??
Jin yayi kansa na Neman daukan zafi Dan haka mum tayi saurin fahimtar dashi tana tinani ne kawai Amma suna buqatan wani oxygen din kafin su tabbatarda Hakan ne.
Fitowa dukai dukkaninsu shine a gaba mum din na Baya Basu sanar da kowa komai ba Sukai musu sallaman zasu dawo anjima suka fito.
A mota shiru yayi yaja sauraron bayanan Mum datake qara Bude masa komai sbd itace take gabansa sosai a kwarewa da sanin aikinta.
Haroon ma kasa yadda yayi da zaa iya samun matsala a cikin oxygen din Daya fito daga asibitinsu sbd wannan babban laifi ne ake magana Wanda zai Saka a dole license na asibitin gaba Daya a rufeta Kuma hakanma zai iya taba aikin likitocinsu da yawa harma dashi Jamaal din.
Shiru Jamaal yayi Bai iya cewa komai sbd Jin zuciyarsa na tarwatsewa idan har ya tabbata akwai abinda yake cikin oxygen din fadila yayiwa lungs nata mummunan illar da Babu gyara bazai taba yafewa kansa ba akan sakacinsa.
Suna Isa gida Kai tsaye hanyar bangarensa sukai parking ya fito da kansa ya budewa mum din mota ya kama hannunta ta fito
Haroon kuwa kayanta ta fiddo dasu daga bayan motar suka nufi kofar palonsa.
Kai tsaye har bedroom din dayake part dinsa Daya yakaita Haroon ma ya shigo da kayanta yana sake juyawa zancen fadila a ransa tareda tsoron halinda Jamaal zai shiga idan Hakan ta tabbata,
Yana tsananin son Dan uwansa fiyeda komai da kowa a duniyarsa Dan haka bayason damuwa ko bacin Rai Bare tashin hankalinsa Dan haka duk ya rasa sukuni.
Key din motarsa ya dauka ya fice Kai tsaye asibitinsu ya nufa ya buqaci oxygen daban da sunan wani patient din zaa sakawa hakama ya buqaci wani daban da sunan fadilansa kafin ya dauko file nata ya fito asibitin.
Wani asibitin abokinsa ya buqaci wani oxygen din take ya biya ya karba ya dawo gida.
Koda ya dawo mum tayi sallah taci abinci ta huta ba laifi Dan haka ta sake wanka suka fitowa zuwa gurin fadila batareda Haroon ba sbd shine yayita kulawa da mum din tareda Mum Atee da Bata nunawa Dr Aleena din komai na hakama mummy Sarat matar Dad Lameenu ta shigo sbd Dr Aleena mutuniyata ce sosai
Tarba me kyau tayi mata tareda asmy da hawwah yayanta.
Kai tsaye daga gida office dinsa suka koma asibiti acan suka hau tsananin bincike da tantancewa tareda aune aune.
Kansa ba qaramin zafi ya dauka ba
Ita kanta mum din tana cikin fargaba da tashin hankalin abinda zasu iya tabbatarwa.
Haroon ya kira yaje ya taho dasu umma da fadila wadda kwata kwata bayason ana damar da ita da yawo.
A cikin Daren kwana sukai shi da mum dinsa da wasu amintattun likitocinsa suna bincike da aune aune harma da hotunan Daya kamata suyi mata duk sunyi.
Sai asuba suka samu kansu tareda tabbatarwa da Jamaal chances na surviving dinta Bai wuce 2% ba sbd koma Menene aka rikida oxygen din data Dade tana shaqa yayiwa lungs nata da cikin mummunan illanda sai addua kawai Amma dai idan har ta take lokacin aurensu zasu tafi da ita waje su miqawa wasu manyan likitocin su Gani ko zaa samu 2% din tayi Aiki.
Sakamakon Bai gama kammaluwa duka ba Dan haka mum ta Hana a sanar da Jamaal din abinda suka fara Gani Dan bandashi Akai sauran aikinba ta sallamesa ne.
Da kansa ya mayar dasu umman gida Haroon Kuma ya tafi da mum gida.
#MAMUH#
#DR JAMAAL JEEY SEELAH
#AMEENATOU SEELAH
#DR ALEENA SEELAH
#MAM SEELAH
#LAMEENU SEELAH
#OMAR SEELAH
*_ZAFAFA BIYAR_*
1 *_Ameenatou!!_*
_Mamuhgee_
2 *_Tsutsar Nama!!_*
_Billyn Abdull_
3 *_Gudun Kaddara!!_*
_Safiya huguma_
4 *_Kwankwason Jimina!!_*
_Miss xoxo_
Guda Daya 400
Guda biyu 700
Guda uku 1k
Guda hudun 1200
*_6019473875 MUSAA ABDULLAH SAFIYAH keystone bank_*
*_ATURA SHEDA ZUWA 09166221261_*
*_MTN/VTU 09134848107_*
_*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din 09033181070*_
*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_**_Arewabooks@Mamuhgee_*
24
Koda suka Isa gida mum tayi magana sosai da Haroon ta sanar dashi matsalan datake shakkan sanar da Jamaal Dan batasan tayaya zai fara ba Kokuma ta Ina zai fara binciken Wanda yayi wannan mummunan aikin na rashin Imani da tsoro tareda rashin tausayin daukan ran Wadda take fama da rayuwarta tin haihuwa.
Shiru Haroon yayi sbd Shima hankalinsa ya tashi da wannan zancen Dan kuwa yafara Jin tsoro da wani irin tashin hankalin na sake shigarsa idan har Jamaal ya tsananta bincike duk da baisan waye yayi wannan aikinba Amma dai Yana shakkar binciken Hakan ya binciko masa abinda zai karasa dagula Rai da kansa bayan yanzu lafiyan fadilan suke tsananin fata Dan itace farin ciki da abinda Jamaal dinsu ke buqata.
Koda Jamaal ya dawo gidan cikin Bai Nemo kowa ba Kai tsaye bangarensa ya nufa ya shige bedroom dinsa ya rufe kansa aciki.
Wanka yayi Yana fitowa sallahn azahar kawai yayi ya kwanta sbd kansa Dake Neman tsagewa da ciwo.
Bacci sosai yayi Wanda yake cikeda mafarkai masu nauyi Dan haka Yana tashi da laasar wani wankan ya sake jikinsa ya sake daga nauyi ya shirya ya fito cikin doguwar jallabiya fara qal Data kwanta jikinsa tayi masa wani irin kyau na nutsuwa.
Masallaci ya fita acan yayi sallah tareda Dad dinsa Wanda yayita Kiran wayarsa Baya samu.
Zuba masa idanuwa Dad din yayi bayan sun gama gaisawa ya tambayesa jikin fadila sbd gobe ne daurin auren nasu Wanda zaayi sa kaman na Wainda suka samu cikin shege sbd kawai yanayin amaryan.
A daidai wannan lokacin da gabar Jamaal din kansa yayi sanyi matiqa tareda shiga wani irin fargaba da tsoro me tsananin gaske.
Kai tsaye bangaren Jamaal din suka nufa hadda Dad din Wanda zaiyi magana da Dr Aleena Dan Basu zauna suka tattauna ba tinda tazo.
Suna shigowa tana zaune Palo tana karanta wasu bayanai ta email dinta da Dr Martinez ya dawo mata dashi Akan matsalan fadilan Data tura masa bayanan da komai nata tin jiyan.
Akan Jamaal idanuwanta suka fara sauka ta rufe iPad din hannunta tareda kifeta gefenta tana mayar da kallanta kan Mam da Shima ita yake kalla cikeda kulawa Dan har cikin ranta Yana Sonta Amma yasan bama zai fara maganar mayar da aurensa da ita ba sbd Jamaal dayaji zafin rabuwarsu fiyeda komai hakama dawo da aurensu Jin yakeyi kaman zata iya sanarda Jamaal wani abin game dashi ne shiyasa bayason zaman Jamaal a hannunta ya dawo dashi hannunsa tintini.
Sannu da zuwa tayi masa cikin sakewa da kulawa tana sake murmushinta me kyau da tsari.
Shima cikin farin cikin ganinta da kulawa yake amsawa yana qarasawa ya zaune kujeran gefenta Jamaal kuwa gefenta ya zauna Yana Saka hannunsa cikin nata sbd samun sassaucin abinda yakeji zuciyarsa na ciki ayau din.
Fira sukeyi sosai tsakanin mum din da Dad da Haroon Wanda