Showing 60001 words to 63000 words out of 93806 words

Chapter 21 - Ameenatou Book Original Complete Book .txt

25 Nov 2024

4042

sosai akan abinda idanuwansa ke gane masa na azabbiyar Son yarinyar dayake hangowa a idanuwa da hawayen 'dansa kwalli Daya daya rage a hannunsa.


Cikin sanyi da tattara nutsuwansa dan fahimtar komai yanda zai fishesa ya Kalli wayarsa shima tareda zubawa hoton Ameenatou idanuwansa zuciyarsa na shiga shakka da rarrabar tinani akan Aminta da ita ko sabanin Hakan sbd bazaiso tarihi ya Kuma maimaita kansa ba.


Dawo da kallansa yayi akan Haroon Yana dauke wayarsa daga kan table din yace


"Sbd itane ka tattarawa dukkanin nutsuwansa kayi Watsi da ita daga aikin dayake gabanka na cika mun alkawarin dakai na sakani alfahari dakai??
Kasan wane yaqin ne a gabanmu akan wannan masifar daka jefamu akan mace?


Muryansa na kasa fitowa sosai yafara kokarin magana Amma zuwa lokacin ran Dad din ya gama tafasa Dan haka ko sauraronsa beyiba ya miqe tsaye Yana cewa


"Ka shirya a yau din zaka bar Nasarawa ban aminta da zamanka ananba bare sake ziyartar Nan din,


Kasan me zai faru daga lokacin da na sake samun labarin ko 'dan uwan yarinyar Nan Daya ka sake muamala dashi???


Zasu bata ne gabaki dayansu danginta bazaka sake samun ko labarin Wanda ya taba saninsu ba bare sanin duniyar da suka tafi...


Qarasa zubewa yayi gaban Dad din Yana fashewa da wani irin kuka Mai tsananin tausayi da tashin hankali tareda Neman ficewa hayyaci Yana bawa Dad din hakuri jikinsa da hannuwansa na tsananta rawar Daya fara bawa Dad din mamaki da tsoro ya janye kafafunsa da karfi cikin zafi zaiyi magana Haroon din ya sake rarrafowa wannan Karan Yana rokonsa da cewa


"Dad Dan Allah kayi hakuri kada ka hanani Ameenatou,
Itace ke bawa zuciyata karfin hali da zuciyan da Banda shi,
Dad nayi Maka alkawarin wanna Karan wlh zan cika dukkanin buri da abinda kakeso idan ka barni da ita,
Dan Allah Dad ban taba tambayarka komai ba sai ayau din Ina rokon ka barni na aureta nikuma nayi Maka alkawarin zama duka abinda kakeso na zama,
Ka bani Daman karshe Dad zan gyara dukkanin matsalan da aka samu a wannan aikin nayi alkawarin Hakan please Dad.


Tafasa zuciyar Dad din ke karawa yanajin kaman ya shaqe Haroon din da kansa ya qarasashi Amma Kuma zuciyarsa na yaqi da Hakan Dan bayason rasa Dan Daya rage masa.


Rikicewa Haroon yayi ganin Dad din baida niyar sauraronsa hakama yasan kaman yanda Dad din ya fada batar dasu Ameenatou Abu ne me saukin gaske duk da Baya tinanin kashesu zaai ko makamancin hakan Amma dai koma Menene rabasa da Ameenatou kaman rabasa da dukkanin sauran Dan hankalin Daya rage masa ne Dan haka yaji Yana Neman zaucewa gaba Daya Yana tino yanda Jamaal ya rasa fadila har abada sai kawai yaji kansa ya kasa dauka ya sake rarrafowa Yana biyo Dad din cikin matsanancin fita hayyaci daidai Nan siddeeq ya shigo sedai kafin ya karasa gurin Haroon din tini yafara wani irin jijjiga Yana buga kansa da kasa Yana ambatar sunan Dad din Dana Ameenatou batareda ma yasan meyakeyiba.


Jini hancinsa da goshinsa suka fara fitarwa harma da bakinsa Yana wani irin fizga take hankalin Dad din yayi mummunan tashin da baitaba tinanin zaishiga ba ya dawo da sauri Yana Kiran sunan Haroon din da sauri sedai tini ya fice hayyacinsa dukkanin jikinsa na qara jijjiga sosai.


Siddeeq ma cikin matsanancin tashin hankali ya kamo Haroon din Yana janyo pillow na kujera ya Saka masa Akai tareda birkitasa Yana hanasa bubbuga kansa a tiles da jininsa ke fita sosai.


Rasa abinyi Dad yai Yana shiga sabon tashin hankali da mamakin Menene yake faruwa da rayuwar Haroon din,


Badai shi Kuma haukacewa zaiyiba akan mace ba,
Innalillahi wainna ilaihirrajiun"


Meke faruwa da yayansa?
Innalillahi wainna ilaihirrajiun.


Duk yanda Dad yake tsammanin lamarin ya wuce Nan sbd Haroon take ya koma tamkar me cikakkiyar tabin kwakwalwa duk tsananin zafi da bacin ran dayazo dashi jin yayi kansa Shima Yana daukan matsanancin zafi.


Siddeeq drawers ya nufa na gado da gaban mirror Yana yamutsa hankali tashe Yana Neman maganinsa Amma kwata kwata ya kasa Gani.


Cikin daga sauti da kidima Dad yake cewa


"Meyake faruwa dashi ne?
Menene Hakan nake Gani?
Ciwon hauka ya kamasa ne kokuwa?
Menene wannan din???


Duk a jere ciki daga murya da tashin hankali yake jero tambayoyi Yana kamo Haroon din Wanda yake jijjiga har lokacin.


A karkarshi pillow siddeeq ya sami maganin bayan ya haukata dakin cikin tashin hankali da mintinan da Basu Fi biyu ba ya iso da sauri yana Bude maganin ya kamo kan Haroon ya Saka masa
Tsaban rudewa Dad dinne da kansa ya dauko ruwa ya miqawa siddeeq ya basa rabi na shiga bakinsa Rabi na zubewa harya hadiye maganin.


Sakewa jikinsa yayi Dad yayi gaggawan Bada umarnin a fito dashi zuwa asibiti shi kansa siddeeq a daidai wannan lokacin yasan likitocin gaske Haroon yake buqata Dan haka ba Bata lokaci aka kwashi Haroon din sai asibiti.


Suna zuwa aka karbesa sbd duka jikinsa ya Dena rawa ko wani abin sai kawai aka miqasa da cewan faduwa yayi.


Dayake Mam yasan abinda zai iya faruwa na zuwan Yan jarida take ya Bada izinin securities kada su bar yan jarida zuwa ko sanin komai.


Har yamma sosai suna asibitin Haroon Bai farfado ba,
Dad magana yayi da siddeeq sosai yaji komai gameda ciwon Haroon da lokacinda ya fara take ya fahimci ba karamar illa maganinsu keyi masa ba Ashe Dan haka take ya sake shiga tashin hankali da damuwan kada Yan jarida ko kadan Susan dansa Barr Haroon seelah na fama da tabin kwakwalwa.


A Daren suka koma Abuja dashi sbd hankalin Dad Bai kwanta ba anan din.


Su Babbah da suka samu labarin anbar Nasarawan da Haroon hankalinsu tashi yayi Dan kuwa ciwonsa kenan yayi tsananin gaske haka suka ringa Kila mintina bayan mintina Dan Jin lafiyansa.




A cikin kwana da wunin Dad yayi sakawa da warwaran datafi dari da hamshin hakama Dad Lameenu ma hakanan ya lallabo ya taho sbd yasan Mam din na cikin damuwa da matsanancin hali Dan haka ya taho su fuskanci lamarin tare duk da Shima ya kasa warware sbd Bai dawo daidaiba idan ba Jin yayi sun samu mafitan warwara ba.


A cikin kwana da wuni Dad ya tabbatarda irin tsananin so da kwallafa Rai da Haroon yayi akan AMEENATOU sunan Daya riqe Kai tsaye sbd Tinanin dasuketa yawo akansa.


A karon farko da zai sauya raayinsa zuwa wani raayin Dan cimma burinsa cikin sauri da samun mafita biyu,tasa data rasa 'dansa.


Shi kansa Dad Lameenu yashiga firgicin tarihin dayake Neman maimaita kansa,
Idan sun rasa Jamaal sun tabarbare haka to Haroon dinma dasuke ganin baida amfani suna rasasa karasa tabarbarewa zasuyi komai yazo karshe shikenan.


Farfadowan Haroon Saida ya bawa dukkaninsu tausayi sbd yanajin jikin sosai Dan wanna Karan maganin ya Riga yayi masa illa sosai da Babu wani abinda zaa iya yi sai ikon Allah.


Su Dad kasa barin kowa yaji zancen sukai sbd a nasu tinanin maganinsu ne yayi masa wannan mummunan illar.


Duk tsananin halin dayake ciki kallan Dad dinsa yayi har lokacin yanajin raunin batawa su Dad din Rai dayayi da asarar da shi kansa baisan ta inda zai fara gyara ba.


Rokonsa gafara da sake basa Dama shine abi farko Daya furta Yana rintse idanuwansa.


numfashi Dad din ya sauke tareda Gyara zamansa Yana kallansa cikin nutsuwa yace


"Zan sake baka Daman karshen Amma ba iya akan aikin kadai ba,
Zan nema Maka auren Ameenatou Amma sai idan ka cika alkawarinka ka gyara mummunan Barna da Tsaka me wuyan daka Saka SEELAHs gaba Dayanta aciki idan ba Hakan ba ka manta da maganar aurenta Dan kuwa har abada bazaka auretaba idan ba Hakan ne ya faru ba"


Rintse idanuwansa yayi hawayen ciki masu dumi suna gangarowa ya gyada kansa cikin wani irin sanyin jikin da mutuwar jikin batareda ya iya cewa komaiba sai tsananin tsoro da shakkan Dayake mamayesa.


Dad Lameenu da Baice komaiba gyara zama yayi Yana kallan Haroon din cikin nutsuwa Shima ya Bude Baki yace


"Haroon nayi Maka alkawarin bazamu bar garin Nan ba ayau sai munje munyi gaisuwar iyaye da iyayenta sbd Neman Maka aurenta idan har zaka nutsuwa ka fuskanci nauyin dayake kanka sbd Kaine kaidai zaka iya gyara wannan Barnar data riskemu sbd kafi kowa sanin halinda muke Neman fadawa idan bamu farfado ba.


Tinda suke magana idanuwansa a rufe suka Hawaye masu zafi na gangarowa a acikinsu Saida Dad Lameenu yayi masa alkawarin nema masa auren ya Bude idanuwan ahankali ya kallesa Yana sauke Kai kasa.


Dad dinsa ma Jin yayi yayi Naam da Hakan Dan shine maslaharsu ayanzu kada su maimaita kuskuren Baya gwara su nema masa auren su juyasa akan abinda sukeso tinda zai iya komai akanta din.


Duk yanda wani zai samu Daman sanin matsalar ciwon Haroon Saida Dad ya tabbatarda Bata fita ba hatta siddeeq Bai bari likitocin sun bari yasan duk wani abinda aka bincika aka Gano ba har suka sake kwana biyu a garin Akai sallamarsa a ranar suka kwasa zuwa Nasarawa Dan Kai gaisuwan Neman auren.
#MAMUH#*_Arewabooks@Mamuhgee_*
39
****Su babbah da suka samu labarin zuwan da Dad din zasuyi gaisuwa tini aka gyara koina hatta kofar gidansa Saida aka share har kofar gidan makota aka shirya tsaf Dan tarbonsu da Aminansa guda biyu da zasu tayasa karban gaisuwan.


Dayake ranar su Dad din zasu koma da wuri suka iso guraren karfe daya na Rana Dan haka su Babbah suka tarbesu da girmamawa da mutuntawa sosai har cikin fara isowan gidan babban suka zauna a babbar dadduman da aka shimfida musu me kyau.


Dad Lameenu Dayake amsa gaisuwansu cikin girmamawa da kulawa sosai Shima tareda farin ciki me tsananin da tin anan aka fara farin cikin Samun Sirikai irinsu da duk kudi da matsayinsu sunsan mutuncin mutane da iya mu'amalantarsu.


Babbah Dad Lameenu yayi kallan tsaf Mintina Yana tantance kamannin nasa da son tabbatarda idan shine Wanda yake tinanin shi dinne.


Ganin irin kallan da Alh Lameenu kewa Babbah ya sakashi sai farin ciki yake sake shiga Yana sake musu barka da zuwa kafin ya tambaya jikin Haroon cikin kulawa sosai Yana dorawa da cewa sai anjima su Abdul su shiga dubasa Inshallah.


Abinda ya tarasu suka shiga gabatarwa Babu wani Bata lokaci suka gabatar da kansu da Neman auren Ameenatou da suka zo nemawa dansu Haroon Wanda su Babbah sun sanshi kuma sunsan aikinsa da halayensa daidai gwargwado.


Naam su Babbah sukai kafin suka suka sake gabatar da kansu da shi babban amatsayin mahaifin Ameenatou wadda shine ya haifa abarsa da cikinsa Kuma yayi na'am da Hakan ya Kuma bawa Haroon aurenta.


Farin ciki da hamdala suka ringa miqawa ana sake taya juna murna Dad Lameenu ya cire kudin Neman auren Naira dubu dari biyar ya bayar kafin suka sake miqa godiyarsu har lokacin zuciyar lameenu wani tsalle takeyi cikin rudewa da rikicewa Dan kuwa ya sake tabbatarda Babbah ne suka tana Gani asibiti gurin Omar a lokacinda aka taba Kai masa attack idan Bai mantaba Kuma ya sake dubawa ya tabbata Babbah ne ya Gani Wlh.


Abdul da shine babban yayan Ameenatou Kuma dashi Akai zaman Neman auren Alh Lameenu ya kalla cikin kulawa Yana tambayarsa Aikinsa da karatunsa.


Cikin nutsuwa da ladabi Abdul din ya amsa masa matsayin karatunsa da aikin dayake yi.


Take Alh Lameenun ya nuna raayinsa na Taimkawa yace Abdul din ya hada takardunsa zai Aiko a karba a aika masa Lagos.


Godiya Abdul din yayi su Babbah dasu Alh sabi'u makocin Babbah godiya sukai suna sake nuna Jin dadinsu kafin su Dad suka saki jiki sosai sukai fira da maganganu dasu babban anan ma sukai sallah azahar kafin suka Shirin tafiya su Babbah suka rakosu har waje inda motocinsu da securities dinsu suke suka shiga take aka bar gurin dasu.


Suna barin gurin Dad Lameenu zufan dayake hadawa tin acan yana shanye abinsa a jikinsa ya zari tissue ya goge kafin ya Ciro wayarsa.


Hotunan da BB ya turo musu nasu babban ya Nemo hannuwansa na Dan rawa ya Nemo na Babbah ya zuba masa idanuwansa.


Mam da zuciyarsa kwata kwata Bata cikin dadi Baida energy din tambayar abinda yake faruwa sbd bayajin zai taba barin ya hada zuria dasu Babbah
Ya nema auren ne sbd yana buqatan Haroon din sbd ya Jamaal ya dawo garesa Amma Badan Hakan ba bayajin zai tana yadda ya Kai kansa Neman auren.


Lameenu Daya sake goge zufansa miqewa Mam wayar yayi Yana cewa


"Wannan shine fitilar da zata kaimu ga sanin duk inda dangin matar Omar suke sbd samun Magajinsa"


Kallan wayar Mam yayi kansa na tsananin sarawa da nauyi Amma Jin Abinda Lameenu ya fada ya sakashi cire hannunsa daga goshinsa Daya dafe idanuwansa a lumshe.


Kallan Lameenu din yayi bayan ya Kalli Babbah a wayar Yana jiran bayaninsa.


Cikin nutsuwa lameenu ya tinatar dashi ganin da sukaiwa Babbah a asibiti tareda Omar shekarun Baya.


A saninsu wancan lokacin daga kauyensu Omar yace musu babban yake Amma basusan Menene alaqarsa dashi ba Dan haka dole babba yasan waye yayan matar Omar Kuma bazasu rasa sanin komai ta hanyar Saba Daman a bagiren Neman ko mutum Daya daga kauyen suke amma tsawon shekaru ankasa samu.


Wani sanyayyan sanyi ne ya ciked zuciyar Mam take yaji nauyin zuciyarsa na rayuwa sedai bayajin zasu samu yanda suke so idan suna nesa dasu Babbah din.


Lameenu Dayasan dalilinsa Daman kenan na buqatan daukan Abdul aiki take ya Saka kira yace a tanadarwa Abdul din aiki me kyau da gidan zama a Lagos inda zai dauko iyayensa ya dawo dasu.




*********Su Babbah kuwa A nasa bangaren sunan jeden da Omar yake amfani dashi shine ya hanasa sanin shima Omar din seelahs ne Dan haka farin cikinsu kawai sukeyi.


Da daddare da kansa shi da su Abdul sukaje suka dubo Haroon din Wanda ya danne ya nuna musu karfin hali duk da Yana cikin tsananin tashin hankali da Tsaka me wuya sbd sanin Neman auren bashine aurenba indai Bai cika alkawarin Daya daukanwa Dad dinsaba,


Bayan tafiyarsu da daddare tsananta damuwansa tayi sbd gwara ace baa nema aure ba zai iya runawa ya hakura da Ameenatou Koda zai rasa ransa Dan kawai yabarsu su ta tsira Amma a yanzu da aka nema masa aurenta yasan ba janyewa sedai Kuma irin kaddarar fadila da Dan uwansa yake guje musu.


A cikin Daren siddeeq ya koma Abuja Bai kwana ba Saida ya samu report na komai da akaiwa Haroon ya turawa JEEY Wanda sakonsu ya isar masa a daren daidai lokacinda ya fito wanka daure da towel dinsa gabaki Daya jikinsa wata irin sheqi takeyi kaman Bai taba Shiga rana ba.


Hannunsa yakai ahankali ya dauki wayar Yana ganin report din ya Bude sakon Kai tsaye Yana karantawa.


Tsayar da fararen idanuwansa masu gigita Wanda suka kalla yayi akan report din idanuwan na sauya ahankali zuwa ja zuciyarsa na daukan wani nauyi take.


Shigowan kira ne ya sakashi rintse idanuwan ya budesu ahankali akan sunan Haroon daya bayyana kan screen din wayar.


Iska me dumi ya sake fitarwa daga bakinsa kafin ya daga Kiran batareda yace komaiba ya Dora wayar a kunnensa Wanda yayi daidai da Haroon din na kasa riqe kansa daga zubar da hawayen radadi da kuncin dayake cin zuciyarsa da rubabbiyar rayuwarsa gaba Daya.


Shiru Jamaal din yayi har lokacin Bai furta komaiba sbd wannan shine Karan farko da Dan uwansa ya bayyanar da tsananin kunci da baqin cikin rayuwar dayake ciki garesa,


Bai taba fada musu rayuwar wulaqanta da qasqantar dayakeyi a hannun su Dad ba,
Bai taba barin sun sani ba,
Bai taba nuna musu ba
Ya shanye komai ya hadiyewa kansa baqin ciki da radadin shi kadai Amma ayau dayake cikin tsananin hali ya kasa danne zuciyarsa daga Neman taimakon Dan uwansa Dan idan ya rasa Ameenatou zai iya rasa rayuwarsa gaba Daya batareda yasan rayuwar tasa tana cikin mummunan hadarin tsaka me wuyar da kowane lokaci komai zai iya faruwa ba.


Kasa magana JEEY yayi sbd sautin fitar kukan Dan uwansa dayake tarwatsa zuciyarsa Yana Kona jinin dayake yawo a jikinsa kawai kashe wayar yayi tareda Saka Kiran Siddeeq wadda Kiran na shiga ya daga cikeda girmamawa.


Magana yayi da siddeeq Yana gamawa ya kashe wayar gabaki dayanta tareda jefar da ita.




********Ameenatou gabaki Daya ta daga hankalin mutanen gidan sbd kwanakin Haroon kusan shida bata samun wayarsa Kuma ya Dena fita koina ko Hafiz yace kwata kwata ya dena fitowa aiki,
Yaya Abdul yaje dubosa harso biyu Amma Sam Baya samunsa hakama siddeeq Sam baa samunsa.


Daga hankalinsu Babbah tayi dadah batada aiki saina rarrashinta Hafiz ma kusan sosai suka damu gurin aiki Amma dai Sir siddeeq yace musu Yana hutawa ne sbd rashin lfy da yayi.


Babbah da kansa yaje dubo Haroon din Amma dai kaman duka kwanakin Bai samu ganinsa ba hotel din sunce Yana Abuja.


Ranarda ya cika sati Hafiz na Isa gurin aiki da safe sunfara aiki kenan lafiyayyar sabuwar motar Haroon Daya sauya batareda sun saniba tayi parking bakin site din.


Siddeeq ne ya tuqo motar Dan haka shine ya fara fitowa kafin aka Bude Dayan bangaren Haroon ya fito sanye cikin black Armani's da sunglasses Daya masifar fitarda hasken fatarsa dayake wani irin kyallin Daya Saka dukkanin ma'aikatan gurin ajiye aikinsu suna kallansa sbd kwarjininsa na yau din daban yake Dan duk Wanda yake gurin saida kwarjininsa ya cika idanuwansa hakama hasken Daya Kara a kwanakin Dan hutun Daya samu ya bayyana fiyeda mamaki.


Manyan ma'aikatansu da sauran manyan Dake cikin project din tasowa sukai dukkaninsu suna tahowa gurinsa Dan ganin sauyi sosai a fuskansa na Babu sakewa ko kadan Dan Kuma kamewa.
#MAMUH#




*_ZAFAFA BIYAR_*


1 *_Ameenatou!!_*
_Mamuhgee_


2 *_Tsutsar Nama!!_*
_Billyn Abdull_


3 *_Gudun Kaddara!!_*
_Safiya huguma_


4 *_Kwankwason Jimina!!_*
_Miss xoxo_


Guda Daya 400
Guda biyu 700
Guda uku 1k
Guda hudun 1200


*_6019473875 MUSAA ABDULLAH SAFIYAH keystone bank_*


*_ATURA SHEDA ZUWA 09166221261_*


*_MTN/VTU 09134848107_*


_*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din 09033181070*_


*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_**_Arewabooks@Mamuhgee_*
40
Takowa yayi ahankali Yana nufar cikin site din Kai tsaye dukkanin sauran abokan aikin na biyo bayansa.


Siddeeq Dake gefensa umbrella yafara kokarin Bude masa Amma ya girgiza Kai ahankali batareda ya juyoba yana kallan site din da gaba Daya ma kusan aikin Daya bari bama ko kusa dashi ne ake kan yiba.


Hafiz Daya aje aikinsa Yana goge hannuwansa ya nufi ruwa ya wanke hannun zai nufi inda su Haroon din suke saiyaga sunzo sun wuce ya inda yake tsaye Yana murmushin Jin dadin ganin Haroon din da lafiyar Daya samu wadda ta sauya musu shi gabaki Daya Dan shi kansa Jin yayi gabansa Yana faduwa da ganinsa tsaban cika ido da wani irin sauyawan da yayi Dan har gashin kansa dayake kwance kaman na mace tsaban gyara ya sake sauya musu shi,


Wucesa sukai batareda Haroon ya Kalli inda yake

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login