Showing 66001 words to 69000 words out of 93806 words

Chapter 23 - Ameenatou Book Original Complete Book .txt

25 Nov 2024

4047

fito lafaffiyar cikinsa dake fidda murdewan jikinsa sbd motsa jiki ya sauko kasa sbd Yana buqatan ruwa da drinks sbd aikin da zai kwana yanayi sallah Kuma Daman kafin su baro Nasarawa sunyi ishai ma kafin su shigo gidan sunyi.


Siddeeq ma tini yayi wanka ya shirya cikin gajerun kayan baccin da sukaiwa jikinsa kyau Shima Dan Shima Yana motsa jikinsa sosai Dan hakane ma yafi Haroon budaddiyar jiki kaman ubangidansa.


Shima fitowansa kenan yaji saukowan JEEY da kamshinsa Dan haka ya dakata harsaida ya sauko kallo Daya yayi masa ya dauke idanuwansa sbd JEEY SEELAH ko namiji Dan uwansa yake kallansa zai iya kamuwa da sonsa bare mata Danma Baya mu'amalantar inda mata suka yawaita da baasan irin matan dazai samu masu jiransa ba, har mamakin yanda JEEY din ya kamu da son fadila yakeyi da yanda zuciyarsa take riqe da iya ita kadai yakeyi.


Ruwa Jamaal din ya buqata da E-Bull energy drink dinsa.


Daukowa siddeeq yayi ya kawo masa ya ajiye a gefe hakama already tarin manyan takardun abinda zasuyi suna gurin zube.


Kafin ya fara aikin bayan ya zauna dago fararen idanuwansa yayi ya Kalli siddeeq ya Bude Baki a natse yace


"Zamu bi morning flight zuwa Lagos ka duba mana idan akwai"


Dagowa siddeeq yayi ya Kalli JAMAAL din cikin mamakin ta yanda zasu fuskanci juna da Dad dinsa batareda ya gane shi bane,
Hakama shi kansa Jamaal bazai iya kwantar musu da Kai ba komai tsanani kaman yanda Haroon kansa bayama dagowa a gabansu saita Baci.


Cikin nutsuwa da tinani siddeeq ya sake kallansa Yana cewa


"Dr ko zan kira Dad din na sanar masa wani uzurin dazai daga tafiyar gobe zuwa jibi idan Barr da Mum din sun iso"


Girgiza Kai yayi a natse Yana cewa


"Ba buqatan Hakan,zangansa da kaina"


Sake shiga fargaba Siddeeq yayi duk da yasan idan Jamaal din ya fada ta zauna Amma a gaban Dad Kam Abu ne me wuyan gaske idan baa take zai sheda Jamaal ne gabansa ba ba Haroon dinba ko daga kamshinsa da Baya boyewa kowa da Kuma fatansa data banbanta data Haroon duk da idan suna rarrabe baka ganesu Se Wanda yayi da gaske gaske idanma kayi musu farin sani kenan hakama izzar Jamaal har abada ba Daya take data Haroon dinba.,
Tayaya Jamaal zai iya tsayuwa a gaban Dad dinsa batareda yayi masa kallan dazai Saka Dad din take Ji ajikinsa Jamaal ne.


Jamaal Daya miqa hannunsa a natse ya dauki drink din gefensa ya Bude yakai bakinsa yasha kusan Rabi ajiyewa yayi Yana Bude laptop din Dake gabansa ya kunna kafin ya fara janyo takardun Yana budewa tareda jerawa a gabansa sbd acikin kankanin lokacinda bazai ci masa time din komawa rayuwarsa ba yakeson kammala dukkanin aikin project din sabo da zaiwa Dan uwansa ya tattara ya koma bama tareda wani yasan ya shigo qasar ya fice ba.


Shima siddeeq tattara hankalinsa yayi sbd nutsuwa ga aikin da Jamaal zasuyi.


Nutsuwa yayi sosai Yana aikin cikin kwarewa da tabbatarda komai ya tafi daidai,Shima siddeeq mayarda hankali yana Wanda zaiyi a cikin aikin.


Har kusan hudu saura na guraren asuba suna aikin kafin suka ajiye suka nufi dakunansu.


Jamaal na shiga bedroom dinsa Kai tsaye toilet ya nufa yayo alwala ya fito ya Dora gatuwar jacket akan kayan jikinsa na bacci ya rufe batiran rigarsa Dake Bude ya Saka qaramar hulan sallah fara akansa ya tayarda sallan nafila.


Yana gama sallolin nafilansa ya miqe Dan sallahn asuba da Akai kira har ana kokarin tayarwa daga masallatan nesa Dayake jiyowa.


Bayan gama adhkar da adduoinsa miqewa yayi ya cire hulan da jacket din ya nufi gadonsa ya haye tareda kashe komai tin daga kan wayoyinsu da wutan dakin ya shige bargo a nitse Yana lumshe idanuwansa.




Bacci sosai yayi ya samu hutun jikinsa Dana kansa harma Dana zuciya kafin ya tashi guraren 10 da wani abu.


Toilet ya nufa Kai tsaye yayi brush da sauransu tukuna yayo wanka ya fito daure da towel ya nufi inda wayoyinsa suke ya miqa hannu ya kunnasu kafin ya wuce gaban mirror Dan shiryawa.


Bai wani dauki time ba ya shirya ya fito cikin Ash kaftan din Tsadaddiyar yadin cashmere data tsananin sake sauya kamanninsa zuwa wani bakon baturen bahaushe hakama hulan Daya Saka ya rufe gashinsa Daya sake banbantasa Dana Haroon ta qara masa kyau sosai.


A Karan farko rayuwarsa dayayi amfani da wani turaren daba nasa ba Dan haka yakejin Baya wani Jin dadin iskan Daya bayarwa a jikinsa duk da Wanda yayi amfanin dashi Shima mugun designer ne sedai qamshinsa Daya Saba dashi daban yake a gurinsa.


Siddeeq da tini yayi musu booking tickets din 12 Dan haka Shima ya shirya tsaf cikin kaftans din Shima sai Jakar takardun aikinsu Dan laptop din dasuke hannunsa.


Jamaal na saukowa cikin girmamawa ya masa barka da saukowa kafin ya biyosa suka fito tare Jamaal din suna magana.


Siddeeq ne me tuqin Dan Jamaal Kam bayajin zaiyi tuqi harya gama ya tafiyarsa inda ya fito.


Kai tsaye office din dazai fara gabatar da aikin anan Abuja ya nufa ya zauna dasu ya gabatar musu da sauyin aikin dayayi tareda sababbin plans din dasuka matiqar Basu mamaki da sakasu farin ciki me tsananin gaske Dan kuwa tini suka fara Shirin gabatar da takardun soke aikin kwata kwata tareda raba hannunsu Dana Seelahs,


Hannu suka miqa masa cikin Jin dadi tareda taya junansu murnan sake samun damar aiki a tare Shima hannun ya miqa musu Yana sake gabatar da kansa BARR HAROON SEELAH.


Cikin farin ciki suka sake amsar tayin aiki da juna take akai hotuna da sabon Saka hannu akan new project din dazai maye wancan.


Sai guraren 11:20 suka baro Kai tsaye daga Nan office din airport suka nufa suna Isa suka ajiye motar anan airport suka shige jirgi sbd sunma iso kusan late.


A cikin jirgin yayi breakfast dinsa hankinsa kwance da nutsuwa sabanin siddeeq Daya kasa samun nutsuwa ko Kwanciyar hankalin sbd abinda zai iya faruwa idan aka samu matsalan Dad suka gane.


Suna sauka Lagos drivern Dad dinne yazo airport daukansu sbd shi Jamaal din da kansa Daya turawa Dad text din azo a daukesa daga airport Nan da awanni.


Da farko kaman Bai gane ba Saida ya sake karantawa ya tabbatarda Haroon dinne yayi masa sakon A tura driver ya daukosa daga airport.


Numfashi ya sauke ahankali Yana jinjina lallai Haroon din yafara samun karfin zuciya tinda ya iya masa sakon Kai tsayen Nan Mai kama Dana Bada order.


Driver na Isa airport Kai tsaye siddeeq ne ya budewa Jamaal kofa ya shige bayan kafin Shima ya zagayo ya shiga gaban motar driver Dake Satan kallan Jamaal din ta mirror cikin girmamawa yace


"Barka da dawowa Sir Haroon"


Gyada masa Kai kawai Jamaal yayi sbd hankalinsa na kan sakwannin asibitin Haroon da aka turo na can Poland Yana karantawa.


Suna isowa mansion din Jamaal ya hadiye wani abu Daya danne maqoshinsa Yana kashe wayarsa gaba idanuwansa na Neman sauyawa Amma ya Hana hakan sbd dawowa ko shigowa mansion din seelahs wani abune dabai taba tinanin zai sake ba har abada idan ba yanzu da Dan uwansa Dake tsananin buqatansa ba.


Sedai abinda Basu saniba shine kaman yanda yayi alkawarin duk ranar Daya Sako kafarsa ya dawo musu Saiya tabbatarda sun rasa komai to tabbas tinda ya Sako kafarsa ayau din ya dawo Saiya gyara musu komai sbd Haroon kafin suna kallo ya rabasu da komai daga ranar Daya tabbatarda Haroon ya mallaki macen dayake so fiyeda komai ayanzu.


Kai tsaye bangaren Haroon ya nufa Yana amsa sannu da zuwan da securities din gidan ke masa cikin tsananin girmamawa da mamaki me girma na sauyin Haroon din.


Yana shiga palon Haroon Kai tsaye bedroom dinsa ya wuce ya shige toilet alwala yayi ya fito yayi Sallah Yana idarwa wayar Dad na shigowa wayar Dake gefensa.


Kallan wayar yayi tareda dagawa cikin nutsuwa yayiwa Dad din gaisuwan Data Saka kirjinsa mummunan bugawa Saida yayi shiru ya sake sauraron muryan da kyau yaji sai yaji Yana Neman rudewa sai kawai yayi Watsi da abinda yaji Kai tsaye ya Bude Baki yace


"Ka sameni yanzu a office din cikin mansion din."


"Ok" kadai Jamaal yace tareda rigan Dad kashe wayan Wanda ya sake Saka Dad din mamakin halayen da Haroon ya fara sauyawa.


Saida yaci abincin da siddeeq yayi masa ordernsa daga tsadaddiyar restaurant ya koshi kafin ya shirya ya fito tareda siddeeq Wanda shine yake nuna masa hanyar da office din yake tinda Bai saniba.


Suna kaiwa kofar office din siddeeq ya tsaya daga waje Jamaal Kuma Kai tsaye ya Bude kofar a natse zai shiga sako ya shigo wayar Haroon Dake hannunsa Kuma Kai tsaye yasan Haroon dinne Dan haka ya dakata tareda duba sakon Daya bayyana akan screen din wayar inda ya rubutu masa tini tareda rokonsa akan yayi masa alkawarin ganin aurensa da Ameenatou ya tabbata kaman yanda tin farko yayi masa wannan alkawarin zai tabbatarda shi din Bai rasa macen da itace farin cikinsa ba kaman yanda shi Bai samu tasa farin cikin ba.
Lumshe fararen idanuwansa yayi da suka fara sauyawa Yana sake Tina alkawarin da yayiwa Haroon din zai tabbatarda su Dad da hannunsu sun aura masa Ameenatou kafin yabar kasar idan har auren Bai tabbataba to Allah ne yayi su din ba ma'auratan bane Kokuma Idan dayansu Baya raye wannan shine abinda mum dinsu ta roka daga Jamaal din sbd bazata so Shima Haroon dinta ya dandani irin radadin da Jamaal ke cikinsa haryanxu ba na Rasa Macen da ita kadai ya bawa zuciyarsa.


Numfashi me sanyi ya sauke ahankali mara sauti kafin Kai tsaye ya shiga batareda knocking ba kaman yanda Haroon yakeyi kafin shigan.


Yana shigowa Dad Lameenu dayake facing kofar ne ya zuba masa idanuwansa Yana kallo cikin Dan mamaki kafin Shima Dad din ya dago Yana kallansa Dan dukkanin idanuwansa mamakinsa a bayyane,


Dad Lameenu Daya rasa abin fada cikin yar rikicewa yace


"Da Jamaal Yana kasar Nan da babu abinda zai hanani tinanin shine a gabanmu,
Haroon hankalinka kuwa kake mayarwa akan aikin gabanka kokuwa gyaran fata ka mayarda hankali Akai sbd mace??


Dad da har lokacin idanuwansa na kan Jamaal din Yana Jin zuciyarsa na kokarin dawo masa da kewan Jamaal da tsananin buqatansa dayakeyi Kuma sai zuciyar ke Jin kaman ta samu Jamaal a gabansa Amma Kuma yasan abune da bazai taba yiyuwaba Dan Koda Jamaal Yana Nigeria ya shigo bazai taba Sako kafarsa SEELAHs ba Dan haka duk yanda idanuwansa ke nuna masa kaman Jamaal ne gabansa bazai yiyuba Dan haka ya dauke idanuwansa daga Jamaal din Yana sauke numfashi ahankali Shima Jamaal din sai alokacin ya ya dago ya zuba musu idanuwansa da suka sauya sosai sedai Bai furta komai ba Dan maganarsa a lokacin zata bayyanarda radadin ganinsu kawai Dake cin zuciyarsa Dan haka ya zabi yin shiru kaman yanda Haroon keyi a gabansu.
#MAMUH#




*_ZAFAFA BIYAR_*


1 *_Ameenatou!!_*
_Mamuhgee_


2 *_Tsutsar Nama!!_*
_Billyn Abdull_


3 *_Gudun Kaddara!!_*
_Safiya huguma_


4 *_Kwankwason Jimina!!_*
_Miss xoxo_


Guda Daya 400
Guda biyu 700
Guda uku 1k
Guda hudun 1200


*_6019473875 MUSAA ABDULLAH SAFIYAH keystone bank_*


*_ATURA SHEDA ZUWA 09166221261_*


*_MTN/VTU 09134848107_*


_*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din 09033181070*_


*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_**_Arewabooks@Mamuhgee_*
43
A cikin murya me nutsuwa Kai tsaye ya gaidasu Dad din acikin jam'i batareda ya Bada amsar maganarda Dad Lameenu ya jefesa da ita ba ta farko.


Dayake dukkaninsu kowa da abinda yake bakinsa na maganar Dake cinsu Basu tantance sauyin muryanba Wanda Daman Shima Haroon idan jikinsa na Sanyaye muryansa a natse da sanyi take fita Dan haka Babu Wanda ya tsaya amsa gaisuwan bare tambayar ya jikinsa Kai tsaye Dad dayaji Baya iya kallansa Dan yau din cika masa ido Haroon keyi sbd kamanninsa da Jamaal sun tsananta ayau dayake ganinsa kaman Jamaal Dan haka batareda y kallesa ba murya a daure da bacin ran abinda yayi yace


"Ko zaka bani dalilanka Daya Saka bawa project dinmu da ma'aikatan aikinsa Hutu harna kwana uku batareda sanar damu meyake faruwa ba??


Numfashi me sanyi ya sauke Yana dauke idanuwansa daga kallansu kafin ya Tako ahankali dukkaninsu sukai saurin kallansa ganin ya tinkarosu Yana kallansu Dad Lameenu ne yayi saurin cewa


"Amsar abinda yake faruwa muke buqatan Dani sbd Haroon Banga alamar zaka cika alkawarin daka dauka ba na sakamu alfahari dakai,
Aikin Nan fa duka duka sauran sati uku ne a time dinsa ya cika,.


Dad kallansa ya sake yi Yana Jin zuciyarsa na son shiga tinani daban daban Amma ya watsar Yana cewa


"Karka manta nutsuwanka akan aikin Nan shine tabbatan aurenka Dan Neman aure ba shine aurenba Karka manta da Hakan Dan nakai maquran rashin nutsuwan Nan taka,


A Hakan kake Neman mutuwa sbd mace kanason kayi aure batareda kasan ciwon kanka ba bare tinanin tsayuwa ka zama abin alfahari ga iyayenka ba tayaya zaka tsayu ka zama abinda matarka ko yayanka zasuyi alfahi dashi....


Dakatawa Jamaal yayi daga inda yake tsaye tareda dago idanuwansa da sukai ja ya Kalli Dad din dashi ma shi ya Dan kalla Yana cewa


"Yes, Haroon haryanxu ka kasa sakani farin cikin Da kowannen Uba yake shiga akan yayansa da alfahari dasu,
Alkawari nayi Maka akan idan kasakani farin ciki akan wannan aikin zan nema Maka auren da kakeso Amma......


Katsesa Jamaal yayi Dan bazai iya tsayawa sauraron wainnan maganganun akan Dan uwansa ba komai zai iya faruwa Dan zai iya bayyanarda kansa Dan haka wayarsa ya daga ya kira siddeeq take siddeeq ya shigo da takardun komai dasuka gama a yau din ya karba daga hannun siddeeq ya ajiye gaban Dad din Yana kallansa yace


"Gashinan Alkawarin zan cika Maka acikin kwanakin da bazasu kai na cikan kwanakin ba Amma Kuma a ranar da komai ya tabbata a yanda kakesonsa a ranar nakeson a daura mun auren da yarinyar....."


Daga dad har Dad Lameenu sakin Baki suke kokarin yi gurin kallansa da mamaki hankalinsu na rabuwa biyu daga abinda ya fada da Kuma karanta takardun Daya zuba a gabansu suna karantawa cikin tsananin mamakin sabuwar project din data dawo musu Da cikakkiyar damansu a hannunsu.


Dad Lameenu Daya kasa Kai karshen takardan cikin farin cikinsa Daya mantar dashi mamakin dasuka shiga yace


"Nayi Maka alkawarin daura Maka auren Ameenatou a washe garin ranar da Akai bikin Budewa duniya wannan aikin project dinnan Haroon idan abinda nake Gani da suna SEELAHs a jikin takardan Nan ya bayyana.


Dad ma mamakin ne yayi mugun kashesa kafin idanuwansa su sauka kan signature din jamaal Dake karshe wayarsa tayi ringing daga turawansu na Abujan ne Yana dauke idonsa Akai siddeeq ya matso Yana rufe file din tareda amsar masa cikin girmamawa Dan basa Daman amsa wayan wadda ta Saka Dad Lameenu washe dukkanin bakinsa cikin tsananin farin ciki Yana sake tabbatarwa da Haroon zuwa wani sati zai tabbatarda Abdul yayo parking da familynsa sun iso Lagos din gaba Daya.


Wayar da Dad keyi ta sakashi Shima dukkanin farin cikinsa bayyana Yana washe Baki Yana wayar cikin turanci Dan nutsuwa Yana Kuma Basu tabbacin wannan Karan Inshallah komai zai tafi daidai Nan da 3 zuwa 4 weeks komai ya zama cikin Shirin bikin qaddamarwa.


Dad na gama wayar Haroon din ya kalla cikeda farin ciki yace


"For the first time da yau nake alfahari dakai Son"


Kalman zafafa zuciyar JAMAAL tayi Dan haka baice komaiba sai sake fuska da yayi ya amshi zancen Dan kawai da zargi.


Buga kofar Akai kafin aka Bude tareda shigowa
BB ne Wanda duk kwakwalwansa take Neman Juyewa sbd ba dare ba Rana a bincike da yawon garuruwa suke da kauyuka gurin Neman da haryanxu Babu me baccin arziki akansa tsakanin shi dasu Mam din.


Tinda yake a rayuwansa wannan shine aiki mafi wahalan dayakesha mara sauko ko kadan a duk shekarun Nan,
Shi kansa sbd baqar wahalan dasuke Sha a wannan aikin yakejin bazai taba samun nutsuwa ko Kwanciyar hankali ba matiqar ba Gano abinda suke Neman sukaiba kaman yanda yasan har abada uwayen gidan nasa bazasu taba samun baccin nutsuwa da Kwanciyar hankali ba idan ba burinsu na shekarun cika yayi ba.


Cikin girmamawa yace


"Sir Haroon barka da dawowa"


Batareda Jamaal ya amsa ba Dad Lameenu ya Kalli siddeeq Wanda Shima Kai tsaye ya juya daga office din ya fice tareda Turo musu kofar.


iPad din hannunsa ya ajiye gabansu tareda bayanan daya samo akan bincikensu ya fara da cewa


"Ranka ya Dade na samu tabbacin 'yayan matar sir Omar Daya gudu da abinda ta haifa a daren yanada nasa 'yayan guda biyu Kuma dukkaninsu Maza ne sedai Kuma matarsa an bani tabbacin kafin barinsu gombe a wancan lokacin ta haihu Wanda nakeda tabbacin ba haihuwa tayi ba babyn sir Omar dinne"


Cikin zaquwa Dad Lameenu yace


"Bayanin inda suke shine babban abinda muke buqatan Jin idan an samo"


Hakama Menene asalin abinda aka haifa din?
Mace ne ko namiji??
Hakurina da bugawan zuciya akan wannan lamarin ya kusa kamani BB a gaggauta samo mana inda suke sbd tashin aikinmu yau da aka samu shi kadai bazai riqe mana matsayinmu da tsagwaran dukiyar da muka rasa ba muna tsananin buqatan dukiyarmu Dake hannun Omar.


Dad da Shima abinda yake ransa kenan ya Kalli Haroon dayake tsaye har lokacin gabansu Yana kallan fuskokinsu da bakinsu yace


"Haroon ya qara muku kudin Daya kamata banason aurensa yazo duk tsanani duk wuya batareda an samo mana inda suke ba,
Idan Kuma bamu samo Hakan ba to tabbas lokacin zuwansa garemu yayi Dan bazai taba yiyuwaba ayi auren 'dana dayake matsayin dansa batareda yazo ba,


Zuwansa Nigeria kuwa ba abune da zai taba yiyuwaba yazo ya tafi batareda ya kaiwa abinda ya Haifa da cikinsa ziyara ba Wanda shi da kansa zai kaimu ga Magajinsa batareda ya saniba.


Kallan Haroon ya sake yi Yana sake cewa


"Ka Basu duk adadin kudaden da suke buqata kaje ka fara Shirin aurenka Dan daga lokacinda Omar ya sauka a Nigeria dukkanin motsinsa a tafin hannunmu zai zama."


Gyara Kai Jamaal yayi Yana kallan BB dayakejin bazai iya barinsa ya sake ahakan iskan yanci ko Daya ba Amma Kuma Yana buqatan sanin abinda yake faruwa kafin komai Dan kuwa zantukansu sun Saka kansa daukan zafi.


Gyada Kai BB yayi Yana Jin nutsuwa da farin cikin Suma wahalallen burinsu ze Kai karshe sbd a saukake ma auren Haroon din zai kawo Omar har gida Kuma zuwansa kaman bayyanar abinda yake boye ne.


Maganganun sauran ayyukansu dasu BB din keyi ne suka fara Kai tsaye tareda tambayan huldan datake hannun BB din da yaransa ya tabbatar musu da komai Yana tafiya lafiya kalau duk da an kama wasu yaransa Amma ya tura yaronsa Daya Daya bari aka kamasa aka Saka cikinsu Sbd ya hanasu fadan komai sedai aka

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login