Showing 51001 words to 54000 words out of 93806 words
ciko idanuwanta da Hawaye tace
"Babbah to ai na Maka alkawarin bazan Fadi bafa ka gaya masa,
Kuma ni Allah wanna sallan shi kadai ma nakeso yamun komai tinda ya koma aikin site...
Wurgi yayi da Brush din hannunsa Yana yowa kanta yace
"Bazaki Dena renani ba ko?
Na rantse a gidan Nan kika kawo faduwan jarabawa silipas bazan Siyaba na sallanki sedai duk me Shure.....
Katsesa dadah tayi da cewa
"Babu me shurewa Dan bakayiba."
"Ai da kin bari ya qarasa da bakinsa Muji waye ze Shure din" inji Babbah Yana karban ledan hannun Ameenatou datake nuna masa kayan babu guga.
Miqawa Hafiz kayan yayi Yana cewa Maza gama shiryawa ka goge mata ko a shagon abokincan naka me dinki ne.
Kallan ledan kayan yayi Yana sake Jin takaici na siqesa ya juya ya kalli inda Yaya Abdul yake zaune Yafara cin abincinsa hankali kwance yace
"Dena kallona Dan kasan Babu inda zani guga yanzu Kaine me abokai masu shagunan dinki"
Kanta ya dawo da kallansa zeyi magana Dadah ta bisa da rarrashinda yasan anriga an cucesa ne ake toshe masa Baki.
Jinjina Kai yayi Dan zata shiga hannunsa ne gobe tinda shine zai daukota makaranta.
Wucewa yayi daki ya qarasa shiryawa ya fito baicewa kowa komaiba ya fice Yana jinta tana masa a dawo lafiya itada Dadah yayi musu shiru ya fice Dan wankan dayayi fita zashi aka sakashi zuwa guga duk yaje ya sake hado gumi duk da Daman shine mai yi mata guga Amma dai yau din ba lokacin yinsa bane.
Bayan fitarsa Abdul ne ya fara yiwa Ameenatou din fada Babbah ya dakatar dashi da cewa yabar zancen Nan tinda dai ba fandarewa yarinyar Nan tayi na.
Da daddaren kafin ta kwanta Saida ta Jira Hafiz din ya dawo sukai karatu dayake sake nuna mata abubuwan da Bata ganeba
Anan dai ya shiririce firar da Bai tafi ba kenan.
Washe gari Abdul ne yakaita makaranta ya wuce aikinsa daga can.
Karfe biyu saura Hafiz ya iso makarantar cikin sauri sbd aikinsa Daya baro ya taho yakaita gida ya koma.
Tana ganin sun kama hanyar gida ta riqe hannunsa tana narkewa tana rokonsa suje site tinda zeyi latti kafin ya dawo kuma ai uku suke tashi Dan haka bama wani Jira zataiba zai gama su wuce gida.
Yana Jin Hakan yasan wa takeson Gani Kuma cikin sa'arta maigidan nasu Yana Nan kaman yanda ta Saka masa suna bature Suma gurin tinda dadewa suka Saka masa suna baturen.
Kaman bazaije da itaba sbd ba gurin zuwan mata bane idan ba irin masu tallan nan ba duk da an dauki nauyin abincinsu acan ake basu abinci tin farkon aikinsu Amma dai yanzu tinda aka dawo dinnan baa fara Basu ba hakanan suke siyan na masu Siya shi Kam dai iyakacinsa ruwa Basa cin abincin siyarwa waje.
Kallanta Yayi Yanajin kaman bazai tafi da ita ba Amma mum matsalarsu shine Bata iya rokon Abu su kasa Bata shi Dan haka yace
"Muje Amma tattara aikina zanyi na ajiye mu dawo gida sai gobe na Dora."
Wani kyakkyawar murmushin daya lotsa simple dinta sosai ta sake tana Jin dadi tace "Eh na yadda Yaya Hafiz dina Rabin Raina"
Harararta yayi Yana yin gaba tana biyosa tareda miqa masa Jakarta ya karba Yana kallan fuskanta kafin ya kalli ranar da ake qwalawa yasan zeyi wuya batai zazzabi ba idan ta Dade a cikin Rana Dan haka kudin aljihunsa ya taba ya ciro yaga nawa ne.
Wani shago ya tsaya ya shirya umbrella ya Bude mata yana miqa mata.
Karba tayi murmushin tsananin kaunar yayan nata datakejin sonsu fiyeda yanda suke jinta kawai dai Bata iya zama basuyi rigima ne ba Amma tasan kaunarta a zuciyoyin iyayenta da yannanta bame misaltuwa bace.
Bata tafiyan sauri Dan haka a natse suka iso site din ya Kaita inda ya Saba cewa ta zauna ta jirasa yace ta zauna ta jirasa din.
Tinda suka iso gurin taji zuciyarta tayi wani irin sanyi da farin ciki Mai nutsuwa lokaci Daya ta rasa wane irin yanayi ne ma takeji akan wannan kyakkyawan baturen Daya fita idanuwa da zuciyarta.
Zaunawa take kokarin yi a inda Hafiz ya goge mata ya wuce idanuwanta sukai kyakkyawar sauka akan Haroon Daya tinkaro inda take Kai tsaye siddeeq na gefensa Yana duba wasu takardu hakama wasu ma'aikatan na biye dashi.
Sanye yake Dan kananun kaya Ash Shima da fcap a kansa sedai Babu sunglasses a fuskansa.
Kasa zama tayi ta tsaya cak tareda zuba masa fararen idanuwansa tana Jin farin ciki na dabaibaiyeta sedai Kuma idanuwanta sai suke ganin sauye sauye a tattareda shi duk da ta Dade sosai Bata gansaba.
Kyakkyawar fuskarsa da batai hasken ta Jamaal ba ta zubawa dukkanin fararen idanuwanta tana kallan mamakinta na qaruwa zuciyarta na sake hasko kamanninsa na Baya da suka tsaya tsaf a cikin idanuwanta.
Wayar dake hannunsa ce tayi ringing Yana gap da isowa inda take ya dakata tareda dago wayar Yana ganin sunan Wanda yake Kai ya daga Kai tsaye Yana ambatar sunansa cikin sautin nutsuwa da turancinsa me dadi Shima.
Lumshe fararen idanuwanta tayi ahankali lokacinda take Jin sauyin a sautin muryansa ma,
Bude idanuwanta tayi tana sake Dorasu akansa muryansa na sake ratsa jinta,
Idanuwanta da kunnuwanta sun tabbatar mata da sauyin abubuwa akansa sedai a zuciyarta shi din daine takeson Gani da Kuma ji Dan haka sai alokacin ta saki wani kyakkyawar murmushin daya sakata Jin kunyar kanta tana rufe fuskanta da tafukan hannuwanta tana Jin tin ganin datai masa farko shine Gani mafi farin ciki dataiwa Abu.
Haroon Daya gama wayarsa ya qaraso Yana kallan abinda sukazo dubawa gurin baima lura da mutum ba saida ya qaraso daf da ita yaganta ciki mamaki ya tsaya zai kalleta daidai Nan ta janye hannuwanta daga fuskanta kyakkyawar fuskanta daukeda murmushi sedai batasan da isowansa a gurin ba Dan haka ganinsa ya Sakata yin Baya da sauri sbd firgita da mamakin data shiga me qarfin gaske.
Shi kansa bayan yayi ahankali sbd kusancin da suka samu gashi murmushin dayake fuskanta wani faduwan gaba ya sakar masa Dan baitaba samun kusanci da mace ba haka a rayuwarsaba bayan Ayesha da yayan Dad Lameenu wainda su kannensa ne ba maganar Jin komai akansu.
##MAMUH#
*_ZAFAFA BIYAR_*
1 *_Ameenatou!!_*
_Mamuhgee_
2 *_Tsutsar Nama!!_*
_Billyn Abdull_
3 *_Gudun Kaddara!!_*
_Safiya huguma_
4 *_Kwankwason Jimina!!_*
_Miss xoxo_
Guda Daya 400
Guda biyu 700
Guda uku 1k
Guda hudun 1200
*_6019473875 MUSAA ABDULLAH SAFIYAH keystone bank_*
*_ATURA SHEDA ZUWA 09166221261_*
*_MTN/VTU 09134848107_*
_*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din 09033181070*_
*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_**_Arewabooks@Mamuhgee_*
33
Hafiz dayake nesa dasu da sauri ya qaraso gurin Yana bawa Sir Haroon din hakuri tareda sanar dashi Kanwarsace ya dauko makaranta yanzu wucewa zasuyi gida tabar gurin.
Ahankali Haroon ya mayar da Idanuwansa akan Ameenatou din ya kalleta Yana mamakin kalman daukota makarantar da Hafiz din ya ambata.
Ita kuwa bayan Hafiz din ya matsa ta batareda ta iya furta kalma ko Daya ba Dan samun bakinta datai da mutuwa 'dokin zuciyarta na ragewa batareda tasan dalili ba Kila Kuma zuciyarta tafi sonsa idan Yana daga nesa da ita ne.
Magana Jafar yayi mata a hankali wadda ta Sakata Dan fitowa kadan batareda ta kallesaba ta gaidasa cikin nutsuwa batareda tayi tinanin Yana Jin hausar ba.
Shi dariya ma ta basa Dan haka Saida ya saki Dan murmushi kadan kafin ya amsa Yana kallan Hafiz yace ya tafi da ita gida kawai yabar aikinsa zuwa gobe.
Ita kanta kaman tana jiran ya fada Hakan Dan haka ta wuce gaba batareda ta waiwayoba Hafiz kuwa wanke hannuwansa yayi tareda daukan Jakarta data barmasa yayiwa Haroon din godiya yabi bayanta Yana Bude mata umbrella data manta Yana cewa
"Salon ta ishesu da kukan zazzabi zai kashewa Babbah yar budewa ne yasakata biyosa cikin wanna uwar ranar gashi duk ta ruda masa aiki"
Shiru tayi masa Saida sukai Nisa ta waiwayo tana sake kallan Haroon Dake tsaye har lokacin Yana magana akan abinda sukazo dubawa.
Tin a hanya bakinta ya mutu har suka Isa gida Bata wani ishesa da magana ba Dan haka suna shiga gidan wanka kawai tayi taci abinci tafara kokarin kwantawa yasata gaba suka wuce islamiya Badan tayi niyar zuwa lolacinba Amma sbd tanason ringa biyawa ta gurinsa site hakanan ta shirya suke tafi.
Su kansu malaman sunyi mamakin zuwanta batareda latti ba yau din Amma dai dayake batajin hayaniyar Babu Wanda ya takurata da tambaya haka ta wuni makarantar ba hayaniya har suka tashi ta dawo gida tareda Yaya Abdul.
Washe gari ma haka suka biya site ya qarasa aikinsa ta zauna tana bin duk inda Haroon yayi da idanuwanta masu haske da kyau tana Jin kaman tace ya zauna ya Dena shiga rana duk da duk motsinsa biye ake dashi da umbrella sbd Rana karta tabasa.
Tinda take zuwa Bata sake bari ya ganta ba harta gama binsa da kallo tana murmushin su koma gida.
Abinda Bata saniba tinda kwanakin suka fara ja Yana sane da duk zuwanta da tafiyarta kuma ahankali ahankali ya fahimci sbd shine yake zuwan ta dauka bature ne shi da gasken.
Da farko lamarin mamaki da dariya yake basa sbd Bai taba Ganin inda asalin gata da tattalin 'yaya yake ba sai akanta hakama baitaba ganin kauna da kulawa me tsananin gaske ba da yanne kewa kanwa irin Wanda ahankali yaga anaiwa yarinyar.
Tinda tafara zuwa Bata taba tsallaken zuwa ba Saida exams dinsu ta karato sosai suna farawa shikenan ta Dena zuwa kwata kwata sbd karatu sosai da Yaya Abdul ya sakota gaba dashi
Shi kansa Hafiz sosai yake Bata lokacinsa suyi karatun exams din tare.
Barin zuwanta ya Saka Haroon tambayar Hafiz ko lafiyanta kalau ya sanar masa axams takeyi Kuma dai Bata jin dadi sosai sbd wahalan karatun.
A nata bangaren ahankali ta dawo hayyacinta akan zuwa ganinsa Dan haka Koda suka gama exam kwata kwata Dena zuwa tayi ga rashin lafiya sosai Daya kwantar da ita na kusan kwanaki Dan haka suketa fama da ita anata lallabawa da ita kaman kwai.
Shi kansa Haroon duk tsananin damuwa da quncin zuciyar dayake ciki Saida yazo har gida ya dubata Wanda Hakan ya Sakata Jin dadi sosai Suma su Babbah haka suka nuna masa Jin dadinsa sosai sbd Ameenatoun.
A nasa bangaren yanda ya samu iyayenta da karamci dakuma sake ganin irin so da tsananin gatan da ake nuna mata ya sakashi fara jinta a zuciyarsa sbd kallan datake masa lokuta da dama idan ta zuba masa kyawawan idanuwanta sai yakejin damuwar datake lullube da rayuwarsa kaman tana ragewa Dan haka ya Dan saki jiki da gidansu Ameenatou din musamman Hafiz dayake qarqashinsa.
A bangaren siddeeq kuwa komai na Haroon shine yake basa kulawa da tsaro yanda ya kamata Dan haka Koda yaga Haroon din yafara samun walwala da yar sakewa a cikin Iyalin Babbah sai Shima yaji ya samu nutsuwa da Hakan take Shima ya sake suka fara samun sabo da mutunci dasu din.
A bangare Daya rayuwar Haroon din na cikin matsanancin daci da damuwa tareda rashin farin ciki ko Daya sbd Dad dinsa da suka Saka ido sosai a lamarinsa hakama Babu alaman aikin Nan nasu zai samu karbuwa a inda zasu gabatar dashi Dan haka kowace dakika ta rayuwarsa cikin damuwa da 'daci me tsanani take Dan haka ciwonsa ma keyin gaba gaba koyaushe batareda sanin kowaba sai siddeeq Wanda ko numfashinsa Baya boyewa JEEY.
Shigarsa cikin Iyalin Babbah ya Saka Dan haske da farin ciki shigowa rayuwarsa a duk lokacinda yake cikinsu Dan takai kusan abinci ma wasu lokutan a gidan yake ci na dadah.
Ameenatou Kam zuwa yanzu tagama shiga zuciyarsa fiyeda yanda yake tinani duk da shagwabarta yayi yawa Amma shi Hakan ne ya kashe zuciyarsa ta mutu gabaki Daya akanta ita Kuma a nata bangaren a yanzu dayake tareda su sai ta aje maganan son datake masa ta jefasu a layinsu Hafiz duk da haryanxu kallansa takeyi a Wanda yafi kowa kyau da tsari Bata taba Ganin kamansa ba.
******Su Dad sun dukafa ba ji ba Gani sai barin kudi sukeyi hankali tashe gurin Neman Maryama Dan kuwa suna gap da zubewa gaba Daya Dan haka suka fice hayyacinsu.
BB ma sun haukace Baki ba ganin sunata tsananta bincike da zufafasa akan Maryama wadda daga karshe suka gano kauyensu.
Bayan barin dukiya me yawan gaske su BB Saida suka gano Maryama saigasu da ita har cikin Lagos sedai ko kwana batai a lagos ba Su Mam suka taho har inda su BB suka boyeta da daddare.
Mam ne ya fara tsayuwa akanta kafin Lameenu ya shigo bayan ya kashe wayarsa gabaki Daya daga wayar dayayi ya tsaya Shima yayi mata kallo Daya Yana komawa ya zauna kujeran alfarma dasu BB suka kawo musu na zama.
Shima Mam zama yayi Yana kallan BB batareda Bata lokaci ba Dan baida time na batawan yace
"Tatso mana bayanin komai daga bakinta banason rasa kalma ko Daya komai nakeson Jin a yanda yake dinsa."
Qwayar datake bakin BB ya qarasa hadiyewa idanuwansa na sake rinewa jajir ya miqawa yaronsa Daya hannu ya Saka masa wata mahaukaciyar wuqa da shape dinta kadai abin tsoro ne.
Nufar Maryama din da idanuwanta suke a daure yayi tareda tsayuwa a kanta ya kamo kanta ya Bude idanuwanta ya Saka mata wuqar gaban idanuwanta da sukasha mugun dauri cikin muryansa me kauri da karajin rashin Imani yace
"Ki kalla Menene a gaban idanunki"
Kafin ma taja numfashin tsoro da tashin hankali bare taga wainda ke zaune a gurin ya mayar mata da daurin idanuwan ya rufe.
Mayar da kaifin wuqar yayi akan jijiyan maqoshin wuyanya Kai tsaye yace
"Meya faru a Daren ranar da matar sir Omar ya ta rasu?
Akwai ciki a jikinta koda ranar tazo?
Wata nawa?
Ta haihu?
Me ya Haifa?
Ina abinda ta Haifa yake?
Waye taredaku a Daren ranar?
Ya Akai kika tsira a Daren????
Cikakken bayani zakiyi sbd rashin kalma Daya daidai take da ficewan ruhinki daga gangar jikinki."
Wasu Hawaye masu tsananin zafi ne suka gangaro daga idanuwanta dasuke a rufe zuciyarta na wani irin rawar tashin hankali da tsoro Dan kuwa tasan shikenan nata karshen yazo abinda taketa yiwa gudu sbd tasan Hakan zai iya faruwa wata ran sbd akwai tabbacin asan data tsira.
Sake daga wuyanta BB yayi Yana qarawa wuqar seti har seda ta Dan fasa wuyan jini ya Dan fito.
Zufa take fitarwa sosai kirjinta na wani irin mugun bugawar da kusan Suma su mam din kirjin nasu harbawa yakeyi sosai Dan kuwa a Baya duk zance ne sukeyi Basu tabbatarba sai yau din zasu tabbatarda masifar Dake gabansu tana can tana yawo a duniya batareda sunsan a Ina ba.
Lameenu kuwa har wani zufa yake tsiyayowa hannuwansa na rawa Da matsuwan Jin Abinda zata fadan,
Allah yasa Omar din Bai haihuba zance ne kawai,
Allah yasa suji abinda zai kawo karshen matsalar tasu idan ba Hakan ba akwai babbar matsala da kura a gaba.
##MAMUH#
*_ZAFAFA BIYAR_*
1 *_Ameenatou!!_*
_Mamuhgee_
2 *_Tsutsar Nama!!_*
_Billyn Abdull_
3 *_Gudun Kaddara!!_*
_Safiya huguma_
4 *_Kwankwason Jimina!!_*
_Miss xoxo_
Guda Daya 400
Guda biyu 700
Guda uku 1k
Guda hudun 1200
*_6019473875 MUSAA ABDULLAH SAFIYAH keystone bank_*
*_ATURA SHEDA ZUWA 09166221261_*
*_MTN/VTU 09134848107_*
_*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din 09033181070*_
*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_**_Arewabooks@Mamuhgee_*
34
Maryama gaba Daya ta cire tsammani daga rayuwa Dan haka cikin rawar murya da tashin hankalin da Bata taba Shiga ba ta fashe Da kuka zata fara rokonsu karsu kasheta BB ya sakar mata wani mugun marin bayan hannu Saida bakinta ya fashe Da jini sosai ya sake cakumo wuyanta Yana Dora wuqar kafin yace komai Baki na jini tace
"Koda ranar tazo tana daukeda tsohon ciki wata Tara......
Wani mummunan zufa da sarawan Kai tareda bugawan zuciya ne ya saukarwa Lameenu da Mam lokaci Daya,
Lameenu yayi saurin kallan Mam zuciyarsa na wani irin bugawa da karfi da tsalle sbd baitaba tinanin Jin Hakan ba,
Da gasken kenan dai Omar nada magajinsa,
Magajin dukiyar da baimasan Yaya zeyi da ita ba,
Gadon dukiyar tin suna samari suke dakonta cikin ransu,
Dukiyar da suka zama abinda su kansu basuyi tinanin zama ba ko a mafarki Amma daga karshe ace share fage ne kawai sukaiwa abinda Omar ze Haifa.
Mam kasa motsawa yayi bare juyawa ya kalla Lameenu sedai zuciyarsa kusan tafi ta Lameenun shiga mafi girman tashin hankali da firgici.
Shi kansa BB wani irin zufan tashin hankalin ne ya jiqasa Dan haka ya sake danna wuyanta Yana jiran sauran bayanan
Cikin rawar murya da ficewa hayyaci taci gaba da cewa
"Bata rasu ba a Daren sai bayan data haife cikin dayake jikinta,
Sir Omar yasan ta haihu sbd da kansa ma ya karbi abinda ta Haifa,
Oga Ahmed ma yasan ta haihu a daren...."
Kukanta karuwa yayi muryanta ya tsinkewa sbd tsoro numfashinta na Neman daukewa tsaban tashin hankali da tsoron wuqar Dake wuyanta tanajin kaifinta.
Lam da duka jikinsa ke rawa da zufa kasa hakuri yayi cikin zafi da matsuwa yace
"Me ta Haifa a Daren?
Waye Wanda kuke tareda shi a gidan wannan Daren?
Ina abinda aka haifa din yake?
Waye ya tafi dashi?
Wani sabon mari BB ya falla mata cikin rashin tausayi bare Imani Yana cewa
"Koro bayanin amsosin abinda aka tambayeki kafin na ratsa wuqar Nan cikin makoshinki"
Bakinta da duka jikinta na rikicewa da jijjiga Hawaye da majina duk sun cakude a fuskanta cikin matsanancin tsoron rayuwarta tace,
"Banda tabbacin abinda ta Haifa sbd a dare duka muna cikin tsoro da tashin hankali daga sir Omar Se oga Ahmed da 'yayan Hajiya Ameenatu din ne kadai suka San Menene aka Haifa tsakanin mace ko namiji...
A Daren yayanta yazo daga gombe gurinta Kuma shine ya tafi da babyn"
Wata sabuwar zufa ce ta tsiyayowa kowannensu Dan kuwa abin yazo a yanda basuyi tsammaninsa ba.
Sake danne wuyanta BB yayi tafara jero musu bayanin komai Daya bayan Daya har address din gidan Babbah dake gombe da yanda suka tsare da Kuma yanda Taga girman son dayake wa yar uwarsa da abinda ta Haifa din tabar masa.
Abu dayane ta boye shine cewan tasan mace ce aka Haifa sbd tsaban rufewa da shiga tashin hankali kwata kwata ta manta mema aka Haifa din.
Tana gama fadan kalamanta na karshe Mam ya miqe tsaye Yana ficewa daga dakin zuciyarsa Babu inda Bata tafasa da daukan nauyi.
Lameenu kuwa bayan ya miqe BB ya kalla da idanuwansa tareda yi masa kallan dayasan me yake nufi kafin Shima ya fice Yana Jin ihun Maryama din datai so Daya Bata Kara ba aka rufe bakinta.
Mota suka suka nufa da sauri BB ya qaraso ya budewa Mam driver Kuma ya budewa lameenu suka shiga Kai tsaye aka rufe driver ya shiga da sauri ya tayar da motar BB na musu a sauka lafiya suka bar gurin.
Tinda suka kama hanya Babu me cewa komai sbd kowa da Saka da warwaran da yakeyi a zuciyarsa cikin tinanin Neman mafita data inda