Showing 45001 words to 48000 words out of 93806 words

Chapter 16 - Ameenatou Book Original Complete Book .txt

25 Nov 2024

4028

hijabin tace


"Ai Babbah yace ko a waje karya taba masa ni"


Takarmanta dadah ta fitar mata kofar daki tana cewa


"Zo ki tafi kinyi latti sosai"


Jin haka ya Sakata fasa Saka takarman tana dawowa Baya ta dauko wayar Dadah din ta danna Taga karfe Hudu saura mintina kadan ita da ake fara tarewan latti karfe biyu da rabi.


Dadah na ganin ta ajiye wayar tana narke fuska tafara daga murya tana Kiran Hafiz.


"Hafiz fito ka Kaita makarantar ka roqi malam Dan Allah ayi mata hakuri bazata sake latti ba uzuri ne yasakata lattin."


Hafiz Dake daki Yana Saka kayansa Yana jinsu yayi musu shiru Dan babu hakurin da zaije bawa malam Dan kullum haka takeyi duk ya lalace ya qare a hanyar makarantarta bawa malamai hakuri da uzurin karya Baya hanyar bokonta Baya hanyar islamiya kaman mara aikin yi.


Sake qwala kiransa Dadah tayi yanaji yayi kaman Baya gidan Dan yakai malaman suna ganinsa suke sauya fuska.


Babbah Daya fito bandaki sarai ya hango Hafiz din a daki yace


"Yana jinki Kaita ne bazaiyiba idanma kin takurasa haka zaibi hanya Yana mangaremun yar budurwa Dan haka muje na Kaita da kaina ai mun Saba ba akanta farau latti ba hakama ai uzuri ne,wuce maza muje.


Saka takarmanta tayi ta fito dadah na miqo mata jakarta tana cewa "A dawo lafiya yar budurwan Babbah"


Hafiz Dake kallansu ta window da harara yabi Bayan Ameenatoun Yana cewa


"Duk anbi an sangarta yarinya Bata ganin girman mutane Dan an renasa ace kullum Saiya Rakata makaranta saikace qaramar yarinya,
Duk an ishemu da wata yar budurwan Babbah da Dadah mtseww"


Dadah Dake jinsa cewa tayi


"Idan ka gama yi mana fada ubanmu saika fito ka wuce inda zaka tafi ka dawo da wuri ka biya mata ku dawo tare."


Yana Jin Hakan ya fito baice komaiba ya fice Yana gyara zaman rigar shaddarsa a jikinsa dan qamshin turarensa me arha na tashi Dan gurin fira zasu gurin budurwansa.


Yana fita Dadah ta bisa da kallan mamaki tana girgiza Kai Dan tasa wannan Doron dayake dagawa Yana qamewa fira zasu.


Yana fita Abdul ya shigo gidan sanye da kayansa na aikin securityn Bankin first bank kadai dayake ta gurarensu.


Gaida Dadah yayi Yana cewa


"Budurwan gidan ta fita ne naji gidan tsit."


"Taje makaranta Babbah ya tafi Rakata jiya da shekaran jiya bataje ba tana fama da yatsarta datai tintibe Se yau ya Sena mata ciwo ta shirya ta tafi"


Yana Jin Hakan yashigewansa Yana cewa


"Wannan budurwan daya bita da Kun cire mata shi Dan Babu Wanda zaiso ta ahaka Kun gama lalata kayarku"


Banza tayi masa ya shige ya tube ya fito sanyeda da wando dogo ba Riga da kwandon kayan wankansa ya wuce Bandaki bayan ya debi ruwa a bokita Dan Shima wankan zeyi ya fice fira zashi Shima yau din Dan ya kwana biyu Bai ziyarci budurwansa ba.


A hanyar makaranta Saida Babbah ya Siya mata agwaluma cikin bakar leda ta Karba ta Saka jaka suka Isa tana Dan narkewa babban shikuma Yana ganin Hakan ya Bada himmar yiwa malam bayanin rauni taji jinya sukai sosai.


Malam iliya ya Saba da wannan karfin halin na Babbah Dan haka baiyi musu ba yace Allah ya tsare gaba ta wuce aji kawai.


Wucewa tayi Babbah na mata adduar adawo lfy da adduar Allah ya Bata ilimi fiyeda kowa makarantar.


"Amin" tace masa tana wucewa gaba kadan kadan tasake cewa


"Babbah kasa Yaya Hafiz yazo daukan fa"


"Tin kafin a tashi zan korosa"


Dariyar mugunta tayi tana wucewa aji da sauri.


Tana shigowa ajin kawarta ta musamman ta tarbota cikin murna daga Nan sukai gurin zamansu.


Dayake sune manyan makarantar da zasuyi sauka a kwanakin kusa a tacesu shiyasa su kadai ne ajinsu daban Amma sauran makarantar kusan aji Daya suke sedai kowa da karatunsa da ake masa Yana bayarwa ranakun laraba da litinin.


Tin kafin lokacin tashi ya qarasa yi Babbah ya ringa Kiran Hafiz a wayarsa me malatsai Yana cewa yaje ya taho da Ameenatou din.


Hafiz idan akwai abinda yafi zafi da takaici Yana cikinsa Dan kuwa a gaban budurwansa yake babbah keta masa wannan Kiran Dan haka dole yayi sallama da ita ya nufi hanyar makarantar Yana tafe Yana masifa da bacin Rai.


Yana Isa ana tashinsu suka kamo hanyar gida Yana Jin kaman ya mata shegen duka a hanya Amma Yana Hana kansa sbd balain Babbah dazai tarar a gida.


Ita kanta dayake tasan a siqe yake da ita Dan haka ta matso kusa dashi tana fada masa Dan Allah idan zaije fira gobe suje tare Taga matarsa su Saba mana.


Duk yanda zata Saka fushinsa sauka ta sani Dan itace ke kunnasa Kuma ta saukesa Dan haka kafin su Isa gida tini suka shirya fira sukeyi sosai hadda dariya.


Dayake magrib ta matso sosai suna Isa gida Baima shiga ba ya juya ya masallaci dagacan Kuma akwai inda zashi.
FOR MORE PAGES FOLLOW ME AT MAMUHGEE @AREWABOOKS
#MAMUH#
#AMEENATOU
#HOTLOVESTORY
#HOTROMANCE
#ZAFIN KAI
#TWINS




*_ZAFAFA BIYAR_*


1 *_Ameenatou!!_*
_Mamuhgee_


2 *_Tsutsar Nama!!_*
_Billyn Abdull_


3 *_Gudun Kaddara!!_*
_Safiya huguma_


4 *_Kwankwason Jimina!!_*
_Miss xoxo_


Guda Daya 400
Guda biyu 700
Guda uku 1k
Guda hudun 1200


*_6019473875 MUSAA ABDULLAH SAFIYAH keystone bank_*


*_ATURA SHEDA ZUWA 09166221261_*


*_MTN/VTU 09134848107_*


_*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din 09033181070*_


*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_**_Arewabooks@Mamuhgee_*
29
Da daddare Bata wani ci abinci ba furan babbah kadai tasha kadan tace batacin abinci ta koshi,


Rakata wanka dadah tayi sbd Bata iya zuwa bandaki ita kadai da daddare sai anrakata Dan haka tana Gamo wanka doguwar Riga kadai ta Saka ta Kwanta bacci Dan Allah yayi mata baccin wuri Dan haka yawanci Se dare Hafiz ke samun cikakkiyar yanci a cikim gidan daga wahalan Ameenatou da takaicinta.


Dakinta shine a tsakiyar nasu Babbah Dana su Yaya Hafiz din sbd duka duka gidan dakuna uku rak sai bandaki da tsakar gida da kitchen dinsu karami.


AMEENATOU BABBAH wadda kusan kowa ya sani da budurwan Babbah kaf wainda ke garin shedu ne Kuma zasu Bada sheda a koina cewan Babu yar gata Kuma sangartacciyar da gata yayi mata yawa a garin kamarta,


Babbah fadan tsananin son dayakewa yar budurwan tasa bama Mai yiyuwa bane,hakama dadah akanta kowa ya sheda yakuma tabbatarda son da ake cewa ana yiwa auta na musamman ne Dan kuwa kauna da banbancin datake nunawa akan Ameenatou daban yake a ranta akan sauran yayan nata.


Su Hafiz kuwa dasuke yannanta sunfi kowa Bata kariya da tattalin tarbiyanta da kiyaye huldodinta da kowa,
Bata zuwa gidan kowa,Bata yawo baa aikenta komai yimata sukeyi,
Tin tana yarinya sune suke Rakata makaranta su daukota haryanxu data zama budurwan datake nanatawa Rakata akeyi makaranta kuma a koma a rakota gida ko Daya daga cikinsu Kokuma Babbah da kansa Wanda duk manyancinsa babu ruwansa zuwa yakeyi takakka idan aka Daketa a makaranta shiyasa kowama ya gaji ya shafa mata lafiya basa dukanta sbd sharia ce da zance Baya karewa har gaban manyan gari Kona makaranta
Babbah Sam Sam Baya yadda da laifin Ameenatou Koda sama da kasa zata hade kuwa Baya yadda da tayi lefi Kuma wani lokacin Yana sane da batada gaskiyar Amma Baya yadda sedai idan sun dawo gida yayi mata fadan kafin ya lallasheta daga baya.


Duk da su bamasu hali bane Suna rufin asiri sbd su Hafiz na aikin karfi hakama babban duk da manyanci sosai Yana Dan babbuga sanaar dabbobin Daya Saba Babu wani samu sosai Amma sbd inganta rayuwan Ameenatou Babu Wanda yayi qasa a gwiwan Nema.


Ameenatou Bata rasa komai ba sbd Tako ina Babu abinda take nema ta rasa,
Tana cikin gata gaba da bayanta hakama har yanzu datake budurwanta batasan basu babbanta ne suka haifeta ba kaman yanda a garin kaf Babu Wanda yasan da Hakan,
Har mamakin akeyi yanda sukeda manyanci sosai Amma sunada qaramar 'ya sedai Babu Wanda ya taba kawo tinanin basune asalin iyayen nataba duba ma da yanda suke tsananin jinta fiyeda komai.


Ameenatou duk gatanta da sangartan da Akai mata tanada tarbiya sosai Dan kuwa sun Bata kyakkyawar rayuwa su Hafiz musamman Yaya Abdul Basu bari gatan ya lalatata gaba Daya.


Bangaren Bata ilimi kuwa sai inda karfinsu ya kare Dan kuwa makarantar primary ma ta kudi tayi Bata gwamnati ba duk da bawai kudi Basu yawa sosai ba Amma dai private school ce.


Secondary ma Bata gwamnatin takeyiba yanzu tana shekarar gamawa Dan haka daidai gwargwado tanada iliminta kaman su Hafiz din da Suma sunyi karatun bokon Dana Addini kowannensu nada diploma Amma dai Babu wani aikin bare Dora karatu me kyau da amfani sai suke Yan buge bugensu.


A cikin gidan kauna da shaquwa ce sosai a tsakaninsu da barkwanci tin daga kan babban har Dadah dasu Hafiz,
Sosai suke cikin Kwanciyar hankali da farin ciki,
Hafiz da Ameenatou akwai shakuwa da rigima sosai fiyeda Yaya Abdul duk da Shima akwai shaquwan da kauna sosai Amma shi Bata renasa ba kaman yanda ta Rena Hafiz.


Duk inda zata makarantar boko ko islamiya ko wani abin daban basa barinta fita ita kadai shiyasama duk irin shirmen soyayyar da kawayenta keyi ita Bata yi hakama Allah Bai Saka mata shaawan soyayyar da sukeyiba kwata kwata batama ganin kanta a wadda ta Isa fara soyayya.


Akwai masu Sonta da yawa sbd kyau da haskenta tareda gatanta da kyan jikinta Amma suna shakkar tinkararta da maganar soyayya sbd kullum tana tafe da babanta ko yannanta hakama gata kaman Me rariya a Baki koka zagaya kaje makaranta kace kana Sonta tana Isa gida take fadawa yayunta ko Babbah azo ana rantse rantse a gaban me gari ace kana bibiyanta shiyasa kowa ya kama kansa da ita duk da akwai Yan nacin da duk masifar Babbah suna Nan kan bakansu.


Tinda dadewa Yaya Hafiz ya daukota daga makarantar boko ya biya da ita site gurin Hafiz yace tinda lokacin tashinsu yayi ya wuce da ita gida shi gurin aikinsa ana nemansa.


A ranar idanuwanta suka ganar mata kyakkyawar halittar da Bata taba ganin me kyansaba tinda take.


Da farko kasa yadda tayi da mutum ne seda ya tinkaro inda suke sanye da baqaqen kayan dasuka fidda farinsa sosai ga Rana tana haskasa sai wani daukan ido yakeyi duk sai Taga su Yaya Hafiz da sauran ma'aikatan gurin sun koma mata kaman wasu halittun daban ba mutane ba.


Bakinta ta sake tana kallan fuskarsa dake sanye da black sunglasses me shegiyar kyau da fcap akansa Yana magana kaman ranar zata kashesa Dan kuwa alamunsa sun nuna Hakan.


Fitowa tayi daga inda take ta nufi inda yake Kai tsaye Dan kuwa idan ba gabansa ta tsaya tayi masa kallan kurulla ba bazata tantance abinda idanuwanta suka ganiba.


Hafiz ne yayi saurin riqeta daidai tana gap da Isa gabansa Yana cewa


"Ke Ina zakije?


Kwacewa tayi tana cewa


"Yaya Hafiz wannan baturen shine oganku?
Kullum ze Riqa zuwa ne??


Tunkuda keyarta yayi ya maidata inda yace ta jirasa tayi wani Dan qaramin ihun Jin zafi tana cewa


"Tambaya fa nayi Kuma baka ban amsaba ai"


Jin maganar mace a gurin ya Sanya JAMAAL juyowa ya Kalli gurin daidai Hafiz na rufeta da bayansa Yana fuskewa.


Ganin Babu kowa yasashi juyawa Yana ci gaba da sauransu bayanin da ake masa ita kuma ta fito tana cewa


"Bazanyi magana ba kallansa kawai zan riqa yi" ta Dora hannunta Daya a bakinta tana zubawa Jamaal din idanuwanta masu haske da kyau tareda yin shiru.


Sautin muryansa me tsananin nutsuwa da kamewa acikine Taji Yana magana Rabi duk turanci Wanda ita bama irinsa malamansu keyiba dasu kansu Dan Wanda suka iya.


Tinda tafara kallansa tana Jin muryansa Yana magana Bata qara motsi ba har Saida ya gama ya juya yabar gurin Bata motsaba sai murmushi takeyi.


Hafiz Daya gama aka sallamesu sbd maigidan nasu Daya wuce kama hannunta yayi yaja suka bar gurin Saida sukai Nisa ta kwace hannunta tana matsowa kusa dashi sosai tace


"Yaya Hafiz Yaya sunansa?
Bature ne ko balarabe?


Suna Isa gida ta bawa babba da dadah labarin Taga irin Wanda zasu Nemo mata a matsayin miji idan zasu mata aure.




Tin daga wannan ranar Ameenatou Babu ranar da Bata maganar baturen ogansu Yaya Hafiz,
Kaf gidan saida suka gaji da Jin kalan kyansa datake fadan kaman Rana zata konasa yanata kyalli.


Haka zalika tin daga lokacin Yaya Abdul ko Babbah suna daukota daga makaranta gurin Hafiz suke ajiyeta shikuma daga Nan yaje da ita gida duk Dan sbd tagansa Amma kuma abin mamaki tin daga ranar Bai sake zuwa ba bare ma ta gansa daga qarshema sai gashi anrufe site din gaba Daya tareda aikin dole suka koma Neman wasu ayyukan kafin idan Allah yasa zaa dawo da aikin sai gashi kuwa kwatsam ance su shirya su koma bakin aikinsu Kuma me gidanma yananan tafe da kansa.
#MAMUH#
#AMEENATOU
#THE SEELAHS




*_ZAFAFA BIYAR_*


1 *_Ameenatou!!_*
_Mamuhgee_


2 *_Tsutsar Nama!!_*
_Billyn Abdull_


3 *_Gudun Kaddara!!_*
_Safiya huguma_


4 *_Kwankwason Jimina!!_*
_Miss xoxo_


Guda Daya 400
Guda biyu 700
Guda uku 1k
Guda hudun 1200


*_6019473875 MUSAA ABDULLAH SAFIYAH keystone bank_*


*_ATURA SHEDA ZUWA 09166221261_*


*_MTN/VTU 09134848107_*


_*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din 09033181070*_


*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_**_Arewabooks@Mamuhgee_*
30
Washe gari Tin 7 na safe Yaya Abdul ya shirya fita aiki ya tsaya jiran Budurwar babban Amma dai lokacin ma dadah ke tadata bacci cikin lallabawa da tausayinta akan tashin safen Wanda yake kular da Hafiz Dake tsakar gidan Yana wankin kayansa Dana Ameenatou din.


Brush tafara kafin Tayo wanka ta fito ta nufi daki Dadah haryanxu data girma tayata shiri takeyi.


Sai kusan takwas saura ta gama shiryawa ta fito tsakar gidan ta zauna gefen Babbah dake zaune kan tabarma.


Farin Koko me kyau da aka zuba mata zuma aciki ta dauka a cup da fanke manya manya da zafinsu sun soyu tafara Sha tana fadawa Babbah gobe bazata je makaranta ba duk idanuwanta rage girma sukeyi Bata samun bacci gashi da Rana ma Bata samu.


Cikin kulawa da yadda da abinda ta fada din Babbah ya gyada Kai Yana cewa


"Na lura da Hakan sarai 'yar budurwata magana ce kawai banba sbd Yan Saka idon gidan Nan Amma gobe Babu inda Zaki ai ana son Rai da hutawa"


Juyowa Hafiz yayi sbd ya Dena mamakin lamarin babbah da budurwan tasa Amma takaici Baya barinsa yin shiru Dan haka Baki sake yace


"Wlh duk ranar da kika sake tsallaken zuwa makaranta bazaki sake zuwa site ba ko oga yafara zuwa aiki kuwa,
Sai naga karshen rashin bacci."


Kallan babbah ta dago tayi da idanuwanta da suka narke tana masa alaman yayi magana.


Inda yake babbah ya juya ya kalla Yana jifansa da wani mugun kallo yace


"Nine nace bazata goben ba sai naga abinda zakayi"


Yaya Abdul da hakurinsa ya fara karewa sbd yayi masifan lattin Danma Babu ranar da Baya latti sbd ita cikin kulewa yace


"Zan tafiyata idan Baki nutsu kin gama abinda yake gabanki ba Kokuma ki tashi mu tafi hakanan Baki gama cin abincin ba."


Dadah Daketa Kaida kawon hada mata jakarta da ruwanta a sabuwar roban ruwa me tsafta sosai da Yaya Abdul ya sake siyo mata miqawa Abdul din dayake tsaye Yana harare harare tayi tana cewa


"Dan taimaka riqe mata kafin ku Isa"


Baida lokacin batawa na musu Dan haka ya karba kawai zai sake magana Dadah ta rigasa da cewa


"Yi hkr saura kadan fa ta gama karta qware duk Kuna Neman rikitata"




Hafiz ajiye wankinsa yayi Yana nufota Babbah ya jefesa da wani kallan daya sakashi tsayawa Yana cewa


"Babbah wai meyasa kakemun hakane duk lokacinda naso gyarawa wannan yarinyar zama duk ta renani ko abokaina fa sunsan ta renani a gabansu Babu kalan sakarcin da batamin gudun nakeyi wataran na harzika na babbalata jinin mutane yayita Hawa"


"Karka wani Sakaya fito fili kace jinina Dana uwarku ya hau,
Zaka koma aikin gabanka kokuwa saina ce Abdul din ya tafiyarsa ka aje wankin ka Kaita"


Ball yayi da takarmanta Dake gabansa Yana juyawa ya koma aikinsa Dan ba qaramin aikinsu Babbah dinne ba ace ya aje wankinsa ko wanka beyiba ya Rakata makarantar.


Miqewa tsaye tayi bayan ta gama tana goge bakinta da tsaftacciyar kyallen sabuwar atampa da Dadah ta miqo mata ta Saka takarmanta masu kyau Wanda suka Hafiz dinne ya siyo mata Dan komai nata Hafiz da Yaya Abdul ne ke Siya
Babba kuwa a siya mata kayan ciye ciye da kwalama Yan canjinsa suke karewa sai fura da asalin Madaran fulani me kyau dayake siyo mata duk dare Wanda yawanci ita take Sha Bata cika cin abinci ba sai idan Yaya Abdul ya siyo mata kwai zuwa makaranta take ci da dare.


Suna fita tana gefensa tana masa surutu suka kama hanyar makarantar Yana amsata sama sama sbd hankalinsa na kan gurin aikinsa dayayi latti gashi Basu yadda da kowaba akanta da tini mashin zai ringa Bata kudi tana Hawa Amma kwata kwata Basu yadda da kowaba akanta shiyasa duk tsananin latti da rashin jinta basa iya barinta taje ita kadai makaranta kuma itama kanta sbd sabo da Hakan Bata iya tafiya koina batareda dayansu ya Kaita ba tsoro ma takeji na bin hanya ita kadai.


Suna Isa gate din makarantar ya miqa mata kayan ciye ciyen Daya Siya mata na break Dan basa Bata kudi kwata kwata.


Karba tayi tana masa Godia da fuska a cakude sbd lattin datai tasan Kuma Yaya Abdul din Babu rokon dazaije yayi mata Dan haka ta juya ta shige tana ciko idanuwa da hawaye Dan a tausaya mata.


Cikin babbar sa'arta malamin data tarar Yana Taron lattin Baya ko kallan inda take kwata kwata sbd tashin hankalin Daya taba Sha shida Babbah da Hafiz akan dukanta Daya taba yi
Babbah yazo makarantar ya rufe ido ya zuba musu tsiya rigima har gaban shugaban makarantar kawu yayi mirsisi ya nuna Yar budewarsa Bata da laifi shine Babu lafiya shiyasa batazo da wuri ba.


Dayake sunsan ba yadda zeyiba daga Nan har hukuma Dan haka suka basa hakuri aka rufe maganar,


Tin daga lokacin da yawa malamai basa taba Ameenatoun sbd Babu me buqatan rigima kowa na fama da kansa.


Simi Simi kaman munafuka ta wuce ciki tana Jin dadi a zuciyarta Dan idan akwai abinda ta tsana a duniya shine a taba lafiyar jikinta,
Bata kaunar abinda ya taba jikinta shiyasa Sam batason duka ko faduwa bare Jin ciwo.


Idan kuwa taji ciwo a gidan jinya zata kwanta a ringa fama,kafin ta warke zuciyar Hafiz saita kumbura ta huce yafi so a kirga sbd yanafin kowa Shan wuya da takaici Dan a kansa sakarcin yake karewa.




Farin jini datake dashine ya Saka yakeda kawaye masu tsananin son binta koina Amma da Aminiyarta Daya Khadija.


Karfe biyu saura Yaya Abdul yazo ya dauketa Kai tsaye gida suka nufa ko shiga beyiba ya juya ya koma gurin aikinsa ita Kuma ta shige a gajiye duk da Yaya Abdul din ya Siya mata yoghurt me sanyi sosai yazo mata dashi Amma dai batasha ba tana shigowa ta miqawa Dadah hadda Jakarta

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login