Showing 9001 words to 12000 words out of 119289 words

Chapter 4 - Jikar Maguzawa Complete Hausa Novels Writing by Asma Baffa .txt

28 Nov 2024

7421

na hudu inda Office dinsa yake.


Ba karamin haduwa Building din yayi ba komai glass da glass office dinsa Kuma komi na ciki fari ne kal ko Ina kamshi da sanyi ke tashi,Office dinsa katon gaske harda Palo da bedroom tare da toilet,wasu takardu ya kwashe Kawai sannan ya fito ya bar Office zuwa gidansa dake Banana Island Lagos unguwace ta sai Wanda ya Isa ya gagara,Yana driving Yana Magana shi kadai,Ido ya lumshe tare da furta Wai aure zanyi? Jawad da aure duk adana jikina da nake Tsaki ya ja kawai sannan yace ko na dakko Nanny ba Kamar matar gida ba,matar gida itace me sa Ido me Nanny zata musu haka ya dinga zance shi Daya har ya Isa katafaren sabon gidansa Da ya gama tsara shi Yana zuwa duba gidan yayi kafin ya zuba furniture ya fito
Ya Shiga mota me gadi ya bude Masa gate ya fita ya koma Ikeja GRA inda yake zaune a hadadden gidansa yan aikin gidan dukkansu maza ne me girkinsa ce kawai mace yare ce me suna Dina Yana Shiga ya iske ta shirya Masa abinci dining ya wuce Bayan yaci lafiyayyen Abinci samansa ya haura tare da sheka wanka ya dauro Alwala ya shirya cikin jallabiyya sky ya wuce masallaci sabo da magriba ta gabato.


Najla tuni na bar kauyen Kakanni na na koma cikin Kano gidanmu har munyi nisa ma da Fara Zana ssce exam.
Yau Friday bamu da Exam Ina zaune Ummiya ta fita unguwa Daddy Yana wurin aiki sai ga Kawata Farisa da Hamziyya sunyi sallama sun shugo,Ina murnar ganinsu nace daga Ina haka mu shiga Palo,Farisa tace ke dakata kiji Jawad me sadakar kudi a company dinsa dake kano gobe za ayiwa mutane interview zai dauki ma'aikata masu degree da NCE,kinsan abin farin cikin? Nace Yi sauri dan Allah ki fada min dama Ina Neman kudi Ido rufe,Farisa tace abincin Yan gayu ake bayarwa a ciki duk abinda mutum yake so kyauta zai karba Indai interview yaje,Naman kaza kala kala,kwai,zabi,friedrice,sakwara,snacks ke abinci dai ance a reception din cikin building din ba abinda babu Kuma Indai kaje interview kyauta zaka ci ko Mene,Hamziyya tace baza taje ba tsoro take ji ko secondary Exam Bamu gama ba da me zamuje interview.


Dariya na saki Ina murna nace kin tabbatar kyauta ne? Yayana yaje fa last year shi ya bani labari,yaushe za a fara? Monday 9am,nace ki zabo kayan Sallah mu shirya muje kin tabbatar abincin Yan gayu ne kuma har da nama? tace ae,Hamziyya tana kallonmu tace Allah ya shiryeku nace Ameen,Kinga Farisa Ni zanje Interview da takardu ,ke ki dauki Certificate dinki ko ma na Mene mu samu file me kyau mu zuba muje,sannan mu dau wanka sabo da raini nan muka gama shirye shiryenmu Hamzy sai dariya take Mana.


Ko da Ummiya ta dawo ban fada Mata ba Allah yasa satin kaf bamu da Exam,ranar Monday da wuri na gama aikin gida naci wanka na shirya cikin wata Atamfata sabuwa dinkin riga da skert maroon and black color nasa takalmi da jaka black da mayafi na ebo takardu biyu na zuba a file dina,Ummiya bata da teaching ranar, Kallo na tayi tace Ina zuwa haka? nace makaranta zamuje za a Mana wani lesson mantawa nayi ban fada Miki jiya su Farisa suka zo Suka fada min,Ummiya ta yarda da ni tace a dawo lfy nace Ameen ta bani dari biyar kudin Napep dana abinci na karba na fita,ban tsaya ko Ina ba sai gidan su Farisa.


Ina zuwa na ganta ta fito ma ta Sha lace dinta itama tayi kyau ta dakko takardu a file nace wanne takardu kika dakko ke? tayi dariya tace Jssce certificate na dakko da Indigene form sai birth certificate,Nace Ni Kuma commern Entrance ne sai birth certificate da state Indegene,Dariya Muka sheke nace shi yasa yau banci komai ba zamu ci kaji,tafawa mukayi sannan muka tafi tare da Shiga Napep.

Muna zuwa muka iske
Mutane dukkansu maza ne ba Mata sai mu sun cika bakin gate securities basu bari sun Shiga ba,ya hadu wajen sosai muna tsaye muma ka rantse takardun arziki Muka ebo mazan har wani magana ake Mana Kuma interview kuka Zo?nace ae wlh gashi ma Naga ba a bude ba Allah yasa Kar a barmu jira,suka ce haba ai oga Yana zuwa za a bude Mana Allah yasa muka ce,Bamu dade ba sai ga wata mota me rai da motsi ta yanko ciki ana cewa ga Oga nan haka aka wangale Masa gate driver dake driving ya shiga da mota,Bayan 15mnt aka Bude Mana gate tare da cewa masu interview su shiga,muka Shige ciki wani hanya aka bi damu Muka haura sama mutane ko Hamsim bamu Kai ba,sama aka hau damu muna ta kallo Farisa tace ko yanzu kasuwa ta tashi Dankoli yaci riba munsha kallo,wani wajen cin abinci aka kaimu akace kowa ya karya,Farin ciki ya kamani,Muka zazzauna katon wajene hadadden restaurant kujeru da Table hadaddu ma'aikatan suka Zo suna tambayar kowa abinda za a kawo masa,suna zuwa kanmu nace Kai bawan Allah ka tattabar akwai lunch? Yana Murmushi yace sosai ma Kuwa nace kawo Mana komai na wajen


Baki bude yace komai? nace ae komai da ake ci kowacce ka zuba Mata a gefe,to yace ya tafi ba a dauki lokaci ba sai gashi ya dawo da katon plate kowacce shake da abinci iri iri,Chips a gefe,yam and Egg with souce a gefe,ga wani pepper chicken, wani snack kala biyu a gefe ya ajiye Mana ya koma ya shako wasu plate din da abin ci iri iri ya ajiye Mana,ya koma ya kawo wani plate din na farfarun Naman rago daban, yace an gama Hajiya ya juya zai tafi Farisa tace tea din fa? yace sorry ya koma ya kawo Mana,nace Juice da karfi,ya kawo Juice da ruwa,sai kallonmu akeyi ana gulmar mu muna ta washe baki nace Farisa mu Fara? tace tsaya a irga uku tace 1,2,3 start muka Fara duri da Bismillah nace muyi Adduar abinci,Allah kasa abinci ya zauna lafiya a cikinmu,ya Mana amfani sai muka shiga ci ba ji ba gani,Ina cin kaza nace Kar mu bar komai sai munyi kara'i muci yanda ko tunawa muka Yi said mun dinga Jin dadi


Farisa tace ai gyatsa ma idan nayi sai naji kamshin Naman Nan,banza ta fadi naji ance sai yayi sati Yana interview kullum sai munzo don irin wannan abinci, Muna ta ci na kalli daya daga cikin ma'aikatan nace Karo Mana ac,ya Kuwa Karo karfinta,muci wannan muci wancan sai da Muka cinye komai tas Muka shanye komai ruwa ne kawai bamu sha ba, toothpick na dauka Ina sakace hakorana na kuskure bakina da ruwa sannan muka zauna Muna hutawa,cikin mazan suna ta Mana Dariya mun lashe komai wasu suna ta mamaki,sai da Muka huta sosai sannan nace a kawo Fruits salat na kwala da karfi masu bada abinci Suka sake kawo Mana,Farisa tace mene ya rage bamu ci ba? nace Coffee,Nan Tace a kawo Coffee Suka kawo Muna korawa a hankali yayinda tuni an tafi wajen interview, fitsari tuni ya fara kamani Amma na daure abina Muka tafi inda ake Kiran mutane suna shiga sharp sharp ya gama da mutane Suka tafi yin lunch sai mu kadai akace mu shiga,Farisa tace wlh bazan iya Shiga ba ai abin kunya ne dama Ni girki ne ya kawoni nace tab ai Ni sai na shiga ko banza na bata Masa lokaci na tsani naga me kudi Yana hutawa, Farisa dariya tayi na mike na Shige da takardun primary dina


Sallama nayi tuni tsaruwar office din kamshi da sanyi sun ratsani har wani bacci na Fara ji,Yana hakimce yasha wata shadda sky ya zuba kyau sai sheki yake ban San Sanda nace Jawad Fariyar Shadda, ya ganeni tsab ya nuna bai Sanni ba har gaban table dinsa na karasa Yana zaune a kujera tana jujjuyawa, tsugunawa nayi nace Ina kwana mun ga abinci kala kala mun gode Allah ya biya ka ci da marainiya Allah ne yasan irin ladan daka samu yau,wlh baka ji farfesun Nan ba dadi har yanzu shinshina hannuna nakeyi Ina Jin kamshinsa,Dan Allah wannan kajin amma daga kasar waje kasa aka kawo,ko kulani baiyi ba Yana ta rubuce rubucensa,nace an gode shayinma ice ko da Madarar Dano aka Yi sa ai kasan dano ta kasar Denmark ko? Hannu ya Miko min yace sit ga sit nan Miko min documents naki


Mika Masa nayi nace Allah yasa ka bani babban matsayi a nan,bai min magana ba ya duba file dina tunaninsa ma NCE nayi lokaci guda Naga ya dago ya kalleni a fusace tsoro ya kamani fitsari na ya fara damuna dama matsewa nayi nan take nace zanyi fitsari dan Allah,bai kulani ba nace dan girman Allah,takarduna ya watso min yace get out,rokon sa na Fara na mike tsaye Ina matse kafafuna nace Dan Allah zanyi fitsari a wando dan Allah,takalmana na cire sabo da yanzu Saura kadan na Fara Yi a wando tsalle na fara Ina Kai kawo a office din nace wayyo Kawai na hango wata kofa a Office din da sauri naje na Murda handle na shiga sai Naga bedroom komai yaji,na duba naga wata kofar na bude Ina shiga Naga lafiyayyar toilet sai kamshi ke tashi komai clean kofa na kulle da sauri nayi fitsari na a nutse nayi tsarki da ruwa me dumi sannan na shirya kaina nayi flushing tare da wanke hannuna na fito,Karo naci da shi a room din tsoro naji yace koma ki wanke min toilet,nace ban bata ma ba bani da Infection, wani kallo ya min ba shiri na koma ciki komai a kwai haka na wanke Masa sannan na fito nace angode na fice da gudu na kwashi takarduna na fice Ina haki na manta da Farisa sai data rike ni sannan na tsaya cak nace wayyo muje dan Allah,tace Naga kin dade nace muje wajen lunch first Zan Baki labari, Sallah Muka je mukayi ta azahar lokacin har 2pm tayi,


Sai da Muka koma wajen lunch mutane har sun gama sun tafi Muka je aka kawo Mana friedrice taji Hadi ga Rabin kaza kowa,juice da ruwa aka kawo Mana wani irin girki na Yan gayu haba nan ma muka Fara duri sai da Muka cinye Muna hutawa Nan na bawa Farisa labarin komai tana ta min Dariya,daga nan nace da masu abinci su zuba Mana take away,Ina fada sai ga Jawad ya fito cikin takunsa na kasaita Farisa ta rude da haduwarsa aka zuba Mana take away sai Naga Jawad an zuba Masa wani Kalar lemo na Apple Nan take aka Masa nace laaaaaaaaaa da karfi sai da kowa ya juyo sun zaci wani Abu ne har Jawad sai da ya juyo nace dama akwai irin juice din Oga Nima a hada min irinsa,Nan take wani ya dinga masifa yace tunda kuka Zo komai sai kunci to irin wannan na Oga ne ba a bawa kowa,nace to jaraba munji karka damemu,Farisa tace muje gida,nace Kinga oga Yana Sha ki tsaya ko zai rage na Sha irin nasa,wani waje na daban ya zauna Yana Sha Yana latsa waya.


Wayo nayi nace bari na dan taka ko Zan samu cikina ya samu space na fara dan zagawa a wajen da wayo har naje kusa da Jawad,idan Naga zai ganeni sai na juya naci gaba da tafiya haka na dinga yawo a wajen a dole dan motsa jiki nakeyi,Tsaki Yaja ya tashi ya bar abin da yake Sha ya fita Yana waya na zaci ya gama Sha ya tafi na dauke na kwankwade na ajiye Masa cup din,Ina juyowa Zan tafi nagan shi a bayana ya dawo, tsoro da kunya yasa na arce da gudu nace Farisa muje Muka kwashi take away dinmu nace dan Allah kayi hakuri Kai masu aiki ku hada Masa sabo me yawa yafi na baya Dadi,na kalleshi nace sorry sir zasu maka wani Wanda yafi na da Dadi da kauri Yi hakuri kaji bazan sake Sha maka abinka ba.


Jawad shi Dariya ma na bashi na maida shi yaro Tsaki yaja Kawai ya Kira driver yace su wuce Airport,mu Kuwa Muna fita Napep muka shiga Muna ta tafawa nace wallahi dole mu dinga zuwa duk ranar Interview har Muka rabu Muna Jin dadin girkin mu,Ina komawa gida na bawa Ummiya take away nace a wajen me makarantar mu yazo ya raba mana tace to mashaallah ke baza kici ba? Nace naci acan Kawai kici


yau Saturday bani da Exam Ummiya ta fita teaching da takeyi a private school nice a gidan nake ta aikina komai sai dana gama na hada furar siyarwa sannan na hau keken dinki ina taya Ummiya dinkin mata,Sallamar Daddy naji ya shigo mikewa nayi tare da amsawa nace Daddy Sannu da zuwa ashe yau zaka dawo,yace yawwa Najla ya aiki ya makaranta? Nace lfy Alhmdllh Maman naki tana makarantar ne? nace ae na mike na karbi ledar hannunsa da jaka ta kai masa daki ta kawo Masa ruwa da lemo,me Kika dafa ne? Nace shinkafa da Miya da salat bari na kawo maka,da sauri na shiga kitchen na hado Masa na kawo Masa Palo yace Allah ya Miki Albarka na amsa da Ameen sannan na koma naci gaba da aikina,Kira ya kwala min na tashi na koma yace na manta kinyi bako Yana kofar gida,mamaki ne ya kamani Wai bako ni inyi bako sabo da kwar jinin Daddy mayafin doguwar rigata maroon na yafa sannan na fita


Ina fita naga mota baka mamaki ya kamani sabo da nidai duk kyau na ban taba samun saurayi me Mota ba tunda mu talakawa ne a unguwar Talakawa na taso haka na karasa jikin motar Ina zuwa naga ya bude kofar motar ya fito Asif na gani Nan take nayi Murmushi tare da furta Barka da rana ya aiki? Alhmdllh ya gida ya su Mama? Lfy suke yace good,Nace Ina Ogan naku? Yana garinsu Lagos,Ido na zaro na tambaya dama dan Lagos ne? ae mana nace Masha Allah,Furar kazo siya ne? Ya kalleni ya saki Murmushi yace wlh sabo da Yar uwarki ta Kauye nazo tun daga Lagos har nan,sai lokacin na tuna karyar da nayi musu a Kauye nace ba nice Najla ba Yar uwarta ce a Kauye sunana Fara,Allah yasa lafiya? Yace hmmm abinda nazo da shi deal zamuyi a biyata kudi,baki na washe nace kudi za a bani ka tabbatar? Yace bafa ke ba kanwarki Fara ta kauye me hankali,nace oh to,fada min ko Mene ai yanzu Maganar kudi ita ake ji duk na rude na gigice nace ai yanzu harka Indai da kudi Kuma ba kisan Kai bace ai ita Fara Shar da ita, Asif ya saki dariya yace be calming down please You have to calm down,nace wace calm down ai nutsuwa ta Kare Ina jinka wanne deal ne?


Ogana Jawad....dakatar da shi nayi da Hannu nace Wai.... Wai ma da Jawad zasu yi deal din? Yace kwarai,me kudin fa? Ae Mana yace,nace angama dama naga Yana da hankali mutumin kirki ne ga hakuri ba ruwansa da duniya duk kudinsa,Asif ya sheke da dariya yace farko fa cewa Kika Yi baida mutunci he is not romantic,nace son zuciya nayi lokacin dama ba gaskiya nake ba Ina jinka fada min Zan sa ta Amince ta aureshi ko zata mutu sai ta aureshi, Asif yace amma Kamar Yan biyu ne ku Sam ba a gane ku,nace baka kula bane ta Kauye Fara tana da digon tawadar Allah a goshinta guda biyu a jere, yace okay ya fara bani labarin Jawad




Sharhi dan Allah bana bukatar godiya ko stickers Ni sharhi nake so.




WhatsApp number ta
08033933642








AsmaBaffa🌏JIKAR MAGUZAWA🌏

11-15


Official


By
AsmaBaffa












Wannan Novel a WOMEN 24 TV Kawai za a iya samun ci gabansa,
karanta kasa kiga tsare tsaren.




SHIN KIN SAN SHAHARARRAN GROUP ƊIN NAN DAYA SHAHARA WAJEN KAWO SHAHARARRIN FINA-FINAN DA SUKA SHAHARA WAJEN SAKA MA’ABOCIN KALLONSA A CIKIN NISHAƊI DA FARIN CIKI?
IDAN HAR BAKI SANI BA LALLAI KUWA ANA YI BABU KE!
KODA YAKE HAR YANZU AKWAI BABBAR DAMAR ZUWANKI DON A CIGABA DA DAMAWA DA KE IDAN HAR KIKA JONE DA MU!

Kuna ina ma’abota kallon shirye-shiryen Arewa24 na ƙasashen waje da suka fara ba su ƙarasa ba? Yi Maza ka garzayo wannan maƙala don ƙarasq kallon shirye-shiryen.


Kuna ina ma’abota karatun lobayya wato ma’abota karatun littafan hausa? Shin na tambayeku akwai wani novel da kuka karanta har yau baka samu karashensa ba? Ko kuwa akwai novel ɗin da kake nema ruwa a jallo ka rasa? To kaima garzayo wannan maƙala domin dacewa da haziƙan fasahan littattafai.


‘Yan gayu sam! Bamu barku ba! Kina son koyon kwalliya ɗaurin dankwali kala-kala? Yi maza ki jone da mu kin ji? In sha Allahu sai dai ki koyawa wasu, domin an tanadar muku kyawawan vedios wanda zasu taimaka ki koyi kwalliya da kanki, ki koyi ɗauri da kanki.


Anzo wajen! Wato fannin girki! Ayyuriririiiii!
Duk kyan mace sai ta iya girki ta cika sunanta kyakkyawa! Maza-maza yar’uwa ki jone da mu don kuwa muna kawo manyan-manyan girki masu daɗi da ɗanɗano wanda ba su da wuya balle ma ace sai ankashe musu kuɗi. Ke dai shigo ki ganewa idonki!


Ƙarshen-ƙarshe kenan! Wato ba anan fa aka tsaya ba akwai wani babban albishir ga masu son group ɗin, shi ne babban tanadin da akai don kawai a faranta muku! Tanadin kuwa shi ne, akwai haɗaɗɗan novel da ya haɗu iya haɗuwa ya tsaru iya tsaruwa da aka yi shi musamman dan ku, wato wanda ake sakinsa a iya group ɗin kacal, wanda wasu manyan marubuta ne ke rubuta su, duk dai sai kin antayo zaki ganewa idonki. Wannan ma na ɗaya daga cikin littafan.
Kalli katsa kaɗan!






*TSARE TSAREN WOMEN24 TV WHATSAPP DA WOMEN24 TV VIP👇🏾*


DAURE KI KARANTA DAKYAU


Akwai groups guda biyar(5) da muke tura littafi wanda marubuta keyi kyauta da kuma

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login