Showing 63001 words to 66000 words out of 116597 words
Chapter 22 - MUWADDAT Complete Document book by Aisha Bagudu .txt
bata son shiga d'an tunda tazo bata ta'ba yin hanyar bangarensa ba ,amman yau dayake babu yadda ta iya da ranta haka nan ta nufi hanyar tana yin sallama ta yaye labulen parlour'n tashiga..zazzakar muryarta ta doki kunnen ala'meen yadda muryarta ta ratsa jikinsa ko daga bacci ya tashi muryar bazata bace masa ba ,gabadaya suka had'a baki suka amsa sallamar datayi kafin ta gama shigowa kamshin turarenta duk yagama shige musu hanci gabadaya hatta parlour'n ma ya gauraya da kamshinta ,ala'meen dake kishinged'e ya d'an lumahe idanunsa ahankali kana ya bud'esu akanta suka d'an kalli juna kafin daga baya ta kawar da fuskarta hisham na nuna mata gurin zama ta gaishesa sannan ta zauna cikin fara'a kad'an bazakace itace take zagewa da Auwal su raba dare suna zuba surutu ba ,da kyar ta sake bud'e bakinta tacewa hisham" ya gida da madam ?
"madam tana nan lafiya tace a gaisheku suka d'an yi shiru batare da sake cewa komai ba kusan second biyu hisham yace "malama muwaddat me yasa kika da wuyar gani gashi baki son mutane ?
Yanzu da ba Dan na tura a kiraki ba har na tafi bazamu gaisa ba kenan? Murmushin gefen baki tayi "kaga kuma ganina ba wahala garesa ba amman ga Wanda bai kama kansa ba zai wuya ya gani sannan batun rashin son mutane, ni mutane masu shegen surutu ne banaso..
"Al'amen ya jefa mata wani irin kallon da shi kansa bai San yayi hakan ba ,nan Dana ta tamke fuska tana sake kawar da kanta gefe hisham ya cigaba.
hisham yace "shikenan na fahimceki "minal tace ki d'aure ki sake kawo mata ziyara acikin zuciyarta tace "ita idan ta matsu tana son ganina why not tazo ,amman a zahirance cewa tayi InshaAllahu zanje "Kamar yaushe kike ganin zakije ?
Ta yatsina fuska had'e da cewa" babu rana gaskiya amman ina da niyyar zuwa ,sai lokacin ala'meen yayi karfin halin cewa karka yarda da zanceta makaryaciya ce da sauri ta kallesa cike da matsanancin mamakin tare da tsaresa da fararen idanunta "yaushe wannan ya fara atsakaninsu da har zaice mata makaryaciya? kalmar datafi tsana kenan a rayuwarta sai gashi a karon banza a kirata dashi, hisham yayi saurin cewar karyar me tayi maka ?
"Ranar da mukaje gidanka muna dawowa gida sai naji tana bada labarin karya wai taga gidan sarkin garin nan taga gidan gwana kai har gidan zoo tace munje ....
sukayi Dariya hisham yace "ina laifi data kareka.
"ta dai kare kanta dai nasan tayi haka ne Dan kar gaba a sake tursasata fita..
Muwaddat ta d'an Mike tsaye saboda shirmensu ya fara cika mata kunne dole daman tasan hisham zai kasance kmr ala'meen gurin zuba tmkr ruwa ,tunda sai hali yazo daya abota kan zo daya ..hishsm yace "ya kuma kika tashi ana hira ?
"Ni zan koma ciki idan kaje ka mika min gaisuwata gurin madam"
Ala'meen ya fahimci shi take son ta gujewa saboda kallon dayake mata hisham yace "amm madam fa tabani sako a amsar mata number wayarki a she Ranan nan har kuka rabu baku amshi number juna ba muwaddat tace "mantawa muka yi saboda hira ta d'auke mana hankali anan take ta gaya masa number ya shigar dashi cikin wayarsa yace "baki gaya min sauran lambobinki ba dan naji ance layuka uku gareki cikin yatsina fuska tace "ka manta da sauran tunda za'a iya samuna Akan wannan layin ,hisham yace "haba muwaddat ina ganin ko mutun yana rowar number baya yiwa kawarsa ba ,duk yadda yayi muwaddat ta tsare gida ta hanna sauran number's dinta Wanda tabashi din ma ta karamar wayarta ce datake amsa kira Wanda abi ya tsiya mata ,wai saboda koda cajin babbar wayar ya kare, Dan bayason yakirata bai sameta ba ..
shi kuwa hisham Dan dai yajata da hira sai cewa yayi "ke din da nake son ki zama surukata sai gashi kun kulla kawance da daman ..
Da sauri tace wace irin suruka kuma ?
"Au baki da labarin ina rikon ihsan ko?
Cikin dariya tace "da dai faiza kace me yuwa na Dan tsaya maka tunda ita ihsan ai uban gidanta na hannun damanka ne ..
Hisham ya jiyo ga ala'meen dayazamanto tamkar sauna a zaune yana kallonta ",kai maigidana kaji abinda surukata ta fad'a....
Ala'meen yayi murmushi yace ",ai ina ganin ko ita surukar taka a halin yanzu bata isa aure ba bare aje ga faiza ko ihsan, hisham yace "haba babban yaya karka raina min hankali mana kawai saboda ba'ason bani kanwa sai kuma ace yaya ma bata isa aure ba ,kina jinsa dai big sister ya fad'a tare da kallon muwaddat.
Ta d'an kawar da fuskarta gefe "eh to abinda ya fad'a gaskiya ne, sai kaje kayita jiran lokacin idan kaji zaka iya "kenan idan na fahimci ki kenan kin goya masa baya akan maganar sa na cewa kema baki isa aure ba ballanata kanwarki?
Ta sake had'e rai "wannan ai maganarku ce ni dai na tafi ka gaida gida tana shirin fita daga parlour'n sai ga eiman ta biyota da wayoyinta big sister an damemu da kiran wayarki muna cikin kallo an hanamu jin gari ya Auwal yakira wasu ma duk sun kira ni dai nace musu kina d'akin yaya ..........
Cikin matsanancin jin haushi muwaddat tace ",to d'an me zaki biyoni da waya d'akin mutane ,ko ance miki dadewa zanyi ,Muje gani nan saukowa eiman na shirin fita aka sake bugowa ta juyo da sauri "to ga Auwal nan ya sake kiranki .
Cikin tsawa tace dan rashin da'a kai tsaye kike kiran sunansa bako rusunawa ?
Bata amshi wayar daga hannunta ba har kiran ya sake katsewa "oya maza ki koma da wayar idan na sauko zan kirasa ..
"Ni gaskiya ki amshi wayar a hannu , ni yanzu meye laifina bayan agabansa bazan kira sunansa kai tsaye ba "ki ma yi kiga yadda zai yi kaca kaca da namanki Dan kinsan shi baya d'aukar shirme ..
eiman ta marairace" murya big sister Dan girman Allah ki taimaki rayuwata ki amsa kinga na rigada na d'auka da farko ,kinsan Halinsa zai d'auka ban kawo miki bane ...
Gabad'aya daga muwaddat din har eiman a tsorace suke ita eiman najin tsoron kar idan yazo yaci ubanta, Dan bai mantuwa, sannan bai yafiya duk dadewar Abu zai hukuntaka akansa, sai dai idan yagadamar Kyaleka, ita kuma muwaddat rashin sanin abinda zata fad'a masa idan ta ashi wayar take, cikin haka ya sake kira "kin gani ko big sister ya sake Kira Dan girman Allah ki rabani da wayar nan .
Ala'meen kasa d'aurewa yayi yace "shi din waye da baza iya amsa wayarsa anan ba ?
"Batare data juyo ba cikin tausashiyar murya kmr zatayi kuka tace "auwal kanina ne fa, sannan ta amshi wayaoyinta ta bar d'akin cikin 'bacin rai , itama eiman sai lokacin ta saki ranta ,tana sakawar a'lameen murnushin Wanda za'a iya kiransa,Dana mugunta ...
Hisham ya juyo ya dubi ala'meen "ina ganin fa yarinyar nan ta gane kana son yayarsu "kai haba bana ji wannan shirmammiyar yarinyar zata fahimci wani abu ,ita kanta uwar gayyar batasani ba .
"Kana son kace min ita makauniya ce shiyasa bata lura da irin mayataccen kallon da kake yi mata ba ko? Sannan me ka fahimta a yanzu da aka kawo mata wayoyinta ?
"Na fahimci kmr tashiga firgice gabadaya dai ta tsorata "shine abinda na gani gaskiya ka tashi tsaye kar hasashenka yazamo gaskiya,kar yaron yazo yayi kuli kulin kubura da kai akasa..
hisham ya k'arasa mgnr yana dariya ala'meen yace "Allah ma bazai sa ba InshaAllahu rabona ce ...
Hisham ya Mike " to Allah yasa, nima bari tafi Dan na fara tunanin madam Dina nasan tana can tana jirana ala'meen ya hararesa nima dai zanyi madam Dina kodan rashin mutuncin da kake min babu ikon ayi cikakkiyar hira da kai sai ka tsiri cewa madam na Jira .
"to ai gara ni da matar tawa ma ina fitowa kai fa tunda bakuwar gidanku tazo aka daina ganinka ,ai ina jin duk ranar daka mallaki yarinyar nan ,an daina ganinka gabadaya suka kwashe da dariya har da tafa hannu sannan suka Mike tare suka sauko zuwa kasa al'amen yayi masa rakiya ya shiga mota ta tafi shi kuma ya dawo gidan har zai hau samansa sai yaji hayaniyar kannensa acan bangaren dady , sai ya tsinci kansa da nufar bangaren ba Dan komai ba sai Dan ya kalli muwaddat yana shiga ciki ya iske gabadaya yaran gidan suna ciki hjy hajara tacel kardai abokin naka ya tafi tun ba'a kai muku abinci ba yace mumy "ai kinsa halin hisham in da yana son ci da kansa zai tambaya..
Idanuwa yashiga budewa yaga ta inda zai ganta ,babu ita babu alamarta a parlour'n Dan haka ya juya ya wuce ya koma samansa hankalinsa a matukar tashe saboda yasan watakilla tana can tare da Auwal a waya
Ilai kuwa abinda zuciyarsa ta kissima masa ne ke faruwa acikin d'akin muwaddat, domin kuwa fad'a ne sosai yashiga tsakanin Auwal da muwaddat ta inda yake shiga bata nan yake fita ba "Dan wulakanci da iskancin banza me ya kaiki d'akinsa ?
Kika bar ni ina kiran wayarki how many hours "wato kin fi damuwa dashi akaina, ke wai ma meye atsakaninki da shi ,?
"waye shi da bazaki d'auki wayata agabansa ba?
"Ni ina nan an tsareni ganina,gani wawa bansan abinda nakeyi ba ke kuma kina can kina shirme da katon banza , Dan haka gobe goben ki shirya zan zo na d'aukoki ki dawo gida zuciyata baza iya d'aukar nauyi nan ba, gara kina kusa dani daman nasan saiko ake son yiwa rayuwata shiyasa aka tsiro da zuwanki wannan hutun ..
"Kema dayake kinsa mugun nufin dake ranki shiyasa kika yi zamanki, bakya ko tunanin dawowa maza daman tun da wuri idan ma sonki yake kice masa kina da miji Dan wallahi babu mai auren ki matukar ina raye ya karasa mgnr yana furzar da iska ..
shiru tayi har yagama balainsa batace masa komai ba ...
Gashi kuma dai suna rike da wayar ,yadda bai yi yunkurin cewa daita komai ba haka zalika Itama bata ce masa komai ba, illa Kunar zuciyar da take, hakika Auwal yayi bala'in rainata wannan wulakanci ko iyayen da sukayi silar zuwanta duniya a yanzu basa mata fad'a irin haka ballanatana shi datake masa kallon kani gareta amman babu Wanda ya janyo wannan tozarcin kamar ita itace silar faruwar haka ta bashi abinda bai cancaci yagani ba ,banci haka tasan babu yadda zai dinga yi mata irin wannan matsefar kamar wani ubanta ..
Ganin tayi shiru taki cewa komai ta barshi shi kadai sai balai yake yi yasa yaja dogon tsaki har sai data yi saurin cire wayar a kunnenta ya fillingin da wayar akan gado batare daya kasheta ba ya sauko daga Kan gadon ya fito kai tsaye part din ummi ya wuce yana shiga ya isketa zaune ita kad'ai tana kallon labarai sallama yayi aciki sannan ya haye sama inda d'akin mahaifinsa yake ,tabi shi da kallo duk yadda akayi ransa a bace yake ",to waye ya bata masa rai ?
Ta tambayi kanta tana runtse ido ,kamar ta Mike ta bi bayansa sai kuma ta fasa tasan da matsalar data shafeta ce dole zai tsaya gareta Amman tunda ya nufi gurin mahaifinsa a sauka lafiya ...
A bakin kofar abi ya tsaya yana kwankwasa kofar abi dake cikin d'akin yana duba wasu mahimman takardun kasuwancinsa yace" waye ?
Muryarsa can cikin makoshi tamkar bai so ta fito tace ".ni ne "abi najin haka yasan kowaye Dan haka ya bashi umarnin shigowa ya tura kofar d'akin yashigo da sallama aciki ,abi ya d'ago ya dubesa yana nazarinsa kallo daya yayi masa yasan yana tattare da damuwa kuma duk abinda ya kawoshi a daidai wannan lokacin mai mahimmanci ne, Dan haka ya tattara takardun dake zube agabansa gefe ya nuna masa gurin zama "ka zauna fatan dai kana lafiya ?
Muryarsa tamkar Wanda zaiyi kuka Dan ma dai nmj duniya ne, kawai ya waske yace ",abi kana son nayi yawanci rai a duniya ?
Da sauri abi ya gyara zama yana girgiza masa kai ",kwarai kuwa Auwal meyasa zaka fadi irin maganar da tasanya gabana faduwa?
"Akan muwaddat ne abi ina sonta kuma da aure, wannan shine karo na karshe da zan furta hakan gareka ka aura min ita ka daina duba kankantar shekaruna, ni aure nake so a halin yanzu "abi ya numfasa yana cigabada dubansa yana nazarinsa tabbas yana hango gaskiyar abinda ya fad'a Amman ta yaya kamar Auwal zaa ace zaa aura masa muwaddat ?
Amman saboda ya kwantar da hankalin yaron yace "shikenan zan duba lamarin sai asan abun yi "zuwa yaushe kenan zaka nemeni kan mgnr, saboda ina son muce tare da ita ne?
"abi yabi shi da wani kallon mamaki kafin daga baya ya kira sunansa "bunayya kasamu natsuwa nace zanyi wani abu akai "bunyya ya ciza gefen lips dinsa kad'an yace "abi to kace ta dawo gida hakan nan nasan kun tura can ne saboda ni ,to wallahi idan bata dawo ba komai zai iya faruwa dani .
ya kamo hannunsa ya d'aura daidai saitin zuciyarsa "abi kaji bugun da zuciyata take ?
"Abi ya runtse ido saboda yaji yadda zuciyarsa ke bugu fastly "shikena zansa ta dawo gobe InshaAllahu zanyi waya da alhji Muhammud yanzu kaje ka kwanta kasamu natsuwa ..auwal ya Mike tsaye yana layi tamkar wani mashayi ya nufi hanyar fita..
Mmn sudais ce
2/4/20, 8:39 PM - imusamuhd(professor): 💗💗💗💗💗💗
MUWADDAT
💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗
~NA~
*AYSHA A BAGUDO*
~DEDICATED TO~
_AUNTY SALAMATU AYYUBA_
_(UMMIN KADUNA )_
~BEST AUNTY FOREVER AND EVER~
alhamdullahi am back again.
warning!!!
don't read this novel if you know you are not married... ❌❌❌coz this book contains only for mature people , if you read it, is for your own risk ......wannan shine.
WATTPAD @HAUESH
bismillahirrahmanirrahim
page 17
....da sauri ta tashi zaune sosai tare da gyara zamanta ,basu daina kallonta ba hakan ya ankarar daita a she fa kanta babu d'ankwali sai lokacin tayi hanzarin d'auka ta d"aura gaskiya irin gyaran da muwaddat takewa gashinta ba namiji ba hatta mace 'yaruwarta zai iya burgeta bare nmj .
Hisham ya d'an juyo ya kalli abokinsa ya lura shima ita yake kallo minal ce ta katsesu ta hanyar yi musu sannu da zuwa sai da kowa ya zauna sannan muwaddat ma tayi musu sannu al'ameen ya amsa idanunsa akanta yace "yau dai kun sha hira ,tun sanda suka shigo muwaddat bata sake yin magana ba saboda tsarguwa datayi da irin kallon da al'ameen ke binta dashi haka minal ta fahimci muwaddat batason yin magana agaban al'ameen da tunda suka shigo ta kasa sakewa hisham ne ma yake d'an janta da magana amman Sam taki saka bakinta acikin surutun da suke .
Al'ameen ya Mike da kanshi ya nufi fridge ya bud'e ya d'auko lemo mai sanyi ya zauna yana sha, sai da ya gama sannan ya sake dubanta "mu tafi ko kar muyi dare ,batayi magana ba sai kawai mikewa datayi ta lalubi Jakarta ta rataya minal ta dubi al'ameen "gaskiya banso dawowarku da wuri ba domin hirar da muke bamu gama ba "to ko zama zanyi ku karasa ?
"Kai ma kasan bakuwa bazata iya sakewa a gabanku ba ,gashi daga shigowarku ta d'auke wuta ko magana bata iya yi ..
Muwaddat dai gaba tayi abunta har gaban mota suka yi musu rakiya minal tayita rokon muwaddat akan ta dinga zuwar mata hira muwaddat tace "bazan iya miki alkwari ba amman idan nasamu lokacin da kuma mai kawoni zan dinga zuwa ...
Hisham ya d'an kalli inda Al'ameen yake yana.dariya domin jin abinda muwaddat tace shi kuwa al'ameen shiru yayi kmr bai ji ba d'an Jan ajinta yasoma bashi haushi ya bud'e mota yashiga ya juyo ya d'n zubawa muwaddat ido domin yaga inda zata shiga amman sai yaga hisham yana k'ok'arin bud'e mata gidan gaba shiru yayi bai yi magana ba sai data shiga ta zauna sukayi sallama dasu minal har ya tadda motar sun fara tafiya sannan yace "na d'auka direban zaki sake meidani irin na d'azu"haba dai ta yaya zan maida kai diteba"eh mana gashi nan da zamu zo kin wani kwanta abaya ina janki tayi shiru ,da yaga bazata yi mishi magana ba sai cewa yayi "halan nayi miki kama da direbanki ne da d'azu ki wani rashi rashi abaya ?
"Ba kayi kama ba, tabashi amsa a agajerce dayake bata fiyye son doguwar magana kamarsa ba ,sukayi shiru gabad'aya can kuma ya sake janta da wata hirar da alamun muryata yake son ji, kallonta yayi tare da cewa "amman fa nayi mamakin yadda kuka dade kuna hira da minal musamman yadda kike ba ma'abociyar son magana ba ,"kasan ita magana zuwa take bawai ayita zuba kmr ruwa ba yace "ko ?
"Tace kwarai kuwa tun daga nan basu sake magana ba har suka iso wani katafarin mail na sai da kayan makulashe yayi parking din motarsa acikin harabar wajen sai daya bud"e ya fito kana ya zagaya ya bud'e mata yace "bismillah fito mu shiga ko, ta d'an yatsina fuska kmr kar ta fito sai kuma taga hakan bai dace ba ko babu komai d'an'uwanta ne yakamata ta nuna kulawarta.
ta fito tana yatsina fuska saboda kai tsaye gida taso taje ta kira bunayya dan tun safe take expecting kiransa amman ko miss call dinsa bata gani ba .
Duk yadda taki son jerawa dashi sai daya saita kafad'unsu suka jera suka nufi kofar shiga mail din suna gota wasu matasa da suke tsaye kusa da kofar shiga mail din ,dayan ya zunguri sauran da suke tare yana yi musu nuni da muwaddat.
"kai kai kai had'uwa ji wata hadaddiyar zalziyya suka kalleta gabad'aya, dayan yace "gaskiya da ba dan wancan gayen da suke tare ba, da sai na d'an latsa ko zan yi sa'ar ta sairareni ,daya daga cikinsu yace "kai tafi can kana ganin yarinya wata muguwar yar hutu