Showing 3001 words to 6000 words out of 116597 words
Chapter 2 - MUWADDAT Complete Document book by Aisha Bagudu .txt
ban zuba acikin sabon gidana ba ,komai akwai ke kawai suke jira .
Cikin murmushi tace "bakasan yadda yaya ya fika d'aukin wannan auren ba ,domin tunda yaji ka furta maganar auren yayi oder a kamfan, hatta kayan kitchen ya gama siya ..
Ishaq yayi D'an murmushi "ina ruwan mutumina ai naga alamar yafi kowa doki auren nan, to tun da yake ya rigada ya siya miki kayan d'aki babu komai asasu a extara room's.
kanta a sunkuye tace "shikenan Allah ya nuna mana ya kara budi Amman ni dai Dan Allah karkace zakayi wata hidima kayan aure komai na yafe, ya D'an dubeta cike da fara'a a zahiri gsky yaji dadin kalamanta "GSKY sai dai kiyi hakuri Dan koni bance zanyi ba dole dangina suyi bare kuma allah ya horemun abinda zan miki dole nayi komai da'akewa matashiyar budurwa kmr ki, kisawa ranki duk abinda ake yi na hidimar aure zan miki ,ni ko banason mace zanyi mata hidimar aure balle ke da zuciyata take kwakwa tayi murmushi "to ai ni nace na yafe ko?
Cikin murmushi ya tsura mata ido yana dubanta salon maganarta da komai na Burgesa "zuciyar ishaq ya fad'a yana sake tsareta da idanunsa "ki duba kanki da kyau ,kiga irin baiwar halittar da Allah yayi miki ai jikinki ya wuce irin macen dazatace ta yafe kayan aure ,kuma ya yafu din.
Ta rufe fuskarta tana dry saboda kunya "dadina dake kin fiyye kunya da yawa wallahi yanzu haka zamuyi zaman aure kina jin kunyata?
"Kayi hakuri zan D'an rage in naje gidanka "gsky yakamata Dan nasoma jin tsoron wannan kunyar Dan hka tun daga waje yakamata ki soma ragewa kinga idan na kaiki gidana na zamo abokin rayuwarki, kinga maganar kunya ma bata taso ba ,kunyar nan ki kawar daita domin mu had'u mu ingata rayuwar aurenmu.
" ni zama abokin wasanki ,abokin nishadinki, abokin Hirarki ,abokin barkwancinki ,kinga ni mutun ne mai son nishadi don hk nake bukatar cire wannan kunyar ,ko tun yanzu ni na cireta da kaina ya kai hannunsa zai ta 'bata tayi saurin dojewa da sauri zuciyarta na bugawa domin tunda taso arayuwata babu nmj daya ta'ba d'aura hannunsa ajikinta "babu abinda zan miki ,domin Sam bakiyi kama da tsagairan mata ba ,akwai cikar Kamala atare dake ,hankalinki da tunaninki tare da natsuwarki yasa nake kyautata kyakkyawan zato acikin rayuwar aurenmu ,Dan haka ina fatan zaki cire kunyar nan kiyi masa babban ma'aji agidan yayanki domin ishaq a yunwace yake dake ,ba zai iya da wannan kunyar ba "ki yi min akwarin cire kunyar ko na soma cirewa da kaina ?
Muryarta a matukar sanyaye tace "karkaji komai nayi maka alkwarin InshaAllahu zan cire ,tun yanxu ma na fara cirewa ...duk yadda taso kauce masa sai daya matsota sosai tmkr zai shige jikinta yana narke mata har yayi nasarar kamo fuskarta ya daidaita da nashi suna shakar numfashin juna ..
Wata irin soyayya ishaq yake nuna wa mukarama mai tsuma zuciya sai dai duk yadda yaso ya dinga romancing dinta taki yarda ,ta dinga nuna masa hkn haramu ne ya bari har sanda zasu mallaki juna .
Ishaq ya turo iyayensa aka kawo komai na aure tare da tsaida lokacin wanda bai wuce wata biyu kamar yadda ya bukata .
**********
Anyi biki lafiya amarya ta tare agidan angonta ishaq ba k'aramin shirya mata gida yayi ba ,gida kmr aljannar duniya komai yaji ban da tsiya babu abinda babu acikin gidan duk wani kayan jin dadi da more rayuwa an zuba mata takowani bangare ,gidan kam sai Wanda yagani ya had'u karshen had'uwa ,kai daga ganin gidan kasan naira ta zauna ,gabadaya mukarama ta tsinke da alamarin ishaq duk da tasan wani kusan attajiri ne ,Amman shigowarta gidansa tasan ya taka matsayin mai girma wajen dukiya.
byn 'yan kawo amarya sun watse mukarama ta sake sabuwar kwaliya saboda shirin tarbar miji duk da yadda zuciyarta ke luguden bugu, ta saka wani ratsetsen blue less ,Wanda tsayawa fad'ar kudinsa 'bata baki ne, ga zinarin da yayanta ya sai mata hannu da wuya sai sheki take irin turarrukan da tayi amfani dasu ita kanta bazata iya lisafasu ba, gabadaya gidan ya d'auki kamshi a haka ango yashigo ya sameta zaune a bakin gado lullube da mayafi ya D'an sa hannu ya yaye mayafin data rufe jikinta dashi yana mata dry.
Tsura mata kyawawan idanunsa yayi yana kallonta hk nan yaji amarya tasa tafi kowace mace kyau a duniya yasan gwanar Ado ce Amman na yau yafita daban kodan ya had'e Dana amarci ne, bai sani ba ,kallonta yake yana kallon halittar Allah irin kallon kurulla ,sai ta D'an sunkuyar da kanta tana murmushi habarta ya d'ago yasanya kwayar idanunsa cikin sannan yace "zuciyar ishaq duk yadda akayi kinyi kuka ko?
Ta D'an dubeshi kawai kana tace "me kagani ?
"Naga idanunki sun canza sunyi ja, kin tuna wani abu daya Sosa miki zuciya ne ?
Tayi murmushin tana neman wayancewa ,in har ta sanar dashi dalilin kukanta zatayi tace mishi me ?
Kmr yashiga zuciyarta yace "kiyi hakuri zuciyata ko baki fad'a ba ni nasan abu daya zai iya sakaki kuka a irin wannan lokacin bai wuce kin tuna da innarki ba, musamman idan mace tayi auren fari Amman ki kwantar da hankalinki ishaq zai rikieki amana, zai zame miki komai ,kani yaya dangi da komai nayi alkwarin kyautata miki InshaAllahu, daga yau bazaki sake kukan mutuwarta ba, komai runtsi zanyi k'ok'arin sanyaya miki zuciya ,zan rikeki amana zan kula da maraicinki, zan kyautata miki, San jiyar dake dadin dake cikin duniya gwargwadon ikona, zan soki, zan kaunaceki, Zan faranta miki bazaki ta'ba nadamar aurena ba, ta 'dan murmusa cike da jin dadin kalamansa sannan tace "nagode da alkwarin daka d'auka zan tayaka da addua Allah yabaka iko sauke nauyi dake kanka "amen.
Ka fad'i komai bakayi mgn akan cigaban karatuna da yayana ya kwallafa rai akansa ba ...ya tsinkayi muryata cikin dodon kunnenshi ya d'ago ahankali ya tsareta da ido kawai sai dry ta subuce mata aiko suka sa dariya gabadayansu ya kamo hannuta cikin nasa "ban manta ba ina sane zakiyi karatu har sai kin gaji matukar kina tare dani, domin ni kaina mai son yin karatu ne ..
Yanzu kin gaji dayawa saboda hidimar biki ,a yanzu Hutu kike bukata ba zance wani karatu ba, Dan hk nake son ki biyoni muje d'akina Muje ki kwanta ki huta..
Batare da mutsu ba ta Mike ta yafa mayafinta ya d'aukar mata sabuwar rigar bacci suka fito tare da kansa ya rufo bangarenta suka fito suka nufi bangarensa suna shiga yace "ina ganin kafin bacci yakamata mu fara gabatar da sallah nafila kmr yadda Manzon rahma ya Umarci ma'auratan da suka yi sabon aure suyi ,Dan neman zaman lfy da samun zuria na gari.....
Mmn sudais
2/4/20, 8:39 PM - imusamuhd(professor): 💗💗💗💗💗💗
MUWADDAT
💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗
~NA~
*AYSHA A BAGUDO*
~DEDICATED TO~
_AUNTY SALAMATU AYYUBA_
_(UMMIN KADUNA )_
~BEST AUNTY FOREVER AND EVER~
alhamdullahi am back again.
warning!!!
for the first time !!!! i will like to say," don't read this novel if you know you are not married... ❌❌❌coz this book contains only for mature people, if you read it ,is for your own risk.
WATTPAD @HAUESH
BISMILLAHIRRAHMANIRRAHIM
page 2
..tana hawa benen mahaifinta, ta d'an zuge kofar glass din parlour'n tashiga bakinta d'auke da sallama, sai alokacin gaanta ya fad'i sakamakon tunawa datayi da kanta babu d'ankwali ,daga ita sai wata hadaddiyar doguwar rigar, yar saudiyya wacce ta sha stone work ,amman kanta babu komai ,hakan ne yasa dogon gashinta data had'a ta tufke da ribbon suka bayyana .
har ta shiga parlour'n tana fargaban fad'an da dad dinta zai yi mata idan yaga kanta babu dankwali,
jikinta a sanyaye ta k'arasa gaban dad ta d'an durkusa ta gayar dashi kana tace" dady gani .
alhaji muhamud mai agogo ne zaune cikin tangameman parlour'n shakatawarsa, wani d'an k'aramin table ne agabansa, cike da kayayyakin motsa baki iri iri..
alhaji Muhamud ya d'an d'ago ya dubi yarsa muwaddat cike da fara'a da sakin fuska, sannan yace "muwaddat me kike yi acikin gidan nan tun safe baki lekoni ba .
tsadadden murmushinta tayi sannan tace dady babu abinda nake kawai a kwance nake, ina d'an hutawa, jira nake sai ka sauko sai na gaisheka.
" ok babu damuwa ince duk kanen naki sun tafi makaranta ne?
"eh sun tafi har ma direba ya dawo "to mai maman taku takeyi da bata zo ta kwashe wad'an kayan abinci ba?
"dady wanka tashiga, amman nasan zuwa yanzu ta fito"
yace" yanzu hk baki ci abinci ba ,kika je kika kwanta ,maza ga abinci nan ki zauna kici "dady bana jin yunwa ,ni bama yanzu zanci abinci ba .
"anya muwaddat kina kyautawa rayuwarki tunda kika xo gidan nan kullun sai ayi miki fad'a akan cin abinci amman bakya ji, wai ke yar gayu ko ?
tayi murmushi kawai, shi kuma yaciga da mgn "ina kika ta'ba ganin ana gayu ciki babu komai.
ta sake yin murmushi sannan ta mika hannunta ta d'auki apple guda d'aya ta kai bakinta ta gutsura tana niyyar tashi yace "ba tafiya zakiyi ba, ki zauna ina son muyi magana dake"
ta mike cikin natsuwa ta koma kan d'aya daga cikin kujerun na alfarma dake zagaye da parloun ta zauna tana jiran abinda zai gaya mata.
ya dubeta kana yace "muwaddat me yasa baki son d'aura d'ankwali?
" wato kin fi son kullun sai na miki fad'a akanshi ko?
"tace dady kayi hakuri wallahi mantawa nayi kuma kaina tsantsi garesa idan na d'aura d'ankwali baya zama sai yayita zamewa yace "zaki san gashinki mai tsantsi ne duk ranar dana saka aka aske miki kan na gata gayu..
muwaddat ta d'an langwa'be kai a kujerar tana dry yake, tasan fad'a kawai yake bazai iya aikata hakan ba..
"au gani kike da wasa nake yi, shi yasa har kike dry ko?
cikin shagwaba tace "to dady to ita umminah tana ina da har zata bari a aske min gashi?
"ai tunda bakijin magana daga ke har ummin taki na daina saurara muku tunda bata iya kwa'barki komai kike so sai ta biye miki, nan gaba in kuka yi wasa agaban ummin taki zan sa bulala in zaneki in ga yadda zatayi "a'a d'an Allah dady kayi hakuri na tuba bazan sake ba , in dai kan d'ankwali ne daga yau zan dinga d'aurawa "
sukayi 'yar dariya gabad'aya sannan yace "wai kuwa kinsan ma abinda nake shirin yi miki magana akai ?
ta girgiza masa kai "bansani ba daddy "yace to karatu nake son na samar miki a jamiar United Kingdom ...
muwaddat tayi saurin dafe daidai saitin zuciyarta dataji yayi wani irin mahaukacin bugu da karfin gaske, saboda tsanar karatun da tayi ,a tsarinta sam tafi bukatar yin aure akan wani karatu, ta girma da muradin son yi aure da wuri saboda yanayin halittarta ,sai dai tsawon lokacin nan bata samu wanda yadace daita ba kmr kaninta auwal wanda take ganin da wuya ta mallakesa arayuwarta, tunda ta kammala karatunta na diploma ,ta cire rai da wani karatu, nest budget dinta shine aure,ita aure take so ba karatu ba. sai dai ahankali zantuttuka mahaifinta ke shiga cikin kunneta kafin daga baya tace "wani irin karatu kuma dady ?
"nifa banida muradin tsanata karatu mai zurfi"
"kin ci gidanku dole kiyi karatu mai zurfi domin shine burin mu iyayenki, na asali da iyayen goyonki ,guda nawa kike yanzu da zakice baki da muradin karatu idan bakiyi karatu a halin yanzu ba uwar me zakiyi?
aranta tace "aure mana daddy ......
" yanzu ne daidai ki natsu ki tsaya kiyi karatu amatsayinki na yarinya yar shekara ashirin da haihuwa "daddy ni dai banason karatun nan yanxu kabarni kawai iya dilomar ma dana ta isheni .. "
"haba muwaddat ni fa nafi son kiyi karatu mai zurfi Allah yasani, "to da kika nace baki son karatu,aure kike so ko me ?
muwaddat ta d'an noke kai ala'mun jin kunyar mgnrsa tana dry "kinga nifa Allah yayoni da mugun son karatun boko bansani ba kodan nasan dadin karatun ne?
"ki taimaki rayuwata dataki ki cigaba da karatu, kafin muwaddat tace wani abu hjy hajara tashigo parlour'n wanda tun kafin ta k'arasa shigowa parlour'n take jin yadda alhj yake jaddawa muwaddat zance karatu mai zurfi yake son tayi.
da sallama tashigo parlour'n tana "cewa ka rabu da wannan yarinya mara wayo kawai ,in da kai ya waye da karatu nan ,shine ita take cewa bazatayi ba, tasamu guri ta zauna tunda bataso "idan bakiyi karatu ba uwar mezakiyi uhmmmmm?
"ki duba kiga yadda mata suka samu cigaba a dalilin karatu mai zurfi, ita kanta ummin taki tafison kiyi karatu mai zurfi kafin aure,amman shine dan iya shege kike cewa baki son karatu?
"baki son karatu sai me?
muwaddat tayi shiru tana jin kmr fito ta sanarwa da iyayenta burin zuciyarta, amman kunya tattare da fargaba ya hanata "ki dai gaya mata gsky karatu na da mutukar mahimmanci agurinta bari ummintata takaraso muji mai zatace, alhj muhamud
na gama fad'ar hk ya mike tsaye ya sa kai ya fice yana takaicin rashin son karatun da muwaddat take yi...
a harabar gidan yaci karo da motar dataje d'auko kanwarta da suke ciki daya, direban gidan na k'ok'arin daidaita tsayuwar motar yana ganinta ya fad'ad'a faraarsa sannan yaja ya tsaya yana jiran fitowarta, hjy mukarama ta fito a natse tana sanye cikin shiga ta alfarma doguwar riga ce har kasa sanye ajikinta da madaidaicin hijab, amman kallo daya zaka mata kasan cewar akwai gidan rana da tsantsar gogewa irinta 'yan boko atattare daita.
ta k'araso ahankali inda d'an'uwanta yaja ya tsaya yana jiran k'arasowarta "kar dai fita zakayi Yaya ?
"eh fita zan yi wai kafin ki karaso,dama wacan 'yar taki ta nemi 'bata min lokaci da tuni na bar gidan "
"me kuma baby muwaddat tayi ?
"da ita kullun bata wuce laifi agurinku shiyasa sam bata son zuwanta garin nan amman nake matsa mata "
"ai duk ke kike d'aure mata gindi amman nasan yanxu idan kika ji abinda tayi sai ranki yafi namu 'baci yadda nasan kike da kulafucin son tayi karatu.. "au akan karatu ne?
"akan shine mana wai yanxu nake mata maganar sai cewa tayi ita bata da muradin cigaba da karatu"
hajiya mukarama tayi murmushi tace "manta da wannn shirmen nata karatu d'an ada tayi sa, dan ma inaji tsoron gur'bacewar da rayuwa tayi yanxu ,ai da tare aka had'asu da bunayya "
"nima abinda naso kenan amman naga kamar ita bada raayin ma yin karatu, ni dai zan fita idan kin shiga kinsan yadda zakiyi daita "
"ai tafiya ma zamuyi zaman shirun ya isheni ni kad'ai a gidan daman itace abokiyar hirar tawa sukayi sallama yayi hanyar waje ita kuma ta k'arasa cikin gidan
*********
alhaji mahamud shine asalin mahaifin muwaddat, sai dai ba a hannunsa ta taso ba, ta girma ne a hannun k'anwanrsa da suke uwa daya uba daya , wato hjy mukarama da mijinta alhj ishaq , hjy mukarama da mijinta suna mugun son muwaddat ,babu irin kulawar da gatan da basu nuna mata ba , ko d'an cikinsu albarka .
su biyu kawai iyayensu suka haifa suka mutu suka bari a duniya, mahaifinsu tun mukarama na k'arama ya rasu ,suka cigaba da rayuwarsu da mahaifiyarsu, sun sha gwagwamaryar rayuwa kafin daga baya mahamud ya isa munzali mutun, d'an ma mahaifiyarsu jaruma mace ce ,ta iya sana'oi iri iri ,da hk ta raini ya'yanta , sai dai shi mahammud bai samu damar karatun boko mai zurfi ba asanadin matsananciyar rayuwar da suka riski kansu a wancan lokaci ,iyakarsa secondary school kawai ya tsaya wanda yayi a karamar hukumar koko ,
domin alokacin primary school kad'ai ce a kauyen nasu babu secondary, sai dai akai mutun wani gari, sai dai hkn bai hanashi jajircewa na ganin kanwarsa tasamu karatun ta kowani bangare ba.
bayan mahammud ya gama makarantar gaba da primary, ahankali ahankali yake sanarsa ta kwadago ta hanyar kasuwanci,da farko dai gyaran agogo yake har Allah yasanya masa albarka ya bunkasa arzikinsa ya zamo wani abu ..
adalilin wannan sana'ar tasa yasa yayi suna ciki da wajen kauyen har ake kiransa da muhamud mai gyaran agogo, wanda duk inda zaka shiga a fad'in kauyen nemansa, matukar baka sanya lakaninsa ba ,sai dai ka gama karad'e kauyen babu mai ce maka yasanshi.
bayan wani lokaci sai mahaifiyarsu ta kamu da ciwo ajali ta sha jinya sosai ,suka rasa yadda zasuyi, gashi ciki da wajen kauyensu babu asibiti sai anjen wani gari mai kuruna dake makwabta taka da kauyensu ,idan akace za'a kai mutun asibin ma zai iya yiwuwa ya rayu domin kafin akarasa mararrabar garin mutun zai iya mutuwa , nawa nawa akayi akan idanunsu suka gani ,dan haka addua suke kullun Allah ya kawo musu d'auki daga gwanati mai ci alokacin data tallafi rayukansu ta gina musu asibiti da makarantar gaba da primary .
tunda mahaifiyarsu ta fara ciwon take barwa d'anta wasiyya a kullun bakinta baya shiru da mgnr diyarta mukarama ta kance "mahamud ko na mutu dan Allah ka kular min da 'yar'uwarka kaga bata da kowa sai kai," kai ne uwarta kaine ubanta domin zan tafi na barta acikin lisafi na kurciya Muhammad ka rike zumunci ,mukarama amana ce a hannunka ina son ka kaunaceta fiyye da komai ka kula da maraicinta da rayuwarta karka bari ta zubda hawayenta akan damuwa kowace iri ce ..
duk sanda mahaifiyarsu ta tasa shi gaba tana bar masa wasiyya ya kan share hawaye yace "ki daina furta wannan kalmar inna cuta ba mutuwa ba,sannan ba'a san inda rai yake ba, babu wanda yasan gawar fari ban da Allah, baki sani ba ko mune zamu rigaki mutuwa.
"kayya d'an nan dayake hk take kiransa kasancewarsa d'an fari , "wannan ciwon bana tashi