Showing 117001 words to 120000 words out of 192750 words
nata Amnah kuwa sukuku tayi sbd Daddyn da Mummynta sune walwanta,farin cikinta da rayuwanta.
Da daddare Shima Bai shigoba sbd Bai sauko ba,
Washe gari ma Bai shigoba ya tafiyarsa office.
Safnah gantalinta Bai bari tasan Bena ta dawo ba sai data kwana biyu tukuna sbd kullum Bata wuni gida idan ta fita sai dare.
Dd babba taje ta gaida harda yimasa girki na musamman
Baya cin girkin kowa yanzu saina Bena Amma Bai nunawa Safnah din ba ya saka mata albarka tareda godia.
Qin zuwa sashen Umme tayi tinda taji Bena ta dawo Dan haka ta sake haukacewa tareda mayar da hankali ga Jan hankalin mijinta Wanda haryanzu suke yanda suke.
Bena kuwa cikin kwana biyu ta shiga Wani mummunan halin sanyi da damuwa,.Sam ta Dena zaman Palo sai ta tabbatarda lokacinda bazai shigoba take fitowa ta zauna cikinsu Umme
Zeenah ma aikinta baya barinta zama gida sosai itama Kuma.
Amnah halinda mummynta take ciki itama ya taba ta Sam ta Dena walwala da Hayaniyan yarinta Datake sosai ta sauya.
Shi Kansa a kwanakin gabaki Daya ya sauya baya cikin walwala ko sakewan,koyaushe ransa ba Dadi a hade fuskansa take
Duk sai abin ya sake taba Amnah Takoma kaman iyayenta ba walwalan.
Shine yafara kokarin dawowa daidai sbd Amnah data fara harda rashin lafiya sbd Bata Saba da qunci ba batama San Saba.
Duk yanda ya sauya Yana shigowa yanzu kullum Bena Bata taba yarda ya ganta ba gabaki Daya ta kaucewa duk Abinda zai hadasu.
Amnah idan zatai vidcall dashi barin dakin takeyi hakama idan har taji alaman Yana bangaren Bata fitowa saiya tafi.
Babban Qarin kame kanta ma harda matarsa Bata shaawan haduwa da ita Sam bare shi.
A haka suka share kusan sati biyu
Duk lokacinda matarsa akace ta shigo Bata fita sai ta fice hakama Shima duk akace Yananan Bata fitowa din.
Dd babba idanuwa ya zuba musu hakama umme sbd batasan meke damunsu ba kowannensu Kansa ya dauki zafi,dad kaante kuwa baimasan meyake faruwa ba.
Yau Zeenah bazata office ba hutawa zatayi Dan haka Suka shirya itada Bena din suka fita outing ko kansu duka zai sake.
Sunyi shopping sosai sunci tsadaddiyar abinci a restaurant na kaantes hotels and suites daga Nan sukas shiga VIP saloon and beauty parlor dake cikin kaantes hotels and suites din.
Ba Wani gyara dasuke buqata sbd kusan duk sati zuwa sati biyu saisunzo gyaran Amma tinda sun shigo Basu fitaba saida suka sake shiga Akai musu manicure and pedicure dasu gyaran Kai da sauransu.
Suna fitowa Bena tace Zeenah ta ajiyeta gidansu zata duba Annenta.
Bayan sun Isa Bata bari Zeenah ta shiga ba tace ta tafi kawai idan ta gama zata kira Abbakar ya turo driver ya dauketa.
Hakanan Zeenah ta barta ta wuce Amma taso duba Annen itama Amma Bena da dubara ta hanata sbd Bata son a ga Annenta cikin halin Datake ciki.
Yau dinma Bata tadda Ababa ba Dan haka gyara Annenta tayi fes ta sake tsaftace mata dakinta tsakan gidan kaman bola sbd babu me shara sai Anne ta Dan dawo daidai tayi musu shara
Shi girki kuwa yanzu Ababa kusan kullum na Siya yakeci lafiyayye hande ma wataran na Siya wataran Anne keyi idan tana daidai, Annen ce kawai kusan yunwa tafara shigowa cikin ciwon nata sbd saisun rage suke Bata.
Ganin Hakan sai Bena ta kawo Mai Aiki gidan ta ringa shara da wanki da girki Amma wahala tasaka me aikin kwana daya tayi ta gudu,
Bayan ita wata ta sake kawowa itama kwananta biyu ta yiwa Ababa Satan da Saida Bena din tayi masa ranko Kuma ya Yanke babu me aikin da zata Kuma kawo masa gidansa daga lokacin.
Ana gama sallan magrib akazo daukanta ta koma gida.
Wanka tayi ta saka straight pencil Sisley doguwan Riga me laushi data kwanta jikinta gabaki Daya bawai matsewa ba.
Qaraman hula ta saka tareda ziro slippers tana fitowa palon Yana shigowa Shima sanye cikin black Ralphs da slippers na chanel fuskansa fresh Yana fidda Wani kwarjinin da sirrin kyau.
Bata dakata ba ta juya kawai zata nufi hanyar kitchen babu tsammani ya riqota sbd ya kasa Hana kansa barin ta tafi.
Baya ya dawo da ita bayanta ya jingina da kirjinsa qamshinta ya shiga hancinsa take ya rufe Ido Yana son magana ta kwace jikinta a hankali tareda yin gaba ya riqota kenan Amnah ta shigo palon daga dakin Zeenah tana ganinsu tayo gurinsu ta tsaya tana kallansu tace
"Daddy Kuna fada ne ko?"
Mummy na ta dena kulaka kullum sai tayi Kuka a daki tayi rashin lafiya harda Kuka nidai yanzu ku shirya ku Dena fada gaskia."
Murmushi me kyau ya sakewa Amnah din tareda furta "I love you my angel" ya Maida kallansa kan Bena datake sake kokarin zare hannunta da riqonsa ya sake janyota ta dawo jikinsa ya zagayeta da hannunsa ya Kalli wuyanta dake buso masa qamshi nta yace
"Angel jeki gurin umme zan shirya da mummynki"
Da murna ta juya tayi dakin ummen da gudu tana farin ciki.
Qwacewa Bena ta hau Yi fuskarta ba walwala
Bai ce mata komaiba ya dagata cak zuwa bedroom dinta ya Bude ya shiga tareda tura kofan kafin ya jiyeta tareda jinginar da ita jikin kofan yayi manneta da kirjinsa ahankali.
Idanuwanta dasuka qi kallansa ya kalla tareda Kai bakinsa kan fatan kunnenta cikin qaramin sautin Daya saka gashin jikinta gabaki Daya miqewa yace
"Kukan me kikeyi kullum?"
Dumin numfashin bakinsa ya sauke direct cikin kunnenta tareda maganarsa Dan haka qafafunta sukai Neman saki zatai qasa ya zagayeta da hannunsa Daya tareda matseta da kyau jikinsa Yana lumshe fararen idanuwansa tareda zira Kansa wuyanta ahankali ya Shaqi qamshinta da qarfi.
Da qyar ta iya Bude baki muryanta ba sauti sosai itama ta furta
"Ka sake ni please"
Kansa dake cikin wuyanta yasaka maganarta shiga kunnensa Shima direct tareda dumin numfashinta Dana haka gabaki Daya ta qarasa kunnasa ya dago a kasalance ya Kalli fuskarsa tareda gangarawa da idanuwansa bakinta zuwa wuyanta da Kirjinta da rigar ta kwanta ta lafe.
Kunnenta ya fara sakar kiss me sanyi ahankali kafin ya sakarwa wuyanta tukuna ya dago ahankali ya kama bakinta da nasa wannan Karan tare suka fara kissing juna cikin sanyi ba da zafi ba.
Baa taba kissing nasa ba sai yau din sbd duk kisses din dasuka taba Yi shine yake kissing nata Bata taba kissing nasa back ba sai yau Dan haka kissing din na yau yafi kowanne shigarsu da tsimasu.
Ita kanta batasan tafara kissing din nasa ba sbd daga ita har shi sunyi kewan juna sosai batareda sun San Hakan.
Sake matseta yayi jikinsa tareda daukanta suka nufi couch har lokacin bakinsu na hade tini wayarta da hularta suka watsar jikin kofa
Ya zauna tana kan qafafunsa Yana Jin notin Kansa suna kuncewa Daya bayan Daya,..
Rigar jikinta ya Zame Daga sama zuwa jikinta Takoma daga ita sai hot red strapless bra data sake gigitasa ya shafo cikinta Yana zuwa kirjinta Yana Jin bazai riqe Kansa ba.
Kirjinta ya dawo da Kansa da baki ya fizge bra din Daman Ba hannuwa ne da ita ba bare Wani qarfi sbd bras masu tsada basuda Wani qarfi,nauyi bare takurawa.
Jikinsa ta shige sbd rabata da bra da yayi shikuma Hakan ya kunce masa last notin Kansa Daya rake Dan haka ya ringa kissing fatar jikinta Yana cakuda ta.
Bai taba samun Kansa a cikin wannan halin ba shi dayayi rayuwar turai da yanda yakeso bare ita data taso a killace cikin Cage Dan haka cikin zazzafan shauqi suka samu kansu da Wani irin crazy romance Daya kaisu wata rayuwar ta tsakanin so da kaunar juna batareda baki ya furta ba.
Miqewa yayi tsaye da ita zai nufi lafiyayyan gadan dakin ta fizgo nutsuwanta tana sauke numfashi ahankali ta Bude idanuwanta dasukai nauyi ta kallesa tareda dakatar dashi tana nuna masa kofan da Akai knocking Ahankali.
Wani irin zazzafan numfashi ya sauke me zafi kafin ya iya datakar da Kansa Yana kokarin daidaita Kansa ya saketa
Ta sauka jikinsa ahankali tareda Maida rigarta ta tana kasa kallansa ta nufi Kofa ta dauki wayarta da hulanta dake gurin tana juyowa ya taso ahankali idanuwansa jajir ya fice daga dakin.
Zeenah dake buga dakin sbd Daman tinanin Yana ciki Dan Amnah tace daddynta na bangaren
Kasa binsa da Kallo tayi sbd ganin yanda ya fita fuskansa a hade.
Shigowa tayi dakin tana kallan Bena data kasa kallanta itama tana kokarin danna wayarta.
Akan bra din Benan dake qasa yashe idanuwanta suka sauka tana ganin Hakan ta Hana murmushinta fita tayi kaman Bata ganiba tafara tambayan Bena Abinda ya kawota.
Kasa amsata da kyau Bena tayi Zeenah na ganin Hakan taji haushin kanta dataxo daidai wannan lokacin da Bena dinta zata samu Karne Virginity din DD kaante.
Zeenah na fita toilet Bena ya shiga tayi wanka ta fito tayi sallan ishai da Kai tin dazu Basu saniba.
Daqyar ta iya fitowa cin abinci sbd har lokacin jikinta a mace yake suna gamawa ta koma daki ta Kwanta.
Washe gari da sakonsa ta farka na cewa Takoma Aiki Dan haka cikin murna ta da farin ciki tayi Shirin office ta fice.
Acan ya wuni gaf da magrib ta dawo sbd tarin aikin data tarar office dinta.
Tana yin parking harabar gidan ta fito mota daidai lokacin Safnah itama motarta ta shigo tayi parking me aikinta na bayanta ta fito idanuwanta suka sauka akan Bena data wuce batareda ta tsaya kallanta.
##MAMUH#
#DBENA
#LOVE
#ROMANCE
#TOO HOT
*_HAMMAK KITCHEN UTENSILS_*
*_INA MAABOTA GAYU DA SON BURGE BAQI DA ME GIDA?_*
*_SHIN KUNSAN HAMMAK KITCHEN UTENSILS SUNA DA QAYATACCIN KAYAN KITCHEN MASU KUDI DA MASU ARHA NA WAJE DANA GIDA NIGERIA_*
*_BA IYA ZUWA SHAGO KADAI KU SIYO BA HARDA AIKAWA SUNAYI KOINA HAKAMA SUNA ADASHEN KAYAN KITCHEN MANYA DA QANANA,MASU SAUKI DA MASU TSADA,NA WAJE DANA GIDA NIGERIA,_*
*_ZAKIYI ZUBINKI A HANKALI KI KWASHI DUK ABINDA KIKESO A AIKA MIKI ABINKI CIKIN SAUKI DA AMANA DAN HAKA SISTERS KARKU BARI AYI BAKU MUN SANI MUN SHEDAR HAMMAK KITCHEN UTENSILS SUNE THE BEST👍_*
@hammakkitchenutensil
Tarauni market Abba hamisu plaza block A shop no 8
or dorayi sabon titi before gidan man b i
Wa.me/+2348067376035
[9/4, 1:07 PM] MG: *_Arewabooks@Mamuhgee_*
66
Dummmmm kunnuwan Safnah sukai mata jinsu na daukewa ahankali tana Jin maganar Rabi me aikinta Sama sama dake tambayanta ko lafiyanta kalau.
Bata iya Jin me take fada daidai Saida qaramin jiri me juyar da Kai ya dibeta Rabin tayi saurin tareta tana kallanta cikin tsoro da mamakin meya sameta a take.
Idanuwanta dake Neman hada mata hadari hadari ta sake budewa da kyau akan Bena wadda ko mutuwa tayi aka binneta ta kwana kabari aka fitar zata Gane itace wlh,
Benazir 'yar uwarta jininta ce ta Gani takuma tabbatarda ita din ce idanuwanta har Wani rawa rawa sukeyi gurin kallanta harta shige
Take Wani jiri me qarfin gaske ya kuma dibanta qafafunta na kakkarwa ta kasa dagawa da Kanta kaman makauniya Rabi ta kama hannunta zuwa bangarenta.
Suna shiga Palo ta tsaya sbd Bata ganin komai sai duhu duhu ganinta Yana rawa cikin masifa da tashin hankalin da Bata taba saninsa ba a rayuwanta...
Harshenta karyewa yayi tana son tambayar Rabi wacece wadda suka Gani din Amma batada hali sbd karshenta dake sake karyewa hannuwanta duka na jijjjiga ta Ciro wayarta Bata Gani sosai daqyar ta iya Gane numbern Momynta ta saka kira sai alokacin ta zamu qarfin halin fizgo magana bakinta da cewa
"Waye,waye...wadda..muka..gani"
Ko gama rufe baki bataiba da kalaman data kasa hadawan
Rabi cikin tashin hankalin da tsoron meyake faruwa ta katseta da Bata amsan cewa
"Aunty Bena ce,dayan Matan Sir DD,maman Amnah 'yar marigayi Sir Bial."
Sankarew Safnah tayi a gurin komai nata na tsayawa cak harda numfashinta da qyar ta iya kemo Kalmar "bana Gane komai me kika fada?"
Cikin tsoro da qara shiga firgici Rabi ta Bude baki ta sake maimaita mata bayanin tana gama maimaitawa
Duhu ne ya rufe idanuwan Safnah gabaki Daya sai ganinta Rabi tayi ta Yanke jiki ta Fadi a gurin Sume babu inda yake motsi a jikinta Kuma daidai lokacin Momynta ta daga Kiran Safnah din Daya shigo wayarta tafara Kiran sunanta sbd Jin ba magana.
Ihun Kuka Rabi ta sake jikinta na daukan rawan tsoro itama tafara Kiran sunan Safnah din cikin fargaba da rashin sanin meyake faruwa.
Jin Rabi na Kiran sunan Safnah cikin Kuka da tashin hankali ya saka momyn kashe wayar cikin faduwar gaba da shiga nata firgicin.
Kiran wayar tayi tareda miqewa daga zaunen datake palonta ta shige bedroom dinta tareda rufe kofar
Rabi na daga wayar cikin masifa tace
"Ke banasan hauka da jahilci ki nutsu ki fadan meyake faruwa ne?"
Hadiye tsoro Rabi tayi cikin Dan daidaita kanta tace
"Aunty Safnah ne ta Suma Kuma Bata motsi Sam harda numfashi ma batayi."
Wani mummunan yawun tashin hankali momy ta sauke tareda Jin itama nata jikin na Neman daukan rawa idan Safnah ta mutu yanzu ai ita Kuma ta shiga uku da sauran buqatoci da burikan da Bata cimmawaba.
Miqewa tayi daga zaman datai bakin gado tace
"Akwai Wanda yasan halinda take ciki ne?"
"Ah ah" Rabi ta amsa tana waiwayawa duk da palon a rufe yake.
"Ki Jata ki Kai daki kada DD ya dawo ya sameku a Hakan karki bari kowa ya sani ganinan zuwa yanzun Nan."
Kashe wayar tayi tareda daukan key din motarta da mayafi ko handbag Bata tsaya dauka ba ta fito hajiya Bata sani ba ta fice daga gidan tana Hana kanta daukan duk Wani negative tinani.
Cikin mintina qalilan ta Isa kaantes sbd gudun data zabgo Amma tana shigowa anguwar ta rage gudun kwata kwata a natse ta shigo da motarta har ta iso gate aka Bude mata ta shige tinda ansan mahaifiyar Amaryar Sir DD ce.
A natse tayi parking harabar gidan ta farko sbd duk bako baya wucewa da motarsa gate na biyu saidai ya ajeta a na farko masu gidan ne kawai ke wucewa gate na biyu suyi parking motocinsu acan.
Bayan tayi parking hakanan ta tilastawa Kanta nutsuwa da kamun kan dole tana Amsa gaisuwan securities harta shige gate na biyu ta wuce zuwa bangaren dazai kaita bangaren Safnah.
Tana Isa ko knocking bataiba ta Bude kofar ta shigo Kai tsaye dakin Safnah ta wuce ta taddata har lokacin Bata farfadoba da alama idan baa taimaka mata da gaggawa ba zata iya macewa ma Kila a Hakan.
Ruwa ta fada toilet da kanta ta debo tana fitowa ta zuba mata su tana Kiran sunanta cikin mamakin Abinda yake faruwa da zai sakata shiga wannan halin.
Cikin mummunan hali ta sauke ajiyan zuciya a fizge tareda Bude idanuwanta idanuwanta da sukai jajir take sbd mummunan tashin hankali da masifar datafi mata rayuwar gidan Ababa.
Kasa motsawa tayi tana Neman sake somewa a Karo na biyu momy ta saka hannu biyu tayi mata wata irin jijjigawa tana cewa
"Ke kimun bayanin meya faru ne kina Neman sakamun hawan jini da wasi wasi da firgici"
Rabi momyn ta kalla tace ta fice daga dakin ta dawo da kallanta kan Safnah dake magana ita Daya kaman ta zauce a rikice tana sake tsinkewa da lamarin ta sake jijjjigata ta kira sunan cikin tsawa da babban tsoro tace
"Wlh zan tafiyata na barki koma wace masifar kika debo ta tsaya kanki.."
Kuka Safnah ke nema ta fasa ko Abinda ya danne kirjinta zai fada Amma ta rasa Dan haka ta dago idanuwanta dasukai jajir ta Kalli momy bakinta na rawar fita hayyaci tace
"Momy Bena matar D itace Benazir 'yar uwata,.uwa Daya ta haifemu,
Uba Daya ya haifemu,Nono Daya muka Sha.....itace matar Dawood,.itace wadda aka fara daura masa aure da ita,.itace uwar Amnah 'yar Bilal dasuka Haifa ba aure.....Somewa ta sake Yi a Karo na biyu momy da tayi mutuwar zaune itama kusan somewan take Neman Yi Saida Rabi tashigo Jin shiru ta debo ruwa ta zuba musu hankalinta na sake tashi tareda shiga tsoron lamarin Dayake faruwan.
Suna farfadowa sai alokacin Safnah ta Dora hannu Akai zata fasa ihu da kukan balai da masifar Datake ji cikin zuciyarta
Momy da itama duka jikinta rawa yakeyi ta rufe mata baki da hannuwanta biyu tana jijjigata cikin bushewan zuciya da tattaro nutsuwa tace
"Ki dawo hankalinki ki nutsu ki tabbatarda benazir 'yar uwarki ce kika Gani ba gizo ba.
Wallahi tallahi Benazir din Dana sani ce,
Wallahi tallahi itace,
Rayuwata tazo karshe,
Komai nawa yazo karshe,
Identity Dina zai bayyana,.
Daddy zai San ni wacece,zai tsaneni,hajia zata tsaneni,ummen D da shi Kansa zasu tsaneni idan sukasan ni wacece dakuma yanda na wulaqanta mahaifiyata na baro gida,ban taba waiwayansu ba,
Yaya aurena da D zai qare?
Qanqame hannuwan momyn tayi jikinta na rawa da fizga cikin mummunan tashin hankali tace
"Momy Dan Allah kiyi Wani Abu akan Hakan,banason na rasa Sunana da matsayina a matsayin Safnah basheer bulama,
Bazan iya barwa Bena D ba wlh,.bazan iya rayuwa a yanzu ba a Safnah bulama Dina ba,
Bazan iya barin D ba,
Karki bari asan Koni wacece sbd zan rasa komai Dan Allah momy kiyi Wani Dan Allah......
Yanda jikinta ke rawa tana maganganun cikin ficewan hayyaci da mummunar tashin hankali yasaka momy sake jijjjigata da qarfin gaske tana cewa
"Ke kiyi shiru babu Abinda zai faru a abubuwan da kika fada,
Babu wata Safnah Ababa a dunia yanzu se Safnah bulama,
Babu wata macen da Dawood kaante zai zauna da ita sai Safnah bulama,
Waye benazir?
Matar data gama budewa Dan uwansa qafa ya gama Abinda yake da ita itace zata warware mana aikin shekara da shekaru??
Wallahi ko Wanda ya tsaya mata bazai warware mana aikinmu ba,
Kina maganar asirinki ya tonu Zaki rasa komai kin manta tonuwar asirinki shine tonuwar nawa?
Wallahi Bena bazata lalata mana Aiki ba Koda Hakan na nufin kawar da ita ne.
A razane Safnah ta dago tana sake jiqewa cikin mummunan zufan dake qarawa jikinta rawa.
A zafafe momy tace
"Kinada Wani tsarin ne bayan na kawar da Bena sbd itace mukullin buduwan sirrinmu,
Idan ta kauce babu Wanda zai haramta aurenki da D,hakama babu Wanda zai ganki anan bare yasan asalin ke wacece.
Girgiza Kai Safnah tayi tana kallan momyn har lokacin cikin tashin hankali tace
"Momy kawar da Bena a yanzu ba shine Abinda zamuyi na farko ba,
Bena D Yana aurenta tsawon shekarun Nan batareda ta tare ba hakama tin zuwana na samu tabbacin babu Abinda ya taba shiga tsakaninta dashi na aure Kinga kuwa inada Chance,
Munada wata Daman.
Cikin tinani momy ta Kalli Safnah tana miqewa tsaye tana Dan zagayawa kadan kafin ta tsaya gaban Safnah din suna kallan juna tace
"Duk tsanani duk wuya kada ki bari ta taba ganinki,.
A yanzu babban abin buqata da burinmu shine D yafara kusantarki kafin Bena din Dan idan bamu samu nasarar kauda ita ba aka Samu akasin ta ganki to tabbas sharia zatayi amfani da wadda ya kusanta a cikinku itace matarsa(inshallah),
Amma duk tsanani duk wuya Muna buqatan bacewan