Showing 9001 words to 12000 words out of 192750 words

Chapter 4 - ZAFIN KAI COMPELET BOOK BY Mamuhgee.txt

12 Dec 2024

7161

dabbobi sbd tsanani da lamarin ya qara.


A ranar da sukai kwana biyar a wannan halin da rana tsaka Suna can suna aikin wankin kayan Ababa dana Hande ga aikin wankin fatar da aka kawo kusan mota biyu sunata yi cikin gajiya da yunwa.


Safnah silalewa tayi ta koma dakin dasuka rufe Annen ta tsaya a kanta tana kallonta tsawon mintina kafin ta sauke numfashi mai zafi ta durkusa ta warware mata daurin da sukai mata na hannuwa dana kafa.


Sanin da rana Ababa baya gida Hande ce take tsaronsu ko ina bata zuwa sbd su din haka koma ta fita tabar musu gidan a bude Annensu bazata taba iya guduwa tabar gidanba sbd aikin da Ababan yayi mata daga ranar daya aureta duk tsanani da azaba bazata iya tafiyaba har sai ranar daya gaji yace ta tafi da kansa.


Janyo Annen tayi ta nuna mata dakin Hande tace mata taje can samirah na ciki Hande ta boye.


Jin hakan yasa Anne da qafafuwanta duk sukai sanyin dauri amma bata damuba sbd ciwo ta nufi dakin Hande da gudu ta fada tana zubar da kaya tana neman samirah idanuwanta a waje bata ji bata gani.


Cikin bacci hande taji kaya tako ina a kanta a firgice ta tashi tana neman dauki sbd komai janyowa Annen keyi ta yadda ta fasa tana neman ‘yarta.


A rikice zani na neman sauka Hande ta fito tana ihu tana neman agaji saidai su benazir na can gangaren dabboni basa ji sosai
Safnah dake boye tana jiran hande ta bude gida ta sake leqowa zuciyarta na wani irin tsalle da azababben tsoron yaya tata qaddarar guduwar zaya qare.


Kan Hande dake daura zani Anne tayi tana kokarin duba ‘yarta cikin zanin
Tini hande tayi hanyar kofar gida tana fizgo dankwalin kanta sa mukullan gidan ke ciki daure ta bude gidan da sauri hannuwanta na rawa dan a duniya tana tsoron mahaukata tunda sukai sanadiyar rasa hakorinta biyu a wani kauye dataje biki.


Tana bude gidan ta fice da sauri tayi bayan gidan tana kwada kiransu Benazir dake ta cikin gidan hankali tashe dan bazata shigoba sai sun kama uwarsu sun daure.


Safnah dataji wani nannauyan abu ya fada daga kan kirjinta bayan ficewar hande fitowa tayi daga mabiyarta ta mufi kofar gidan batareda ko so daya ta waiwaya ta kalli inda mahaifiyarta ta fadi qasaba tana buga kanta sa qasa ta fice daga gidan ta bi ta bayan da Baa nan Hande takeba ta lullube kanta ruf da qaton mayafin Hande data dauka a igiyar shanya ta dosa daji kai tsaye sbd idan ta nufi cikin gari zata dade bata bar garin ba.


Su Benazir dake galabaice suna aiki ba wani qwari ko cikakken kuzari a jikinsu sukaji ihun kiran da Hande ke musu ta katangar bayan gidan da sauri suka taso hankalinsu tashe.


Benazir ce tayi kan Anne da gudu tana riqeta daga ciwon datake jiwa kanta,


Sumayyah kuwa tsaban rikicewa da firgici ‘dakin handen ta nufa tafara tattarawa babu inda baya rawa a jikinta cikin mintina kadan ta gyare dakin ta maida komai inda yake ta fito har lokacin a rikice take dan tasan yau suda mahaifiyarsu sai Allah.


Benazir kuwa cikin matsanancin tashin hankali take jan Annen takaita daki ta fashe da kuka mai qarfinda bata taba sakiba a rayuwarta.


Kukan Benazir yasa Anne tsayawa cak daga mutsu mutsun datakeyi ta zubawa Benazir din ido kaman me nazari.


Kuka sosai Benazir keyi tana sarewa daga komai na rayuwa,
Sumayyah na shigowa a firgice sunan safnah tafara kira tana cewa,


“Ina safnah?
Ina tayi?
Bangantaba?
Bata koina…


Dakin tabi da kallo bataga safnah din ba qarin sautin kukan Benazir ya tabbatar mata da safnah ta tafiyarta kuma tabbas itace ta warware Anne ta sakota,
Kenan da mahaifiyarsu tayi amfani dan cimma burinta a mafi wulaqancin hanya tayi amfani da uwar data haifeta.


Silalewa itama tayi qasa ta fasa kuka mara sauti dan batada karfin yin me sautin ma koda taso.


Wani irin kuka sukeyi wanda radadinsa ke fitowa daga qarqashin qasan rai mai ciwo da qunci da baqin ciki tareda qaqa nikayi.


Kaman an yayyafawa wuta ruwa ta mutu haka Kukansu ya yayyafawa yanayin Annensu sanyi gabaki daya ta rakube guri daya tayi shiru tana kallonsu da idanuwanta dasu kansu ciwo sukeyi na rashin bacci da zarewa.


Lokaci mai tsayi suka dauka a hakan kafin suka fito sukai Alwalan sallar magriba suka dawo sukayi kafin suka kama Annen suka fito da ita zuwa can bayin baya da akai musu a cikin dabbobi sukai zaunar da ita kan kujerar karfe sukai mata wanka fes sbd tunda tafara ciwon bata samu wanka ba.


Kaman yarinya qarama haka suka kamota suka dawo da ita abincin da Hande ta basu cin mutum daya shi suka barwa Annen tacinye rabi rabin duk ya zube.


Shiru sukayi a daki babu me iya magana sbd rashin sanin makomarsu data Annensu suna jiran dawowar Ababa.


Addua sukaita tofawa Annensu suna rokon Allah sauki da mafita sai gashi cikin yardar Allah bacci ya dauketa a inda take zaune dan haka suka gyara mata kwanciya tareda rufeta da wani barkakken zani.


Guraren karfe tara sukaji bude kofar gidan a tare dukkaninsu suka miqe daga kwancen da suke jikin sumayyah na wani irin kerma da fizga ta kalli benazir wadda su kadai suka ragewa juna gashi benazir nada juriya da jarumta amma sam ita Allah bai bata ko daya ba sbd kusan rauninta yafi na kowannensu.


Ahanakali Benazir ta tashi tsaye tareda kama sumayyah din da bazata iya miqewa ba sbd tsananin kerma da tsallen da zuciyarta keyi kaman zata buga.


Kafafuwansu na rawa suka fito tsakar gidan da tini Hande tafara zayyane masa abinda ya faru.


Tsayawa sukayi daga inda sukasan yana basu umarnin nesancinsa dasu.


Wani wulaqantaccen kallo yake musu kowaccensu kanta na qasa suna kokawa da tarin tsoron dake zuciyoyinsu.


Ganin su biyu kawai yasashi juyowa da kyau yana kallonsu babu alamar rahamar kauna ko tausayi na digo daya a fuskarsa da Amon muryarsa me gigita duk wani ruwa da abinda yake aiki a jikinsu kai tsaye yace,


“Ina Safnah?”


Wani qarar kuka mai qarfin gaske ne ya fito daga cikin Sumayyah datake gab da shidewa sbd tashin hankali.


Idan yana tsaye sumayyah bata taba iya magana sbd firgita dan haka Benazir da itama take cikin mawuyacin halin tashin hankali dole tayi qarfin halin bude baki muryarta na wata irin rawa tace,


“Bata nan ta tafi……..Wani jahilin marin bayan hannu ya saukar mata ba zata a fuska wanda yasata kifewa a gurin bakinta na fashewa.


Tasowa tayi batareda ta dora hannu a gurin ba still kanta na soke a qasa dan basa dagowa a gabansa.


Shaqota yayi idanuwansa waje take wani kumfa na tsananin masifa ya cika bakinsa yana fesowa ya sake sauke mata wasu marikan guda uku a jere yace,


“Bata nan ina taje??


Duk wuya baya tambaya aqi amsawa dan haka cikin azaba tace,


“Ta gudu”
Wurgi yayi da ita dukkanin jikinsa na rawar masifa da tsananin bacin rai na wutar masifa dake babbaka jininsa ya shaqo sumayyah wadda takusa sumewa dan numfashinta iya wuyanta yake tsayawa baya kaiwa cikinta sbd ganin tashin masifarsa.


Mari daya yayi mata ta zube a qasa tana jan numfashi da qyar bakinta na jini dukkanin jikinta na kerma.


Take qafafunta yayi ya janyo Benazir da hannuwansa yana cewa,


“Tayaya zata gudu?
Ni zaku boyewa uwarku na hauka acikin gidana?
Duka guduwa kuke da niyar yi ku barni da asara batareda na fanshe kudina ba da asarata?
Wallahi akan ku biyun nan saina fansa daga kan sisi har Dubunnan dana kashe akanku da uwarku,
Kune zaku biya duk wata asarata ficika woh bazan yarda na rasa ba.


Shaqe Benazir sa bakinta itama yake jini yayi ya damqo sumayyah dake yashe qasa ya ringa jansu kaman ba mutane ba yakaisu dakin da uwarsu take ciki tana bacci ya hadasu su duka ukun yayi musu shegen dukan dayasa babu mai iya tashi zaune daidai acikinsu.
#MAMUH#
#KANTEES#
#BENAZIR
#LOVE
#ROMANCE
#DEEP
#SISTERS


ZAFAFA BIYAR🔥


-ZAFIN KAI
Mamuhgee


-TABARMAR ‘KASHI
Safiyya Huguma


-FURAR DANKO
Billyn Abdul


-BAKON MUNAFIKI
Miss xoxo


Duka hudu 1k
Uku 800
Biyu 600
Daya 400


Pay at
09033181070
09032345899


Zafafa🫶🔥🔥
[8/13, 3:29 PM] MG: _Arewabooks@Mamuhgee_
8
Hankalinsu duka baa kwance ba suka isa gida saidai cikin saa har lokacin Ababa bai dawo gida ba Hande ce kawai taketa fadan sun samu sake sunyi dare babu wanda yayi magana acikinsu saida tagama yi musu tatas kafin suka hanzarta yin sallah suka fito suka karbarwa Annensu aikin da bata gamaba har lokacin.


Wani sabon wankin ne suka fara cikin dare basu gamaba sai guraren karfe tara na dare
Daqyar sukai sallah sukaci dan abincin da aka basu suka kwanta kowannensu gababin jikinsa na ciwo.


Washe gari haka guraren 9 na safe suka isa makaranta.
Sumayyah kai tsaye libry ta isa sbd acan zasuyi karatu da wadda sukai jiya,
Tana isa zata shiga ta nema id card dinta ta rasa,
Gefe ta koma ta zazzage jakarta tafara dubawa hankalinta na fara tashi sbd batasan ya zatayi ta samu wani ba komai Benazir ce take yi mata bata iya zuwa da kanta.


Dubawa takeyi da gaske tana bin pages damuwarta na bayyanuwa duk da tanada tabbacin yana jakar bata fiddasa ba.
Duk abinda yake jakar tayi masa daddaya amma bata gansa ba,
Tattara kayanta tayi ta maida jakar ta nufi gurin Benazir cikin dan sauri da damuwa,tsoronta da tashin hankalinta shine ace sai ka biya kudi zaa maka wani,
Ina zata samu kudin?Ababa idan suka fada masa saiya kusan rabata da duniya kafin ya bada kudin,ya Allah yasa ta gansa kokuma baa biyan kudi ake bada wani.


A yau dinma tashin hankalinta bai bari tana tantance inda take saka kafafunta ba kanta a qasa har ta isa department dinsu Benazir din.


Kiris ya rage tayi karo da wanda yake tahowa yana amsa waya cikin nutsuwa da sanyin hali
Da sauri ya dago hannuwansa yayi saurin tareta sbd kada jikinsu ya hadu.


A firgice ta dago tana ja da baya cikin qarfin gaske sai gata a qasa
Bata damuba ta miqe da sauri kanta na yin qasa a sanyaye ta basa hakuri tana sake sauke kai kaman wadda take gaban Ababa.


Cikin dan mamaki ya kalleta yana tabbatarda itace mai student id card din hannunsa,
Juyawa tayi zata wuce batareda ta dago ta kallesa ba zuwa lokacin jikinta rawa yakeyi sosai dan gabaki daya Azabar Ababa kawai take jin har tafara sauka jikinta.


"Hey Miss" yafada da muryarsa mai kamala yana taba Aljihun tsadaddun qananun kayan givenchy dake jikinsa baiji card din ba ya dan rintse ido a hankali yana tino yana cikin motar daya shigo makarantar jiya da ita.
Ba damuwan komai a ransa ya ambaci sunanta kai tsaye daya tina shine a jikin katin ganin tana sake sauri kaman mai tsoron mutane a bayyane sai kawai ya qyaleta ya wuce yana duba time din agogonsa sbd ba lokaci zai bata ba a school din zaiyi magana ne kawai da prof ya wuce gurin aikinsa.


Yana wucewa Sumayyah data labe daga gefen wasu students ta futo tana kallon inda yabi da ido tsoronta na qaruwa sbd ta tina fuskarsa shine ta gani jiyan ya tsaidata.
Meyake so a gurinta?
Baiyi kama da student ba sbd shekarunsa da jikinsa tareda maturity dinsa sun bayyanarda hakan,
Kyawunsa da kwarjininsa tsoro ya bata matuqa tareda firgitata,babban tashin hankalinta kada ya sake tsayar da ita wani yagani tsautsayi yasa Ababa ya sani Alkiyamarta ta tsaya.


Benazir data qaraso gurinta tana dafata daga baya saida sumayyar takusa shaqewa sbd tsoro da tashin firgita,tana waiwayowa taga Benazir ce wasu hawayen mutuwat jiki suka ciko idanuwanta ta sauke tana kokarin hanasu saukowa.


Benazir data ga hakan hankalinta ya tashi cikin mamaki qasa qasa sbd kar ajisu tace"


Me yafaru?
Ababa yazo nan ne?
Wani abu yafaru ne?


Kasa magana sumayyah tayi ta silale ta zube zaune kan gurin zama tana kokarin daidaita numfashinta dayake futa da sauri na tashin hankali biyu datake ciki na batan student id card dinta dakuma mutumin daya tsayar da ita wadda sunfi kaunar hadarin mashin da wani namiji ya tsaidasu.
Shafa bayanta Benazir ta ringa yi ahankali ta cikin hijab dinta tana cewa


"Ki kwantar da hankalinki kada ki bari yanayinki ya sauya asan halinda muke ciki kaman yanda Ababa yafada mana."


A hankali ta ringa sauke numfashi tana kokarin daidaito nutsuwarta har tsowon mintina kafin ta dan dawo daidai ta dago idanuwanta da har sunyi jajir ta kalli Benazir dake jiran bayaninta cikin fargaban idan ba wani abin ne ya sameta ba.


Bude baki tayi ahankali ta yiwa Benazir din bayanin batan student id card dinta tareda kasa fada mata mutumin da yayi mata magana sbd tinowa da hakan kawai girgiza kayan cikinta da zuciyarta yake bare iya bude baki ta fadawa ko Benazir cewan wani namiji ya tsaidata.


Shiru Benazir tayi sbd itama batasan ta ina zara fara ba tunda ba muaamala sikeyi ba da mutane bare su tambaya qarin bayani.


Shiru sukayi sun jima a hakan batareda sanin abin yi ba,ganin hakan Sumayyah taji gabaki daya hankalinta ya qara tashi suka fito daga department din suka nufi gurin da babu mutane sosai suka zauna take Sumayyah ta fashe da kuka mara sauti tana jin yanda zasu sanar da Ababa hakan.


Shiru benazir tayi itama jikinta na mutuwa sbd tasan bawai tsallakewa zatayiba itama hadasu zaiyi ya musu hukunci daya.
Kasa cewa Antyn tata sumayyah ta dena kuka tayi sbd batasan wane qwarin gwiwar zata bata ba dan haka sukai tsit sai kukan sumyayah da ita kadai ce take jin sautinsa.


Basu san zaune suke gefen wata lafiyayyar black beymack ba saida mai motar ya doso gurin kai tsaye idanuwansa akan Sumayyah wadda idanuwanta sukai jajir jikinta yai sanyi gaba daya.


Kallo daya Benazir tayi masa tayi qasa da kanta bugun zuciyarta na tsananta tareda wata irin fargaba mai tsanani wadda ta sanya numfashinta fita da sauri saidai tinda tayi qasa da kanta bata dago ba.


Shi kuwa sumayyah data qarasa rikicewa da ganinsa yake kalla mamakinta na sake kamasa sbd kai tsaye ya gane tsoron maza takeyi kokuma irin tarbiyar da aka bata ne daga gidansu.


Tsoro ya hana sumayyah dauke idanuwanta daga kansa hannuwanta dake qanqame da jakarta suna rawa.


Kasa shiga motarsa yayi sbd zuciyar kulawa da tausayi tareda sanyi da Allah yayi masa fiyeda kowa a familynsa ya juyo ahankali cikin nutsuwa ya dawo gabansu ya tsaya murya a kamale yacewa sumayyah


"Student id card din ki na gurina nayi kokarin baki a jiyan amma baki tsaya ba,
Yau kuma ban fito da motan dana barsa ba a jiyan amma insha Allah gobe zan sake shigowa wani abin zan taho dashi ki jira ni anan around 4 haka lokacin na shigo sai na baki"


Daga sumayyah din har Benazir a tare suka dago suka kallesa suna masa wats irin godiyar data bayyanar da fadawar tashin hankalinsu.


Da mamaki ya zubawa Sumayyah idanuwansa masu haske yana cewa
"Kina kuka ne sbd Batan card din ne?"
"Are you for real?
Share hawayenta ta hau yi tana sauke kanta qasa daga idanuwansa dasuka fara firgitata.


Kamanninta da Benazir yasashi fahimtar 'yar uwarta ce kuma kusan halinsu daya na rashin iya kallon mutune da alama itama tsoron mazan takeyi.
Wani gajeran murmushi ya saki tareda bude motarsa ya fada ya tada tabar gurin yana kallansu ta mirror harya bace basu dago sun kalla inda yabi ba.


Ajiyar zuciya Sumayyah ta ringa saukewa a jere tana jin sanyi na mamaye zuciyarta data kusa bugawa da tsoro.
Tashi sukai suka koma kowannensu ya nufi gurin da zaiyi lectures basu koma gida ba sai 6 saura.
Suna isa sallar magrib kawai sikai sika fito aikin wanki saida suka gama aka basu abincinsu suka zauna sukaci tareda Annensu dake dan fama da zazzabi kwana biyun sbd yammacin dasuke kaiwa aikin na mata yawan dayafi karfinta.


Basa karatu gida ko sun dawo sbd basuda abin haskawa haka suke hakura duk yanda sukazo karatu musamman sumayyah datakeson Benazir din ta ringa dan wayar mata da kai akan wasu kalmomin.


Washe gari tinda suka wayi gari sike cikin faduwar gaba da fargaban yanda zasu tafi gurin wani namiji karban student id card din na Sumayyah,
Sumayyah tafi Benazir din shiga tsoro da fargaba sbd itace tayi sakacin yar da card din hakama saninsu ne Ababa wasu lokutan yana sakawa ana bibiyarsu dan haka sike cikin fargaban.


Har sika isa makaranta babu mai walwala ko nutsuwar zuciya,
Haka sika wuni ba sukunin rai har 4 din tayi sika isa inda yace din suka tsaya suna waige waige ciki fargaba.
Sam hankalinsu bai kwanta ba da haduwar dan haka a matse suke kusan mintina ashirin kafin motarsa ta danno kai a gurin dan shi tini ya manta dasu din saida ya qaraso gurin ya gansu tsaye ya tina Allah yasa da motar yazo.


Yana parking tin bai fito ba ya ciro card din ya miqa musu ta window
Hannu biyu sumayyah tasaka ta karba batareda ta dago ba cikin girmamawa mai tsanani sukai masa godiya kaman wanda yayi musu wata babbar kyauta.


Mamaki suka sake basa tareda birgesa musamman sumayyah wadda Sanyinta da rauninta dayake bayyane yafi basa tausayinta da burgewa.


Juyawa sukayi suka bace bat daga gurin qafafunsu na sarkewa.


Saida suka bacewa ganinsa kafin kowannensu ya saki boyayar ajiyar zuciya basu cewa juna kala ba suka tinkari hanyar ficewa daga makarantar zuwa gida.


Saida suka isa gida suka shiga dakinsu suka zauna kusa da Annensu hankalinsu ya kwanta daidai suka sake ajiyar zuciya a tare batareda sunyi yunqurin zantawa akan komaiba game da lamarin batan id card din gaba daya.




******kaddara zaace ko tsautsayi kokuma rabo?
Haduwar sumayyah da Bilal kaante daga wannan lokacin sai ta zama kaman wainda ake turowa dan kuwa kusan babu ranar da zai shigo makarantar Allah bai qaddara haduwarsa da sumayyah ba wadda tsoro da firgicin datake shiga a duk lokacinda zata gansa yake sake qarfafa masa tinanin hulda da ita dan kuwa nutsuwarta da kamala tareda tarbiyarta a bayyane take,
Rauninta kaman wani abin birgewa ya zama garesa dan kuwa hawayenta a kusa suke
A kwai ranar daya tsayar da ita ga mamakinsa hawaye yaga suna gangaro mata sai hakan ya sake sakasa tinani da kwadayin son saninta a ransa.
#MAMUH#
#DD KAANTE#BENAZIR#
#LOVE
#MARRIAGE
#ROMANCE#
#BILAL KAANTE#SUMAYYAH#


ZAFAFA BIYAR🔥


-ZAFIN KAI
Mamuhgee


-TABARMAR 'KASHI
Safiyya Huguma


-FURAR DANKO
Billyn Abdul


-BAKON MUNAFIKI
Miss xoxo


Duka hudu 1k
Uku 800
Biyu 600
Daya 400


Pay at
09033181070
09032345899


Zafafa🫶🔥🔥
[8/13, 3:29 PM] MG: _Arewabooks@Mamuhgee 7_


Wani babban tashin hankali mafi tsoratarwa da Benazir ta shiga bayan wasu shekaru shine fara lura da sumayyah data fara samun ciwon qwaqwalwa kaman Annensu sbd lokuta da dama haka zata zauna tayi shiru ta qurawa guri daya ido tana magana a hankali kokuma ta ringa kuka a hankali tana kiran sunan Ababa dana samirah sbd Safnah haka kawai Allah ya cire musu ita cikin ransu sbd abinda tayi din kafin guduwarta wanda kuma guduwar naya ya sake tsanananta musu komai daga gurin Ababa din.


Azabar dasuke ciki da qunci yayi nasarar taba qwaqwalwanta

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login