Showing 90001 words to 93000 words out of 192750 words
ba tinda tasan yanzune zata dage tayi karatun Kaiwa matsayawa.
Da zasu shiga lectures Nafisat ta goyawa Amnah bayan ta Bata Madara Tasha Takoma bacci.
Mota Nafisat suka koma sbd babu inda driver ya tafi Yana Nan saita gama idan dare zata Kai zai Jira tinda aikinsa kawai shikuma na ta ne.
Suna fitowa 12 to 2 kai tsaye mota ta nufo tana Isa wayarta dake jaka kira ya shigo
Cikin Wani irin sanyi ta Ciro wayar sbd bayan Su Anne babu Wanda take magana dashi a wayar.
Sunan Umme tagani ahankali ta sauke ajiyan zuciya sbd wannan shine Karo na farko data fito kaantes tin kaita shiyasa ummen duk ta Dan damu sbd Amnah da Bata fita Rana.
Daukan wayar tayi cikin nutsuwa da sanyin murya tace
"Umme Ina wuni"
Ajiyan zuciya ummen ta sauke daga can bangaren tana cewa
"Bena Yaya makarantan?
Akwai Rana da yawo ko?
Ga Amnah tanata rigima Kila ko?
Ajiyan zuciya Bena ta sauke tana lumshe fararen idanuwanta zuciyarta na na'am da kaunar Umme akansu Dari bisa dari Dan haka tayi kokarin gwada Sakin murmushi me sauti tace
"Amnah a mota na barsu tin dazu Nima yanzu na fito daga lectures din Amma zamu sake shiga 2 zuwa 4."
Ajiyan zuciya ummen ta saki tana cewa "ok ki kula da kanki da Amnah akwai Rana sosai,saikin dawo."
Ahankali ta iya Bude bakinta dayayi nauyi sbd mutuwar jikinta ta furta "Nagode Umme Allah ya saka da Alkhairi."
Murmush kawai ummen tayi tareda kashe wayar daidai shigowan DD palonta Yana amsa wayan Safnah da kusan kullum take kiransa ahankali,ita wannan dake gabansa baimayi noticing nata ba hakama Bai taba tambayar ta ba sbd baisan Tayaya zai fara kulawa ko Neman matan yayansa daya rasu tinda dai Amnah dinsa zai ringa ganin babynsa Hakan ma is ok.
Sallah Bena tayi a mosque na mata
Ta bawa Amnah Madara ta canja mata diaper da kaya zuwa Versace overall marasa nauyi da qamshi kafin suka koma ta shiga lectures suka zauna mota.
Sai 4 har da Rabi suka baro makarantan suka nufi gida.
Suna Isa driver yayi mata Saida safe ta wuce Nafisat na biye da ita gajiye duk da Bata ciki yunwa sbd akwai biscuits da drink da Umme ta sako musu cikin jakar kayan Amnah.
A gajiye suke sbd sabon da suka fara samu daga ita har Nafisat me aikin nata na zama guri Daya cikin hutu.
Babu kowa a palon Dan haka Kai tsaye dakinta ta wuce ta tube ta fada toilet Saida tayiwa Amnah wankan tayi tayo alwala ta fito ta shirya cikin Riga da straight skirt na atampar super wainda kusan duka atampopinta babu qarama bare laces da baa maganar kudadensu.
Sallah tafara Yi kafin ta shirya Amnah cikin guntayen overall blue da safa Mai taushi itama suka fito zuwa dakin Umme Dan gaidata.
Suna zuwa tayi knocking ahankali ta Bude ta shiga ahankali ummen na zaune tana amsa waya cikin nutsuwa.
Tana ganinsu ta sake fuskarta da farin ciki tana miqa hannu ta karbi Amnah din tana ci gaba da wayarta.
Bena kuwa ficewa tayi ta nufi dakin Zeenah batanan Dan haka ta fito ta nufi kitchen acan taci Brown spaghetti da aka dafa Dan ita kawai da yamman.
Sama sama taci ta koshi sbd Sam batada cin abinci sosai hanjinsu sun Dade da tsukewa daga Horan da Akai musu tin tasowansu.
Ruwan sanyi Tasha kadan kafin ta kamawa su Madam beba aikin abincin dasuke Yi na dare.
Tuwon semovita sukai da Miya kala biyu sbd banbancin raayi kowa yaci wadda yakeso.
Ita tayi miyan fresh veggies da Alayyahu sai uban Naman Kazan da babu qashi da nikakken nama
Madam beba kuwa miyan yauqi sukai da kifi da Naman rago.
Suna gamawa Zeenah na dawowa ta Kalli benazir din tana tambayarta me takeyi a kitchen.
Murmush kawai tayi ta sanar da ita Aiki sukai na abinci.
Sallar magrib tayi Bata fito ba sai bayan datai ishai dinta ta miqe ta fito.
Tana saka qafarta tsakiyar palon hancinta ya shaqar mata qamshin Daya sakata dakatawa sbd sanin Yana kusa kokuma Yana cikin palon Dan haka ta silale Takoma daki.
Koda aka Aiko kiranta cin abinci cewa tayi ta Kasho Bata Dade da cin spaghetti ba.
Kyaleta sukai sukaci abincinsu batasan DD baya part din ba shigowa yayi Kuma ya fita da Amnah.
Saida ta tabbatarda sun gama cin abinci ta fito Zeenah ta Rakata gurin dd babba gaidasa da masa godian komawarta makaranta.
Sun shiga Zeenah ko qarasawa batayiba ta juya sbd Kiran Daya shigo wayarta Dan haka ita kadai qafafunta na Dan rawa ta qararasa cikin palon da sallama a natse cikin siririyan muryanta me sanyi kanta a qasa.
Kallan Dawood da Bai dagoba dd babba yafara Yi kafin ya amsa sallamarta tareda Kiran sunanta
"BENAZIR? Qaraso ki zauna kinji.
Sunan da dd babba ya ambata ya saka DD dakatawa daga kallan datakewa Amnah cikin nutsuwa da tsananin kauna Amma Bai dagoba duk da sunan ya tabbatar masa da Mummyn Amnah dince ake nufi.
Itama Bata dago ba bare ta iya kallansu batama San waye da waye a palon ba Dan haka kanta a qasa ta zauna natse kaman yanda dd babba ya umarceta.
##MAMUH#
#LOVE
#HOT
#DBENA
#BABY MAMAH
[8/29, 8:12 AM] MG: *_Arewabooks@Mamuhgee_*
50
Bude baki tayi nutsuwar muryanta a bayyane ta gaida dd babba cikin ladabi da sanyi.
Murmushi me sanyi dd babba ya sake cikin kulawa ya amsa tareda tambayarta Yaya school.
Sake Dan qasa tayi da kanta tana damqe hannuwanta dake Dan rawa cikin nutsuwa tace "lafiya kalau."
Dawood da kaman baya gurin dd babba ya kalla kafin ya Maida kallansa kan benazir din da ita Kuma batasan ma da waye a gurin ba ya Dan sauke numfashi Mai sanyi da kulawa sosai yace
"Benazir ga mijinki Nan a zaune ki gaidasa."
Faduwa Mai tsanani gabanta yayi kirjinta ya fara bugawa da qarfi ahankali ta Dan karkata gefensa batareda ta dago ba kanta a qasa ta Bude baki muryarta na Dan rawa sbd sanyi tace
"Ina wuni."
Shi Kansa DD din shiru yayi na seconds sbd kalman dd babba ta cewan ga mijinta a zaune yasa ya Tina da auren mata biyu ne a hannunsa wainda babu wadda yasan ta inda zai iya sakata a mizanin lissafin rayuwarsa harma da matsayi na matar da ake tinanin yayi rayuwar Jin dadi kwanciyar hankali da nutsuwa da ita.
Batareda ya juya ya kalleta ba ya amsa Kai tsaye tareda miqewa ya fice Yana Ciro wayarsa da kiran Lizz ya shigo.
Bayan fitarsa dd babba ajiyan zuciya ya sauke tareda numfashi kafin ya saki qayataccen murmushi mara sauti ahankali Yana jinjina Kai.
Benazir data kasa motsi ya kalla yace
"Jeki benazir ki saki jiki kiyi karatunki ki qarasa wannan session din a gwada sauya Miki gurin karatun "
Godiya ta sake masa cikin sanyi tareda masa fatan Qarin lafiya tai masa seda safe ta fice.
Ita kadai ta Isa sashensu Dan haka tana Isa babu kowa a palon tana dap da Isa dakinta taji kukan Amnah ta juyo Kai tsaye sbd mantawa a hannunwa Amnah din take tintini.
Juyowanta yayi daidai da shigowansa palon Shima Yana kokarin riqe Amnah din dakyau sbd kaman zata Fadi da motsin kukan datakeyi.
A kyakyawan farar fuskarsa idanuwanta suka sauka gabansa a yayi mummunan faduwan Daya saka hannuwanta rawa da fitan numfashi da sauri tayi saurin dauke idanuwanta zata shige daki taji muryarsa me nutsuwa da kamewa yace
"Karbeta."
Saida ta damqe hannuwanta ta tattara nutsuwanta guri Daya kafin ta iya dago qafafunta ahankali ta iso gabansa ta tsaya
Ya dago Amnah ya miqa mata tasaka hannuwanta dake Dan rawa ta karbeta tareda juyawa Kai tsaye tayi bedroom dinsu ta shige
Shi Daman tin kafin ta juya ya juya Yana cigaba da amsa cikin rashin daga hayaniya.
Bayan shigarta daki Hana kanta zama tayi bare dadewa acikin rawar hannuwanta da faduwan gaba ta hau kintsa Amnah hannuwanta na Dan rawa har lokacin.
Tana gama shirya Amnah itama tayi Shirin kwanciyar ta kwanta tareda rintse idanuwanta.
***Washe gari morning lectures take dashi Dan haka da wuri ta shirya tayi breakfast a dining tareda Umme da itace ta hada musu kaya a jaka yau ma Zeenah Kuma tana bacci suka fice yauma cikin wata tsadaddiyar Noriea Abaya ash da Rolling.
Sai yamma ko yau din ta dawo a gajiye sosai,
Sallah magrib tayi tayi wanka tea kawai Tasha ta kwanta bacci ya dauketa tabar Amnah a can gurinsu Umme
sallar ishai ma sai cikin dare ta farka tayi taga Amnah kwance gefenta an Kwantar mata tasan Umme ce ko Zeenah suka kawo mata ita.
******Ahankali rayuwar makarantan da Amnah ta sabo da ita tin tana Jin stress da gajiyan Hakan harta Saba Bata Jin komai yanzu musamman Mai aikinta Nafisat na kokari sosai gurin kulawa da Amnah Bata wasa da lamarin Amnah ko kadan,. hakama drivernta Ahmed Yana mata biyayya kaman Bai girmeta nesa ba kusa ba Amma sbd a qarqashinta yake biyayyarsa tayi mata yawa take Gani.
Rayuwar gidan ta Saba a yanzu da ita kusan ta ko Ina,
Dd babba kauna me tsanani da kulawa yake nuna mata Wanda kusan kowa ya fara shedar da Hakan musamman da yanzu takai komai nata kaman ba lissafi ake Siya mata har Abinda Bata buqata sosai Dan haka itama a zuciyarta matsayin dd babba da Umme a ranta daban suke,
Tana Jin su kaman zata iya iya komai dominsu kaman yanda zata iya komai domin Annenta idan Bai Saba sharia da musulunci ba,
Wannan ya sakata Sake kokarin Sakin jikinta tana sabawa dasu sosai.
Har lokacin Bata sake haduwa da DD kaante ba sbd kusan duk lokutan Dayake zuwa gidan Bata Nan kokuma ta shige Dan haka Sam Basa haduwa hakama bisa ga umarnin dd babba babu Wanda yayi wa Dawood din maganar yanada mata a gidan kaman yanda Shima ya nuna ya manta kokuma Daman auren Dan karban Amnah ne yayisa.
Kullum sbd Amnah yake zuwa gidan ya dauketa sai idan zai tafi zai dawo da ita,.Hakan yasaka yanzu benazir barinta wasu lokutan idan zata tafi makaranta.
***Lokaci ya Dan ja ahakan har sukai exam suka sake samun hutu Kuma alhmdllh wannan Karan karatun me nutsuwa da kwanciyar hankali takeyi.
Ababa Bai taba kiranta ba sbd kudin da dd babba ke Basa Yana dakatar dashi daga Neman Benazir sbd ta samu nutsuwan karatunta ba tsoro ko firgicinsa,
Annenta kuwa a yanzu dd babba da Kansa yake saka Abbakar Yana kaiwa Ababa ziyara Akai Akai ana dubo lafiyarta tin komai sai ahankali ake tafiyar da rayuwar.
Ababa da ake Kaiwa ziyara Akai Akai ta sakon kudi Kuma baa tura masa ta bank a hannu ake Kai masa dole ya ringa inganta rayuwar Anne sbd duk Abbakar yazo ya ringa kame kamen kada ya Gane Annen na cikin tsananin ukuba da wahala ga ciwonta ya tashi babu Wanda ya sani
Dan haka dolensa ya ringa inganta Annen da abinci da kulawa sbd yawan zuwan da ake masa.
Koda dd babba ya tabbatarda sun samarwa Anne sauki ta Hakan sai ya bawa benazir tabbacin Annenta yanzu tana cikin Aminci inshallah Dan saita Kwantar da hankalinta tayi Abinda Annen kesan tayi.
******Benazir Ababa kaante take amfani dashi a yanzu da rayuwarta ta samu sauyi Kwata kwata,
Kamanninta sun sauya sosai sbd lafiyan jiki Dana fatan dayake bayyane a tattare da ita,
Ta ciko koina Amma har lokacin batai qiba ba,
Jikinta na cikakkiyar mace a yanzu bayyane yake sbd hutu Daya ratsata ba laifi kam sosai.
Tsakaninta dasu Umme kauna da kulawa ce sosai shi kuwa dd babba baa ma fadan kaunarta Dayake a bayyane kusan bayan DD a cikin ransa yanzu ita din ce gata da Wani irin ilimi dayakesan ace 'yayan family dinsa suna dashi shiyasa yafi son Dawood tin asali sbd iliminsa da babu me shi ko a cikin iyayensa sai gashi matarsa ma ta kasance cikin masu irin baiwarsa.
Amnah da ayanzu tayi wayo tasan Daddynta kaman me sbd shine Wanda yafi Santa fiye da kowa a rayuwarsa yanzu.,
Duk Abinda takeyi idan taji muryansa zata taka ahankali da tafiyarta da batai qwari ba taje gurinsa.
Duk Wani Abu na Amnah a yanzu shine ya siyesa,.komai nata daga fari sai black kaman yanda su kadai ne kalan Dayake sakawa hakama 'yarsa su kadai ne kusan kalan dayake Siya mata,Dayake fara ce tas kaman shine ya haifeta sai kalolin na mata kyau.
Duk wannan tsawon lokacin Basa haduwa,.daga shi har ita babu me buqatan ganin Dan uwansa Dan haka suke kaucewa haduwa da juna
Shi a nasa bangaren ma kaman har lokacin baiyi noticing nata ba.
Duk da tsawon lokacin da Basu taba haduwa suka tsaya gaban juna ha Abu dayan Daya hadasu shine kowannensu ya San qamshin Dan uwansa ko acikin qamshi nawa zasu shiga suna Gane na juna sbd Amnah.
Duk daukan dayakewa Amnah idan ta dawo hannunta qamshinsa a kame yake jikin Amnah da kayanta na turaren Caron poivre Mai Wani irin qamshi me sanyi da nutsuwa kuma duk qamshin Datake ji a mutane Bata taba Jin me irin qamshin wannan tiraren ba ko a familyn kaantes din kuwa Datake cude a cikinsu yanzu.
A nasa bangaren duk yanda baya bawa Abinda Bai shafesa mahimmanci ba Saida qamshinta dake jikin Amnah koyaushe samun shigewa Kansa Dan kuwa A jikin Amnah ne kawai yake samun wannan qamshin nata na aqua di parma da dd babba ne ya tsaya mata take amfanin da abubuwan da tsadansu bama gaskia bane a rayuwarta.
Wannan shine Wani communication da yake tsakaninsu kawai bayanshi babu Abinda yake hadasu da juna.
A bangaren Safnah kuwa tinda ta samu labarin yanada wata matar bayan ita ta daga hankalinta
Ita da mummynta suka dagawa hajiya da Daddynta harma da Umme hankalin akan Safnah ta fasa bataso Saidai ita a saketa kokuma a saki waccar dayar matar.
Umme da Alh basheer hankalinsu tashi yayi Amma suka ringa lallabata kada ma Dawood din yaji a take zai saketan ba Batawa Kai lokaci.
Da suka ga abin yaqi sauki sai dad dinta ya hanata dawowa yace tayi zamanta sai ansamu mafita.
Itama Umme amincewa tayi da Safnah din tayi zamanta tukuna su shawo kan Dawood din,
Ta Wani bangaren Kuma ita ummen tafison Safnah tayi zamanta acan kafin Dawood yafara noticing Benazir da ayanzu tafi Jin ta a zuciyarta matsayin matan Dawood akan Safnah duk da itama tana kaunar nata sosai.
Dd babba kuwa shiru yayi musu akan zancen safnah din da akace shakara Daya ya rage mata a karatu ta gama ta dawo ta tare Amma tsaban Rena hankalin mutane har shekaran ta wuce ba dawowan Safnah wadda itama ko sunan dawowanta Nigeria din bataso tafison DD din ya ringa zuwar mata can yafi mata.
Benazir ce matar Dawood a zuciyarsa Dan haka kaman yanda iyayen Safnah sukai biris da zancen dawowanta Shima yayi musu biris
Abinda ya sani Dawood tinda ya auresu su Biyun to saiya zauna dasu.
******Benazir na gama final exams dinta taje ta dubo Annenta wadda a yanzu tana zuwa dubota Akai Akai Kuma ba laifi Annen na cikin Aminci sbd kudin da dd babba ke bawa Ababa yaha hanasa Kiran Benazir akan saita gama karatu.
Hutun sati uku tayi sukai tafiya ita da Umme da Zeenah zuwa India dad kaante yaga likita harma da Ummen daga can suka wuce Costa Rica.
Watansu biyu suka dawo Benazir Bata rufa watanni biyar ba dd babba ya turata Cairo Wani business course na shekara Daya da wata biyar Kuma ita kadai ta tafi ba da Amnah ba dan haka take cikin kewan 'yarta sosai.
******Dd babba da Kansa yaje bikin kammala business course dinta har Cairo tareda Umme hakama Zeenah data gama nata karatun a Zurich gurin DD Daya jima da komawa Shima tare suka dawo Nigeria
Motocin dasuka je daukosu suna harda Abbakar Wanda yayi farin cikin dawowarta sosai sbd kaunar Dayake mata Shima kaman shine ya haifeta.
Amnah na ganin mummynta tazo da gudu cikin farin ciki ta maqale ta tana cewa
"Mummy" cikin muryanta na Yara.
Rungumeta benazir tayi tana sake kyakyawan murmushin Daya qayatar da kyakyawan fuskarta ahankali cikin tsananin kaunarta tace
"Oh my, I missd my baby so much"
Dariya Amnan tayi tana sake maqale mummyn tata tana cewa
"Where's my daddy?"
Murmushi Benazir ta sake tana shafa fuskarta tace
"Baki ga Aunt Zeenah ba tana kallanki tayi missing naki sosai itama."
Gurin Zeenah din tayi da gudu ta fada jikinta tana mata oyoyo itama.
Umme dake dariyarsu tini tayi hanyar bedroom dinta a Dan gajiye tana cewa
"Daddynta kawai take tambaya yarinyar Nan"
Dakunansu da aka gama gyarawa suna sanyin qamshin suka nufa kowa yayi nasa
Amnah na biye da Mummynta cikin tsananin farin cikin ganinta.
Ta sauya skin products nata zuwa Aesop Dan haka su ta fitar cikin kayanta ta Jere toilet kafin ta tube tayo wanka ta fito daure da blue towel Brown skin dinta na daukan idon sheqin hutu da lafiya.
Mai Tai shafa sama sama ta fesa spray na turarenta ta saka pyjamas farare tayi sallan magrib da Akai a daki tasaka Nafisat ta kawo mata abinci taba fito ba tanayin ishai ta kwanta bacci.
Washe gari dukkaninsu kowa a daki yayi breakfast suna gamawa ita Kuma ta fita taje gurin dd babba daga can da kanta taja mota zuwa gidansu.
Ba laifi Bata samu Annenta cikin wahala ba Dan haka ta samu nutsuwa a can suka wuni ita da Amnah sai yamma suka dawo.
Tana parking suka fito kafin ta rufe motar Amnah ta saki hannunta da gudu ta nufi bayanta tana Kiran
"Daddy"
Ya Riga ya kawo bayan kaman yanda Shima ya Riga iso hanyar Dan haka tana juyowa akan fuskarsa idanuwanta suka sauka ta dauke Ido ahankali sbd kullum fatarsa qara daukan Ido takeyi.
Juyawa tayi zata bar gurin sbd Amnah tace
"Mummy ga daddynah ya dawo"
Cak ta tsaya tareda damqe handbag din dake hannunta ta juyo ahankali cikin nutsuwa da muryarta me taushi tace
"Sannu da dawowa."
Bai taba dagowa ya kalleta ba sai ranar sbd ranar ne yafara Jin qamshin aqua di parma a daga jikin nata direct ba daga jikin Amnah ba.
Kallan da yayi mata ya sakata Dan daga qafa zata bar gurin Amnah ta sake kiranta tana cewa tadawo kar tabarsu itada Daddynta a baya.
#MAMUH
[8/29, 9:06 PM] MG: *_Arewabooks@Mamuhgee_*
51
Cak ta dakata ta tsaya tana kasa juyowa sbd kaman tana Jin idanuwansa akanta Wanda suka hanata motsawa hakama ta kasa juyowa saidai bugun zuciyarta Daya Dan qaru.
Qamshinsa taji ahankali kaman Yana qaruwa a iskan dake shiga hancinta ta tabbatarda tahowa ne sukeyi Dan haka tana Jin takunsa gap da ita sai ta daga qafafunta taci gaba da tafiyarta cikin nutsuwa.
Amnah datakesan jinta tsakiyan iyayen nata hannu ta miqa zata kamo Benazir din tana Kiran sunanta
hannunta Bai Isa gurin Mummyn tata da batasan da ita ba tayi gaba cikin tsautsayi Amnah din ta subuce daga hannunsa tayi qasa
dagashi har Bena dataji