Showing 6001 words to 9000 words out of 192750 words

Chapter 3 - ZAFIN KAI COMPELET BOOK BY Mamuhgee.txt

12 Dec 2024

7139

kamata
Kallo daya zakayi mata tausayinta ya kashe jikinka sbd ciwo ne a jikin wanda baya cikakken hayyacinsa,
Bata jin ciwon zazzabi da juyin qwaqwalwar datake samu,ciwo ne a zuciyarta datayi mata wani irin nauyi da sankarewa batajin komai bata gane komai sai fuskar ‘yayanta guda ukun dake gabanta tsananin sonsu na sake toshe kirjinta,


Maqalqale Safnah tayi tareda kafe sauran da ido bata iya cewa komaj sai jijjiga kanta datakeyi da karfi tana murza idanuwata dasukai wani irin ja na azabar ciwon dake cinta amma batasan me zatace ba batama san meyake mata ciwon ba ita.


Wani irin kuka sumayya ta fashe dashi mai ciwo da rashin sauti tana riqo hannuwan Annen datake sake matse safnah da karfi kaman zata illatata,


Safnah ma hawaye takeyi tana hana kukanta sauti kaman sumayya din tanajin zuciyarta na nauyi sbd tasan kila Anne taji a jikinta itama rabuwa zasuyi wata kila ta dawo ta fanshe su da kudi a hannun mahaifin nasu idan har ta tsira wata kila kuma rabuwarsu ce ta har abada bazasu sake haduwaba…wasu hawayen ne masu zafi suka gangaro mata tana kallon Annen wadda itama ita take kallo amma bata iya magana sbd daman idan abin ya motsa bata iya magana.


Sunkuyar da kai sumayyah tayi tana tsananta kukanta hannuwanta na toshe bakinta ganin hawaye na gangarowa daga jajayen idanuwan Annen,


Benazir datakai hannu ahankali ta share hawayen annen jin tsananin zafinsu yasata fashewa da wani irin kuka mai tsananin ciwo sbd zafinsu ya tabbatar mata da dole a tsananin hali Annensu take amma bata iya fada.


Kukan benazir yasa dukkaninsu sake fashewa da kuka a tare mara sauti hadda Annen data ga ‘yayanta na kuka cikin kunci musamman ganin kukan Benazir yasa kukansu qaruwa dan ba qaramin qunci kesa Benazir din kuka ba.


Sunaji suna gani suka baro Annen a daki tareda safnah dataqi saki suka fara ayyukansu sbd basason Hande tasan jikin annensu ya tashi Ababa na dawowa zata fada masa dan haka suka ringa boye boye dan karta gane.


A dakin kuwa Safnah kai tsaye ta bude baki ta sanar da Annensu tafiya zatayi idan ta mutu kaman Samirah ta yafe mata.


Gabaki daya rikicewa jikin Annen yayi da kalaman safnah wanda ya sata fita hayyaci haukar ta taso tuburan dan haka ta kirawa sun benazir suna zuwa hankalinsu ya tashi take suka daddaureta a dakin suka hanata motsi sbd Hande naji zata kira Ababa a waya
Idan ya taddata a wannan halin a yau zai rabasu da ita
A yanzu da baisan gidan mahaukataba wani gurin zai iya kaiita ya saki tabi duniya ta yanda bazasu taba ganinta ba ko Allah yasa sun tsira a gaba.


Fizge fizge takeyi sosai tana hawayen radadin zuciya duk da tana cikin hali na gushewar hankali radadin uwar da zata rasa yarta cin zuciyarta yakeyi gashi su benazir basusan abinda Safnah din ta fada mata ba jikin nata ya rikice hakan,


Har dare suna cikin tashin hankali da boye boye dan zuwa lokacin har bakinta suka rufe suna kukan wannan azabar ta dauretan da sukayi ba dan ransu ya so ba amma basuda zabin daya wuce hakan tunda suna tsananin son abarsu ko me zata zama.


Safnah kuwa shedan samun damar tsayar mata da zuciya yayi akan Amafani da ciwon Annen ta gudu sbd a yanzu takai gabar da itama ta rasa nata hankalin qwaqwalwarta na gab da juyewar kaman ta Anne koma fiye,


Kusan dukkaninsu idan aka cire Benazir qwaqwalwarsu kaman ta dade ta tabuwa baa ganewa ne sbd basa tareda kowa haka basuda yanci ko na haukar.


Yanda suka rana haka suka ga dare sbd a zaune dukkaninsu suka kwana sbd yanayin jikin Anne daya kasa sauki ko kadan
Duk wani qarfinta ga qare a fizge fizge takai har bata iya motsawa sai hawayen dake bin gefen idanuwanta
Idanuwanta kuwa kaman zasu fado waje tsaban ja da fitowarsu.


Koda sukai sallar Asuba basu saketa ba dan bazata iya sallah ba a halinda take ciki saidai idan tadawo daidai tayi rankon salloli,


Koda suka fito babu mai iya bude idanuwansa har karshe sbd kumburin kuka dan haka duka aikin sukayi kansu a qasa kada a gane.
#MAMUH#
#DEEP
#LIFE
#PURE
#LOVE
#MARRIAGE
#BILLONAIREROMANCE
#BENAZIR


ZAFAFA BIYAR🔥


-ZAFIN KAI
Mamuhgee


-TABARMAR ‘KASHI
Safiyya Huguma


-FURAR DANKO
Billyn Abdul


-BAKON MUNAFIKI
Miss xoxo


Duka hudu 1k
Uku 800
Biyu 600
Daya 400


Pay at
09033181070
09032345899


Zafafa🫶🔥🔥
[8/13, 3:29 PM] MG: _Arewabooks@Mamuhgee_
6
Anne data fisu jiqata sbd ba zato tana barci taji saukan masifar tako ina gashi daman bata da lafiya kasa kuka tayi sai wani wahalallen numfashi datake saukewa tana daga kwance kanta na juyawa,


Sumayyah ma kusan kaman a sume take dan bata iya jan numfashi daidai cikin tsananin firgici da azaba take koina nata rawa yake ta qame guri daya idanuwanta a kafe da tsananin tsoron da tashin Hankali ina safnah ta gudu ta tafi tabarsu cikin masifar barnar data aikata dan kuwa har ranar da Allah zai yanke musu wannan wahalar sune zasu ringa azabtuwa da hukuncin wannan abin data aikata.


Benazir kuwa data fi sumayyah da Anne dakuwa sbd kusan itace ta ringa hawa samansu sbd dukan ya fi sauka akanta,bakinta jini yakeyi sosai ga gefen fuskarta ya kumbura a take kaman wadda mashin ya kade,
Wasu hawaye ne masu dumi da bayyanarda radadi da ciwon dayake cikin zuciyarta suka gangaro daga cikin idanuwanta ta rintse idanuwan a hankali tana kasa cewa komai dan kuwa a yanzu qaddararsu ita da 'yar uwarta da mahaifiyarsu ta sauya ne zuwa wani yankin azabar da zatace safnah itace mummunar sanadin sauya musu rayuwa zuwa wata sabuwar wahalar da basusan inda zata kaisu ba.


Shiru dakin yayi tsit babu motsin kowannensu sbd babu mai iya maganar ko abin cewar,


Har tsakar dare kowannensu na makure a inda yake batareda sun motsa ba.


Rawar da kakkarwan da jikin Annensu keyi sosai yasa Benazir da jikinta yayi tsananin tsami motsawa ta isa gurinta da qarfin hali sbd bakinta itama ya kumbura ya sauya kamanni sosai,
Kamo Annen tayi taji jikinta yayi wani irin zafi mai tsanani
Numfashi ta sauke a kasalance sbd rashin sanin abin yi amma kuma ko yayane dole zata rage mata ko zafin jikin ne dan haka ta miqe da qyar ta dafe cikinta dayasha harbi da qafafun Ababa din tana takawa ahankali ba kuzari ta fito ta debo ruwa a roba ta dawo ta zauna gefen Annen tafara goge mata jikinta da fuskarta da itama yaji mata ciwo gurin dukan.


Sai data gama goge jikin Annen taji sumayyah itama jikinta yayi zafi sosai har taja jijjiga dan haka itama ta dawo kanta ta ringa goge mata jikinta tana rungumeta sbd sumayyar tafi Anne jigata gashi daman rauninta yafi na Annen.
Daqyar benazir din tasamu jikin sumayyah ya dena fizga tana neman sumewa,


Kwantar dash tayi ta rufe kowannensu sbd baccin wahala dasuka samu ya daukesu.


Ajiyar zuciya mai zafi ta sauke a hankali tareda jinginar da bayanta jikin bango taba cusa kanta cikin qafafunta daga zaunen tana rintse idanuwanta sbd itama wani azababben zazzabi da tsamin jiki takeji mai radadi amma batada mai dubata bare bata kulawa dan haka a hakan baccin wahala ya dauketa.


Da sassafe itace tafara tashi tafara duba jikin nasu kafin ta miqe daqyar sbd jiki daya qara tsami ta fito tayi alwala tazo tayi sallah tana idarwa ta tada Sumayyah da itama jikinta ke tsananin ciwo da tsami ta fito daqyar tayo alwala tazo tayi sallar suna idarwa suka fito dan ayyukan dasuke dole akansu.


Da Ababa suka fara cin karo ya fito cikin farin yadi fuskarsa a hade tsaf babu sakewa bare rahama,
Da sauri dukkaninsu sukai qasa suka gaishesa cikin girmamawa da 'da,a mai tsanani kansu a qasa.


Ko kallonsu baiyiba ya wuce kai tsaye dakinsu ya fada bai tsaya komaiba ya damqo Annensu dake zaune tana rarraba ido cikin azaba ya fara janta ya fito da ita yana cewa
"Zamanki a nan ya qare sbd daman na fada muku tana bayyanarda haukarta ta gama zama a nan bolar mahaukata zan kaita tabi mahaukata yan uwanta can su qarata a bola bola"


A tare Benazir da sumayyah suka zube qasa gabansu suna wani irin hawayen mafi munin tashin hankali suna rokonsa akan karya rabasu da mahaifiyarsu.
Ko sauraronsu baiyiba sbd basu kai matsayin da zaiji ko rokonsuba, sake jan uwar tasu yakeyi wadda take riqe Benazir da qarfi kaman ranta duk da hankalinta bai gama dawowa daidaiba dika tasan su din yayanta ne da bazata iya rabuwa dasuba ba koda zaa rabata da ranta ne tafison a rabata dashi a tana tare da su.


Sumayyah kuwa a neman rasa kanta takeyi sbd itama qwaqwalwan tata neman juyewa takeyi da uwa da ake kokarin rabasu da ita dan haka ta dunqule guri daya tana kasa motsawa sai fizga da kanta keyi.


Benazir data ke neman zaucewa itama kuka ta fasa mai qarfi tareda rarrafawa ta riqe qafafunsa tana rokonsa cikin qasqantar da kai tana masa Alqawarin yin duk abinda yakeso na 'yan uwanta dasuka tafi samirah da safnah indai zai bar musu Annensu koda bangaren dabbobinsa ne sun yarda zasuyi duk abinda yakeson harda nasu safnah data gudu da samirah data rasu.


Da farko dakatawa yayi sbd dama baida niyar yafewa ko bata fada ba daman rabonsa na sisi da kwabo akanta da sumayyah zai fanshe harna samirah da safnah.


Hande da sai alokacin ta fito ta kalli su benezir din da uwarsu kafin ta maida kallonta kan Ababa daya tsaya lissafin yanda zaiyi amfani da Annesu ya juya rayuwarsu yanda yakeso hankali kwance koda kuwa karuwanci ne indai zai fanshe kudinsa akansu.


Hande kuwa tana kallonsa tace
"Kai yanzu Abubakar Tinanin me kayi daka yanke shawarar korar Benazir bayan kasan matuqar ka koreta rubatacce ne guduwar 'yayanta daga gidan nan dan kuwa koda namansu zaka yanka ka tsaga qashinsu ka saka musu kwado da kaca ka daure wlh matuqar sun san uwarsu na can tana yawon bola wlh sai sun gudu sun nemota kaga kuwa asarar dai da kake gudu itace zata bika dan haka maza ka sauya shawara ka barsu da uwarsu idan kanason zamansu a qarqashinka itace jigo"


Shiru yayi tabbas yasan ko zai kashesu ya binne bayan rabasu da Annensu sai fatalwarsu ta fita nemanta musamman Benazir,
Sakin Annen yayi tareda saka qafa yayi ball da ita yana sakin hucin bacin rai ya kalli benazir data sauke kanta kasa tana kallon yanda yasa qafa yayi ball da mahaifiyarta.


Mahaifiyarku itace a tafin hannuna ku sani daga yanzu ko kofar gida wani a cikinku yakuma kalla da wani nufin guduwa wlh tallahi uwarku ce zataji a jiki da jininta.


Qafa yasa ya take hannuwan Benazir din dake gabansa ya wuce yabar gidan yana cewa Hande kar wanda aka bawa abincinsa sai washe gari.


Yana fita Benazir ta rintse ido tareda zubewa zaune hawaye na tsiyayo mata mai zafi da radadi dan kuwa tabbas akan Annensu babu kalar azabar da bazasu iya jurewaba.


Hande Annen tasu dake kwance ta kalla tareda nufarta ta kamata ta tayar tsaye saidai bata iya tsayawa
Kallon Benazir data kasa motsawa sbd nauyin zuciya tace"
Kizo ki kamata kuyi ciki baqi zanyi kada suzo su sameku anan ku ja mana abin magana asan kiwon mahaukata mukeyi a gidan.


Bude idanuwanta da sukai jajir tayi ta tareda miqewa ahankali tazo ta kama Annen takai daki ta dawo ta kama sumayyah da itama kanta ke neman juyewa takai daki bata tsaya musu komaiba dan batasan me zatai taimaka musu dashi ba dan haka ta fito tahau ayyukan gidan datasan wajibinsu ne yinsu kuma sumayyah bazata iyaba a halinda take ciki.


Sai magriba ta gama ayyukan dasuka saba yi su biyar harda Annensu a baya amma ayau ita daya ce tayi aikin dan haka koda ta gama ta dawo dakinsu tayi sallar magrib da ishai kwanciya tayi gefen sumayyah da har lokacin take kaman bata dawo hayyacinta ba.


Washe gari daqyar ta iya ayyukan gidan tasamu aka basu abincinsu ta kawo daki suka rufa su ukun suka cinye batareda ko wannensu ya koshi ba dan haka gurin wanke wanke wanda Ababan ya rage ta kawowa Annensu ta qarasa cinyewa ta koshi ita kuma sumayyah wanda Hande ta rage ta kawo mata itama ta qarasa koshi.


Washe gari ma haka itace tayi ayyukan gidan sbd har lokacin sumayyah bata gama dawowa daidaiba.


A cikin kwana biyu ta qarasa zabgewa sbd wahala da rashin bacci ga damuwa da tinanin da yayiwa rayuwarsu daurin minti.


*********A hankali sumayyah da Anne suka warke suka dawo daidai
Annensu ta dawo saidai kaman batai haukar kwana biyu ba tadawo yanda take saidai kullum cikin fargabar kada ciwon ya sake tashi suke dan haka suketa kokarin hanata tina su Samirah da safnah suka dage suka maye mata gurbinsu batareda bata dama ko kankanuwa ba ta tinasu dan sai saukin haukan yazo mata da mantuwa mantuwa kwata kwata sai tana mantawa da basu biyun ne kawai yayanta ba sai can lokaci lokaci tace ina samirah?ina safnah?


Data fara maganarsu da sauri suke dubarar dasuka mantar da ita zancen sbd kada ciwonta ya tashi komai ya lalace musu.


A yanzu rayuwa tayi musu wani irin juyi zuwa mafi wahala da ukuba sbd wahalarsu tafi yawa a yanzu da suke iya su biyu kawai,
Ababa a yanzu Annensu itace mukullun daya kama na juya rayuwarsu yanda yake so sbd yagama gane itace kawai abinda zai kama yace su fada wuta su fada batareda tinanin komaiba,


A yanzu daya dauki wannan tsarin sai haukarta dake hawa tana sauka tayi masa daidai,
Ya zauna ya tsara sabon lale ga rayuwarsu gabaki daya ta hanyar miqasu ga auren jari ga wasu dilolin miyagun qwaya da masu safarar mutane da ya samu amma sam hadin bazaiyi ba saiya wadatar dasu da ilimin boko mai dan zurfi dan haka kai tsaye ya fidda kudi aka nemar musu gurbin karatun diploma wanda yafi wata yana lissafin kudin dazai kashe kafin yakai ga maida kudinsa yana jinjina maqudan dukiyar da zai samu daga manyan dealers din na qwayoyi da akace suna sakarwa matayensu da iyayen matansu.


Ita benazir kai tsaye Wani hamshaqin drugs dealer dake zaune a lagos da qasar Germany ana tallata masa hotonta yace ya amsa aurenta sbd dari bisa dari tayi masa dan haka ita take yafara yiwa Ababa barin kudi dan haka koda Ababan ya dawo dag lagos ita take aka sauya mata karatun da zatayi zuwa degree.


Cikin saa Tana rubuta jamb taci Admission dinta bai wani zama wahala ba sbd komai acikin saa ta rubuta taci.


Sumayyah ma kusan komai nata ya kammala itama Aminin Ababan Alhaji Sadau shine ya gabatar musu da komai aka jira lokacin fara karatun nasu.


A rayuwar quncin da suke ciki babu abinda ya sauya saima qaruwa sbd duk ya kallesu a yanzu tsagwaron dukiyarsa yake musu kallo dan kuwa kudin daya kashe a shigar dasu makaranta jin yake idan kudinsa basu dawoba ko qasar qetare sai yaje ya nemo masu siyan bayi sun siyesu an basa kudinsa.


Tsananinsa akansu ya qaru fiyeda ko yaushe sbd wasu irin dokoki da tsananin daya dora musu akan ko kallon wani namijn sukai a waje wallahi saiya maidasu makafi dan babu wadda bai gama jingar aurentaba ga wainda zasu maida masa asararsa.


Maganar kula kowane irin namiji a waje ko makaranta ya tsayar dasu ya maimaita musu kusan fiyeda yanda yake maimaita musu qiyayyr dayake musu,


Daga qarshe yayi musu alqawarin binne uwarsu da rai duk ranar dayaji koya gan dayarsu tareda wani.


Hankalinsu tashi yayi da maganar dan kuwa sai tsoron karatun gabaki daya ya shigesu sukaji basa shaawa musamman daya shimfida sabuwar dokar duk wahala da aikin gidan akan uwarsu zai koma duk suna fita harsai sun dawo.
#MAMUH#
#LOVE
#QADR
#MARRIAGE
#BILLONAIRES KAANTES#
#BENAZIR ABABA
#ROMANCE#


ZAFAFA BIYAR🔥


-ZAFIN KAI
Mamuhgee


-TABARMAR 'KASHI
Safiyya Huguma


-FURAR DANKO
Billyn Abdul


-BAKON MUNAFIKI
Miss xoxo


Duka hudu 1k
Uku 800
Biyu 600
Daya 400


Pay at
09033181070
09032345899


Zafafa🫶🔥🔥
[8/13, 3:29 PM] MG: _*ZAFIN KAI*_
_Mamuhgee_


5
Haka suka sake kwana da Anne a hakan babu sauki ko kadan saima galabaituwar datayi ga daurin da sukayi mata yana cin hannuwanta da qafafunta dole suna kallo sbd ba yanda suka iya,


Sumayyah ce ta fara fahimtar Yanda duk suka bar Annen da safnah a daki sai jikin Annen ya tsananta musamman fizge fizgenta gashi duk ta goge gefen fuskarta har jini yakeyi sbd yanda take goga fuskar daga kwancen datake tana buga kanta.


Cikin mamaki da kasa gasgatawa suka tambayeta meyake faruwa duk suka bar anne tareda ita
Bata boye ba ta sanar musu ta fadawa Anne ne zata tafiyarta kaman samirah.


Cikin firgita sumayyah tafara hawaye tana riqo safnah din tace “ me kika yiwa Mahaifiyar data haifeki?
Kinason kasheta ne?
Kinada tinani kuwa?
Wane irin burin guduwa ne ze saika ki ringa cinnawa mahaifiyarki hauka dan kawai ki gudu.


Benazir fararen idanuwanta dasukai laushi da galabaita ta zubawa Anne dake sake goge fuskarta da qasa batareda da jin zafin ciwon data yiwa fuskartata ba,
Sarewa qafafuwanta sukayi tanajin kaman zata gaza,
Itama taya qwaqwalwar jin tayi kaman zata buga dan lamarinsu na gab da qarasa tabarbarewa idan suka fara samun son kai da rashin tausayin juna a tsakaninsu.


Safnah da zuciyarta tafara bushewa ta kallesu tasake tabbatar musu da guduwa zatayi ta zabi bin duniya akan zama karkashin Ababa.


Sumayyah kuka kawai takeyi tana kokarin dawo da tinanin safnah din a hanya amma sam safnah taki sauraranta sai hayaniya taso barkewa tsakaninsu
Benazir data rasa abin fada ko yi sai kawai ta qarasa gurin Anne ta dagota zaune ta kwantar da kanta a jikinta tana goge mata jinin fuskarya da hannun zumbuleliyar doguwar rigar gwanjon dake jikinta sbd sune suturarsu.


Sumayyah da duk ta firgice da tashin hankali da tsoron jin kudirin Safnah din kallon Benazir tayi cikin tsoron abinda zai iya biyowa baya tace


“Benazir kiyi mata magana dan Allah kada ta aikata hakan”


Rintse idanuwa Benazir tayi tareda yiwa safnah din kallo daya wadda ke kallonta itama kaman suna yiwa juna kallon dayake faduwar da gabansu su duka biyun saidai kowannensu ya kasa furta kalma ko daya.
Daga hakan dakin ya dauki shiru sai hawayen sumayyah dake zuba tana fidda karamin sautin kuka.


Da daddare duk fada da yada maganganun Hande akan rashin fitowar Anne basu ce komaiba sbd kada ta tsananta tace sai Annen ta fito.


Safnah bata saduda ba cikin kwana biyu ta tabbatarda ta zaburar da ciwon Anne gabaki daya ta hanyar dawo mata da yanda Samirah ta rasu da yanda itama zata tafi ta barta,
Babu mai imanin da zai kalli Annen bai zubar mata da hawaye ba hakama su benazir sun shiga mawuyaci matsanancin hali na yanayin mahaifiyarsu haka Safnah kusan takoma tamkar maqiyarsu sbd yanda ta fidda asalin son kanta da tsame kanta daga halinda Annensu take ciki gashi basuda ikon hayaniyar da zata ankarar dasu Hande halinda suke ciki dan haka suka zabi tattarawa su koma bangaren

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login