Showing 84001 words to 87000 words out of 192750 words

Chapter 29 - ZAFIN KAI COMPELET BOOK BY Mamuhgee.txt

12 Dec 2024

7153

cikin damuwa sosai da tausayawa ta zauna tana cewa


"Shine tintina baa fada mana ba da sai ayi wata dabarar da breast milk din zaixo,.Amma gaskia Hakan madaran zallah kawai bazai isheta ba."


Karbanta ummen tayi tana goge mata baki tissue tana Jin tausayin Amnah din na rashin Nono gashi yanzu har anyi kusan sati uku da haihuwa bare ayi wata dabarar.


Fitowan Zeenah daga wanka yasa ummen kallan benazir dake zaune Kai a qasa tace


"Kiyi hakuri ki kwana a Nan din yau gobe zaa gyara Miki naki dakin ne a canja Miki komai kafin a saka ranar tarewan ki idan kin Dan Saba da Nan din Kuma Dawood din sai yaje Zurich ya dawo saiki tare gaba Daya kinji?


Ki sake jikinki inshallah zakiji Dadin zama damu hakama Amnah.


Ahankali hadiye Wani numfashi Mara qarfi ta Dan dago batareda ta iya kallan ummen ba ta gyada Kai tana Bude baki cikin nutsuwa da sanyi tace


"Nagode."


Murmush Mai sanyi itama ummen ta saki cikin mutuwan jikin halinda suketa samun kansu aciki.


Miqewa tayi tareda Kwantar da Amnah din zata fice tana cewa


"Zeenah Kinga ga Amnah Nan da benazir kada ki saki ac da yawa sbd benazir na Bata gama jego ba hakama baby Amnah sanyin zai mata yawa ki kula sosai."


Ficewa tayi tana sake jadaddawa Zeenah wadda taketa cewa to sbd itama tasan bama zata saki ac din sosai ba.




Bayan fitar Umme Zeenah kallan benazir tayi bayan ta gama sauyawa Amnah kaya tayi mata Shirin bacci tace


"Ki Kwantar da ita kema kina buqatan gasa jikinki sbd wannan hidiman dole akwai gajiya."


Benazir da batasan me zata ce ba hakama bazata iya musantawa sai ta Kwantar da Amnah din ta nufi bayan Zeenah datace ta biyota toilet din ta taimaka mata da sabbin abubuwan amfani.


Duk quncin rayuwar dasuka taso aciki da rashin gata da rufin asiri Allah Bai taba saka musu kwadayin rayuwar datafi karfinsu ba hakama sunada nutsuwarsu a duk inda zasu samu kansu shiyasa data shiga bathroom din Mai kama da wata duniyar daban Bata daga hankali ko Damar da kanta ko Jin tana shaawar tsayawa kallan Abinda yake toilet dinba,wankan ma kasawa tayi ta Saida ta jima sosai tana Kukan data rasa Kona meye kafin tayi wankan ta fito sbd idan batayiba ta fito Kila su baa kwanciya a gidan sai anyi wanka ancire datti komai kankantarsa.


Qaton towel din da Zeenah ta Bata shi ta dauro ta fito jikinta rufe da Wani sbd Bata Saba fitowa ahakan ba.


Koda ta fito Zeenah ta rage hasken dakin sosai Wani qamshi da sanyi kadan ne ya gauraye dakin ni'iman qamshi na ratsa kowane numfashi da zaka ja a hancinka.


Kaya ne Zeenah ta nuna mata Riga da wando masu tsayi da kauri sosai da taushi suna qamshi Mai sanyi tace ta saka.


Karba tayi ba musu ta koma toilet ta Sako ta fito sbd bazata iya tsayawa musawa a rayuwar datasan kaman anriga an siyota ne Dan haka batada Wani zabi bayan yin kusan duk Abinda aka umarceta batareda ta tsaya azabtar da kanta ko batawa Wainda take zamansu lokaci.


Tana sakawa Zeenah ta nuna mata inda zata kwanta babu musu tazo ahankali ta kwanta kaman mara lafiya a rakube ta janyo Amnah cikin jikinta tana rintse idanuwanta tana Jin zuciyarta na Neman karyewa da tinanin a wane hali Anne take ciki a wanna Daren da zata kwanta ita Daya babu ko Daya acikin 'yayanta.




Zeenah bata jima ba bacci Mai nutsuwa ya dauketa,
Ita kuwa benazir har kusan karfe Biyun dare bacci Bai ziyarci idanuwanta ba sbd radadin rashin sanin halin da Annenta take ciki.


Amnah ce ta motsa daidai karfe uku Dan haka ta tashi zaune ahankali ta sauko gadon jiki ba qarfi ta hada mata Madara da komai da aka aje musu akan bedside.


Madaran ta Bata ta sauya mata pampas harma da Riga sbd sanyin madaran Daya Dan taba rigar kada sanyi ya shigeta.


Tana gamawa ta Kwantar da ita Takoma itama kaman me tsoron kwanciyar ta kwanta tareda rufe Idanuwanta wannan Karan Bata jima ba baccin ya dauketa sama sama.


Rashin baccin datai da wuri ya saka Zeenah kyaleta dataga tasamu baccin sai qarfe 7 ta tada ita tayi sallah.


Zeenah komawa bacci tayi ita Kuma Amnah tasake bawa Madara tanason mata wanka tana jiran Zeenah ta tashi ta Basu ruwan zafi Dan haka ta zauna kan dadduman datai sallah rungume da Amnah data koma bacci itama.


Tana zaune har qarfe Tara na safe lokacin Zeenah ta tashi ta sauko gadon tana kallan benazir din da mamaki tana shafa wuyanta Dan ya Dan sake tace


"Bena a zaune kikai baccin safen ne?"


Girgiza mata Kai benazir din tana cewa


"Ban koma ba Amnah na bawa Madara"


Toilet Zeenah ta wuce tana cewa


"Duk da hakan ya kamata ace kin koma baccin safe sbd samun Qarin lafiya.




Brush tayo ta fito tana kallan benazir dake jiranta tayiwa Amnah wanka.


Komawa sukai ciki ta Tara mata ruwan zafi Dayake Bata Saba ba a roba suke mata a can gida
Itama Kuma Zeenah din kwata kwata batama San ya akewa babys wanka ba Dan haka dole kusan tare sukaiwa Amnah wanka sbd kasawan da benazir tayi ita Daya anan din.


Duka su Biyun sun gama jiqa kayansu Dan haka Zeenah ce ta fito da Amnah tace Benazir din tafara wankan kawai.


Bata jima ba ta gamo wankan da sabulun Zeenah da qamshinsa ya cika toilet din ta fito ta karbi kayan da Zeenah ta miqa mata na wata dagowan Ashape din embellished English super exclusive purple.


Undies data Bata dasu takasa kalla sbd su Basu Saba da panties irin haka ba gajerun wandina suke sakawa Suma hande idan taje siyowa wasu ma kaman na gwanjo,
hakanan ta saka da sauri kada Wani ya shigo dakin saidai rigar sai takejin kaman ta kamata daga saman tinda Bata Saba saka kaya irin Hakan ba.


Tana gamawa ta zauna ta shirya Amnah wadda tafara Kuka tin tanayi a hankali har tafara Yi sosai duk ta rikita benazir din wadda Daman duk a cikin damuwa da rashin kuzari take.


Umme ce ta shigo bedroom din Jin kukan Amnah din Dayake Neman cika koina.


Shigowar Umme ya saka Benazir sunkuyar da kanta qasa cikin sanyin jiki tana sake rufe kanta da dankwalin kayanta tinda Zeenah bata Bata mayafi ba gashi ita batama San Ina aka Kai nata kayan ba bare ta dauko ciki.


Cikin nutsuwa da girmamawa ta Bude baki a hankali ta gaida Umme.


Amsawa ummen tayi cikin kulawa tana cewa


"Meya faru ne?
Kin Bata madaran kuwa?
Ko kun kwana cikin sanyi Mura ya shigeta ne??


Kasa magana benazir tayi sbd batasan me zata ce ba tinda itama batasan me Amnah din kewa Kuka ba.


Kallanta Umme tayi tace sake hada mata madaran ki kawo mugani.


Ficewa tayi dakin da Amnah tana jijjigawa cikin kulawa da kauna.


Rintse idanuwa Benazir tayi sbd kanta Dayake Neman daukan zafi.


Madaran ta hada ta tsaya dakin ta rasa ina zata dosa sbd Bata Saba wannan free rayuwan dasuke tinanin tayi a gidan ba.


Zeenah ce ta kalleta bayan ta saka doguwan riga mara nauyi tace


"Follow me." Gaba tayi tana latsa wayarta data kunna lokacin benazir ta biyota a baya kaman mara lafiya sbd rashin kuzari da sanyin jiki.


Wani mahaukacin palon Daya gama Jin komai na Jin Dadin da kake buqata a zaman duniya suka fito komai da koina yagama daukan sanyi da qamshin kwanciyar hankali da nutsuwa.


Duk inda ta saka tafin kafarta sanyi ya shigeta sai ta rintse idanuwa ahankali tana qanqame madaran Amnah Dayake hannunta.


Dakin Umme Zeenah ta Isa da ita ta Bude suke shiga Benazir din ta tsaya daga kofa
Zeenah kuwa gurin Ummen ta nufa tana Kiran sunan Amnah dake Kuka har lokacin.


Dagowa Umme tayi ta Kalli benazir din tace


"Qaraso kawo abata mugani idan ba Wani abin yake damunta."


Takowa tayi ahankali ta qaraso ta tsaya daga gefe ta miqawa Zeenah madaran Umme ta amsa tafara Bata cikin sa'a kuwa ta amsa tanasha da sauri.


Gama Bata Akai Umme ta gyara mata jikinta da kanta ta Kwantar da ita take tayi bacci tana sauke ajiyar zuciya ahankali.


Kusan dukkaninsu ajiyar zuciya suka saukar Suma kafin benazir ta silale ta fito ta Maida kanta dakin Zeenah ta zauna qasa a darare zuciyarta ba Dadi Dan batasan Tayaya zatai rayuwa a Nan dinba Kuma,
Duk da alqawarin data daukanwa Anne na zata Kwantar da hankalinta tayi rayuwa me nutsuwa to Amma ta Ina? Tayaya?.
#MAMUH#
#DBENA
#MARRIAGE
#ROMANCE
#BABY MAMAH
[8/29, 8:12 AM] MG: *_Arewabooks@Mamuhgee_*
47
Neman Nisa takeyi cikin tinani da damuwa Akai knocking kofar kafin aka Bude aka shigo.


Masu aiki ne guda biyu suka shigo a tare kowannensu dauke da fararen trays masu kyau dauke da breakfast dinta.


Cikin girmamawa Mai tsananin gaske sukai qasa da kansu suka gaidata.


Shiru tayi Bata dago ba sbd batasan da ita suke ba Dan haka Bata dagoba itama kaman yanda Suma Basu dagoba suka sake gaidata wannan Karan suna Dan dagowa.


Zeenah ce data shigo ta amsa musu tana cewa su Daya a cikinsu yaje ya kawo mata lemon zata ci abinci dashi.


Dayar ce ta fara Jere abincin a gaban Benazir da sai alokacin ta Dan dago ta Gane tin farko da ita suke.


Sake gaidata sukai ta amsa tana Maida musu da gaisuwa itama a sanyaye.


Ana kawowa Zeenah Abinda tace suka fice ta zauna tana kallan benazir data kasa kallan kayan da aka Jere a gabanta qamshinsu na cika hancinta zuwa cikinta.


Chips ne da ketchup da scotch eggs se pepper soup na Kazan da aka cirewa qashi dakuma tea mara Madara me qamshi da zafi sosai.


Bata dauka ita aka kawowa wannan abincin ba saida Zeenah ta sakata cinsa tareda Tayata zuba komai cikin wasu irin plates da suka saka benazir din hankalinta na Neman tashi da wannan rayuwar data samu kanta aciki alhalin mahaifiyarta na can cikin zafaffiyar rayuwa.


Duk yanda Zeenah taso Benazir ta sake taci abincin Bata iya cinsa sosai ba sbd ba cimarta bane irin wannan abincin Dan haka sama sama taci komai taji ya isheta.


Tattara kayan Akai aka fice dasu Mai Aiki ta shigo ta sake gyara dakin ta Kuna humidifier ta fice.


Umme da Zeenah ma shiryawa sukai suka fice zuwa Asibiti dubo dd babba.


Ita kadai aka bari sai Amnah da masu aiki.


Da Rana ma haka masu aiki suka kawo mata abinci aka jera mata
Daqyar ta iya cin kadan tace ta koshi suka dawo suka kwashe.


Kaman mara lafiya haka ta wuni a daki jigum tana renon Amnah duk a sanyaye ba kuzari.


Sai magrib suka dawo har lokacin tana daki zaune ba motsin kirki.


Shigewa sukai kowa yayi wanka suka Dan huta kafin suka fito cin abinci wannan Karan haka aka sakata fitowa zuwa dining Wanda har Akai aka gama Bata iya Sakin jiki ta zauna ko daidaiba bare iya cin abinci a cikinsu.


Dole aka maidata daki aka Kai mata Wani abincin acan Shima Bata iya ci ba saida Umme da kanta ta shigo tace taci.


Yau dinma hakuri Umme ta Bata akan su sake kwana dakin Zeenah kafin gobe.


Wanka sukai kaman yanda Zeenah ta sakata ta shirya ta shirya Amnah suka kwanta.


Yau ma kaman jiya sai kusan hudu ta samu bacci ya Dan dauketa.




Washe garin ranar tana daki masu aiki suka zo aka cire tsadaddin furnitures na dakin dake maqale Dana Zeenah da basuyi komaiba aka saka komai sabo a dakin tareda tsarin abubuwan dakin babys.


Me Aiki aka kawo ranar sabuwa wadda hidiman laluran benazir da Amnah ne kawai aikinta da haka ita aka saka ta Jere kayan lefen Benazir tsaf a closet hakama tarin kayan da aka siyawa Amnah duk ta Jere komai
Duk da babu inda yakeda Wani Abu me suna datti ko qura a dakin Amma Saida Nafisat me aikin ta tsaftace koina ta wanke toilet din da a ranar Shima aka zuba mata toiletries da komai na buqatanta Dana Amnah.


Ac aka kunna tareda qamshin masu Dadi Zeenah ta kawota dakin ta fice sbd wayan da zatayi.


Tinda ta baro gidansu babu Abinda ta dago tayiwa kallan ko sakan uku bare kallan tsaf sai dakin.


Turkish Royal bed ne da set dinsa na komai tareda Wani mahaukacin Katan mirror Daya ci kusan Rabin bangon gefe Daya.


Komai na dakin Ashe ne da fari aka saka sai daukan Idon nuna kudin Dayake cikin siyansa,
A gefen makeken gadon daga qurya gadon Amnah ne fari Mai kyau da tsadan gske Shima hakama da kayan qasan baby a jikinsa,.


Ko beddings dake shimfide a gadon fari ne hakama pillows Akai kusan guda 8 dasuka sakata sauke ajiyar zuciya ahankali jikinta na mutuwa sosai.


Carpet da table dasu stools harma da sauran kayan dakin kusan tsoro suka Bata saidai batada mafita ko tudun dafawa a wannan rayuwar data tsinci kanta aciki Dan haka ta Tako ahankali ta Kwantar da Amnah ta nufi inda take tinanin toilet ne ta shiga Nan Wani firgicin Yakuma cikata ta ringa saukar da hawaye masu zafin tonowa da Annenta tinanin anan ake nufin zatayi rayuwa Annenta na can cikin halin qaqanikayi.


Sosai tayi Kuka jikinta na sake mutuwa kafin tayo alwala ta fito ta tayarda sallah.


Tana idarwa taga har lokacin Amnah na bacci Dan haka ta koma toilet tayo wanka sbd tinanin al'adar da Dokan gidan ne wanka kafin kwanciya musamman ganin wannan gadan tasan bama zai yiyu ta hau musu gadon ba.


Tana fitowa ta dauko kaya inda Zeenah tace mata ta ringa daukowa ta saka doguwar Rigar jallabiya sbd a kwana Biyun datai dakin Zeenah cikin mawuyacin hali tayi su sbd kayan datake Bata tana sakawa Riga da wando.


Tana gama shiryawa Zeenah ta shigo ta zauna tana Tayata bawa Amnah data farka Madara.


Bayan sun gama Zeenah anan ta kwanta Saida Amnah tayi bacci kafin ta fice musu bayan ta nunawa benazir inda zata Kuna wutar dakin da kashewa kokuma rage hasken.


Zeenah ce ta sakata Hawa gadon kafin ta fice Dan haka tinda ta hau take shiru kaman wadda tayi bacci Amma zuciyarta cike take da tinanin inda ta samu kanta a yanzu.


Baby Amnah kaman tasan sunyi dakin kansu ranar bacci tayi sosai har safe ko madaran Bata farka ta Sha ba.


Suna yin sallar Asuba benazir ta gyara gadan ta sauko da Amnah suka zauna kan tattausan carpet din dake gefen gadon suna gyangyadi.


A gurin bacci ya sake dauketa sai kusan karfe Tara Nafisat ta shigo tafara kokarin gyara dakin ita Kuma benazir tayi toilet da Amnah Dan Yi mata wanka.


Yau ma a jiqe suka gama wankan ta kawota daki ta Kwantar Takoma itama tayo ta fito suka shirya suka zauna jiran tsammani kaman kullum.




Breakfast din na yau a dining aka kirawota a dosane tayisa cikin tsoro da rashin kwanciyar hankali.


Suna gamawa ta silale Takoma daki sukuma suka sake ficewa zuwa Asibiti sbd dd babba da zaa wuce dashi Zurich yaga likitan DD.


Dayake tafiyan tareda Dawood din harma da dad kaante zaayi sai Basu Wani tsaya Bata time ba cikin kwanaki 10 aka gama komai suka wuce Kuma tin ranar da aka tafi da dd babba asibiti Dawood Bai dawo kaantes ba sbd kullum a Asibiti yake haduwa da ummensa harma da dad kaante.




******Bayan tafiyarsu dd babba Umme ta samu nutsuwan dawo da hankalinta da kulawanta kan benazir data fara sabo da zaman daki da rayuwar kadaici data sake samun rayuwarta aciki duk da Zeenah na iya kokarinta gurin ganin tana debe mata kewa da Bata kulawa tareda nuna mata wasu abubuwan.


Wata sabuwar meyiwa Amnah wanka aka dauko dattijuwa wadda ita Kuma aikinta kawai na yiwa Amnah wanka ne sbd mura data fara shigarta na ruwan wanka da kullum saita shaqa sbd benazir Bata iya mata wanka toilet.


A jiki Umme tafara Jan benazir sbd lura da akwai tsoron mutane da rashin sabo da mutane sosai a tattare da Bena din,


Mum Khadija ma da bata cika son mutane ba tana 'dan kaunar Bena din sbd fahimtar zatayi biyayya makan baiwa ita Kuma Daman tanasan Wanda zai Basu girma da biyayya ya nuna su dinne a sama.


Zaman daki da qarfi da yaji Umme da Zeenah suke Hana Bena kullum indai zasu fito sai ankirata ta fito.


A dosane take zama cikinsu Bata iya magana idan ba tambayarta ummen tayiba ko Zeenah.


Ahankali mura Mai qarfi ta shigeta ita da Amnah sbd sanyi da wankan Datake musu so biyu kullum tinda tazo sbd tsoron shafawa Wani Abu ko gidan datti ganin masu gidan da gidan kaman saika wanke hannu zaka taba su.


Boye zazzabinta Mai tsananin karfi tayi ta danne Bata bari ansaniba tinda haka Suka Saba gida,
Na Amnah ne yakasa dannuwa sbd rigimar Datakeyi ba sassauci.,


Ta Dena baccin dare sbd ciwon Amnah ga nata ciwon ga rigimar Amnah ga kadaici ga damuwar mahaifiyarta sai kawai tafara Neman zauncewa ciwo ya Kwantar da ita gadan gadan harda Kuma Qarin sauyin cima da muhalli.


Hankali tashe aka kirawo likita har gida yazo ya dubata aka duba Amnah itama.


Wannan ciwon da sukai ya saka jikinta yin sanyi sbd kauna me tsananin dataga Umme nayi mata itada Amnah sai Hakan ya taba zuciyarta akan yaudarar ummen takeyi a matsayin wadda Bilal dinta ke tsananin so.


Wannan tinanin ya sanyayar da zuciyarta daga bushewan da tayi batajin kowane feeling a gidan da mutanen gidan.


Idan zatayiwa Umme adalci Bata cancanta wannan yaudarar da ake mata ba Amma Kuma itama Batada zabi sbd ba itace ta zabarwa kanta wannan rayuwar ba.


A haka dole ta fara sakewa dasu Dan faranta ran Umme Dan Zeenah dasuke nuna mata asalin kauna da kulawa.


Da farko kokarin cin cimar da duk aka Bata tafara tareda daurewa tana cin abincin taredasu a dining kowane lokaci.


Hakama takan daure da kanta ta fito Koda dakin Zeenah ne taje,


Kullum da safe da kanta take zuwa dakin Umme ya gaisheta ta dena Jira sai an Aiko kiranta ta fito.


Hakan data fara ba qaramin faranta ran Umme yafara ba Dan haka suka sake dagewa sosai gurin kulawa da benazir din.




*****dd babba ya samu sauki sosai Amma Dawood ya hanasa dawowa sai ya huta daga tashe tashen hankalin da akaita samu a baya Dan haka sukai zamansu sbd shi Dawood din yanada abubuwan da zaiyi a qasar Kuma ahakan yaqi barin ko so Daya Safnah ta gansa Kuma data kira yace Bai aminta ta samesa ba ta zauna inda take zai nemeta da Kansa.


Wata daya suka share harda sati uku kafin suka fara Shirin dawowa shi dad kaante Daman tini ya dawowarsa yabarsu acan.


*****Acikin wannan watan da satikan rayuwar Benazir a Kaantes ta fara amsa Wani sunan da matsayi na sauyi data fara samu,


Dukiya gaskia ce,hakama rayuwar hutu da daula gaskia ce,


Benazir ta fara samun sauyi na rayuwa Dana

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login