Showing 9001 words to 12000 words out of 52375 words

Chapter 4 - KISHIYA KO BAIWA BY REAL ESHAA.txt

06 Mar 2025

3315

saurin hade bakinsu waje daya,tashiga aika masa da sakonninta masu wuyar fassarawa Wanda batasan ta Iya ba,besan time dayafara mayar mata da martaniba suka rikewa juna"seda taga takawar da tunanin Nadiya aransa kafin tajanye jikinta daga nasa ta'fada toilet"sabon wanka tasake sannan tafito hango shi tayi yayi matashi da hannunsa yakurawa P.O.P dakin ido,kallo 'daya tamasa tadauke kai, direct jikin siff tawuce Riga da skirt na atamfa pink da ratsin fari tasanya"dinkin yazauna 'das ajikinta,skirt din yafitar mata da shape dinta hakama rigan yaimatukar amsar jikinta zama tayi akan stool tayi simple make up sannan tashafe jikinta da humra masu dadin kamshi,'dan kwalin tadauko tayi daurin ture kaga tsiya(No respect)abin hannu da sarka dakuma dankunne tasanya.Masha Allah kawai Ahmad ke maimatawa aransa ganin wani irin masifeffen kyau datayi,kasa hakuri yayi danhaka yamike cikin san'da ya isa gareta ya runguneta tabaya yana shakar dadda'dan kamshin humran datake kansa yacusa atsakanin wuyanta ya lasa.Murmushi tayi tasanya Hannu tadauki wayarta dake gaban dressing mirror tafarayi musu selfie ahaka ganin yanda sukayi kyau.'dago kansa yayi yakarbi wayan yana kallon pic din data dauka yayi wani irin kyau naban mamaki tamkar wasu jaruman India"Shima selfi ya shiga yimusu kala kala wani yana kissing dinta wani tasakalo hannunta awuyansu wani tana kan cinyarsa sunyi pic sunfi kala ashirin kowanne style dinsa daban"wayarsa yadauko yatura baki daya pic din dasu kayi,kamar Wanda akace yaduba time yaga 12:00pm ido yazare yace oh my God My Kainat dubi yanda time yawuce bakiyi breakfast ba bejira amsartaba yasun gumeta yayi dining area dake sashen Nadiya da ita.


Nadiya na fita adakin afusace direct dakinta tawuce, kan tangamemen bed dinta ta'fada tare da fashewa da kuka,wurgi tashigayi da duk wani Abu dake kan bed din Cikin matsanancin tashin hankali tace karyane Ahmad karya kakeyi baka isa katozar tani ba nafi karfin wulakanci Ahmad nafi karkin wani da namiji yawulakanta kunyi ka'dan ta'fada tana fincike bedsheets dinta dakarfin gaske"wayar ta dake kan bedsite drower ne yahau ruri, dasauri tasanya hannu tadauko hannunta harrwa yake wajen picking Call din.cikin matsanancin tashin hankali tace hema Na shiga uku wlh mutuwa zanyi Ahmad zekasheni da ciwon zuciya ni Ahmad ze kuntatawa arayuwa wlh sena haddasawa wancan la'ananniyar yarinyar bakin cikin da harta mutu bazata manta daniba.
Daga daya bangaren hema tace dan Allah kitsaya ki yimin bayani yanda zangane anma ni bamfahimci komai Cikin maganar kiba ki nutsu"hawaye tashare kana tazayyanewa hema duk abinda yafaru daga daren jiya zuwa yau.....tsaki hema taja tace wai meyesa bakiyin Abu da lissafine Nadiya?, a tunanin ki wannan abin ne zekawo mafita?, kibari
Gobe zanzo danazo komai yakare dan haka ki kwantar da hankalinki sannan kinutsu,karki nuna musu komai sauran abunuwan kuma senazo yanzu kitashi ki wanke fuskarki sannan ki koma parlour ki kizauna dan karsu fahimci kina cikin damuwa.Sake share hawayen ta tayi tace toh inajiranki anma zakizo goben ai?,"eh zanzo kede kiyi abinda nace kawai,zanyi"kokefa tace da ita sannan sukayi sallama.mikewa tayi tashiga toilet tawanke fuskarta tafito tayi make up sannan taje parlour tazauna kamar yanda hema ta'fada mata anma kasan zuciyar ta wani irin tafasa yake...
Jin 'karan dariya yasanyata 'daga kai dasauri danganin kowaye?,Sukainat tahango ahannun Ahmad tamkar wata baby yadaukota tasakalo hannunta ta wuyarsa.Da sallama abakinsa yashigo, ganin Nadiya zaune awajen yasan shi saurin ajiye Sukainat yana sosa 'keya dan beyi zaton ganin ta a parlour ba yadauka yanzu tana bedroom dinta ne.'dauke kai tayi kamar batagan shiba"Ba'kin cikine yamamaye zuciyar Sukainat talura aduk sanda Ahmad yaga Nadiya muddin suna tare seyayi kokarin raba kansa da ita.Tana cikin wannan tunanin taga Nadiya agabanta hannunta tarike tace 'kanwata zomuje kiyi breakfast dan inkika biye Honey baze barki ki hutuba"murmushin dabe wuce saman la'b'ba ba Sukainat tayi tace toh momyn rufy"aranta kuwa cewa tayi lalle wannan matar muguwar she'daniyace wai nice kanwarta?"Dining suka zauna tayi serving din Sukainat,Ahankali Sukainat ta daga kai gani tayi haryanzu Ahmad yana inda yake atsaye.
Ka 'karasomana ya Ahmad tace dashi,hannu yasanya yashafi sajen fuskarsa yace naki tunda me dakin bata gayyaceni ba"wani shegen kallo Nadiya tawatsa mai tace aikuwa sede inbaza kaciba don babu wani gayyatar ka da zanyi"itade Sukainat shiru tayi batace komai ba taciga da breakfast dinta, tanagama wa tamike tace nagode aunty,ni zankoma ko kallon inda Ahmad yake batayiba tawuce sashen ta,ta lura kamar Ahmad tsoron Nadiya yake agaskiya bazata dauki wannan abinba.
Ahmad nagin fitanta yayi saurin karasowa kusa da Nadiya ya rungumeta tabaya yace I Miss u so much my Queen, wani irin turesa tayi tamike tsaye tace wlh karya kakeyi Ahmad bakayi kewata ba agabana fa ka ha'da bakinka da wata kuke romance din juna dan kaci min fuskarsa hakan be ishekaba seda kukabiyoni Har sashena dan kunsake kuntata min Ahmad kabani mamaki bantaba zaton haka daga garekaba takarashe tana me fashewa da kukan takaici. Rungumeta Ahmad yayi cikin muryan lallashi yace dan Allah kiyi hakuri My Queen wlh banyi haka dan intozar takiba hasalima lokacin dakikeje dakin banyii zaton ka bace nayi zaton idanu na ke yimin gezo dan Allah kiyi hakuri nasan kina dashi anma kikara akan Wanda kike dashi kinji kinsa Ahmad nakine kuma baze taba yin wani Abu danyasaki a damuwa ba pls kiyarda dani...da 'kyar yasamu yashawo kanta tahakura"sannan tayi serving dinsa yayi breakfast bashi yabar sashen ta ba se bayan la'asar....
Lokacin daya koma sashen Sukainat dan takaici bata Iya cemasa komai ba"daddare Nadiya takirasa wai suje sunyi dinner.Bayan sungama dinner suka dawo daki,toilet Sukainat ta'fada ruwa tawatsa tayi brush sannan tafito wani Jan sleeping dressed me kyan gaske tasanya kana tashafe jikinta da humran ta masu dadin kamshi Wanda Aunty Aliyah ta ha'da mata.Gefen Ahmad taje takwanta tare dajuyamasa baya hannu yasanya yajanyota zuwa jikinsa tabude baki zatayi magana yahade bakinsu waje daya ya shiga aika mata da sakonni masu wuyar fassarawa,jin sakonnin dayake aikamata yasa ta manta da fushin datake dashi daga nan suka Lula wata duniya me dadin gaske Wanda bakowa kesanin dadin dayake ciki ba....


Washe gari:misalin 1:00pm Hema tazo direct sashen Nadiya tashiga ganin bata parlour yasata nufar bedroom din ta zaune tasameta dawaya ahanunnta"dasauri Nadiya tamike tarungume hema Cike da farin ciki,zama hema tayi tana murmushi"Fita Nadiya tayi badadewa tadawo hannu ta rike da tray cikawa hema gabanta da snacks dakuma drinks tayi,bayan tasha drinks dinne tace bazama zanyiba shawarar da dazanbaki nafarko shine kiyi maza ki dauko 'ya'yanki sudawo gabanki domin bakaramin temaka miki zeyiba shawaran na biyu kuma kirike wannan tadauko wani kunshi magani tabata da takarda aciki tace duk bayanansa ya yana ciki wannan paper, sannan shawara na uku ki kima kanki daga gareta sannan ki kara kissa akan Wanda kike yi kada kice zaki garamarta,nizan wuce saboda Dadyn Muslima,besan nafitoba"Washe hakora Nadiya tayi tace ngd kawai semunyi waya har compound tarakata sannan ta koma cikin gida....Duk yanda hema ta'fada mata zatayi haka tayi ba'abinda tarage sema Wanda takara"sede mahaifiyar ta tace bazata tur mata su rufy ba senanda 1weeks....


Bayan sati daya yau yakama sati daya datarewan Sukainat agidan Ahmad ayaune kuma zekoma dakin Nadiya."cikin yanayin damuwa yace agaskiya zanyi kewar ki my kainat ,'dan murmushi tayi tace ba komai aikamar yaune zaka ga kadawo,fatanade kakulamim da kanka"murmushi yayi yace bakida matsala nima kikulamin da kanki,hira sukayi mecike da so da kaunar junansu Wanda basu ta'ba irin sa ko kafin ya aureta,duk inda zatayi yana manne da ita yinin wannan ranan komai tare sukayi.Da Yammaci Nadiya tasha wankanta cikin wani English wear's tayi make up,sannan tajere komai a dining area"jitayi anturo kofa tana juyawa taga kanwarta,murja,da rufy,Hanan,dakuma,junior "dagudu tatafi tarungume yaran tace I Miss u much my blood suma Rungumeta sukayi sukace miss u more momy.murja tasa tasakeyi musu wanka akashiryasu lokacin magriba tayi danhaka ana idar da isha suka zazzauna a dining lokacin murja tatafi sesukadai.Da sallama Sukainat da Ahmad suka shigo suky taci gayunta cikin Wani bakar abaya tayi rolling kanta da mayafinsa.Kujera Ahmad yajanyota yazauna yana Kallon fuskarsa yayan nasa cike da so,kujeran dake kusa da rufy suky taja zata zauna,cikin shammata rufy tasanya kafa tature,cikin rashin sa'a Sukainat tazame akasa tare da buga goshinta a tiles.....










_VOTE_ โœ…
_COMMENTS_
*AND*
_SHARE_












*_ESHAA CE~_*๐Ÿค™๐Ÿป
[3/23, 15:13] ESHA: *KISHIYA KO BAIWA???*
_(TRUE LIFE STORY)_


*NA MARUBUCIYA*
*REAL ESHAA ~*




*WATTPAD* _Realeshaa_




*_Ya Allah ubangiji kajikan mahaifina ya Allah kagafar tamasa kurakurensa ya Allah kakai haske kabarinsa ya Allah kajikan dukkan musulman dasuka rigamu gidan gaskiya ya Allah kasa innamu yazo mucika da imani_*




*PAGE 15&16*๐Ÿ–Œ๏ธ


________________________๐Ÿ“–Dasauri Ahmad yataso yazo ya'dagota"subhanallah sannu Sukainat ya'akayi haka yafad'a yana kokarin zaunar da ita akujeran dining in Cike da tasauyinta.Goshin tadafe tanajin wani azabebben ra'da'di yana mamaye gaba 'daya ilahirin kanta.
Hannu yasanya yashafa goshin yana mulmula mata Ahankali" Ido taruntse hawayen azaba na mamala daga idanunta,se sannu yake mata cike da tausayin ta.Daga Nadiya har 'ya'yan ta babu Wanda yadaga kai yakallesu bare susan Allah yayi digon halittan 'dan Adam awajen sema cin abinci su dasukeyi cike da nisha'di.Wannan Abin dasu kayi ba'kara min zafi yayima Sukainat ba,kasancewar tana ganin time da rufaida ta ture kujeran tafadi da farko tayi zaton mistake ne anna yanzu ta tabbatar da gangan tayi,,mikewa tayi dafe da goshinta tanajin jiri na dibanta anma ta gwammaci tabar wajen da wannan takaicin.Dasauri Ahmad yabi bayanta yari'ko hannunta a'daya daga kujerun dake parlour Nadiya ya zaunar da ita kana ya tsugunna agabanta yace sannu, bari na dauko man zafi inshafa miki?"Kai tagirgiza cike da dauriya tace a'a zantafi in 'dan kwanta zedena zafin.Toh abincinfa ya tambayeta cike da kulawa?? sake girgiza masa kai tayi tace bazan ciba",cike da tausayinta yarike hannunta suka fice daga sashen.
Nadiya naganin fitansu suka fashe da dariya" hannu tamikawa rufy tace give me higt 5 yarinyar kirki,hannun rufy tabata suka tafa
Cike da tsiwa rufy tace wlh momy bana san Sukainat din natsaneta kuma se tabar mana gidan mu tunda bana ubanta bane,sede takoma tsohon gidan ubanta wanda babu AC aciki kuma babu tiles"Cikin dariyar mugunta Nadiya tace aidaman kwa'dayine yakawo ta gidan,So take dadynku yamutu ta kwashi kudin sa takai gidan su suyi facaka daahi.
Cab 'dijan wlh bata isa ba shegiya kawai kuma satabar mana gida, kota haifi yara bama sansu ba kannen mubane se mundinga dukansu cewar rufaida.'Kirji Nadiya tadafe cike da fargaba hakika bazataso Sukainat tahaihu agidan ta ba"domin dukiyar Ahmad mallakinta ne da 'ya'yan ta su ka'dai"cabbb aibazata tabari ta haihuba duk runtsi duk wuya...haka suka cigaba da kulla mugan kalamai akan Sukainat itada rufaida inkunji yanda yarinyar take magana zakuyi zaton babba wacce ta mallaki hankalin tane...
Suna shiga daki tafa'da kan gado tare dafashewa da kuka mai tsuma zuciya"tallabota Ahmad yayi yace haba Sukainat meye abin kukane inkuma haryanzu ciwon yake miki kitaso inkaiki clinic adubaki!!Cikin muryan kuka tace a'a basemun jeba zedena insha Allah"Ok Allah yakara sauki yanaga ma fadin haka yafice abinsa batare dayasake cewa komai ba"kuka taci mai isarta kafin tayi shiru,!Wayarta dake kan dressing mirror ne yahau ruri Ahankali tamike taje tadauki wayar sannan tadawo tayi picking"Muryan Aunty aliyah ce yakara de Cikin wayar Cikin yanayin maganarta na zafi tace wato Suky baki Iya Neman mutane awaya bako?ko duk amarcin ne yahanaki kira?ko kuwa Ahmad dinne yace karki kiramu dan nasan ze iya aikatawa!!Hawayen fuskarta tashare tace a'a aunty bahaka bane wlh katine babu awayata anma kuna raina kiyi hakuri,yasu Ummi da Abba na dakuma Uncle kice ina gaishesu kafin nakirasu dan nayi matukar kewar Ku...Dasauri Aunty Aliyah ta katseta tahanyar cewa ke suky yanaji muryan ki haka bakida lafiya ne?, ko kuma sakarcin kin kikaje kikeyiwa Kishiyar taki nakuka??,Sake share hawayen tayi tace a'a aunty bahaka bane banjin dadin jikina ne kuma bacci ma nakeyi kiran yatashe ni shiyasa kikaje murya ta haka.
"Kin tabbata babu wata matsala ko?"Eh babu komai Aunty" masha Allah, haka akeso"abinda nakeso dake suky kicigaba da hakuri kinsan yanzu kinshiga wata sabuwar rayuwa, rayuwar Aure wata rayuwa ce wacce zakiyita mecike da dumbin lada dakuma biyayya,anma sekin yi hakuri musamman keda kike da abokiyar zama dakuma 'Ya'yan miji" domin zaki fuskanci abubuwa da dama acikin zamantakewar Ku sekin yi hakuri kin kuma jure kafin kiga cigaba"kada kisakewa 'ya'yan mijin ki surenaki,bawai ina nufin kada kijasu ajikin ki bane a'a sede ina nufin kada kiyi abinda reni ze shiga tsakaninku haryakai kigamusu dasu ta yanda zasu fada miki duk maganan dasuka ga dama"Inma sukayi miki abinda bedaceba kifadawa mahaifinsu,ko mahaifiyar su,muddin basu dauki mataki akaiba toh ki dauki matakin daya dace akai"koda kuwa mahaifinsu bazeji dadin hakan ba kiyi saboda kar reni ya shiga tsakanin ki dasu matsayin ki na matar mahaifinsu ki kiyaye kanki daga matar Ahmad tunda tunfarko tanuna bata kaunar ki toh kifita ahanyarta,gudun kartacutar dake watarana."
Insha Allah Aunty zankiyaye ngd da wannan nasiyyan taki kuma insha Allah zanyi amfani dashi"karki damu kede kikula da kanki dakuma mijinki."toh aunty zankula,yaushe zakizo toh??,Dariya Aunty aliyah tayi tace se munzo suna dan yanzu hakama nakirane in miki sallama dan jirginmu yakusa tashi nace bari nasar dake kar kice natafi ban miki sallama ba"kuka Sukainat tafashe dashi tace Allah Aunty nibanyar daba taya zaki tafi bamuyi sallama ba..ke bansan shashancin banza fa saura minti talatin jirginmi yatashi ko sokikeke muyi missing flight din ne??A'a toh kijirani yanzu ya Ahmad zekawoni muyi sallama pls kijirani,tana gama fadin haka takashe wayar gudun kar tahanata zuwa.


Dariya aunty aliyah tafashe dashi tana munawa Ummi wayar, tace ohh suky rigima jifa wai se tazo munyi sallama"Dariya Ummi tayi tace aiduk lefin kine dakika fada mata kinsan Sukainat da jaraba yanzu seta taahin hankalin ta kan setazo kunyi sallama,kuma inace se jibine tafiyar naki??" dariya Aunty aliyah tasake akaro nabiyu tace kawai zolayarta nake fa daman sonike inji muryanta.Aikuwa kisake kiranta kisanar mata wasa kike inko bahaka ba nanda wasu mintina kiganta agidannan dan ba hankali gareta ba cewar Ummi"Cikin dariya aunty aliyah takira number Sukainat anma haryayi ringing y katse ba'a'dagaba"kallon Ummi tayi tace kinga bata yi picking ba da'alama tashiga toilet ne kokuma tasa wayar a silent "Kai Ummi tagya'da batare datace komai ba tacigaba da jan tasbahanta...


Cikin sauri tafice daga bedroom din ta tanufi sashen Nadiya tana Addu'ar Allah yasa Ahmad yakaita.
Zaune tahangosu Ahmad nawasa da 'ya'yan sa se dariya yake 'kyal'kyalawa da'alama hira suke mishi me ban dariya"Jitayi jikinta yayi sanyi daga ninsu ahaka da 'kyar a amince ya kaita,anma haka tadaure takarasa bakinta dauke da sallama"Ahmad ne kawai ya amsa shima hankalinsa nakan hirar dayake da 'ya'yan sa.'Karasawa gabansa tayi ta tsaya cikin yanayin na Neman temako ta langwa'bar da kanta tace Dan Allah ya Ahmad kakaini muyi sallama da Aunty aliyah zatatafi yau kuma saura minti talatin jirgin su yashi,dan Allah katemaka ka kaini plssss.
'Dan murmushi yayi yace toh muje in kaiki yafada yana mikewa"Kuka Rufaida tafashe dashi tace Abba inazakaje kabarmu muna hira shikenan kaje tunda kafi santa damu ta'fada na rugawa da gudu zuwa bedroom dinsu,Da kallo Ahmad yabita hartashi dakinsu "Wani dogon tsaki Nadiya taja tace karyar banza ko tayar mota babu agidan tsoho anma azo anayima na feleke da karyar hawa jirgi dan ba asaba hawa ba kai wlh duk kutunbinarki haka zakibarni da mijina ma'karyaciya kawai.shiru Sukainat tayi duk da taji zafin zagin,Maganan Aunty aliyah ce tafado mata arai inda takecewa karkirena ta kokuma kimusguna mata anma fa idan tayi miki karkiraga mata muddin kinason 'kwatar 'yancinki.
Cikin karfin hali tace ya isheki momyn rufy meye abincin mutunci acikin wannan maganar?,dan Allah kiyi hakuri dan bansaki cikin magana ta ba kikama girmanki wannan maganar tsakani na da mijina ne"Azabure Nadiya tamike tace ke harkin kai INA magana kina mayarmin ko?,wacece ke 'yar matsiyata kawai dangin jaraba?,Harara Sukainat tamaka mata cike da tsiwa tace yo ainaga arzikin basiyansa akeba kuma kema bashi ne ubanki keda...ai bata karasaba Nadiya tadaga Hannu daniyan kwasheta dawani azabebben mari,Dasauri Sukainat tarike hannunta tace karkisoma gangancin marina dan wlh zaki yi da nasani,tanagama fadin haka tayi wurgi da hannu.Kallon Ahmad dake tsaye kaman gunki Nadiya tayi cike da takaici tace ngd da abinda kukayimin agabanka wannan yarinyar ta keyimin zagin cin mutunci kana Kallon ta bakace komai ba, hakan yanuna kafifita akan ni da 'ya'yan ka!.Kamar jira yake Nadiya tayi magana ya Murtuke fuska 'bangaren da Sukainat ketsaye yajuya yace kibata hakuri,galala Sukainat tatsaya tana kallon sa jin wai ita zatabawa Nadiya hakuri,tabb abinda ba zefaru baa kenan tafada aranta.Ba magana nake dakeba,banza tayi dashi tajuya takoma sashen ta batare data sake kallon kowa acikin suba dan harga Allah Uba befi Uba ba tafara zagarmata da mahaifi sannan dan rashin adalici yace wai tasake bata hakuri aikuwa shima yasan fada kawai yake."Afusace Nadiya tace aiga irin tanan yarinya karama tarenaka saboda taga gadon baccin ka to wlh ni bazam dauki wannan rashin mutunci ba dan babu abinda nake nema awajenta,nawa wannan yarinyar take dahar zakaba umarni taki yi in banda tamaida ka sakarai Wanda bakasan mekakeba run wuri gwara kataka mata nurki "kalaman Nadiya bakaramin sake harzukasa yayiba na shariyar da Sukainat tamasa dan haka yanufi sashen ta cike da matsanancin bacin rai.....












_VOTE_ โœ…
_COMMENTS_
_AND_
_SHARE_










*ESHAA CE~*๐Ÿค™๐Ÿป
[3/23, 15:13] ESHA: *KISHIYA KO BAIWA???*
_(TRUE LIFE STORY)_


*NA MARUBUCIYA*
*REAL ESHAA ~*




*WATTPAD* _Realeshaa_




*_Ya Allah ubangiji kajikan mahaifina ya Allah kagafar tamasa kurakurensa ya Allah kakai haske kabarinsa ya Allah kajikan dukkan musulman dasuka rigamu gidan gaskiya ya Allah kasa innamu yazo mucika da imani_*




*PAGE 17&18*๐Ÿ–Œ๏ธ


________________________๐Ÿ“–Tana shiga daki ta'fada kan gado tare da fashewa da wani irin kuka me cike da takaici da bakin ciki meyesa ko yaushe se Nadiya tacimata zarafin mahaifa shin meye laifin iyayenta acikin wannan abin?,shin Nadiya wai wace irin macece Mara tsoron Allah me mugun bakin hali dakuma zamba cikin aminci talura idan agaban Ahmad ne zata nuna barunta shiyasa Ahmad ke goyon bayanta akoyaushe...tana cikin wannan tunanin taji tsayuwar mutum akanta Ahankali ta'dago kanta tanajin zuciyarta natsinkewa"Ahmad tagani tsaye akanta fuskar nan amurtuke tamkar Wanda aka aikowa da sakon mutuwa"Sosai ta tsorata daganin fuskarsa,dan haka

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login