Showing 24001 words to 27000 words out of 61588 words
Chapter 9 - AGOLA BOOK COMPLETE DOCUMENT BY Nabila Lawan Zango .txt
nataso harka ganni kace kanaso, idan tadawo nan, mezatayi maka, kaima da bazama kakeba, kuma acan tana taya Inna zama tunda ita kadai ce.
Allah yabaki hakuri Hajiya wlh ba haka nake nufiba, kawaide nafada ne, amma kiyi hakuri ba za,a sakeba. Kallon mamaki Jalila take bin Umminsu dashi, ganin yanda takema Dadynsu fada, wanda ada ko gardama batayi mashi, amma wai yau shine yake bata hakuri, har muryarta tana fin tashi yin sama. Tunowa tayi da wa,azin da malam Sameer yayi masu akan hukuncin matar datake daga ma mijinta murya. Wasu zafafan hawayene suka rika fiyo mata, saurin gogesu tayi.
Alh, yace Jalila zaki iya tafiy, amma kizama cikin shiri nan da sati mezuwa zaki tafi, anjima kizo ki amshi kudi seki siyo abunda kike bukata. Tashi tayi jikinta duk amace, tafita.
Halima tace Sameer lallai akwai abinda yake damunka, kuma ba karamin abu bane, kallifa dan abincin daka ci. Sameer yace wlh Umma banajin dadin abincin ne. Rufe kwanon tayi tace inajinka fadamun damuwarka.
Gyara zama yayi, ya kwashe duk abinda Baba mairo tafada mashi yafada ma Ummanshi. Kasan cewar Halima mace me tausayi, bata san lokacin da hawaye suka wanke mata fuska ba.
Tana goge idonta tace wai Sameer wannan labarin ba ta tsunniya bace kake bani kuwa. Wlh Umma ni kaina faba Babbar mace bace tabani labarin Falak ba, dabazan yarda ba, kuma nima naga wasu alamomi agurinta lokacin damuka hadu kasuwa, bakiga kayan jikinta ba, bazakice daga gidan masu kudi tafito ba.
Umma tace tabbas nima bantaba jin abinda yabani tausayi da tsoro irin labarin Falak ba, agaskiya Sameer ina yimaka sha,awar aurenta, koda bakace kana sonta ba, nizanyi maka umarni da aurenta kodan kafidda ta daga rayuwar datake ciki, dan wannan mata batada imani zata iya kasheta wlh.
Kuma naji dadi, dakace kana sonta, tunkafin kaji labarinta, hakan zesa nayarda bawai tausayinta ne yasa zaka aureta ba, dama nafison ace akwai soyayya atsakaninku kafin kuyi aure, hakan zesa auren yafi dadewa.
Tunda baze yuwu kaje gidansu ba, meze hana kadauko Baba mairo kuzo nan muyi magana ba. Yace shikenan Umma zanyi yanda kikace. Yauwa Sameer amma dan Allah kacire damuwa aranka, insha Allahu bakada mata se Falak, zantayaka da addu,a har Allah yadoramu akan wannan muguwar mata. Sameer yayi murmushi yace ai damuwa takare, dama ina tsoron kiji labarinta kice bazan aureta ba. Dariya tayi tace haba Sameer ai yakamata kamun sheda mekyau, Allah kada yakawo ranar dazan tauyemaka hakkinka, kamar yanda kakemun biyayya dolene nima inso abunda kakeso, matukar baze cutar da kaiba.
Sameer yace amma Umma anan gidan zamu zauna ko? Kinsan banason nisa dake, tace a,a kada ma kafara, bazan zauna da surika agida daya ba, gara de muna nesa, idan kata fima akwai A.isha diyar yaya Zainabu tagama makaranta kuma dama tace mun zata bani ita, tunda tana da yan mata, seta dawo nan mucigaba da zamammu.
Sameer yace to umma ina zan zauna? Tace bade ka gama karatunka ba, haya zaka kama kafin Allah yabude se kafara gina wancan filin naka. Amma Allah bazamu zauna tare ba. Dariya yayi yace toshikenan Umma ai base kinrantse ba, yanzu de bani abincina incinye. Dariya tayi tace oh baka koshiba kenan.
Sati yana zagayowa Jalila tagama hada komai, nata, dakin Baba mairo tashiga, zaune ta iskesu suna fira, mikama Falak takaddu tayi, idonta yana kallon kasa, saboda gab take da fashewa da kuka, ita kadai tasan abinda takeji. Falak tace nameyene Jalila? Budawa tayi tafara dubawa, cike da farin ciki ta rungume Jalila, ganin result dinta ne ta amso mata kuma gaba daya tacinye both waec dan Neco.
Kuka sosai Jalila tasak tana kara kankame Falak, cikin muryar kuka tace Falak kiyi hakuri nasan Ummice tasakaki cikin halin da kike ciki, gashi yanzu zantafi makaranta batare dakeba, wlh saboda ke nazabi intafi boarding saboda bazan iya kallonki cikin damuwa ba, ki kara hakuri akan wanda kikeyi.
Kuma dan Allah ki amince da malam. Sameer yafito kuyi aurenku kema kibar gidan nan, dan wlh koni bansan lokacin dawowata ba, banason gidan nan, gara inzauna amakaranta yafi mani zaman gidan nan. Nizan tafi, inada no Baba mairo zamu rika waya, Kudi masu yawa tasaka ma Falak ahannu sannan ta bata wata leda wadda kayan shafa ne, aciki masu yawa. Tasiyo mata.
Kuka sukeyi sosai, harseda Baba mairo itama ta tayasu, seda suka gaji sannan sukayi shiru, kufi Jalila tamika ma Baba mairo,godiya sukayi mata. Har bakin kofar dakin Baba mairo suka rakata da kyar Baba mairo taja Falak suka koma ciki ita kuma Jalila tafita tana kuka tasamu su Alh, da zarah suna jiranta awaje, dan sune zasu kaita.
Urs,
NABILA RABI,U ZANGO
( Nabeelert Lady)
08028525263
[7/13, 09:41] Nabilat Author: 🙆🏻😭😭🙆🏻 AGOLAH!!! Nah
Marubuciyar Zamani
NABILA RABI,U ZANGO
( Nabeelert Lady)
@ (H,O,N,A)
Part 75.....80
Washe gari Falak ta tashi da karfin jiki, haka tagama aikinta, sannan tashirya ta nufi kasuwa.
Yauma tana gama siyayyarta tahadu da Sameer, bayan sungaisa yajata zuwa cikin shagonsu, zama tayi kanta akasa duk kunya takeji saboda kayan dake jikinta.
Falak, taji yakirata. Amsawa tayi amma bata dago takalleshi ba, hakika naji labarinki wanda yafirgitani, gaskiya inga rayuwa, koma ince kina cikin ganinta, abinda nakeso dake ki kara hakuri abisa wanda kikeyi, babu wani rai daze rayu aduniya, face se Allah jarabceshi, da duk abinda yayi niya.
Kuma bakowane yake iya cin jarabawar da Allah yayi mashi ba seme imani. Falak akwai abinda nakeso infada maki, kuma inafatan zaki fahimceni, banaso kidauki maganar dazan fada maki kamar saboda tausayinki ne yasani fadamaki ita.
Wlh Falak tun ranar dana fara ganinki arayuwata Allah yajarabeni da sonki, ina maki son daban san irinshiba, alokacin danaji labarinki sonki da tausayinki suka kara shiga raina. Dan Allah Falak kada kice bazaki amshi roko naba, kiyi hakuri nasan natsaidaki kilama ayi maki fada, bansan inda zanganki ba, idan ba nan ba. Amma bazan matsa maki dajin amsarki yanzu ba, ga wannan wayace nasiyo maki sekirika boyeta kada akwace maki.
Ina Jalila fa? Se asannan tadago kai tana kallonshi, tace ai ta tafi A,B, U Zariya, jiya, yace tasamu admission ne? Tace e tasamu biological science suka bata. Yace yayi kyau, kema kiyi hkr insha Allah wata rana zakiyi naki kinji. Murmushi tayi tace Allah yasa. Wayar yabata da kyar ta amsa, tayi mashi godiya, sannan suka fito yarakota.
Harkusa da gidan yakaita, sannan yamika mata wata leda yace gashi tace ta meye ne, yace idan kinje kiduba zaki gani, idan kuma bakiso sekiba Baba mairo, dariya tayi tace toshikenan, nagode Allah yasaka da alkhairi, yace ameen, amma fa dakinje ki kunna wayarki nasamki ita charji, haka sukayi sallama tashige gida, sa,arta daya Zarah bata nan.
Da dare Zarah tana daki tana waya da Asabe, Baba mairo tazo domin kawo mata abincin da tace akawo mata. Harzata shiga taji Zarah yana wata magana, kara labewa tayi domin sauraron abunda take fada.
Wlh Inna Asabe sonake da inkori yarinyar nan, banaso tana zaune gidan nan wata rana Alh, ze iya ganeta, dan kinsanta dashegen tsaro da addini, kuma tanada addu,a banaso ta karya mani shirina, amma idan nakoreta tabar gidan shikenan nahuta.
Tsayawa tayi alamun sauraron Asabe, Can tace toyanzu Inna wakike ganin za,a aura mata, nifa kinsan bawani sanin yan iskan unguwar nan nayi ba, da se insamu wani yazo ni ko kudi zan iya bashi ya aureta, kona shekara daya ne bayan yagama wulakanta ta, imma da rabo yayi mata ciki sannan yakoreta, dazanfi jindadi.
Banaso yarinyar nan tabar gidan nan batare da wani mugun tabo arayuwarta ba, kibari kawai zan nemi duk dan iskan danaga yayi mun nakirashi inbashi ita kawai, damma kada yan unguwa su zargj
[7/13, 09:41] Nabilat Author: 🙆🏻😭😭🙆🏻 AGOLAH
Cigaban. Part 75..... 80. AFUWAN BANGAMA TYPING5 BA YAYI SAVING BY MISTAKE, GA CIGABAN
NAN.
Banaso yan unguwa su zargi wani abu wlh da acikin kwana 2 za,a daura masu aure yadauketa duk inda ze kaita ma yakaita. Shikenan Inna nagode, a,a wannan aiki ai base munkaima boka ba, nima zan iyayi kinsan Alh, atafin hannuna yake kome nafada mashi zeyarda. Toshikenan kibani nan da kwana 2 idan har ban samuba, zan maki magana idan yaso seki samomun anan, ti nagode, idan Jidda tadawo kigaishemun ita, nakira wayarta bata shiga.
Komawa da baya Baba mairo tayi saboda wani tashin hankali dataji yana shigarta, ta dade afalo kafin naga cikin sauri tanufi dakin Zarah, da sallama tashiga, Zarah tace shigo mairo, shigowa tayi tace Hajiya ga abincin nan, Baba mairo tafada tana goge kwalla.
Zarah tace Mairo lafiyarki kuwa naga kamar kina kuka? Kara rushewa tayi da kuka tasamu guri tazauna, tashi Zarah tayi tace dan Allah Mairo kifadamun ko wani naki ne, ya mutu? Fyace majina tayi tasa zaninta tagoge, sannan tace Hajiya da irin abunda akamun aigara ace mutuwa akayi mani zan iya hakura akan cin mutuncin da wannan yarinya tayi mani.
Ace yanzu duniya babu gaskiya, duk yanda karike mutum da gaskiya da amana shi kokari yake yaga bayanka. Wlh, danasan haka yarinyar nan take simi simi da ita da bandauki amanar da mamanta tabani ba. Amma koyanzu nafada mata najanye rike amanar da aka bani, kuma nace tafitarmun adaki bazan iya zama da ita ba.
Zarah tace aini mairo baki fadamun dawa kike ba kinzauna kina ta kuka. Dawafa nake idan ba wannan Banzar AGOLAR gidan nan ba, wlh, Hajiya kinyi gaskiya tsintartar mage bata mage, wani irin murmushin dadi Zarah tayi tace Mairo wani abu Falak tayi maki ko?
Haba Hajiya, ashe yarinyar nan yar iska ce bansani ba, shiyasa damatunda kika fara aikenta kasuwa takejin dadi,kullum bata dawowa dawuri, kuma idan tadawo sekiga tadawo da kaya masu yawa, Inazuwa bari kiga wani abu dan kada kice sharri nayi mata. Fita tayi domin dauko abun.
Wani irin tsallen murna Zarah tayi tafada bisa gado tana fadin wlh, karyarki tasha karya Hajjo kice zaki hada kanki kishi dani kizauna lafiya, nayi nasarar kaudaki keda yaronki, yanzu gashi cikin sauki diyarki zata zama karuwa. Gaskiya naji dadi da Mairo tagane gaskiya, kinga yanzu nakara samun yar uwar dazamu huro maki wuta.
Shigowa Baba mairi tayi hannunta rike da Leda, zazzageta tayi sega kayan shafa masu kyau da tsada. Zarah tace ey! Wannan kayan duk natane? Baba mairo tace sosai ma. Kuma waini ina ganin kamar na isa da ita, shine dazu nayi mata magana akan ina take samo kudi haka, se cemuntayi yawon karuwanci takeyi tana samowa kamar yanda nima nakeyi.
Wlh, hajiya kinji abinda yasani kuka wai kamar ni Falak zata kalla ta fadamun wannan maganar. Gaskiya hajiya nadawo rakiyar wannan yarinyar, gata nan duk abinda zakiyi mata kimata, babu ruwana aciki, idan ma kina da bukatar temako na domin akoreta daga gidan nan ashirye nakw da inbaki gudummuwa.
Dariya Zarah tayi, tace aini nasani Mairo, komin dadewa zakidawo gurina, domin ke renona ce, tunda nazo gidannan muka hadu dake, nasan dole kidawo gareni, nasan dama tausayine yasaki temakawa Falak, bade So ba.
Agaskiya naji dadin zuwanki adede lokacin danake neman temakon yan gari irinku, kuma maganar iskanci datakeyi wannan ita tasani, aure ma zanyi mata kowa yahuta, sede ba irin auren da kika sani ba. Anan Zarah takwashe komai tafada ma Baba mairo, sannan tace yanzu Mairo kenake ao kibani shawara ina zamu samo dan iskan dazan bashi auren Falak?
Murmushi. Baba mairo tayi tace haba Hajiya wannan aikin ai semu, kafin infara aiki agidan nan nayi sana,ar saida abinci atasha, nasan yan iskan tasha sosai, bakida damuwa, akan wannan matsalar.
Zarah tace yauwa, mairo amma naji dadi sosai, da Allah yasa kikazo awannan lokacin, yanzu yaushe yakamata ace kinkawo mani shi inganshi? Baba mairo tace kada kisamu damuwa gobe da safe zanje tasha, akwai wani mugun da shaye shaye ne dan shine ogansu atasha, babu irin aiki da baya yi, sede aikinshi kudi ne. Zarah tace karkisamu damuwa, abinda yafi wannan ma nakashe kudi akanshi, kawai kigada mashi duk abinda nake bukata, ni kuma zan damka komai agurinki, dan abanaso Alh, ya fahimci wani abu, kije kugama komai, sede zuwa jibi inason ganinshi. Baba mairo tace angama Hakiya, kada atausaya mata ko kadan, bara inje inga kota kwashe kayanta. Zarah tace a,a mairo kiyi hakuri ki kyaleta. Ai takusa barin gidan
Zaune adaki Baba mairo tasamu Falak suna waya da Sameer, zama tayi tana kallonta cike da tausayi, Baba mairo tace Falak nasan Sameer ne, idan kungama kice masa gobe yazo dasafe gurin karfe 9 yadaukeni zamuje gidansu akwai maganar dazamuyi.
Kwanciya tayi tana jiran su gama, haka sukasha fira kafin sukayi sallama, kamar kada surabu, Falak tanajin aon Sameer aranta sosai.
Baba mairo tayi dariya tace kaga masoya, amma idan nace kina sonshi sekice a,a Falak tace to nadeji yanzu ai kingane abinda muke ciki ko.
Baba mairo tace e nagane shiyasa ma nazo maki da albishir medadi, sede kuma akwai wata matsala, wadda sekinyi hakuri kafin mudace da abinda mukeso, Falak tace lafiya meyafaru kuma? Kiyi hakuri da abinda zan fada maki Falak dole ne nima tasani zabar wannan hanyar, dan ita kadai ce zata bulle mana,
Anan Baba mairo ta kwashe duk abinda taji Zarah tana fada, da kuma. Shawarar data yanke tajetasamu Zarah sukayi magana.
Kuka kawai Falak takeyi dataji irin tsanar da Zarah tayi mata, da kuma yanda Baba mairo take kokari gurin kareta aduk halin data shiga. Kwanciya tayi bisa cinyar Baba mairo tace bansan dame zan saka maki ba Baba mairo, badan keba da rayuwata tagama shiga matsala.
Bakomai Baba mairo, duk abinda kika yanke akaina yayi dede, nasan bazaki taba yimani abunda ze cutar dani ba. Baba mairo tace gobe zanje gidan au Sameer zamuyi magana da Mamanshi, da kuma shi, duk yanda mukayi zakiji. Amma dan Allah kiyi hakuri da irin yanda naci mutuncinki agurin Hajiya. Falak tace Baba mairo banaso kina bani hakuri, akan irin wannan abun, haka rayuwata take, dole se anyi irin haka inde anaso insamu abinda nakeso, babu komai, Allah yashige mana gaba kuma yabamu sa,a. Baba mairo tace ameen, haka sukayita fira, sannan suka kwanta.
Jidda ce kwance adakin Al,amin suna waya da Zarah, Jidda tace Ummi dan Allah kisan yanda zakicema Dady, banaso yakira wayata yaji bata shiga nasan yana iya zuwa zariya, nemana, kuma kinga kawata zan raka london zata hado kayan lefenta, bazamu wuce sati 2 ba.
Zarah tace waini Jidda ke haryanzu bazakiyi kokarin kawo mijin aure ba, sede kirika bin kawayenki, kina masu wahala ke kuma kin kasa fitar da gwani, gaskiya nima nafara gajiya, nima inason inga jikokina. Jidda tace haba Ummi, duka yanzu shekarata nawa dazanyi aure, kina ganin yanda mazan zamanin suke fa yanzu, dazaran sun aureka shikenan duk wata hidima dasukeyi maka awaje sundenata. Wani lokacin ma kudin siyan anko seya gagari mutum, kuma kinga ni ba karatu nayi ba, idan ban tsaya natara kudi ba, kinsan karshenta bawani me arxiki bane zezo aurena.
Nide gaskiya Ummi kibari ayanzu inasamun kudi masu yawa dazaran nagama samun kudina zanyi aure, kinga alokacin nima nazama bussiness woman ko? Zarah tayi murmushi tace yauwa Jidda ta, kokefa, aigara kema kitara kudi kozaki fara zama cikin mata masu aji, to Allah yabada sa,a Allah yasa daga can kena kisamo Alhjin, london kinga semu kaiki can kawai. Shi kuma Alh, kibarni dashi nasan yana zanyi dashi, kije kawai sekun dawo. Amma dan Allah kada kiwuce sati 2, kinsan Alh, dason ,ya,ya.
Damma nima. Bana daga mashi kafa, ai dayanzu yana takani son ranshi. Jidda tace waini Ummi ina Falak da Ameer kuwa? Zarah tadaure fuska tace meye kuma ana maganar arxiki zaki sako mana ta wasu banzaye. To Ameer yajima da mutuwa, Ita kuma Falak tana nan tazama karuwa, shiyasa zanyi mata aure kowama ya huta. Jidda bataji dadin abinda Umminta tafada ba.
Tace Ummi wazata aura? Tace dede da ita ne, zata aura, kewai yanzu bakiga yanda Falak tazama yar duniya ba, har zagin Mairo takeyi fa. Jidda tace dan taga tana da kyau ne shiyasa, ai garama kiyi mata aure kowama ya huta. Ana. Mn sukayi sallama .
Al,amin ne yashigo zama yayi yace baby wlh nagaji nasha wahala, sosai yau, garin samun visa , amma gashi anan nasamo mana, ina fatan kinga kashe boss na gidanku? Dariya tayi tace tunima, yanzu de karfe nawa jirgin zetashi? Yace karfe 7 na safe. Dariya tayi tajawoshi yafado kanta tana fadin nagode sosai my luv.
Urs,
NABILA RABI,U ZANGO
(Nabeelert Lady)
08028525263
[7/13, 09:41] Nabilat Author: 🙆🏻😭😭🙆🏻 AGOLAH!!! Nah
Marubuciyar Zamani
NABILA RABI,U ZANGO
( Naneelert Lady)
@ ( H,O,N,A)
Part 80.....85
Washe gari bayan Baba mairo tagama aikinta gurin karfe 10 kamar yanda Falak tafadama Sameer segashi yakirata yace mata yana inda yatsaya.
Sallama Baba mairo tayi mata, tawuce dakin Zarah tace Hajiya nagama zantafi, dan tunjiya nakira wata kawata damukayi aiki atasha nace mata idan Asid yazo ta tsaidamun shi. Murmushi Zarah tayi tace gaskiya nagode Mairo, Allah yasa amince da bukatarmu.
Baba mairo tace ameen, kudi har dubu 10 Zarah tabama Baba mairo tace tafara bashi kafin sauran suzo, dubu 1 tabama Baba mairo tace tahau abin hawa. Godiya tayi mata tace ta tafi.
Akusa da wani shago Baba mairo taga Sameer duk da bata sanshi ba, amma tana zuwa gurin yace Baba mairo ko? Dariya tayi tace ka canka dede, yace ai tunda kika taho jikina yabani kece. Ina kwana, tace lfiya lau, Sameer, yace muje ko, hawan mashin din tayi suka wuce.
Zaune suke abisa tabarma Sameer kuma yana zaune abisa kujera, bayan sun gama gaisawa, Baba mairo tafara magana. To Halima, nasan de bakisanni ba, amma kuma kinsami labarinmu agutin Sameer.
Bawani abu bane yakawoni se akan maganar da nasan Sameer yafada maki. Halima tace kwarai kuwa yabani labarin Falak me cike da tausayi, kuma yayi mun magana akan yana son aurenta, kuma nima nayi na,am da maganarshi.
Sede yanzu bansan wace magana zakiyi ba. Baba mairo tace hakane, kuma naji dadin yanda kika amshi maganar, babu abinda zamu ce maki sede muce Allah yabiyaki. Kamar yanda kika sani nide ban hada komai da Falak ba, Allah yahadani dasu, tunbayan da Alh, yakawosu gidan danake aiki.
Munyi zama na mutunci da Maman Falak, wadda itace takawomun yanci agidan danake aiki, ada babu wanda yakemun daukar uwa agidan, duk da na a haifena haifi ita kanta Hajiya ba ,ya,yanta ba. Amma suduka mutum 1 ce take bani girmana, wato Jalila. Zuwan Hajiya Hajjo tasakamun Baba mairo, dan ita tace bazata iya kiran sunana kaitsaye ba, hakan yasa tundaga kan Alh, har ,ya,yanshi suka koma kirana haka, sede Hajiyace kadai take kirana da mairo.
Bayan mutuwar Hajiya nacigaba da rikon yayanta,