Showing 3001 words to 6000 words out of 61588 words
Chapter 2 - AGOLA BOOK COMPLETE DOCUMENT BY Nabila Lawan Zango .txt
acikinsu.
Kuka sosai Hajjo da Falak sukeyi, Bashir ma duk dauriyar shi seda yayi kuka, sosai ya tausaya ma Hajjo, ahaka yayi ma abokinshi sallama suka juya, tunda sukaje gida yake aikin lallashin Hajjo, kuma yayi mata alkawarin bazatayi kuka dashi ba, da haka yasamu ta hakura.
Haka rayuwarsu tacigaba da tafiya, arzikin Bashir se kara habaka yakeyi, dan yanzu yadena zuwa gusau Lagos kadai yake zuwa, tunda suka Haifi Falak basu kara samun haihuwa ba, Hajjo taso suje asibiti amma Bashir yace a,a haihuwa ta Allah ce tunda sun samu daya ma ai sungode.
Falak tana ss 2 ayanzu, bangaren islamiyya kuwa gab take da saukewa
Awannan lokaci tana da shekara 16, takara zama budurwa, komai natana yafito, hakan yasa iyayenta suka kara saka matakan tsaro akanta, dan kawu yace arika bata abincinshi tana kai mashi amma Bashir yahana.
Acikin yaranshi akwai babban yaronshi me suna Idi ana kiranshi da Jungle, shine yake bama Kawu shawarar yasa su sato mashi ita yabiya bukatarshi kawai. Kawu yayi murmushi yace kabari akwai tarkon danake dana ma Bashir saboda yanzu yaga yayi iyali shiyasa yamaidani abaya, duk wasu kadarorinshi yasaka sunan yarinyar nan ajiki, ka kyaleni dashi, yacemun zeje lagos, kuma nayi mashi magana akan inason wasu kudi masu yawa, inaso yabani su sannan in aikata mashi. Dariya suka sa gaba daya.
Zaune suke adaki Bashir yace Hajjo wlh kawu ya matsamun, gani yake kamar wasu kudade gareni, shiyasa yake tambayata kudi akai akai, mika mata wasu takaddu yayi da check na banki yace wannan takaddun gidan nan ne, wannan check din kuma na bankin Falak ne, domin aciki nake ajiye duka kuda dena,inaso kiyi masu boyo sosai, dan nayi alakawrin bazan kara bama kawu kudi masu yawa ba, koda yaje yaduba account dina baze samu komai ba, dan besan da wannan account din na Falak ba, tunjiya dana dawo daga Lagos yakeson ganina ni kuma boyewa nakeyi, se dazu yamun maganar kudi nace mashi banda kudi nayi asara sosai, yanzu mota ta ma zansa kasuwa insamu inbiya mutane kudinsu.
Haka yatashi yatafi yana bambami, tashi Hajjo tayi taboye. Abinda yabata sannan tadawo kusa dashi tazauna tace Dadyn Falak hakuri zamuyi da halin kawu, ni kaina ina tsoron shi wlh, kana ganin irin yanda yake sakama Falak ido, banaso wata rana yayi mata.......... Bata karasa maganar datakeyi ba, sukaji an banko kofar dakin, wasu mutanene suka shigo , kuka Hajjo tafara tana fadin shikenan munshiga 3. Marin da,aka yimata ne yasata yin shiru, anan suka kama Bashir suka daureshi da Igiya, kukan Falak suka jiyo abakin kofa, dasuri tafada jikin ummanta tana kuka, abinda suka ganine yanasu mamaki, Kawu ne yashigo yana dariya.
Bashir yace kawu me muka yimaka arayuwa? Duk irin yanda nake yimaka biyayya amma baka gani, dariya Kawu yayi yace dama ai nafada maka, sbd haka yanzu zankashe ka kuma inmaida matarka da yarka dadirona, dan kasan tunda ka aurota nakejin kishinta, amma ka tare komai, ahaka har ta haifi yarinya me kyau, wadda naji bazan iya hakura da ita ba. Kuka sosai Bashir yakeyi sbd abinda yaji Kawu yana fada, ahankali yace kawu dan girman Allah kayi hakuri, wlh kome kakeso zanbaka kada kayimun haka, Kawu yace aikin gama ya gama, Bashir, yanzu da dukiyarka da iyalanka duk sun zama mallakina.
Zeyi magana kenan, Jungle yakwantar dashi, hanin yafiddo wuka yasa Hajjo da Falak suka matsa kusa,da kawu suka kama kafarshi suna kuka suna rokonshi, karar dasukaji ne yasasu juyawa. Kwance suka ga Bashir cikin jini Jungle yayi mashi yankan rago.
Anan take Hajjo tafadi kasa asume. Kanta Falak tayi tana kuka,
Anan kawu yasa su Jungle, suka dauki gawar Bashir yace suje can cikin daji su gina rami su rufeshi, bayaso subarshi batare da sunrufe shiba.
Bayan awa 2 su Jungle suka dawo, afalo suka iske Hajjo da Falak adaure se kuka sukeyi, anan kawu yace masu suje su kwaso mashi kayanshi su dawo mashi dasu nan, yace kasan yanzu nine megida, anan zan zauna har Hajjo tagama iddarta sannan na aureta, ita kuma Falak sa daka zanyi da ita. Dariya suka sa gaba daya, Jungle yace Oga tunda kadauki uwar dani kabama diyar ai.
Hade fuska kawu yayi yace banaso kana kawomun wasa acikin iyalina. Dariya suka kara sawa. Kawu yace jungle gobe kaje gurin malamin can katambayomunshi Shekara nawa macen da mijinta ya mutu takeyi kafin takara wani auren.
Dariya jungle yayi yace haba Oga ai sekasa ayi mana dariya kamata inje ina tambayar yanda ake idda, kasanfa nima nayi islamiya. Kawu yace yauwa, shikenan ma, fada mana muji, dan data gama zamuyi aure, kasan komai inaso inyishi yanda Allah yace kada inyi aure akan aure.
[7/6, 1:17 PM] YAYA HAYAT: 🙆🏻😭😭🙆🏻 AGOLAH!!! Nah
Marubuciyar Zamani
NABILA RABI,U ZANGO
(Nabeelert Lady)
@ ( H,O,N,A)
Part 15.....20
Dariya sauran sukayi, kowa yana sauraron abinda Jungle zece, Hajjo ta kalli Falak wadda idanuwanta harsun kumbura saboda kuka, kai ta girgiza hawaye suna kara zubo mata a idonta, jin irin rashin mutuncin da Kawu kemasu.
Jungle yace ai Oga bata wuce shekara 1. Murmushin jin dadi kawu yayi yace haka nakeson tafiya damasu ilimi, ina ganin idan zamuyi aure kaine waliyina.
Kallon Hajjo kawu yayi yace daga ranar dakika gama iddarki aranar zaki zama matata, kuma inaso kije kidauko mun takaddun gidan nan, idan bahaka ba wlh agabanki zan keta mutuncin diyarki. Dasauri Hajjo tace wlh zan dauko maka akwanceni dan Allah kada kataba mun Falak. Kome zakamun inde bazaka taba Falak ba, nayarda. Sawa yayi aka kwanceta ta tashi tanufi dakin Bashir tana waigen Falak.
Check din daya bata tafitar tadauko wata karamar jaka wadda tasa awarwaron Falak aciki tasaka check din sannan tadaura ta akugunta tayi saurin fitowa, tana zuwa tabashi, amsa yayi yana murmushi, yace saura kudi, tace kawu kasan Bashir beda kudi, dazu yake cemun zesayar da motarshi ma, kawu yace anyi haka, Jungle daga yau munyi mota.
Tashi yayi yacema su jungle zaku iya komawa gidana nabaku, nikuma ina nan, ke Hajjo keda diyarki ku koma dakin ki dazama ni kuma zankoma dakin Bashir, Sawa yayi aka kwancesu, yace wlh duk ranar da kikayi kokarin guduwa sena kasheki diyarki kuma tazama tawa, ke babu ba hanyar tazaki fita sbd zansa tsaro me kyau. Garama kun kwantar da hankalinku munyi rayuwar jin dadi. Tashi yayi ya sallami yaranshi shi kuma yawuce dakinshi domin kusan karfe 3 saura. Haka su Hajjo suka koma dakinta suna kuka, Falak tace shikenan yanzu umma haka zamuyi ta zama kawu yaci bulus kenan? Hajjo tace inaso kada ki daga hankalinki muyi hakuri komai yayi farko zeyi karshe, insha Allahu bazamu dawwama ahaka ba. Tashi tayi ta dauko duk wasu takaddun Falak da zinaranta dana Falak taciro jakarta tasakasu ciki ta maidasu akugunta . Falak tace Umma meyasa kika dauresu anan? Tace insha Allahu zamu fita daga gidan nan, koni banfita ba, ke zaki fita, nasan wadan nan kayan zasuyi maki amfani. Falak tace Umma kidena fadar haka, idan har kina gidan nan to tare zamu zauna , tashi sukayi suka dauro alwala suka fara nafila.
Haka rayuwarsu tacigaba da tafiya, kullum Hajjo ita da Falak zasuyima kattin Allah girki, Hajjo tahana Falak zuwa makaranta, sbd harin da yaran kawu suka taba kawo mata ranar data dawo islamiyya.
Kullum kawu cikin kirga watanni yake, alokacin har Hajjo tagama iddarta besani ba, danshi kirgen shekara yakeyi, ita kuma taki tafada mashi, ko dan kunne daki sakawa dan bataso yagane ta. Kullum cikin tunanin hanyar dazasu gudu take, amma ina, kawu yasamasu matakan tsaro.
Aranar da Bashir yacika wata 5 da mutuwa, aranar su kawu suka fita wani aiki da dare,suka bar mutum daya domin yayi gadinsu Hajjo, Jungle yace Oga kana ganin babu matsala abar mutum daya? Kawu yace ayanzu Hajjo ta hakura dazaman gidan nan, tasan idan ta tafima bata da gurin zuwa, kada kadamu muje kawai.
Bayan tafiyarsu da awa1 Hajjo taleka, murnace takamata ganin megadin yana bacci, komawa tayi tadauko wani karfe, tazo kusa dashi, tadaga karfen ta kwada mashi akai, nan take yayi kara yafadi asume, komawa tayi tacema Falak tadauko hijabinta takama mata hannunta suka fita suka fara gudu.
Alokacin dasu kawu suka dawo asume suka samu megdin, cikin sauri yashiga vikin gidan, babu inda be duba ba, amma begansu ba, fusace yafito alokacin har megadi yasha ruwa ya farfado, shakoshi kawu yayi yace suna ina? Megadi yana zare ido yace wlh nima ina. Kwance naji saukar wani karfe bankara sanin inda kaina yake ba, se yanzu. Kawu yace kufita nasan duk inda suke basuyi nisa ba, ku kamomunsu.
Gaji labarina Alhaji, kuma ina me tabbatar maka babu karya ko daya acikin labarin dana baka, idan har karya nake maka kada Allah yamun......saurin rufe. Mata baki yayi, yana me girgiza mata kai, shikanshi wahaye ne suke fita acikin idonshi.
Hannunshi yacire yace wlh Hajjo nayarda dake dari bisa dari, bakiyi kama da marar gaskiya ba. Hakika labarinki abune me girgizawa, dole duk wani me imani ya tausaya maku, lallai kunga rayuwa wadda ba duka mutum bane ze iya daukar kaddarar da Allah yadora maku.
Nayi alakwarin rikeku bisa gaskiya da amana. Hajjo inason infada maki wata magana sede ina tsoron kimun wata fassara, ko kuma kice sbd na temakeku ne yasa zance haka. Hajjo ta goge idonta tace wlh babu abinda zaka nema agurina bnyi maka shiba, kafadi abinda ke ranka.
Shiru yayi sannan yadago kai yana kallonta yace Hajjo bazan iya boye maki ba, agaskiya tun bayan mushigo gidan nan nadora idona akanki Allah yasakamun sonki araina. Idan harzaki amince dani ashirye nake dana aureki kuma inrike Falak tamkar diyata. Matata daya Zarah da yarana 2 mata, Jidda da Jalila, inaganin Jalila zasuzo sa,anni da Falak.
Murmushi takeyi kanta akasa haryagama bayaninshi. Yace Hajjo kinyi shiru bakice komai ba, kada kidamu idan har bakida ra,ayin aure yanzu na amince zan zamo yayanki kuma mahaifin Falak wlh babu damuwa. Kai tadago tace bakomai Alhaji inaso kabari zuwa gobe zanyi shawara da Falak. Murmushi yayi yace badamuwa Allah yakaimu goben, kije ki kwanta dare yayi natsareki nikam yau babu barci, tace sbd mene? Yace yau kam ai buzu zan hau naneman sa,ar gobe. Dariya tayi tashige daki. Murmushi yayi yakwanta bisa kujera, hakanan yakejin wani farin ciki yana shigarshi , godiya kawai yakema Allah daya bashi ikon temakonsu Hajjo.
Washe gari dasafe bayan sunyi sallah sukayi wanka, anan Hajjo takalli Falak tafadi mata duk yanda sukayi da Alhajin daya temakesu, Murmushi Falak tayi tace wlh Umma ki amince mashi, kinga zamuyi nesa dasu kawu, bazasu taba tsammanin muna kaduna ba, kinga hankalinmu ze kwanta sosai. Hajjo tace Falak amma fa yana da mata hada yara 2, ina tsoron tashin hankali. Falak tace Umma kowafa da halinshi ze zauna, mude muyi kokarin zama da duk wanda Allah yahadamu zama dashi tsakanin mu da Allah. Hajjo tace hakane, Allah yazaba mana abunda yafi zama alkhairi.
Fita sukayi afalo suka sami Alh. Har yadawo daga cikin gari yakawo masu abin karyawa. Bayan sungaisa Alh, yamika masu abincinsu shima yaja nashi suka faraci. Falak tafara tashi takoma daki, kamar jira yakeyi yasauko kasa yace Hajjo wlh banyi bacci ba jiya amsarki kawai nake jira. Fuskarta ta rufe da hijabinta tana murmushi, yace kin amince? Kai tadaga mashi, godiya sosai yayi mata, yace sufito sukama hanya.
Zarah ce take tafaman gyara gida sbd megidanta zedawo, Jalila da me aikinsu Mairo suna kitchen suna hadamasu abinci. Jidda kuma tana dakinsu tana wanke bandakunan gida. Misalin karfe 2 na rana kowa yashirya suna jiran zuwan Alhaji. Jidda tace wlh nakosa Dady yadawo nasan zemana tsaraba sosai. Zarah tayi murmushi tace ai kunsan kowace tafiya idan Alhaji yayi tsarabata tafi takowa girma. Jalila tace kai Umma yaude tamu setafi taki tsoka, dariya suka dukansu, anan sukaji karar bude gate, da gudu suka fita domin taroshi, Zarah tashige daki domin kara gyarawa.
Mamakine yakamasu ganin Dadynsu dawasu mata, hakade suka yimashi sannu dazuwa suna kallonsu Falak, Jidda aranta tace kai ammade wadannan sunada kyau, tsayawa sukayi domin karbo tsaraba. Se sannan Alh. Yatuna bema yimasu tsaraba ba sbd tsabar farincikin amincewar Hajjo. Alh, yace mushiga cike yau babu tsarabar ci sede ta mutane, ciki suka wuce kowa da irin abinda yake rayawa aranshi.
Urs,
NABILA RABI,U ZANGO
( Nabeelert Lady)
08028525263
[7/7, 9:54 AM] 🙆🏻😭😭🙆🏻 AGOLAH!!! Nah
Marubuciyar Zamani
NABILA RABI,U ZANGO
( Nabeelert Lady)
@ ( H,O,N,A)
Part 20.....25
Da sallama suka shiga cikin gidan, cike dasauri Zarah tafito tayi kyau se kamshi takeyi zuwa tayi ta rungume megidanta tana dariya, shima dariyar yakeyi.
Janshi tayi zuwa daki, su Hajjo suna tsaye bakin kofa, Jalila ce tajasu zuwa wani daki, bandaki ta nuna masu sannan tashimfida masu abun sallah tafita domin kawo masu abinci da ruwa, bayan sunyi sallah sukaci abincin da Jalila takawo masu.
Atare suka fito bayan yayi wanka, yafito cin abinci, zuba mashi tafarayi, saurin tashi yayi yana kiran Jidda da Jalila, bayan sunzo yace ina bakin da mukazo tare? Jalila tace suna dakin baki sunyi sallah suna cin abinci, ajiyar zuciya yayi yace yau Jalila nagode.
Ya mutsa fuska Zarah tayi tace Alh, wane irin baki ne suka shigomun gida bansan da zuwansu ba, zama yayi yafara cin abincin shi yana murmushi. Zamatayi kamar zatayi kuka tace ina magana amma kayi shiru, haba hajiya, ai komenene kinbari ingama cin abinci ko.
Zaune suke afalo suduka, ayayin da su Hajjo suke zaune kasa. Zarah se cika take tana batsewa, Hajjo duk jikinta yafara sanyi ganin irin kallon da Zarah take yimasu, ko gaisuwarsu da kyar ta amsa, dama Zarah batason mutane, bare kuma dataga kyawawan mutane suzo tare da mijinta.
Gyaran murya Alh, yayi anan yayi masu bayani akan su Hajjo, har labarinsu seda yabasu. Jalila se kuka takeyi, gaba daya tausayinsu yakamata. Jidda da Zarah kuwa yatsuna fuska sukayi, zuciyar Zarah kamar zata fashe dan haushi.
Alh, yace sbd haka nakawosu gidan nan inafatan kuma zaku rikesu tamkar yan uwanku.... Zarah tace dan Allah Alh, dakata, kayi mani bayani yanda zanfahimta, idan ma masu aiki ne ka kawomun ni banida bukatarsu, inada me aiki, dan gaskiya wadan nan sadakar yallan bazasu zauna mun agida ba, idan ma temakonsu zakayi kabasu kudi sukama gabansu.
Murmushi Alh, yayi yace Zarah ai baki tsaya kika gama jin abinda zance ba ko, kinrufeni da fada kamar kinsami wata Jidda ko Jalila, kuma dan rashin mutunci agaban mutane zaki rufe ido kina fadamun abinda kikaga dama.
Ina fatan acikin bayani na danayi bakiji nace zan ajesu agidanki ba. Agidana nace zan ajesu ko? Dan haka ki kula da kalamanki. Kuma wannan dakike gani Hajjo, insha Allahu cikin satin nan za,a daura mana aure, Falak kuma zanriketa kamar yanda zanrike Jalila ko Jidda.
Bana son inkara jin wata magana kuma Jidda ku kiyaye, dan haka wancen part din acan zasu zauna, bance ku hada girki ba, kowa nashi zeyi, abinda nakeso asamu zaman lafiya acikin gidana, kinfi kowa sanin halina banason tashin hankali ahakan yasa bamu taba samun sabani nida ke ba, seyanzu. Dan haka ki kiyaye.
Jalila ga key din wancan part din nan zanyi magana da megadi kuje keda Mairo ku tsaya ya gyara idan nafita zansa akawo kaya azuba aciki dan yau nakeso su koma.
Murmushi tayi tace angama Dady, tashi yayi yace Hajjo kutaso muje. Fita sukayi suka shiga mota. Kasuwa yanufa dasu.
Wasu irin zafafan hawaye ne suke zarya afuskar Zarah, tunda take da Alh, betaba yimata koda tsawa bace bare fada. Amma yau gashi sbd wasu banzaye yana fadi mata maganganu. Jidda tamatso kusa da ita tace haba Ummi meyasa sbd wannan maganar zaki daga hankalinki, tunda nataso agidan nan bantaba ganin kukanki ba seyau, tayama za,ayi inso wadan nan mutanen masu kama da aljanu.
Wlh Ummi kinfi karfin yin kishi da fillo, ki kyalesu zaman gidan nan seya gagaresu, naso ace acikin part dimmu zasu zauna wlh damun samu. Masu aiki, amma bakomai idan sunsan wata basusan wata ba.
Jalila tace haba Yaya Jidda, da bakinki kike fadin wannan maganar, kada kimanta fa suma mutane ne kamar kowa, kuma ko ba komai duk abinda Dady yakawo gidan nan ai yakamata mudaukeshi da daraja, kuma ai...... saukar marin dataji ne yahanata karasa maganar datakeyi.
Zarah tace dama batun yauba nasan bakida kishi akaina, nadauka kune masu goyamun baya aduk halin danake ciki, amma segashi dabakinki kike fadin wannan maganar. Wlh idan kinaso mushirya kifita aharkar wadannan mutanen, idan bahaka ba, kuma zamusa kafar wando daya dake. Tashi tayi tashige daki taci gaba da kuka, aduniya babu abinda ta tsana kamar kishiya, seyanzu take ganin wautar ta narashin mallake Alh, tuntuni ta biyema shawarar Karima, gashi nan duk irin kissar datakeyi mashi be hanata yimata kishiya ba. Lallai wannan tafiya ni akaimawa, kuma nasamu tsaraba me tsoka. Amma wlh duk yanda zanyi matar nan bazata dade agidana ba.
Kafin sudawo har angama gyaran part dinsu, masu kaya sunkawo ansaka aciki, komai yayi dede tun daga labule , kujeru, gadaje da kayan kitchen babu abinda ba,a saba, dakin Falak kadai ya isa ya burgeku, komai na bukata seda aka saka aciki sannan driver yashigo da kayan abinci yasaka a store ya kulle gidan, yatafi.
Se yamma suka gama siyayya lefe sosai yahada mata. Itama Falak babu abinda be saya mata ba, Hajjo har kuka tayi sbd murna, gidan abokinshi yawuce dasu, anan yayi mashi bayanin komai, matarshi Zainab mace me kirki ta tausaya masu sosai. Alh, yace inaso kuje muje gurin telanki domin abashi dinku nansu dan dawuri nakesonsu.
Farouk yace bakomai Dauko hijabinki muje nima inyi rakiya, abokina kace nanda kwana 5 zaka angwance, lallai wannan tafiya tayi riba.
Seda ya gwadasu sannan Alh, yabashi kudin dinkinshi yace nan da kwana 2 azo akarbi kala 5 na amarya kala 3 na Falak zeyi kokarin kara wasu kafin biki, idan yaso sauran zuwa bayan biki se azo akarba. Godiya