Showing 33001 words to 36000 words out of 61588 words
Chapter 12 - AGOLA BOOK COMPLETE DOCUMENT BY Nabila Lawan Zango .txt
basuda irin shagon saida kayayyaki haka.
Baba mairo da Umman Sameer hankalinsu kwance suke sana,arsu cike da girmama juna, dan Baba mairo ta girmi Halima sosai, dan ita Halima bawani tsufa tayi ba, kawai de halin rayuwa ne yamaidata babba, amma yanzu da kwanciyar hankali tafara zuwa masu tuni tafara maida jikinta. Duk wata shawara dazasuyi Baba mairo suke kawo ma ita, idan kuma abun yafi karfinsu, Kawun Sameer suke kaima ita.
Zarah ce zaune adakin Asabe, bayan sungama gaisawa, tace waini Inna haryanzu shiru babu Jidda, nifa hankalina yafara tashi, kawai ina cikin kwanciyar hankali yarinyar nan zata sani cikin damuwa, aduniyar nan babu abinda ke damuna se rashin sanin inda Jidda take, tun Alh, yana tambayata ina mashi karya har nafara gajiya.
Jiya yake cemun zezo har nan yatafi da ita, kuma idan har bata fitar da mijin aure ba, duk wanda yasamu zebama ita. Shine nazo dan Allah kirakani gurin boka yaduba mun inda take, kotana raye, kuma arufema Alh, baki yadena maganarta, kota dawo kada yatambayeta inda taje.
Asabe tace gaskiya ni kaina abun yana damuna, kuma kinga idan haryagane bata gidan nan muze zarga, gara muje arufe mashi baki kawai. Ita kuma nasan duk inda take zata dawo. Malam dayake bakin kofa yana jinsu yashigo, ya kalli, Asabe, duk da yanajin tsoronta, amm wannan karon seda yayi magana.
Yanzu ke Asabe kina ganin abinda kikesa yarinyar nan tanayi dede ne? Na dade ina jin duk wani abu da kukeyi akan bawan Allan nan, wai seyaushe zaku tuba kudena abinda kukeyi? Kadafa ku manta akwai wata rayuwa bayan an mutu, kum kowa ze tsaya agaban Allah yafadi abinda yayi, wanda aranar baki baze iya magana ba, saboda shima makaryaci ne. Ke kuma Zarah abinda nakeso dake kiji tsoron Allah, kina ganide tun aduniya yafara nuna maki ishara, akan diyarki, yanzu Allah kadai yasan inda take, kuma duk inda take, ba halin kwarai take aikatawa ba.
Nasha ganinta da manyan mutane suna sauketa kofar gidan nan, amma dayake baku daukeni abakin komai ba, bakwajin maganata, yaude nafada maku iya gaskiyata, idan harkunji to, idan kuma bakuji ba, wlh inaji maku tsoron ranar danasani, ranar da babu lokacin gyara barnar da kukayi.
Zarah ta zunburo baki tace wai kai Baba mekaga munyi? Nifa wlh banason takura, dama naga duk sanda nazo gidan nan labe kake mana, kuma kana nufin Inna Asabe ita zata cuceni ne, ko gorin haihuwa zaka mata? Kuma ni nasan babu abinda Jiddata take aikatawa se alheri, kawai de kanamun bakin cikin yanda na auri me kudi, itama tasamu. Kuma mekaji munce zamuyima Alh?
Inna Asabe tace ai gara ke dayake diyarshi ce kifada mashi, wato Malam yanzu duk irin rikon danayima Zarah beyi maka ba? Lallai nayarda da,akace namiji ba dan goyo bane, to ai kadeji da kunnanka, abinda diyar taka tace. Kuma wlh wannan shine karo na karshe da zakaji muna magana kashigo kasa mana baki. Wuce kabani guri, namiji da akai kana halin mata. Allah yabaki hakuri ammade Zarah kiji tsoron duniya, kuma ni kike fadama magana. Kije duniyace ta isheki komai, wanda bezo bama jiranshi takeyi.
Dallan can kawuce kabamu guri, fita yayi yana matsar kwalla, wai yau diyar daya haiface take fadamashi magana. Asabe tace aikinyi mun dede, maza zuma ne, dole seda wuta. Shiyasa nace kada ki saurarama mijinki, kina ganinde duk irin biyayyar danakema Babanki amma yau yayimun gori. Kukan munafurci tasa, anan Zarah tashiga bata hakuri. Asabe tace tashi muje inrakaki dan Dije bata nan tayi tafiya. Tashi sukayi suka wuce gurin boka.
Tundaga ranar da Zarah tasama Alh, magani a abinci bekara maganar Jidda ba, shiyasa hankalin Zarah yadan kwanta, duk itama bata bacci sosai, dan tanason Jidda, tamafi sonta akan Jalila, dan halinsu daya da Jidda. Saukinta daya boka yace mata Jidda tana raye kuma yakusa dawowa gida.
Yau Jalila tagama final exam dinta, kuma ayau tagama shirya kayanta domin tafiya gida, driver take jira. Yana zuwa yadauketa, seda tafara biyawa cikin kasuwa inda kakansu yake. Dan ita bata zuwa gidansu, kwata kwata jininta be hadu dana Asabe ba, shiyasa tunda tafara karatu so 1 taje gidan.
Abakin shagon dayake zama tasameshi, tasowa yayi yana fara,a ganin Jalila, dan yana sonta sosai, tana temaka mashi, da yan kudi duk sadda tazo gurinshi, har bakin motar yakaraso, bayan motar yashig, bayan sungaisa da driver, Jalila tace ma driver yadan jirasu awaje. Gaisawa sukayi take fada mashi batun tafiyarta yau, dan tagama karatu, sosai yayi mata murna, sede beji dadin tafiyar taba zedena ganinta, dan itace abokiyar shawararshi. Jalila tace ai kaka kona tafi zanrika zuwa, kuma baga waya nan nabaka ba, zamu rika gaisawa, idan akwai wani abu seka fadamun tanan, idan yakama inzo senazo, ai babu nisa daga Kaduna zuwa Zariya.
Goge kwallan data zubo mashi yayi, Jalila tace kaka akwai abunda ke damunka, bantaba ganinka cikin damuwa haka ba. Murmushi yayi yace Jalila akwai abunda kedamuna sosai ma, kuma akan mahaifinki ne, da kuma Zarah,,,,,,,, anan yafada mata duk irin firar dayaji su Asabe sunayi da irin cin mutuncin da Zarah tayi mashi.
Seda Jalila tayi kuka, jin irin abinda Umminta keyi, hakuri tayi ta bashi, tace Kaka nima nasan akwai abubuwa da dama wanda Ummi takeyi, kuma bakowa bane yake zugata se su Inna Asabe da Dije. Amma Ummi tayi mani kashedi babba akan idan taji ina shiga maganar da babu ruwana aciki, har cewa tayi zata tsinemun, hakan yasa ma tunda nataho karatu ban koma gida ba, Dady ne kuma yanazuwa muna gaisawa.
Addu,a kawai nake masu, amma Kaka yaya Jidda tayi nisa batajin kira sede addu,a. Yace kikara hakuri insha Allah wata rana gaskiya zata fito, mucigaba dayi masu addu,a, kuma kamar yanda Zarah tafada maki, banason kishiga abinda babu ruwanki. Allah yayi maki albarka, kuma dan Allah Jalila kinga kingama karatu, kada kitsaya ruwan ido, kifitar da miji kiyi aure, banason zamanki agidan nan, kinga Falak tayi aurenta tahuta,kema Allaj yabaki miji nagari. Haka sukayi sallama takawo kudi tabashi, suka tafi.
Ayau Al,amin suka shirya yanda zasu dauko Jidda, Daniel yace kabari zan shiga gidan tunda yau munci sa,a shidaya yadawo, zanje muyi fira, zan bashi wiky nahada mashi da maganin bacci, dayayi zankiraka seka taho. Al,amin yace to amma megadin gidanfa? Daniel yace kabari nasan yanda zanyi dashi, kaide kazama cikin shiri, kadauki visa dinku da kayanka, nayima me taxi magana yanzu zezo yajiraka kuna fitowa kushiga yawuce daku. Godiya sosai Al,amin yayi mashi kuma yayi mashi alkawarin idan yasamu dama zezo surika gaisawa.
Zaune ya iske Joseph afalo yana kallo, bayan sungaisa Daniel yace joseph kaboye yanzu kaja kaya ko. Murmushi Joseph yayi yace haba ogana kaine bana ganinka, ya labari? Daniel yace lafiya lau, wata sabuwar whisky nakawo maka jiya wani abokina yabani ita, amma kasan bana shan irinta, shine nakawo maka. Katabar kwalbar Joseph yayi yace wow amma nagode, budewa yayi yafara sha, Daniel yace yauwa bama gateman dinka yasiyomun, irin whisky danake sha acan bakin titi.
Karbar kudin joseph yayi yafita yana tangadi yafita, bayan ya aiki megadi yadawo yacigaba da shan whisky dinshi suna fira, cikin lokaci kadan yafada bisa kujera bacci yadaukeshi.
Cikin sauri Daniel yadaukeshi yakaishi daki, yakira Al,amin. Jidda tana kwance adaki tasha giya da kwaya summata yawa tana bacci, Al,amin be tsaya bata lokaci ba yadauketa daga ita se riga da dogon wondo, kanta babu dankwali yasha tsohon kitson attache, fita sukayi ko tsyawa daukar jakarta beyi ba, ga uban kudin da Jidda ta tara aciki haka yabarsu suka fita, me taxi suka samu dan nan suka shige yadaga ma Daniel hannu suka nufi air pot, shima Daniel yafita. Tun acikin mota Al,amin yaciro jallabiyar daya siyowama Jidda yasa mata, yakama gyalen yadaura mata, sede duk abinda akeyi bacci take.
Suna zuwa ya sallami me mota suka jira aka kira sunansu yakamata suka shiga, ko acikin jirgin kwantar da ita yayi bisa cinyarshi tacigaba da baccinta. Suna isa yayima wani abokinshi waya yazo yadaukesu suka nufi gidanshi.
Ayau su Falak suka tare. Asabon gidansu daya keru, yayi kyau sosai, duk da bawani ginin karya akayi ba, amma yayi kyau, duk wanda yashiga ciki seya burgeshi, anzuba kaya masu kyau, dakin Falak yasha kaya masu kyau, kitchen dinta kamar nawata diyar me kudi.
Kwance Falak take akan cinyar Sameer suna fira, wayarta ce tayi kara, dauka tayi tace habawa Jalila nikam nayi fushi, yau satinki nawa da dawowa, amma kinkasa zuwa kiganni. Jalila tace dan Allah kiyi hakuri wlh banaso Ummi tasan gidanki zanzo, amma yanzu kiran danayi maki ma kwatancen gidan nakeso kimun ganinan ina shiryawa.
Falak tace to Allah yasoki, bara inturo maki da address din yanzu. Jalila tace Allah sa de mijinki baya nan dan wlh tsoran masu shaye shaye nake. Dariya Falak tayi tace ai babu abinda zemaki, kuma bayama nan, Jalila tace Allah Falak dande kinmatsamun inzo banason zuwa inga halin dakike ciki. Falak tace nide banason wani dogon surutu sekinzo. Kashe wayar tayi tana dariya, ta tura mata da address din.
Sameer yace keda Jalila ne hala? Tace emana, kasan metace, yace a,a wai cewa tayi Allah sa baka nan tsoron yan shaye shaye take. Dariya yayi yace ai zanso inga irin mamakin da Jalila zatayi idan tagammu amatsayin ma,aurata.
Au, kinga namanta tundazu inaso infada maki, dana fita shago nahadu dawani babban abokina Saleem, tare mukayi Zariya dashi amma shi yasamu aiki, awani kamfani na babanshi. Dama kuma bussiness yakaranta, nikuma nayi Pharmacy. Yarigani gamawa da shekara 1 danmu shekara 5 ne sukuma 4.
Bayan mungaisa yake tambayata menakeyi anan, nace mashi ai shago nane, shine yace meyasa ban bude chemist ba, natsaya bude shago, shine nace mashi kasan bude chemist ba sauki bane dole sekana da hanya shiyasa kawai na bude plaza.
Yace mun bana aiki ne, nace mashi wlh na nema harnagaji bansamuba, shiyasa kawai na hakura. Shine yace anjima da dare zezo yasameni ashago muzo nan gida ze amshi takarduna ya bama babanshi yanemamun aiki, kinsan babanshi babbane dan a Abuja ma yake aiki.
Falak tace kai amma gaskiya naji dadi sosai. Allah yasa asamu, yace Ameen. Tace bara intashi inshiryama Jalila abinci kafin tazo, yace to nide ina daki bacci zanyi idan tazo kitadani.
Jalila tafito cikin shirinta tace ma Zarah Ummi nagama shiryawa, zantafi. Zarah tace kijira driver yazo ya kaiki mana, yanzu zedawo. Jalila tace a,a Ummi kawai kibarshi zantafi sauri nakeyi kuma kawata tana tajirana. Kudi tamika mata tace gashi nan sarkin sauri, kigaisheta, amma kada kiyi dare fa. Tace to Ummi nagode.
Fita tayi tahau taxi tayi mashi kwatancen inda ze kaita, yace yagane gurin. Tafiya suke tana tunanin halin dazata iske Falak aciki. Dede wani hadaddan gida suka tsaya yace mata hajiya mun iso seki kirata kiji wane gidanne aciki. Jalila tace malam anya nanne unguwar kuwa, nifa duk cikin gidajen nan babu wanda yayi kama da irin gidan da,aka cemun Falak tana ciki. Yace tonide sauka kibani kudina ki kirata mana idan bata fitoba seki nemi wani ko. Sauka tayi tabashi kudinshi taciro wayarta takira Falak.
Urs,
NABILA RABI,U ZANGO
(Nabeelert Lady)
08028525263
[7/15, 10:26] Nabilat Author: 🙆🏻😭😭🙆🏻 AGOLAH !!!Nah
Marubuciyar Zamani
NABILA RABI,U ZANGO
(Nabeelert Lady)
@(H,O,N,A)
Part 110..... 115
Cike datashin hankali Zarah tace Asid yaushe ka koma haka? Dama ba dan iska bane kai? Meyasa Mairo ta munafunceni? Zubewa kasa tayi tana kuka, Murmushin mugunta Asabe tayi, sannan tadauki kayanta tace tofa, Allah ya kyauta, nizan wuce hajiya kada dare yayi mun.
Saurin kamota Zarah tayi tace haba Inna kibari ki kwana mana, ai yanzu yamma tayi. Komawa tayi tazauna tana dariya aciki ciki, Sameer yace Ummi kiyi hakuri Baba mairo bata munafunceki ba, tayi abunda yadace ne, domin kinkasa rike marainiyar Allah shiyasa tayi kokarin kubutar da ita daga sharrinki.
Anan Sameer yafadama Zarah komai, kuka kawai takeyi. Falak tace Ummi dady bayanan ne? Dadyn Ubanki, ke awa dazaki tambayeshi? To wlh tunkafin inkirga 3 kubacemun daga gidan nan, cuta ce kun cuceni, bakomai amma wlh duk ranar da kika bari kafarki takara taka gidan nan sede adau gawarki.
Kuma duk ranar dakika zo neman mijina Allah ya isa, dan idan har ina raye bazan barki ki kara hada ido dashi ba. Kutashi kubarmun gidana, kai kuma nabaka daga yau zuwa gobe kamaidomun kudina dakasan nabaka, idan bahaka ba, wlh kotu zata rabamu.
Murmushi Sameer yayi yace haba Ummi meyayi zafi haka? Ni dama can bantaba kashe ko kwandalarki ba, wata jaka yadauko agefenshi yamika mata yace wannan kudinki ne, tundaga dubu 10 da kika fara bama Baba mairo har kudin sadakin da kika bani, babu kwabonki dayayi ciwo. Hannun Falak yakama wadda take ta kuka, suka fita, abakin kofar falon suka hadu da Jidda wadda tundazu take tsaye tana sauraronsu.
Da kallo tabisu harsuka wuce, mamaki kawai takeyi wai Falak ce da mijinta, harma ga alamar ciki ajikinta. Baki ta tabe takalli Umminsu datake ta kuka ta kalli jakar kudin dake gabanta tayi murmushi tajuya tayi waje.
Asabe tace hajiya kitashi mukoma daki kada Alh yazo ya iske ki haka, muje inada mafita cikin sauki. Jakar kudin tadauka suka wuce daki. Seda Zarah tagama kirga kudin tsaf taga sun cika, sannan tasakasu cikin drawer tadawo tazauna.
Inna kenake saurare, banida sauran wata dabara, dolene muje gurin boka babu bata lokaci kashe Falak zanyi, shi kuma mijinta da Mairo wlh bazan kyalesu ba, tunda suka munafunceni, haba dama biri yayi kama da mutum.
Nayi mamakin yanda Mairo tayi saurin canzawa daga son datakema Falak zuwa tsana, duk yanda akayi aranar da mukayi waya dake aranar taji duk wani plan dina, saboda inagama wayar babu dadewa tashigo tana kukan munafurci. Kuma gashi bayan bikin Falak babu dadewa itama tace zataje ganin gida, gashi haryanzu bata dawoba.
Asabe tayi dariya tace aini dama nayi zargin wani abu agame da Mairo, kawaide nayi shirune. Toyanzu duk ki kyale wannan maganar, akwai mafita sede tana da wahala, na manta danazo ban fada maki ba, Boka ya mutu.... zunbur Zarah tayi ta mike taname dafe kirjinta, tace nashiga 3 ni Zarah, boka yazakamun haka seda bukatar nemanka tayi sannan zaka mutu.
Asabe tace kwantar da hankalinki wannan badamuwa bace, duka shekaranjiya Dije tadawo daga tafiyar danace maki tayi, dama ban fada maki bane, kasar yarbawa taje wata mata ta aiketa gurin wani babban boka, domin bakaramin hatsabibi bane, yashafe bokan dakika sani, dan aikinshi alokacin dakika fadi bukatarki alokacin take biya, kuma shi aikinshi beda makari.
Sede bakananan mutane yakema aiki ba, daga matan gwabnoni shugaban kasa, sarakuna se manyan yan kasuwa da yan siyasa, sabida aikinshi ba dubunnai yake amsa ba, miliyoyi ne. Ko Dije Matar sarkin Zariya ce ta aiketa.
Zarah tazauna tace yauwa Inna wlh harnaji dadi, yanzu yaushe za,aje? Asabe tace kina ganin zaki iya harka dashi, kinsan fa bawasu kudi gareki ba, kada yayi maki aiki ki kasa biyanshi aiki yadawo kanki.
Zarah tace wlh Inna kozanyi yawo tsirara bazan bari Falak tacigaba da rayuwar jindadi aduniya ba,( wa iyazubillah). Zankashe konawa ne domin ganin burina yacika akanta, kuma aikin ba ita kadai za,ayi mawa ba, hada Alh, inaso ta karbomun maganin mallakar zuciya tayanda beda makari, kuma bazanji shayin suhadu da ita ba.
Asabe tace kinga kudi sunkaru tunda aikin mutum 2 ne, kawai hotonsu zaki bada atafi dashi sekuma kudi, amma bari inkira Dije ince takirashi taji yawan kudin. Amma hajiya inazaki samu kudi masu yawa haka? Uhm kede bari Inna, kinsan Allah yana temakona aduk lokacin danashiga matsala, jiya Alh yabani million 6 na kayan auren Jalila, dama niyata inkashe mata million 3 indau 3, kuma gashi yanzu wani aiki yashigo, inaganin kawai zanyi mata siyayyarta anan kinsan Alhjn atafin hannuna yake bawani abu zece ba.
Asabe tace hakama yayi, inaganin kisiya mata na million 2 kirike 4 kinga kome aka bukata bakida sauran damuwa. Zarah tace haka za,ayi Inna shiyasa nake sonki nasan idan har kina raye, Allah yabarmunke.
Bara inje insa Jalila tadora abinci ki kira Dijen kiji konawane nafison ayi komai cikin sauri. Tana fita Asabe takira Dije tafada mata komai, nan take Dije tafada mata yanda zata ce.
Bayan Zarah tashigo Asabe tace uhm, aiki game kareka, kinsan Dije da mutane, muna gama waya takira bokan harsungama magana, tafadi mashi matsalarki, harya yanke mugun hukuncin dazeyima Falak, danshima yanajin haushin masu cin amana. Dariya Zarah tayi tace kai amma naji dadi, gaskiya Dije kawace tagari. Nawa yace kudin aikin?
Uhm aini hajiya abunne naji dayawa, kodayake biyan bukata yafi dogon buri, boka yace maganin dazeyima Alh, zaki mallakeshi, dayanda shine zerika aiki amma kudi suna gurinki, ko naira 1 baze iya kashewa ba, seda izininki, daya samu kudi kece ze kawomawa. Kara washe baki Zarah tayi tace kai, kice nazama babbar Hajiya, kawai fadimun kudin konawa ne, nasan nan da dan lokaci zanmaida mafiyansu.
Uhm na Falak de yace kibada million 2, na Alh kuma 1 da rabi, se kuma kudin da Dije zatayi kudin mota dasu dubu 50 sena abinci dan kwana 2 zatayi. Zarah tace kai kudinma babu yawa tunda acikin million 4 ina da saura, bakomai zan bata dubu 100 gaba daya nasan zasu isheta, gashi ku kuma ba accounta gareku ba bare intura maku.
Asabe tace mene account, kai mude munfi gane murike kudi ahannu, barema Dije ai tasaba tafiya da manyan kudi, haka kawai kitura mata kudi a banki taje cirowa ma aikatan suga batayi kama da wadda zata fidda kudi masu yawa ba, su kira mata yansanda. Kawai asamu. Babbar Gana, ashirya mata su aciki, seta dora kayanta asama babu wanda zece kudine aciki.
Zarah tace toshikenan ai tunda aikinta ne, yanzu kibari gobe monday, se inje banki da Ganar su shiryamun su acan idan nazo gida se tasaka kayan asama. Asabe tace nima gobe zankoma dawuri semu dawo tare da ita jibi idan narakata tasha se inwuce, amma bake zaki kaimu ba, kisaka driver saboda idon mutane. Zarah tace toshikenan, kema kinada dubu 20. Asabe tace ah, lallai nagode.
Zaune suke adakin Baba mairo Falak tanata kuka, Baba mairo tace dan Allah kidena wannan kuka, babu abinda ta isa tayi maki wanda Allah neyi maki ba, tabbas dole munemi temakon Kawunka Sameer, kasan ance idan kana da kyau ka kara da wanka. Halima tace ai baza,a bari se gobe ba, kutashi kawai muje, tashi sukayi suka nufi motar Sameer.
Azaune suke afalonshi bayan sungama gaisawa Baba mairo tayi mashi bayanin komai. Shiru yayi nawani lokaci sannan yace toku baku