Showing 54001 words to 57000 words out of 61588 words

Chapter 19 - AGOLA BOOK COMPLETE DOCUMENT BY Nabila Lawan Zango .txt

lallai duniya kenan, baku ganeni ba? Jidda ce. Gaba dayansu suka zaro ido suka hada baki sukace Jidda Abba Bala? Ta daga kai tace kwarai kuwa. Umman Sameer tace bayin Allah mun tsaya ahanya kumuje dakinta gashi can sekuyi maganar acan.


Al,amin da Ameerah kuka sosai sukeyi dasuka gama jin labarin da Jidda tabasu, tace na cuci kaina, Ameerah kece silar shigata wannan harakar, Al,amin kaine mutumi na farko daka fara sanina 'ya mace amma yau gashi kudayake kunada rabon tsira Allah yatema keku kunshiryu, abun mamaki kuma harkunyi aure hada rabo atsakanin ku.


Ameerah tagoge idonta tace tabbas Jidda na cuceki, sbd nice silar shigarki wannan rayuwar, sede wlh tun bayan damukayi fada dake akan nazo inaso inmaidake ruwa lokacin da kika tuba, mukayi fada tundaga lokacin mukabar unguwar da muke, kuma nasake waya shiyasa bankara nemanki ba, dan naga kinbar harkar danakeyi, haka nacigaba da rayuwar bariki.


Dalilin shiryuwata shine lokacin da Babana yarasu, tundaga ranar naji tsoron Allah, sbd agabana yarasu, nashiga firgici, dama akullum addu,ar Mamana Allah ya shiryeni, segashi Allah ya amshi addu,arta, nashiga damuwa tunbayan mutuwarshi nakara canza layi, duk wasu kawayena seda narabu dasu, sbd malamin dana samu nafada mashi irin rayuwar danayi kuma nace mashi inason intuba, yace abu nafarko dazan farayi shine inrabu da duk wasu kawayena.


Sbd yace mun idan har mutum yana aikata alfasha, kuma yatuba, matukar berabu da abokanan shiba, tamkar be tuba bane, dan wata rana zasu iya dawo dashi ruwa, alokacin hargidanku nazo sede bansamekiba, Umminku tace mun kina zariya, na amshi no ki amma nakiraki bata shiga, alokacin naso mukulla sabon kawance tunda nasan kin tuba.


Tundaga ranar nikuma bankara tunanin zuwa gidanku ba, haka nashiga islamiyya wannan malamin yatsaya mun sosai nayi karatu me yawa, wata rana nadawo daga makaranta, nahadu dawani dan unguwarmu tare da wani, na tsaya mugaisa kawai senaga ashe Al,amin ne, anan muka gaisa shima yayi mamakin ganina haka, shine ya amshi no ta yace zezo muyi magana, dan bayason muyi agaban abokinshi.


Naji matukar tausayinki lokacin dayabani labarinki, alokacin yayi kuka shima, dan yacemun shine sanadiyar komawarki ruwa, kuma ya kaiki inda kika hadu da matsala, haryake cemun yaso kuyi aure amma kika kiya, alokacin daya temakeki kuma yace yana zargin kina dauke da cuta, yaso kije kiyi gwaji idan baki da ita kuyi aure amma baki yarda ba.


Ganin nima nashiryu, shima yafadamun irin kallar tubar dayayi kuma yace idan zan amince ze aure ni, dama alokacin mijin aure nake nema ni kuma na amince mashi, yanzu haka yaronmu daya Sultan, kuma haryanzu banwuce karatu ba, dan gani nake gara nayi zamana nayima mijina biyayya yafi dan tsoron yan matan Jami'a nakeyi, keni zan iya cemaki kawata daya yanzu ma kwafciyata, itama tadan girmeni.


Al,amin kuwa kasa cewa komai yayi sbd kuka yakeyi tamkar mace, kowa yakasa lallashin shi. Jidda ma kukan takeyi, da kyar tayi shiru tace bakomai Ameerah wlh nayafe maku, duk da kune silar shigata wannan rayuwar amma babban laifin yana gurina da gurin Ummin mu, mekikace yanzu? Mamanki kullum addu,arta Allah ya shiryeki, toni banda wanda yakemun addu,a se kanwata. Kuma kinsan yanda addu,ar Uwa takeda tasiri akan 'ya'yanta, yakike gani idan da ace Ummina ce takemun addu,ar da Jalila takemun?.




Mutum yasamu Uwa tagari ma babban abin alfahari ne, Baban nawa daya kamata shima yatuna dani yamun addu,a bata bari yasan halin danake cikiba, bare yamun addu,a. Asalima tasashi yamanta dani acikin yaranshi.


Wannan Uwa tagari ce? Uhm, nikam ahaka nazo duniyar banci ribar komai ba, kuma gashi zanbarta babu wata riba. Al,amin bakayi laifi ba, dan ka auri Ameerah, laifi nane, fatana kobayan raina kada kumanta dani kurika sakani cikin addu,arku kuma duk wanda zebani sadaka, inarokon daya aje bayan raina agina mun koda rijiyace wadda mutane zasu amfana da ita, koda hakan nasan da kudina nabar abinda wasu zasu amfana dashi, kuma Allah zekai ladar akabarina, amma tabbas ban tara komai na lada ba, wanda zanyi guziri dashi natafiya,,,,,,, kuka ne yaci karfinta.


Shiru dakin yayi sbd gaba daya dakin kowa kuka yakeyi. Al,amin da kyar yace Jidda kiyafemun kiyafemun dan Allah, tashi yayi yadauki Sulta ya aje masu kudi wanda besan yawan suba yafita sbd gaba daya zuciyarshi tayi mashi zafi, Ameerah ta mike tana kuka tamika ma Jidda hannu sukayi musabaha, itama tafita tana kuka, akofar fita suka ga mutum tsaye ya juya baya, da alama shima kuka yakeyi.


Alh, ne yazo tafiya dasu Jalila dan Baba Mairo tace mashi suna nan, tunda yazo zeshiga yaji firarsu kawai ya tsaya akofar dakin. Tausayin Jidda yayi mashi yawa, haka yashiga dakin daka ganshi kasan yasha kuka, bakin glass ne a idonshi amma duk da haka afuskarshi ana ganewa.


Kwance ya iske Jidda tana ta kuka, yace Jalila kumuje kunga har la,asar tayi, Falak kuwuce muje. Jalila ta matsa tarike Jidda sosai, tana kuka, tace Yaya Jidda kiyafemun, zantafi, amma gobe zamuzo, Allah yabaki lfiya. Jidda tace bakitaba yimun komai ba Jalila, nice yakamata inrokeki gafara, na cutar dake, kiyafemun, Falak kema haka dan Allah kiyafemun. Falak tace nadade dayafe maki, Allah yabaki lfiya.


Da kyar aka cire Jalila daga jikin Jidda sunata kukan saurin fita Alh, yayi danshima kukan yakeyi.Jidda kwanciya tayi tana kukan zuci jitake dama Allah yadau ranta yanzu.


Da misalin karfe 7 aka gama shirya amarya, tayi kyau, sede fuskarta ko kwalli bata bari anshafa mata ba, bamaze zauna ba ko anshafa, sbd hawayen dasuke zarya afuskarta, afalon Alh, aka kaita suyi sallama, zaune suke da Mal. Garba, da Kawunshi, anan kowa yayi mata nasiha sannan akace Alh, yayi mata nasiha, kasa cewa komai yayi, sede yace Allah yabaki hkr Jalila, saurin tashi yayi yashige daki sbd kuka, daya taho mashi, itama kukan takeyi, haka matar Kawun Alh, ta dagata suka wuce, Falak kuwa dama tundazu Sameer yadauketa yakaita gidan amaryar dan yace baya so tasha wahala, manyan mata 2 ne suka sakata tsakiya, da yan uwan Kakanta, se dangin Dadynsu.


Sauran mutane suka biyo bayansu. Gidanta yayi kyau sosai, haka suka shiga da ita, bayan sunmikata ga dangin mijinta akayi abubuwan al,ada sannan Sameer yashiga yace sufito amaidasu, dan ance manya bazasu kwana ba, Falak ma Sameer ne yace ta kwana sbd Jalila. Da kyar Falak tasata takara yin wanka sbd gidan kowa ya tafi daga Falak se su Bilkisu da Farida, su 3 ne zasu kwana, lallashinta sukayi taci abinci. Suna zaune Jalila tace wlh Falak gabana faduwa yakeyi, Falak tace badole ba, tunda gobe kamar yanzu kina gaban angonki. Tace ke wlh kincika fassara, nikwai inaji ajikina kamar wani ya..... bata karasa fadi ba, Saleem yayi sallama yashigo shida Sameer, daka kalli idanunsu kasan akwai abinda yafaru. Zunbur Jalila tamike tace Ummi ko? Yaya Jidda ce? Kufadamun waye ya mutu acikinsu? Kamota Saleem yayi yace babu wanda ya mutu kawai jikin Yaya Jidda ne yatashi. Murmushi tayi tace wlh banyarda ba, shikenan kawai, nashiga 3 yazakimun haka Yaya Jidda kinsan banda kowa seke, meyasa zakimun haka,,,, kuka tasa masu, Falak taja Sameer tace meya faru, Yaya Jidda tarasu ko? Share hawayen idonshi yayi yadaga mata kai,


Wata irin zufa taji ta taso mata, mararta tawani murda, saurin dafe cikinta tayi ganin halin data shiga yasa Sameer yayi saurin kamata, yace Saleem muje inajin Falak haihuwa zatayi, kadauko Jalila kawai dasu Bilkisu kasa megadi yakulle gidan bari intafi da ita asibiti. Juyawar da Saleem zeyi yayi ma Jalila magana yaganta kwance akasa ta sume.
😭😭😭😭😭😭😭😭
Washhhhh!!!!! bara inbarku haka, nima najike sekunjini a page na gaba. Tnx alot


Ur's
NABILA RABI'U ZANGO
(Nabeelert Lady)
08028525263
🙆🏻😭😭🙆🏻 AGOLAH!!! Nah
Marubuciyar Zamani
NABILA RABI'U ZANGO
(Nabeelert Lady)


@ (H,O,N,A)


Part 180.....185


Suna zuwa aka nufi labour room da ita, shi kuma Saleem yashiga da Jalila su Bilkisu suna binshi abaya, itama daki aka nufa da ita domin adubata. Sameer gurin su Baba Mairo yanufa, koda yaje ya iske har ansaka gawar Jidda ambulance, za,a kaita gida, Baba Mairo tace lafiya Sameer naganka arude? Alh wanda fuskar shi take jike da hawaye, ya goge idon shi yace lafiya de Sameer? Yace bakomai dama Falak ce zata haihu tana dakin haihuwa.


Alh, yace to ina Jalilan kotana gidanta? Kai yasosa yace a,a nabarta ita da Saleem inaji befada mata ba, yauwa kada kufada mata kawai yadauketa yakaita gida. Baba Mairo kikoma gurin Falak din mucemu wuce da gawar, tunda Halima tana gurin Zarah.


Goge kwallan idon ta tayi tace a,a Alh muje inaso inyima Jidda wanka da kaina, kai Sameer kasamu Halima tunda dazu akayi ma Zarah allurar bacci kace taje gurin Falak din, nizanje can gidan. Yace to nima yanzu zanzo kafin agama shiryata tunda ance yau za,a kaita tunda dare beyi ba.


Haka suka nufi gida da ita kowa yana cikin damuwa. Babu bata lokaci Falak ta haifi kyawawan yaranta guda biyu, Mace da namiji, cikin koshin lafiya, bayan angama shiryasu aka fada masu Sameer, Bakaramin murna Sameer yayi ba, dan betaba tunanin samun yan biyu ba. Wayarshi ce tayi kara, yana dubawa yaga Saleem.


Dauka yayi yace Saleem ya Jalilan ta farfado? Yace E amma haryanzu kamar bata gama dawowa hayyacinta ba, amma likitan yace zeyi mata allurar baccin dazata kaita har gobe dan tasamu ta huta. Sameer yace toshikenan yanzu itama Falak ta haihu, ansami twins, fito muhadu semuwuce can gidan.


Saleem yayi farin cikin ganin jariran masu kyau dasu, bayan ankai Falak dakin hutu, itama haryanzu kuka takeyi, suka dubata da jiki, suka ce zasuje sukai Jidda, Falak tace Allah sarki Yaya Jidda Allah yajikanta, naso ace nakara ganinta. Sameer yace se hkr addu,a zamu cigaba dayi mata, bara muje semun dawo, nasan se gobe za,a sallameki gara kizauna ana ku huta, tace tosekun dawo ina Jalilafa? Anan suka fada mata abinda yafaru, tace to Allah yabata lafiya, haka suka fita suka bar Umman Sameer agurinta.


Gida mata se kuka sukeyi, Baba Mairo da Matar Kawan Alh, su sukayima Jidda wanka, suka shiryata, babu bata lokaci aka fiddota, akayi mata sallah,aka nufi gidanta na gaskiya da ita.
Koda sukaje Alh, kasa sakata kabari yayi, sbd kukan dayakeyi, sede su Kawu ne da Baba na Zariya da Kawun Sameer suka sakata, Alh, yabama kowa tausayi agurin, haka aka gama sakata akabarinta aka rufeta, suka dawo.


Aranar haka kowa yazauna masu bacci kadan ne, dan Alh, tunda yashiga daki, yayi wanka yayi alwala yayita nafila da karatun Qur'ani har seda aka kira sallah sannan yanufi masallaci. Bayan sunadawo ne, yake tambayar Sameer yabega Jalila ba, anan yake fada mashi halin datake ciki, da kuma abinda Falak tasamu, yayi murna sosai, yace tobai bazama zamuyi ba, muwuce muga jikin nasu.


Lokacin dasukaje asibitin har Falak tayi wanka Anyima jariran wanka suma, sunyi gwanin kyau, sede daka kalli Falak kasan tana cikin damuwa. Baba Miaro tana kusa da ita dan agurinta ta kwana, ita kuma Umman Sameer ta kwana agurin Jalila ita dasu Bilkisu.


Jalila kuwa tafarka, tunda tayi sallah itama take kuka, se lallashinta sukeyi, haka Alh, yasameta, yana ganinta shima yaji wani sabon kukan yazo mashi, da kyar yasamu yadedeta kanshi yashiga, shima lallashinta yashiga yi, sannan suka nufi gurin Falak, acan ma du lallashin ne, daga can yawuce gurin Zarah.


Zaune suka sameta duk ta kwance bandage din da aka rufe mata ciwon tana ta wasa dashi, cikin sauri Saleem yaje yajira nurse, ana suka riketa aka sake mata wani sabon dressing din. Tagumi Alh, yayi, yana kallonta, yarasa neke mashi dadi aranshi, addu,a kawai yakeyi itace take kara sanyaya mashi ranshi. Fita yayi yace bara yatafi tunda gari yayi haske sbd masu zuwa gaisuwa.


Karfe 10 aka sallami Falak da Jalila, Baba Mairo tace awuce da Falak gidansu Jalila, idan kunje se a bude part dinsu nada tazauna aciki, sbd asamu saukin zirga zirgar. Sameer yace hakan ma yayi, tace nima anjima zanzo sbd nasan babu wanda ze zauna agurinta, idan yaso se Halima tazauna agurin Zarah, anjima se indawo.


Sunzo tafiya, su Bilkisu sukace bara suwuce gida anjima zasu dawo, godiya sukayi masu, Saleem yabasu kudi suka tafi, sun fito kenan suka hadu da Al,amin, Jalila yagane, hakan yasa ya tsaya suka gaisa, kallonta yayi tana kuka yace ina fatan kunshedani? Al,amin ne, yame jikin? Falak tashare idont tace Allah yayi mata rasuwa jiya da dare. Kiyayi kamar ansara mashi icce akanshi, wasu irin zafafan hawaye ne suka zubo mashi. Yace shikenan Jidda ciwo ya warke, darabon mugana ashe, sallama yayi masu yace zeje yadauko Ameerah suzo tare.


An gyara part din su Falak na da dama kuma babu abinda aka cire aciki, tunda Hajjo tarasu da aka kulle shi ba,a kara amfani dashi ba, share shi akayi aka goge, sannan Falak da Jalila suka shiga ciki, amma Falak cewa tayi adakinta na da zata zauna bazata shiga dakin Ummanta ba, Sameer yaje yadauko mata duk kayan dazasuyi amfani dasu yakawo, Baba mairo ta dora ruwa takara yima yaran wanka, tasa Falak itama takara yi.


Saleem ne zaune afalo shida Jalila, haka yayita lallashinta da kyar yasamu taci abinci shima kadan taci, yace Jalila inaso ki kwantar da hankalinki yanzu babu abinda Yaya Jidda take bukata daga gurinmu se addu,a. Kirika yawan ambaton Allah da addu,oi zaki samu sauki aranki, nasan dole kiyi kuka amma hakuri zakiyi. Allah yaji kanta, yabama Ummi lafiya, tashi yayi yace zeje waje. Itama shiga gurin Falak tayi, dan batason zuwa bangarensu.


Haka aka cigaba dazaman gaisuwa, Al,amin da Ameerah sunzo gaisuwa, itama tasha kuka, Al,amin yakira Jalila yace yadauki nauyin ginama Jidda rijiya amakarantar almajirai kamar yanda taroka, kuma zeginata ne da sunan ta, amatsayin sadakar daze bata. Sosai Jalila tayi mashi godiya, seda suka jera kwana 7 suna zuwa gaisuwa, ranar da akayi sadakar 7 aranar akayi sunan Falak, bawani taro akayi ba, bayan sadakar 7 akayi radin suna.


Namijin aka samashi sunan Alh, wato Abba, ana kiranshi da Ameer, dan Falak tace tana son sunan, Macen kuma Aka samata sunan Hajjo, Zainab, ana kiranta da Ameerah. Falak tayi mamaki sosai da Sameer besa sunan babanshi ba, har seda tayi mashi magana, murmushi yayi yace haba Dear, Alh, shine mutumin da yayi sanadiyar haduwata dake, kuma ya cancanci abinda yafi haka agurina dake baki daya. Umma kuma dana sa sunanta, kinga tarasu kuma saka sunanta zesa murika tunawa da ita, jawota yayi yace kada kidamu nasan nan da shekara 2 zaki kara sama mana wasu babies din. Murmushi tayi tace nagode.


Ayau ne, Jalila zata koma gidanta, dan Alh, yace sutafi gida zatafi samun sakewa idan tana kusa da mijinta, sauran mutane ma, duk sun watse se yan uwa kawai suka rage, yan Zariya ma yau zasu tafi, Alh, yasa aka kira kowa yace yana son magana dasu, anan falonshi suka taru, hada Kawunshi, da Kawun Sameer, da Mal. Garba dasauran mutanen.


Bayan anbude taro da addu,a, aka kara yima Jidda addu,a sannn Alh, yafara magana, hakuri yakara bama kowa, sannan yace Jalila,Falak, ayau nakeson kowa takoma gidanta, wanda yarasu yariga da yarasu, dan haka addu,a kawai zamu cigaba dayi mata, banaso insamu labarin acan kun kasa sakin jikinku, kowa hkr yakeyi arayuwa, kuma dama dan Adam baya zama haka, har se Allah ya Jarabceshi, dan haka murika daukar kowace kaddara tazo mana da hannu 2, Allah yayi maku Albarka.


Kuma itama Zarah munyi magana da Malam, yace gobe Malaminshi zezo yafara yimata rukiya, dan haka nayima Dr, magana zamu maidota gida yau, idan yaso se arika zuwa gida ana mata dressing, tunda yanzu yakoma bayan kwana 2. Kallon Kawaunshi yayi yace Kawu ko akwai abinda zakace?.


Gyara zama yayi yace hakane, duk abinda kafada yayi dede, sede abu 1 nakeso inkara, Baba Mairo mungode kwarai da irin abunda ku kai mana, daga ke har Halima, tabbas kunzama yan uwa, sede ina rokonki wata alfarma, daga ke har Halima, duk da bata nan, amma ga malam nan, muna neman alfarmar daka barsu sudawo gidan nan dazama, kaga akwai marar lfy, kuma yanzu Zarah ba matsayi matar Abba take ba, asali ma, babu sauran igiyar aure atsakaninsu, idan har kayarda mun rokon alfarmar dasu dawo nan dazama, hakan zeyima Abba sauki dan baze yuwu ace mubama shi mal. Garba ita yatafi da ita ba, duk da tayi mana laifi amma ba,a kallon abinda yawuce, idan ka kalli alherin da mutum yayi maka zaka iya temaka mashi dashi.


Kaima Abba dole kayi hkr da duk abinda Zarah tayi maka, tabbas tacutar da kai da kowa naka amma, ka kalli darajar yaranku kayi hkr, inaso tacigaba dazama agidan nan har Allah yabata lafiya, daga nan kuma seta zaba ma kanta abinda taga zefi mata.
Amma inaso inji daga bakinka ka amince zata cigaba dazama agidanka harta samu lafiya?.

Se kunjini a next page dina wadda insha Allah shine last page. Nagode da kaunarku gareni.


Ur's
NABILA RABI'U ZANGO
(Nabeelert Lady)
08028525263
🙆🏻😭😭🙆🏻 AGOLAH!!! Nah
Marubuciyar Zamani
NABILA RABI'U ZANGO
(Nabeelert Lady)


@( H,O,N,A)


Part 185.....200
The Last Page.........


Shiru Alh, yayi nawani lokaci, sannan yace shikenan Kawu duk abinda kace yayi dede, Allah yabata lfy. Kuma nagode da abinda kuka yi mani, Allah yasaka da alkhairi. Kawu yace Alhmdll, anjima malamin ze iso, dan haka se kuje kudauko ta. Haka suka tashi kowa yafara shirin tafiya.


Bayan andauko Zarah daga asibiti duk wanda yaganta seya tausaya mata, takoma kamar skeleton ne aka sama fata, tayi baki, ga kafarta da aka yanke tundaga cinyarta har kasan kafar sun shanye tazama siririya, ta yanda bazata kara amfanuwa ba, sede ciwon dake jiki yayi sauki, sbd Kawu yabada ruwan addu,a ana shafa mata akan ciwon, hakan yasa yadena fitar da ruwan dayakeyi, kuma dama aljanun jikinta ne suke sakashi zuba.


Jalila da tunda ta kalli Zarah take kuka, a part dinsu Falak Alh, yace akaita, awani daki dayake farkon shiga daga gefen falon, anan aka saka mata katifa, dayake akwai bandaki aciki, sede dakin bawani girma gareshi ba, bayan su Baba Mairo sunyi mata wanka, suka gyarata aka daureta tana kwanciya tayi bacci.


Saleem ne yazo daukar Jalila, tana kuka haka suka tafi su Baba Mairo se hkr suke bata, Falak ma seda tayi mata kuka, Sameer yace kema shiryawa zakiyi anjima zamu tafi, Baba Mairo tace gsky bazaku tafi ba, dama inaso inga Alh, muyi magana, dama ace yaro daya gareta se kutafi, amma yara har biyu, sannan kai kuma aikinku idan kafita wani lokacin har dare kake kawai, yazatayi da yaran? Kuma kaga muduka muna nan bare ma ace ni inje

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login