Showing 39001 words to 42000 words out of 61588 words
Chapter 14 - AGOLA BOOK COMPLETE DOCUMENT BY Nabila Lawan Zango .txt
yake kamar kamar duk wata damuwarshi ta kau, saboda yarabu da Asabe.
Gidan Dije taje suka kara tattaunawa, sbd gobe zasu tafi, Asabe tace kinsan daga gidan Tabawa nake dillaliya, anjima zatazo tasayi kayana, dan babu abinda zanyi dasu muda zamu bar gari. Dije tace nima de sayar danawa zanyi, dama bawani yawa garesu ba, ni har na kosa gobe tayi wlh mubar garin nan nahangomu a Lagos cikin daula. Dariya sukayi suka kashe.
Bayan sunkoma asibitin dayake dare yayi suka dan zauna dan jikin Jiddan yayi sauki tasha drip, Zarah tace Alh, kutafi kaida Jalila nizan kwana da ita, Jalila tace a,a Ummi kibari inkwana. Alh, yace aike yarinya ce Jalila jinya kuwa ai se babba. Kibarta takwana tunda kwana daya ne gobe zasu dawo gida ai. Sallama suka yimasu suka tafi, ganin suntafi Zarah tafita takirawo Asabe, tafada mata abinda yafaru, tace amma goben zanciro kudin bana son Alh, yagane, nasan dawuri zasuzo duba Jidda zansa likita yabar sallamar se da rana, suna zuwa sena barsu nadawo gida amma fa kutaho dawuri.
Washe gari dasafe Dr, yashigo anan Zarah tafada mashi bukatar ta, yace toshikenan babu damuwa dama akwai saura drip 2 daza,a samata zuwa azahar nasan sun kare seku tafi.
Gurin karfe 8 Alh da Jalila suka shigo, hamdala Zarah tayi, bayan sungaisa, suka tambayi jikin Jidda, Zarah tace dasauki sosai ma, dan tadena aman kuma taci abinci sosai jiya. Alh, yace Allah yakara sauki, bara inje gurin Dr, inji yaushe za,a sallameta. Zarah tace ai yashigo dazu, yace seda rana sbd akwai drip 2 da za,a samata. Amma kuzauna bara inje gida inyo wanka bazan iya yin wanka anan ba, idan nadan huta se indawo. Alh yace hakane gsky nasan bakiyi bacci sosai ba, jiya, bakomai kitafi nima zuwa 9 zan wuce office akwai abinda zanyi tunda ga Jalila nan seta zauna agurinta, Jidda tashi kici abinci kinji. Sallama Zarah tayi masu ta amshi makullin motar Alh, tace idan taje seta bama driver yakawo mashi.
Tana zuwa gida ta iske su Asabe har sunzo, farinciki ne, yakamata tabude gidan suka shiga tabama driver key din motar tace yakaima Alh, wanka kawai tayi tace sukirata taje takarbo kudin, tace suduba kitchen idan akwai abinci suci idan kuma babu sesu dora kafin tadawo.
Tana zuwa banki babu bata lokaci dayake akwai wanda tasani dan danan aka shirya mata kudin acikin jaka, tadawo gida, duk da tadan dade, tana zuwa gida tasau driver yadawo, tasashi yadauko mata kudin. Kaya aka dora asaman kudin babu wanda zece kudine aciki, takirawo driver tace yadauka zekaisu tasha, yana fita ta dauko hoton Alh, dana Falak wanda tasamo adakin Jalila tabasu, Dije takarba tasa ajakarta, Zarah takawo dubu 30 takara ma Dije tace tarike ahannunta. Asabe tace nima ai tare zamu tafi senaga tashinta daga can nima inwuce dan nace ma Babanki bazan dade ba, Zarah tace toshikenan Allah ya tsare nima asibiti zankoma. Sallama sukayi mata suka fita, itama tashiga motarta tawuce asibiti.
Suna zuwa sukaci sa,a mota takusa cika, seda driver yatafi sannan suka se su 2 ne zasu tafi, Dije tace wannan jakar asata abayan mota kayane aciki amma dan Allah aturata ciki sosai kayan sana,ata ne, drivern mota yace karkiji komai madam kawai shiga mota muware, seda suka biya kudin motar sannan suka shiga, Wata inyamura suka samu akusa da ita Asabe tazauna Dije dazauna kusa da Asabe, suna jiran mutum 1, Asabe baki yakasa rufuwa sun sami duniya. Dije tace gsky Kawata nayi farin cikin haduwarmu gashi ta sanadiyarki zanzama babbar hajiya. Asabe tace kede bari wlh idan muka isa Lagos dole muyi kara,in yanmatancin mu baruwana da harka da tsofaffi, yara zansamu masu jini ajiki tunda inada kudi inkashe masu surika biyamun bukatata. Dije tayi dariya tace ashede kema kina irin tunani na. Kinsan hanyar Lagos batada kyau shiyasa nace asaka mana kudinmu abayan mota nace masu kaya ne, sbd kada wani yasan akwai kudi masu yawa acikin jakar, kinga baruwanmu da tunanin yan fashi. Asabe tace gsky kina da dabara. Dahaka mota tacika suka daga zuwa Lagos.
Sameer ne da Saleem da Falak, amota suna hanyar zuwa asibiti dan Falak tayi waya da Jalila take fada mata suna asibiti Jidda ba lfy shine suka wuce dubata dan tadafa mata Dady yana asibiti shima.
Waya takira Jalila tafito tayi masu jagora, Saleem se kallonta yakeyi yana murmushi, Sameer yace kun tsaya sewani sunne sunne kukeyi sekace bakin fulani, mude bamuson kilibibi. Saleem yace ina ruwanka sa ido, kasan kowa datashi kalar soyayyar. Falak tace Allah baka hkr kada kacinyemun miji, dariya suka saka baki daya.
Da sallama suka shiga dakin, Alh, yana zaune abisa kujera ya amsa sallamarsu, har kasa suka duka suka gaishe shi, ya amsa da fara,a suka tambayi jikin Jidda yace dasauki. Falak tace Dady ina kwana, mikewa yayi yana kallonta cike da mamaki, dede lokacin Zarah tashigo da sallama, cak ta tsaya ganin abinda yake faruwa, kowa hankalinshi yana kansu, babu wanda ma yasan da shigowarta. Ganin babu wanda yakula da ita yasa tayi saurin juyawa tafita, mota tanufa tayi gida dasauri hankalinta tashe.
Alh, yace Falak, tace na,am Dady, komawa yayi yazauna yadafe kanshi dan jiyayi yana juya mashi, Sameer ya matso kusa dashi yana fadin Alh, lfy de? Yace kiramun Dr, dasauri. Fita yayi shida Jalila suka kirawo Dr, yana zuwa Alh, yace bayajin dadi kanshi yana juya mashi, nan Dr, yace ya kwanta bisa dayan kadon yafita yakawo mashi magani yabashi yasha sannan ya aunashi, yace Alh, babu abinda yake damunka kila de rashin bacci ne yasama ciwon kai, amma ka kwanta kadan huta zaka samu sauki, godiya yayi mashi sannan yafita.
Ruwa Sameer yadauka yayi mashi adduo,i sbd dama kawunshi yafada mashi akwai asiri ajikin Alh, hakan yasa ya tofa mashi addu,a dan yasan ganin Falak ne yasa mashi ciwon kan. Cikin ikon Allah yana shan addu,ar yasamu sauki.
Zarah tana zuwa gida tashiga daki kamar zatayi ihu sbd tashin hankali, durowarta tabude tafara binciken sauran maganin mallakar da boka yabata tasama Alh, a abinci dayake tarage kadan. Ajiyar zuciya tayi dataganshi.
Kitchen tanufa domin doramashi abinci farinciki duk ya rufeta tana fadin wlh karyarki tasha karya kitonamun asiri, kai kuma Alh, zanga bakin dazaka samu damar yimani maganar Falak, dakaci abincin nan zaka dawo hannu, Dadi nama dayane, tana gidan mijinta bazasu samu damar zama su dade tare ba, kafin sukara sabawa nasan Dije ta isa gurin boka daga ranar kungama yawo. Kwance maganin tayi tajuyeshi acikin plate tayarda ledar ta ajeshi tadauko tukunya takunna famfo zata daurayeta. Maganin tazuba acikin tukunyar tazuba ruwa, tana fadin gara kutafasa tare nasan zefi jikuwa kuma zefi aiki, dauko tukunyar tayi zata dora bisa gas, juyawar dazatayi silbi yajata tafadi tukunyar tafadi ruwan yazube.
Wani irin ihu tasaka tana fadin nashiga ukku, shikenan tawa tasameni, tashi tayi takashe gas din tafita tana kuka, daki takoma tazauna tabuga tagumi tarasa meke mata dadi, wayarta ta dauko takira Asabe, amma akashe, wurgi tayi da wayar tasa kuka. Ganin kuka baze mata ba, yasa ta tashi tashiga wanka tana fadin ai nasan yarinyar tanada Imani bazata iya fadama Alh, abinda namata ba, kawai zan gwada mashi komai lafiya kafin wani lokaci aikin boka yafara, da wannan tunanin tasamu kwarin guiwa tashiga wanka.
Alh, yakalli Falak abin mamaki yaga hada ciki ajikinta, wasu hawaye yaji suna zubomashi yagoge yace Falak se kuma yayi shiru, tashi yayi yace haryanzu Zarah bata dawoba, kila bacci yadauketa, nara inje office inbada sako, daga can zanwuce gida banajin dadin jikina, tunda ruwan yakusa karewa zancema Dr, kutaho gida idan yakare kusameni agida.
Zaune suke afalo Alh, yace ma Jalila kirawo Umminku najita shiru, Cike da karfin guiwa Zarah tashigo tace a,a Alh, harkun dawo kunganni shiru wlh, kaina naji yana ciwo ina gama wanka nasha magani nakwanta kawai ina farkawa naga lokaci yatafi, sannunku.
A,a yau kuma amare ne agidan namu, ai dama nasan da kunji Jidda ba lfy zaku taho, hala Jalila ce tafada maku, zama tayi kusa da Alh, wanda yaketa kallonta cike da mamaki, danshi yaji ana fadin Falak amarya, kuma gata da ciki towai yaushe ma tayi aure? To tama gama karatunta? Shi yadade beji ankira sunanta agidan ba, bare kuma yasata a ido. Zarah takatse mashi tunaninshi tace Alh, munkusa samun jika agidan nan fa. Sameer, Saleem, Falak, Jalila harma da Jidda kallon mamaki sukema Zarah.
Alh, yace dan Allah kufitar dani duhu, naji kuna wasu maganganu wanda bansan dasuba. Zarah tayi murmushi tace Alh, kana nufin baka gane Falak ba? Yace a,a ammade nasan Ameer yarasu, Falak da Jalila sungama makaranta, nayi masu alkawarin wucewa wata, kuma gashi Jalila ce kadai tayi karatu ya akayi Falak batayi ba, hartayi aure nibansaniba? Zarah tace lallai Alh, da badan nasanka ba da se ince kasamu tabin hankali, kabada auren Falak da hannunka, kuma kazama waliyinta kabani kudi nayi mata siyayya sannan kace kamanta, haba Alh, kode ciwon mantuwa yafara samunka? Falak fa da bakinta tazo tace tasamu mijin aure bazatayi karatu ba, har na hana kace bakomai tunda mijinta yanada hankali setayi agidanshi.
Dafe kai Alh yayi sbd rudun daya shiga, ganin Zarah tana iya sakama shi ciwon kai yasa Sameer yamatso kusa dashi yace Alh, kada kasama kanka dogon tunani ba,a son irin wannan yana iya yawo maka matsala, addu,a yakama kayi hakane Ummi batayi karya ba, nine mijin Falak kuma kaine kabani ita kazama waliyinta idan katambayi mutanen unguwar nan zasu fada maka anyi haka. Alh, yagoge kwallan idonshi yace shikenan nagode Sameer, tabbas nasan akwai abinda yasameni, sede bansan komenene ba, amma naji dadi sosai tunda Falak tasamu miji nagari, Allah yabaku zaman lfy.
Falak inaso kiyafemun kada ace nakasa rike amanar da Hajjo da barmun, idan har akwai wani abu dana yimaki kiyafemun bansan awane yanayi nake ciki ba, sede zanyi yanda kace bazan tsananta bincike ba, sema ingodema Allah daya yayemun abinda nakeji. Nagode. Sosai. Gashi ankusa bikin Jalila kema Jidda naso ace kinsamu miji dase ayi tare, amma bakomai Allah yakawo maki mafi alkahiri.
Zarah tayi murmushi tace ameen, Alhn yace wai ina Baba mairo ne, haryanzu bata dawo bane? Zarah tace e kasan ai tadade bataje gidaba, dama tace zata kwana 2. Anan suka cigaba da fira sosai Falak taji dadi yau tana fira da Dadynsu wanda rabonta da haka tadade, tashi su Sameer sukayi suka masu sallama yace zedawo anjima yadauketa. Jalila tace tashi muje daki, Alh, yace a,a kuzauna anan munyi fira kinga anjima zata tafi. Zarah ta maka mata harara, tace Jidda tashi muje kiyi wanka kici abinci ki kwanta nasan kingaji. Haka suka zauna suna tafira cike da jindadi.
Tafiya sukeyi duk sungaji sunyi bacci harsuntashi, gashi magriba hartayi basu isa ba, Asabe tace kai, gsky Lagos akwai nisa, aini tunda nake bantaba tafiya menisa haka ba. Dije tace kede bari, sede dana tuna rayuwar jindadin dazamuyi idan muka isa se inji banajin gajiya. Asabe tace.........Innalillahi wa inna ilaihir raji,un shine abinda sukaji driver yana fadi, hakan yasa Asabe tahadiye maganarta suka maida hankalinsu ga driver. Meyafaru mukaji ana salati? Driver yace to jama,a Allah yahadamu da yan fashi kowa yafara addu,a. Tunkafin yagama maganarshi yataka burki ganin ansetasu da bindiga, parking yayi gefen hanya. Dije tace ma Asabe anshi wannan dubu 15 ne idan akace mubada kudi kibasu nima. Zan basu na hannuna, kada kifada masu akwai kudi ajaka, nasan dasun duba zasuga kaya tunda sauri sukeyi dare beyiba bazasu tsaya dubawa ba.
Kowa yafito, sukaji ana fadi, haka kowa yafito suka fara karbar kudi suna binciken motar, inyamura ana bude jakarta aka samu dubu 50, suka anshe nan tasaka kuka tana fadin nabani kuyi hakuri Oo, yarona beda lafiya zankai masi kudin magani, daya daga cikinsu yace kimana shiru ko in fasa kanki, aka zo kan Asabe ana buda jakarta aka samu 15k, suka dauke, ana zuwa kan Dije aka samu 20k itama suka kwashe, ganin sunsamu kudi agurin kowa yasa wani yace ya isa haka kuzo muware kunsan oga yana jiranmu gashi dare biyi sosai ba, kutashi ku bace mana anan, suka fara shiga mota, Inyamura ce tafara shiga se kuka,takeyi, sannan Asabe tashiga
Asabe ta kalleta ganin yadda take kuka yabata dariya tace inbanda abunki darashin dabara inrin taku yaushe zakitaho Lagos da kudi ajaka har dubu 50. Kinga sunyi maki hankali gobema seki kara tafi baki boye kudiba. Muyanzu wazece muna da miliyoyi acikin boot? Kuma gashi an anshi kadan zamu wuce abunmu. Driver yace wai mekuke jira ke ki matsa masu su shiga muwuce mana. Dije tace ai bansan wane irin surutu Asabe takeyima wannan matarba duk kintare hanyar.
Dasauri Inyamura ta ture Dije tayi waje tana fadi wallasi akwai kudi a boot. Cak kowa yatsaya yana kallonta. Dan fashi ya ce wane boot, tace amota. Dariya yayi yace kowa yafito, nan take jikin Asabe da Dije yafara rawa, Asabe tace nashiga 3 bakina yajamana. Anan aka fiddo kaya, aka ciro jakarsu, yace suwaye keda wannan jakar, su Dije suka ce mune, yace tokuzo nan, kai driver daga ina kuke, yace Kaduna, to kusauran kowa yashiga mota, suna bude jakar suka cire kayan sama anan suka ga makudan kudi, nan take suka maida ma kowa kudin shi suka ce sutafi subar su Dije anan,
Haka suka tafi suka barsu suna ta kuka, haka suka tasa keyarsu suka nufi gurin Ogansu, suna zuwa suka zazzage duka kudin, Ogan yace shegu, ina kuka samo wadan nan kudin haka? Wlh Oga wata inyamura ta temakemu muka samesu agurin wadannan, Yace sake dubamun jakar hannunsu, ana duba jakar Dije, aka ciro hotuna, yace Oga babu komai se hoto, yace mugani. Cike da mamaki yamike tsaye yana kara murza idonshi yace Hajjo, dama kina Raye??????
Urs,
NABILA RABI,U ZANGO
(Nabeelert Lady)
08028525263
[7/16, 12:28] Nabilat Author: 🙆🏻😭😭🙆🏻 AGOLAH!!! Nah
Marubuciyar Zamani
NABILA RABI,U ZANGO
(Nabeelert Lady)
@( H,O,N,A)
Part 120.....125
Wani irin murmushi Ogansu yayi, yace nadade ina tunanin wata rana zamu hadu, segashi cikin sauki nasameki ahannu. Kai, ya daka masu tsawa, a ina kukasan wannan matar tajikin hoton nan, mesuna Hajjo? Cike da fargaba Asabe tace wlh ba ita bace amma de itama mamarta sunanta Hajjo, kuma tarasu da dadewa, wannan sunanta Falak.
Murmushi yayi yace tabbas yarinya kingirma, harkin kai minzalin aure, kinzo adede dama ina bukatar abokiyar hutawa. A wane gari suke? E to dama de AGOLAH ce agidan diyar mijina, kuma bayan mamanta tarasu itama tayi aure. Mene? Aure? Wlh dasake, kinsan koni wanene agurinta? Kai Asabe tashiga girgizawa tana hawaye.
Kawun Babanta ne ni, kinga ko inada hakki akanta, to wai ku inama zakuje da makudan kudi haka, kuma mezakuyi da wadan nan hotunan, kode wannan shine mijin nata? Dan Allah yallabai kayi hkr, wlh muma bamu akayi mukaisu gurin boka shine mukuma mukace bazamuje ba, shine mukayi kokarin guduwa da kudin.
To waya aikeku? Diyar mijina ce, itace kishiyar Maman Falak, wannan kuma mijinta ne, shine takeso amallake, ita kuma Falak akasheta. Hahhhhh, kawai kicemun kuma maciya amana ne. Lallai tunda hadaku za,a hada baki akashemun jinina, lallai kuma zaku amshi rabonku, danni bana yafema wanda yashiga gonata.
Dije tace kawa Allah kayi hkr, mude kudauki koda rabin kudin ne, kubamu sauran mutafi, wlh dama can bamuyi niyar zuwa gurin wani boka ba, muma muna tausayinsu ai..... Saukar marin datajine yasata yin shiru, ke harkin isa kizo gabana kina fadin indauki rabin kudi inbaki sauran. To bara kiji, ko wadanda suka kawo kudin basuda hurumin karbar rabin kudin bare kuda muka kama, wanda lokaci kadan yarage maku aduniyar gaba daya.
Wayyo Allah nashiga 3,ni Asabe, ina zamana Dije kinja mani, gashi nan nibanyi kudiba, zan rasa raina abanza, nide Allah ya isa tsakanina dake, duk kece kika sakani cikin wannan bala,i. A,a kada kidoramun laifi, dama can da bakin halinki kikazo garinmu, keda kika kashe mazajenki har 2, kuma kike fadin nina koya maki bakin hali.
Ya isa,,,,,,,., Ashe de kuma kananan yan ta,adda ne. Lallai kunyi kokari. Duk ku saurara, banida lokacin batawa, ke a ina zan iya samun Falak? Wlh nima bansan gidansu ba, amma de nasan gidan diyar mijina. Ok, fadamun dan sauri nakeyi.
Idan kaje Unguwar sarki kaduna duk wanda ka tambaya Alhaji Abba Bala, yasan gidan. Da kyau, kai mugu gama masu aiki kasan ni bana barin baya da kuurah. Tasssss kakejin karar bindiga andauke Asabe da Dije. ( se ince karshen Asabe da Dije kenan, dama duk wanda ya gina ramin mugunta, wata rana shine ze fada. Allah yatsaremu, sunyi 2 babu).
Mazaje, kowa yafara shiri, gobe da asuba zamu dauki hanyar kaduna, bansan ranar dawowarmu ba, harsena cika burina na tahowa da Falak, tunda munsamu isassun kudi bamu da damuwa, kudauki jakar kudin muware, lallai yau munyi babbar sa,a. Daukarmun hoton fuskarsu awayata, hakan zemun amfani idan naje gidan, diyar mijinta.
Sedare Sameer yazo yadauki Falak suka wuce gida, Zarah ko sallama bata bari sunyi ba, har mota Jalila da Alh, suka rakosu, Alh, wani irin farin ciki yakeji. Sameer yace Alh, gobe zanzo indaukeka a office kawuna yana son ganinka, yace lallai muje tare akwai wani temako dazeyi maka. To to babu komai, Allah yakaimu, bara insamaka no ta idan kazo seka kirani, yauwa gata, zantura maka da address din office din. Sallama sukayi masu, Falak kamar kada ta tafi takeji.
Kwance Jidda take abisa gado tana tunanin halin datake ciki, gashi cike take da bukatar namiji idan takira Viju akashe, tarasa yanda zatayi, murmushi tayi, tace wlh bazan tausaya ma duk wanda yanemeni da bukataba, yanda aka likamun cuta kowama yasamu badamuwata bace, Allah yakaimu inkara samun sauki, dole insamo me biyamun bukatata, meza,a fasa, tunda harnazo gargara, ai gara kawai incigaba da shakatawa ta. (Lallai kinyi kuskure Jidda, Allah yashirya). Tashi tayi tabude jakarta tadauko maganinta tasha sannan ta kwanta.
Zarah kuwa aranar kasa zuwa dakin Alh, tayi adakinta tayi kwanciyarta sbd batason yawan tambayar da Alh, yake mata, ga abin duniya yafara isarta, takira no wayar Asabe yafi akirga, amma bata shiga, gaba daya ta gama shiga tashin hankali, addu,a kawai take Allah yasa lfy. Amma ta kudira aranta dole gobe taje Zariya. Da wannan tunanin tasamu bacci yadauketa.
Kuyi hkr da wannan.
Urs,
NABILA RABI,U ZANGO
(Nabeelert Lady)
08028525263
[7/16, 12:31] Nabilat Author: 🙆🏻😭😭🙆🏻 AGOLAH!!!Nah
Marubuciyar Zamani
NABILA RABI,U ZANGO
(Nabeelert Lady)
@(H,O,N,A)
Part 125.....130
Karfe 9 na safe Zarah tagama shiryawa tasami Alh, afalo yagama cin abinci yana shirin fita. Bayan sun gaisa, tace Alh, dama zuwa nayi infada maka inaso inje gidan,