Showing 18001 words to 21000 words out of 61588 words
Chapter 7 - AGOLA BOOK COMPLETE DOCUMENT BY Nabila Lawan Zango .txt
baya, sosai Al,amin yake kashe mata kudi, dan shide Allah yajarabeshi da son Jidda, itama haka tana masifar sonshi, dan danan Zarah takara jawo Jidda jikinta ganin yanzu tana samun kudi fiye da da. Haka tafara zirya zuwa Zariya, itama kanta Asabe tayi murnar dawowarta, dan tasan zata cigaba da cin dadi, dan ita tasan abinda Jidda take aikatawa, kuma bata damuwa, dan itama tsohuwar yar duniya ce. Jidda har kasar waje tafara fita ita da Al,amin sbd yanzu arzikinshi yakara habaka, har waje yake zuwa saro kaya, kuma duk sanda zeje tare suke zuwa da Jidda, dan Jidda akwai gayu da gyara, bata wasa da kayan mata.
Zarah ce zaune adakin Asabe, tagama fadamata abinda takeso bokayayi mata. Asabe tace ai dama kyaleki nayi mutuwar tadanyi nisa, sannan inzo maki da irin maganar nan, segashi kinrigani, bara inkira Dije muje, amma ai baje yuwa ba ace AGOLA tafi masu gida. Kuma wlh wannan yaron damuke rainawa, idan har bakiyi da gaske be, wata rana zesaki kuka daga shi har AGOLAR.
Bayan Dije tazo ne suka fada mata abinda suka shirya, murmushi Dije tayi tace meyasa kukeson yin abu bakwa tunawa da mutanen gari, kunsan fa yanzu mutum ake kiwo ba dabba ba, akwai matsala 2 dazaku fuskanta idan har kuka aikata abinda kukace. Tafarko de idan kuka sa aka kori Falak da Ameer daga gidanki, mutane babu wanda zasu zarga seke, har Mijinki keze zarga.
Matsala ta 2 kuma idan har kuka kashe Falak da Ameer, wlh ina me tabbatar maki da kotu seta daureki, dan nasan mijinki baze taba yarda dakeba, dole yasa yan sanda su bincikeki,
Asabe tace wlh shiyasa nakesonki kawata, yanzu me kike ganin za,ayi? Gyara zama Dije tayi tace zanbada shawara 1 amma fa idan tayi maku, Zarah tace wlh kifada zatayi,
Nafarko de za,a kashe Ameer, amma ta hanya mafi sauki wanda babu wanda zeyi zargin kasheshi akayi.
Na biyu kuma, dole zaki mallake Alh, za,a kawar da kanshi daga Falak, tayanda zemanta da ita acikin gidan kome zakiyi mata baze ce komai ba, sauran yan gida kuma ke keda iko akansu, bakamar wannan tsohuwar munafukar, wadda kika yarda da ita sosai.
Se kuma Jalila, ita kuwa diyarki ce kinsan yanda zaki tafiyar da ita. Falak kuwa kada kiyi mata komai, hakan zesa kifita daga zargin mutane, Ameer dama kowa yasan beda lafiya. Amma Falak kimaida ta ita da almajira basuda bam banci, duk wannan dadi datakeji kihanata, Mairo takoma girki kawai, sauran aikin gidan sukoma kanta. Wannan kyawun nata kimaidashi muni, kuma kirabata kwana daki daya da Jalila,
Kimaida ta store tarika kwana ita da kwari sucinye wannan shegen jikin nata, duk wani kayan more rayuwa ki anshe su, kayanta ma zanbaki wasu tsofaffin kayana ki kaimata, tarika sawa, ko aike kasuwa yatashi daga kan driver yakoma kanta.
Kuma kicema Mairo tamaida rikon Ameer hannun Falak bazaki iya cin abincinta ba, tana renon yaro me zubda miyau. Daga karshe kuma kisamu dan kwaya ki aura mata shi, idan bahaka ba kina gani masu kudi zasu aureta, dan kinsan tafi yayanki kyau.
Shiru Zarah tayi, Asabe tace yanaji kinyi shiru, tobari infada maki, wlh ba,a samun duniya da tausayi, idan baki sani ba, nidin nan seda nakashe mutane 2 saboda kudi, kuma duk mazaje nane, nakuma gudu da dukiyarsu, Babanki ma........ Saurin hadiye maganar tayi tuna dawa take magana tayi. Babanki ma saboda irin Son danake mashi ne, yasani zuwa naroki ya aureni, kinsan tunda nake bantaba son wata halitta kamar Babanki ba. Shiyasa gashi nan muna zaune lafiya abummu. Murmushi Dije tayi jin irin saurin kwaskwarimar da Asabe tayi.
Dije tace idan har kika iya aikata abunda nace maki, kawai kihangoki cikin jerin manyan mata masu fada aji akaduna, yanzu ina kawarki Karima, bakince tunda mijinta yamutu ba, tabar garin tana can Abuja gidan kudi, batada aiki sefita kasashe, ina da bakinki kikecewa yanzu ko wayarki bata dauka saboda tayi kudi, wani lokacinma sese me aiki tadauka tace tana bacci.
Haba Hajiya kalleki fa, yanda kike da kyan nan rashin samun kudi masu yawa ne da hutu yarage maki kyawunki, yanzo dan kasuwancin dakikeyi ma kudin duk sushige gurin boka, yanzu haka kila bakida wanda zamuje gurinshi yanzu, dan kinsan aikinshi kamar yankan wuka ne shiyasa yakeda amsar kudi masu tsoka.
Zarah tace wlh, ashirye nake da inyi abinda yafi hakama matukar zansamu kudi, kuma arayuwata babu wadda na tsana kamar Falak, zanyi duk yanda zanyi in kunta tama rayuwarta, bazata taba fin yayana ba, ita Kuma Jalila nasan yanda zanyi da ita, kunsan babu abinda ta tsana kamar fushi na, ko kuma ince zan tsine mata, bakaramun shiga tashin hankali take ba, idan taji furucina ba.
Saboda tana zuwa islamiyya, kuma suna aiki da abinda ake koyamasu sosai, Mairo kuwa kubarni da ita, akarkashin ikona take, kome zanyi bazata iya fadama kowa ba, Alh, ne kawai zata iya fadamawa kuma shima zan mallakeshi. Dariya sukayi gaba daya. Suka tashi zuwa gurin boka.
Wata irin dariya boka yayi yace lallai Hajiya kinzo da babban aiki, kuma aikinki zeci kudi sosai, dan wannan karon zakisani karya maganata dan banayin aiki 2 alokaci 1, amma idan har zaki saki kudi bakida matsala.
Zarah tace boka kamar nawa ne kudinka? Aikin Alh, mesauki ne, zaki bada 150, shikuma Ameer nashi 200 ne, sekizabi 1 idan bakida kudi.
Zarah tace atemaka mun boka yanzu babu kudi sosai, amma ga na Alh, afara yimani aikinshi, se abani na Ameer dana koma bayan kwan 2 nayi maka alkawarin zanturoma Inna Asabe, kudin aikin Ameer takawo maka.
Dije tace boka atemaka mata, kasan yanzu munzama daya. Magani 2 yadauko yabata 1 yace wannan zaki saka ma Alh, acikin abinci, dazaran yaci kingama dashi, wannan kuma wuta zaki samu ko garwashi kifita waje kizuba kamar yanda hayakin nan zetashi sama baze kara dawowa ba, haka tunanin Falak zefita daga zuciyar mijinki, ko yaganta baze tuna amfaninta agurinshi ba.
Wani dan butum butumi yadauko yakama wuyanshi yasa zare yashake wuyan, yace wannan kuma Ameer, tundaga yau babu abinda zekara shiga cikinshi, kome yaci iyakarshi makoshi zedawo, nabaki nan da wani lokaci zemutu. Kuma daya mutu Alh, zemanta dashi, zakici duniyarki da tsinke, sauran kuma sekinje gurin me hukunci. Dariya yasa yace kutashi kutafi, Dije kije sebayan anbaku kudin kwa dawo, Zarah de bata fahimci abinda yake nufi ba.
Baba Mairo itadasu Falak suna zaune adakinta suna fira, ita kuma tana bama Ameer abinci abaki, Jalila tace wai gashi har yamma tayi amma Ummi bata dawoba, bansan meyasa yazu Ummi yawan zuwa Zariya ba, wanda ada batason zuwa.
Baba mairo tace keko tunda tana da mahaifi araye ai dole tarika zuwa. Aranta kuwa tana fadin Allah yasa bawani mugun abun bane yakaita...... bata karasa ba, Ameer yashiga amayar da abunda yakeci, cikin sauri ta dagashi tana sannu ka kware ko,
Ruwa Falak tamika mata tana fadin aishine yacika cin tsiya, ke kuma Baba mairo kita bashi abinci, karbar ruwan tayi tana fadin tunda beda baki aidole inrika bashi abinci akai akai, kodan ke abincin beda meki ba ne, Jalila tace kyaleta Baba mairo sotake shima yazama kamarta yar siririya,,,,,,,, ruwan Baba mairo tabashi, yana amsa yasake amayoshi.
Tadashi zaune tayi takara bashi, abun tunbe basu tsoro har yafara basu, jikinshi Bab mairo ta taba taji babu zafi, tace tomeke damunka Ameer haka? Jalila tace Baba kawai akira driver yakaimu asibiti tunda dady nenan nasan gobe zedawo.
Shiryawa sukayi suka kulle gidan suka ba megadi key din suka tafi, kafin su kai duk yajike Baba mairo da miyau, dan har miyan baya iya hadiyewa. Sunazuwa suka wuce gurin Dr, bayani Jalila tayi mashi, ruwa yadauko yabashi amma yamaidoshi.
Abu kamar wasa jikin yaro yafara rikicewa, tun likita yana daukar abun wasa, shima yafara shiga damuwa, daki yabasu aka kwantar dashi aka samashi karin ruwa da allurai, sannan yayi bacci.
Baba mairo babu wadda take zargi se Zarah, dan tariga data lura duk lokacin da taje Zariya sewani abu marar kyau yafaru akansu Hajjo, yanzu gashinan ta kauda Hajjo takoma kan danta, duk da tasan cewar itace tayi sanadiyyar maidashi dolo, yanzumma bata debe tammanin tanada sa hannu acikin wannan ciwon nashi ba.
Jalila takira dadynsu awaya tafada mashi, yace gashi nan yanzu zetaho, haka sukacigaba dazama, Falak se kuka takeyi, Jalila tana lallashinta, duk itama hawayen takeyi.
Koda Zarah tadawo, megadi yabata key, yace mata sunje asibiti kai Ameer, murmushi tayi aranta tace boka aikin ka nakyau, saurin shiga cikin gida tayi, kayanta kawai ta aje tadauko gawayi tadorashi akan electric burner seda yayi ja, sannan takashe, dauka tayi tanufi gurin part din Hajjo daga baya ta ajeshi, maganin tadauko tazuba aciki, nan take hayaki ua turnuke, sama yayi tayi har yacinye, kakkabe hannunta tayi tana fadin su AGOLA anzama baiwa. Saura kai Alh, Allah yamaidoka gobe.
Ciki tashiga tayi wanka tana saka kaya taji horn din. Alh, murmushi tayi tace wato kai game da anayi maka waya harkataho, nasan Jalilan banzan nan ce zata fada maka, kema zaki dawo kisameni ne,
Da sallama yashigo yace ah, Hajiya bada ke aka tafi asibitin ba? Yatsina fuska tayi tace nim yanzu nadawo daga Zariya, megadi yake fadamun, wanka nayi nake shirin tafiya, ok fito mutafi gaba daya. Falak ce takiraka ko? Shiru yayi yana kallonta, jin ankira sunan Falak seda kanshi yasara.
Murmushi tayi tace yanaji kayi shiru, Fala...... tsawar daya daka mata ce tasa ta yin shiru, meye haka wacece kuma wata Falak, kada inkara jin wannan sunan agidan nan, kema kika santa, Jalila takirani amma kirika fadamun wani suna, banaso, kiwuce mutafi.
Suna zuwa office din likita yawuce, bayan sungaisa Dr, yace agaskiya Alh, nakasa gano wace irin cutace ajikin Ameer, duk wani gwaji munyi mashi amma bamu sami wata cuta dazata nuna mana asalin ciwon shiba.
Abinda nake ganin zefi kumaidashi gida acigaba dayi mashi na hausa, dan gaskiya ina ganin ciwonshi kamar akwai aljanu aciki. Alh, yace hakane, nikaina nafara tunanin haka, tun sadda yafara zubar da miyan bakinshi, da kuma kanshi da baya zama, haryanzu fa Ameer baya iya zama. Bakomai nagode bara naje mutafi, dr, yace nacire mashi karin ruwan ma dan naga jikinshi baya bukatar ruwa, sede matsalar rashin cin abincin shi, idan har kuka koma gida yacigaba da mayar da duk abinda yaci, zan iya zuwa gidan, ko insa azo arika samashi karin ruwa. Godiya sosai, yayi mashi yatashi suka fita.
Tunda yashiga dakin Jalila da Falak sukayi mashi sannu dazuwa, ya amsa yace Jalila yagidan, tace lfiya lau dady, ko kallon inda Falak take beyiba. Baba mairo tagaisheshi ya amsa yana tambayarta Ameer da jiki.
Zarah farin ciki ne aranta, fal, ganin yanda yayi ma Falak, sukuwa basu kawo komai aransu ba, ganin halin da ake ciki, Alh, yace sutashi sutafi gida, ansallamesu, anan yayi masu bayanin da Dr, yayi mashi. Baba mairo tace idan ko haka ne, Alh, se akaishi gurin Malami. Zarah tace koma de menene kuwuce muje, gida. Kallon mamaki Baba mairo tabita dashi, haka suka wuce da driver ita kuma tabi Alh, aranta tana fadin dole yau kaci maganin nan ko aikina zefara dawuri.
Urs,
NABILA RABI,U ZANGO
(Nabeelert Lady)
08028525263
[7/13, 09:40] Nabilat Author: 🙆🏻😭😭🙆🏻 AGOLAH!!! Nah,
Marubuciyar Zamani
NABILA RABI,U ZANGO
( Nabeelert Lady)
@( H,O,N,A)
Part 60..... 65
Suna zuwa gida Baba mairo ta kwantar da Ameer, su Falak kuma suka wuce daki domin yinsallar magrib. Wucewa kitchen Baba mairo tayi domin dumama masu abinci tayi, shikuma Alh, tadora mashi abinci mesauki, daki takoma tayi sallah.
Bayan tafito ta koma kitchen tana hadama Zarah abincin Alh, Zarah ce tashigo kitchen, din, tace yau mairo jeki dakina kidauko mun wayata bisa gado, tana fita tayi saurin bude cooler din Alh, taciro magani tazuba, kokarin maidawa tayi azaninta, juyawar dazatayi taci karo da mairo tana kallonta mamaki dauke afuskarta.
Cike da duniyanci Zarah tace shigo mana Mairo naga kintsaya kina kallona, Mairo tace dan Allah Hajiya wane irin magani ne kika sama Alh, kinga duk abinda yasame shi ni za,a zarga tunda ni nayi girkin.
Murmushi Zarah tayi, tace bazan fada maki ko maganin menene ba, idan yaci kome yasameshi aka kamaki, zakiyi bayani, ido waje Mairo tace kirufa mun asiri dan Allah hajiya.
Zarah tace naji. Amma da sharadi, banaso kowa yaji wannan maganar, kuma daga yau duk abinda zance maki banason gardama kinsan de ni nakawoki gidan nan ko? Saboda haka kina karkashin ikona, banason shishshigi, ki tsaya amatsayinki na me aiki, daga yau banaso ki kara fitowa daga dakinki matukar Alh, na gidan nan.
Kuma daga yau, zaki maida Ameer hannun Falak, dan baze yuwa kina girki kuma kina renon kazamin yaro ba, aiki yanzu ze koma girki kawai, naruwanki da wanke wanke nasamu wadda zata rikayi mani harma da wankin kayana.
Inafatan kingane menake nufi, idan kinbi umarnina kicigaba dazama agidan nan, idan kuma kinki, zaki tafi kuma kibar amanar da Hajjo tabaki, dan nasan kafin tamutu tamika amanar yaranta agurinki.
Zabi yarage naki, kuma wlh idan kika kuskura kika rika shiga harkar Falak sekin barmun gidana. Zaki iya tafiya. Fita Baba mairo tayi tana kwalla, wannan wane irin sabon yanayine yashigo gidan nan, anya Hajiya bata fara shaye shaye ba? Ya Allah katsare bayinka kuma marayunka, tabbas Falak nasan rayuwarku zata shiga, kunci, sede bazan bari inyi abinda za,a koreni daga gidan nan ba, nasan idan natafi zakifi shiga damuwa sosai, kuma nasan wasiyar ummanki bazata bari kibar gidan nan ba, dasemu tafi tare.
Abincin tadauka takaima Alh, yana shirin zuwa yaga Ameer tashiga, tace ina kuma zakaje Alh,? Yace Ameer. Zan dubo, tace daga can nake yasamu bacci, kuma yaci abinci, kabarshi yayi bacci tunda yasamu yayi. To Alhamdulillah, Allah yakara bashi lfiya, wlh har hankalina ya kwanta, banason ciwon yaron nan.
Abinci tazuba mashi tana ta janshi ta wasa, sewani shige mashi takeyi, shi kuma duk ya rude, abaki tadebo zata bashi, ganin yana niyar yin bismilla, yasata fadawa jikinshi, dariya yasaka yana shirin yin magana tayi saurin saka mashi abincin abaki.
Taunawa yakeyi yana fadin Hajiya yaude naga alamar amarci kikeso musha, ko? Kara debowa tayi tasaka mashi yakarba, tana ta yimashi kwarkwasa, shikuma duk ya rude. Ahaka haryagama ci beyi bisimilla ba.
Yana gama ci yasha ruwa, ana take yai kanshi yayi mashi nauyi, rike kanshi yayi, kamoshi tayi ta dorashi bisa cinyarta tana shafa bayanshi, da haka haryaji kan ya lafa. Shiru yayi nawani dan lokaci, sannan yatashi yace zanyi wanka idan nafito se inje inga jikin Ameer. Bata fuska tayi tace nace bazaka jeba, kabari se gobe. Nan take yace to hajiya, inje inyi wankan ko?
Wani murmushi Zarah tayi, aranta tana fadin wlh dagaske maganina yaci, kai amma dole incika ma boka alkawarinshi. Kara daure fuska tayi tace zauna inason magana da kai, zama yayi yace inajinki. Kudi nakeso zansaro kaya. To to kamar nawa kike bukata? Dubu dari 5 nakeso.
Yace toshikenan yanzu na hannuna basu kaiba, tace ina check dinka? Yace yana nan, to kadauko karubutamun gobe se inje incira. Tashi yayi jiki na rawa yadauko ya rubuta mata, yamika mata, tace haba Alh, atsaye zaka bani kamar wata yarka, yace yi hakuri Hajiya, dukawa yayi yabata. Tace tashi kaje kayi wanka idan kafito kuma bance kafita ko ina ba, sallar isha,in ma kayita agida, idan kagama katsaya afalonka kayi kallo, idan kanajin bacci kayi kwanciyarka. Yace to Hajiya sekin shigo.
Fita tayi tana me cike da fari ciki tana shiga dakinta tace wlh, Alh, sekayi dana sanin yimani kishiya, sena maidaka abun tausayi arayuwa, daga yau bakai ba Ameer da shegiyar AGOLAR KA.
Juyawar dazatayi taci karo da Jalila tana gyara mata gadonta. Cike da firgici, tace Uban waya kawoki dakina? Jalila da tunda taji kalaman Umminta jikinta yafara rawa, kafin tayi magana hawaye sun wanke mata fuskarta.
Jawota tayi ta kwada mata mari tace ina magana shine zakimun shiru, wato labe kikemun ko, Jalila tace dan Allah Ummi kiyi hakuri, nibanji abinda kika ceba, kawai nashigo inamaki gyaran dakine.
Zarah tace idan ma kinji, bakiji karya ba, kuma zauna kibude kunnuwanki da kyau kije abinda zan fada maki, nasan sarai kinji maganar danayi, to haka yake bakiji karya ba, tunda Babanku ya auro uwar su Falak naji natsanesu, gashi nj bantaba haihuwar naminj ba, amma tana zuwa tahaifa.
Saboda haka idan harkina kishina, kuma kindaukeni amatsayin uwa, wadda ta tayi renonki tunkina jini harkika koma tsoka, akasa maki kashi, kika girma acikina, ki hanani bacci, kocin abinci, kika hanani sukuni, sannan nasha wahalar haihuwarki, seda nadauki tsawon awa 1 ina nakudarki kafin kika buda jikina kika fito.
Nashayar dake daga jinin jikin, suk dare duk rana kina tare dani, bana bacci sekinyi, kimun fitsari da kashi in wanke, har kika girma ina dawainiya dake harzuwa yanzu.
Shin akwai wani umarni dazan baki ki kasa binsa? Kai tashiga girgizawa tana kuka, jin yanda Umminta tasha wahala akanta. Murmushi Zarah tayi ganin yanda jikin Jalila yayi sanyi.
Tace Jalila amatsayina na mahaifiyarki, inaso duk abinda zakiga ya canza agidan nan kada kiyi magana ko kuma kiyi tambaya akanshi.
Daga yanzu tarayyarki da Falak tazo karshe abanason ina ganinku tare, bazata kara zuwa isilamiyya ba, kuma ayau zata bar dakinki, zata koma store itada kaninta dan renonshi yakoma hannunta, kuma daga yau itace sabuwar me yimun wanke wanke da wanki, harma dazuwa kasuwa.
Idan harkika kara yima Dadynku maganar Ameer ko Falak, sena tsine maki, dasauri Jalila tadago kanta tana kuka, tace Ummi dan Allah kada kitsine mun, wlh wuta zanshiga, nayarda zanbi duk abinda kikace, amma kijanye maganar tsinuwa.
Murmushi Zarah tayi, tace bazan janyeba harsenaga kinbi umarnina, ko Alh, yamaki maganar makaranta, nasan naze saka da Falak ba, danshima yamanta da ita, bance kimashi maganarta ba. Kinji abida nafada maki ko? Tace E Ummi, kiyi hakuri dan Allah, tace shikenan nayi tashi ki kiramun Falak.
Fita tayi tana wani irin kuka, tana zuwa takalli Falak gaba daya tausayinta yakamata. Falak tace Jalila lafiyarki kike kuka? Tace bakomai kije Ummi nakira, fita tayi tana murmushi tace yanzu haka laifi kikayi mata ko, bara inje inji mekikai mata, idan har bata mata rai kikayi kisani nima baruwana dake. Wani sabon kuka ne yazoma Jalila, tanajin tausayin Falak sosai.
Tana zuwa tayi sallama tace Ummi hala Jalilace tayi...... Saukar marin datajine yahanata karasa maganar datakeyi, zaki tsugunna ko kuwa sena takaki agurin nan, munafuka me kama da Uwarta. Mamaki ne yakama Falak jin yanda Ummi take zagin Ummanta, zama tayi akasa, taan fitar da kwalla.
Zarah, tace kibude kunnuwanki