Showing 51001 words to 54000 words out of 61588 words

Chapter 18 - AGOLA BOOK COMPLETE DOCUMENT BY Nabila Lawan Zango .txt

yashiga tashin hankali, kuma sbd shi da diyarshi zan nema mata magani, amma da munbarta duniya ta koya mata hnkli, duk da ayanzu ma tafara gane kuranta, tunda ance anyanke mata kafa. Umman Sameer tace ai bakomai yanzu suma sunzama yan uwanmu. Allah yakara basu lfy.


Malam Garba mahaifin Zarah da Alh, ne suka shigo asibitin, kasancewar ya iskeshi agida shine suka taho tare. Mal. Garba yace dan Allah Alh, kayi hkr da irin abinda wannan yarinya tayi maka. Babu irin yanda banyi da ita ba, amma bataji magana taba, tabbas babu abinda zance tsakanina da Asabe sede ince Allah ya isa, duk da kacemun ankashe su, amma bazan yafe mata ba, ita da kawarta, sun cuceni, gashi seda cutar takai harzuwa diyata, duk da itama da laifinta amma Asabe babbar annobace agidana.


Alh, yace bakomai Baba, Allah yakara basu lfy. Yace ameen, kuma hukuncin daka dauka akanta kayi dede, nima dande kawai zuciyar Imani amma da ko zuwa bazanyi ba, to Jalila tayi tamun kuka, kuma ina son Jalila, shiyasa nace zanzo sbd ita. Amma tabbas idan ta warke sede taje wani gurin tayi haukanta amma ba gidana ba. Alh, yace kayi hkr muje de muga jinkin nasu.


Suna shiga suka wuce Office, anan Dr, yayi masu bayani. Alh yayi shiru dan yana kunyar mal. Garba, ganin yayi shiru Babanta yace to ai ita tasani, kuyi mata abunda zaku iya kawai ku sallameta. Alh yace a,a Baba baza,ayi haka ba, Dr, inaganin abinda ze faru zansamu wani malami zamuyi maganar dashi dan gsky haukanta bana asibiti bane, kome kenan zanzo mukara magana. Dr, yace gsky dayafi, dan tana cikin wani hali, kome tayi kubarta da halinta amma ceton rai zakuyi kuma kamar jihadi ne, koba komai ai Uwar yaranka ce, kai kuma Baba ai diyarka ce, kasan da mahaifiyarta tana nan kome zata zama bazata iya barma duniya ita ba. Jikin Baba yayi sanyi yace haka ne, likita, kuma nagode da tunatarwar dakamun. Allah yamana jagora. Fita sukayi suka nufi dakin Jidda.


Adakin suka sami su Falak harsunzo, bayan sungama gaisawa, Alh, yace Jalila yajikin nata? Tace to Dady dasauki za,a ce, amma kome taci amai takeyi, yakalli Jidda gaba daya tausayinta yakara kamashi yace sannu Mamana, tace yauwa Dady, kidaure kirika cin abinci maganin baze maki amfani ba, idan baki cin abinci. Kuma banaso kirika saka damuwa akanki, mutane nawa suke dauke da irin cutarki gasunan muna hudda dasu wasu ma harsun fimu lfy da kyan fata, babu wanda ze kallesu yace suna da wata cuta. Meyasa suka zama haka? Sbd suna shan maganinsu, kuma suna cin abinci me kyau, dan haka kicire komai aranki, nide nayafe maki, insha Allahu zaki samu lfy.


Baba Mairo tace yanzu Alh, yajikin Zarah? Yace to banje ma naganta ba, dan Dr, yace mun sunyi mata allurar bacci, dan da asuba data tashi haukan yadawo sabo, duk tajima kanta ciwo, kuma ta fama ciwon kafarta, shiyasa yace dole asamu wanda zerika kula da ita.


Baba Mairo tace bakomai Alh, kome zamuyi, zamuyi ne, dan Allah da kai da kuma yaranta. Nizan zauna agurinta ita kuma Halima zata zauna agurin Jidda, tunda Jalila tayi yarinta ace tayi jinya. Alh, yace to mungode sosai Allah yasa da alkhairi. Baba Mairo tace, ammade bikinta dagawa za,ayi ko? Alh, yace ina tunanin haka, duk da nariga dana gama gayyatar abokanaina, amma tunda lalura ta gifto dole adaga.


Mal. Garba yace a,a baza,ayi haka ba, wannan yarinya ta dade ana shiga hakkinta, acikinsu babu wanda tacema yashiga rayuwar da yayi, dan haka saboda su baza,a daga bikinta ba, acikinmu waye yasan lokacin dazasu warke? To kuma kawai se ashiga hakkin baiwar Allah ace sesun warke za,ayi bikinta. Shima mijin ai anshiga hakkinshi, yagama fada ma kowa nashi, ai bikin magaji baya hana na magajiya, dan haka abar bikin nan da kwana 5 kmar yanda akasa, Allah yabasu lfy.


Alh, yace shikenan dama gani nayi kamar Jalilan bataso ayi acikin wannan halin shiyasa zan daga, amma shikenan ke Jalila kiyi hkr, nasan bazakiji dadi ba, ace za,ayi bikinki a irin wannan yanayin komai zezo karshe, ranar asabar za,a daura aurenki kuma aranar za,a kaiki. Kuka Jalila tasaka ta tashi tafita, seda tabama kowa tausayi adakin.


Ur's
NABILA RABI'U ZANGO
(Nabeelert Lady)
08028525263
🙆🏻😭😭🙆🏻 AGOLAH!!! Nah
Marubuciyar Zamani
NABILA RABI'U ZANGO
(Nabeelert Lady)


@ ( H,O,N,A)


Part 170.....175


Haka suka wuni a asibiti, Falak da Jalila ne, suka koma gida suka yomasu girki, Kawun Sameer kuwa dakin Zarah yaje shida mal, Garba da Alh, anan yafara yimata addu,oi, shiyasa lokacin data farka batayi wani hauka me yawa ba, Baba Mairo tana gefenta ita tarika bata abinci da kyar taci sbd wasan datakeyi.


Lokacin da Saleem yazo shida Sameer bayan yaduba jikin Jidda yakira Jalila suka fita waje, cike da tausayi ya kalleta yace my dear wlh harkin rame. Murmushi tayi tace ba dole ba, yace haka ne, dazu munyi magana da Sameer har nake cemashi koza,a daga bikinmu ne, yace mun a,a Dady yace baza,a daga ba. Jalila tace nima naso adaga amma Baba na Zariya yace a,a.


Saleem yace babu damuwa ki kwantar da hankalinki babu abinda ze gagara insha Allah, fatanmu de Allah yabasu lfy, tace ameen. Yanzu mekike bukata, nasande bawani abu kikace zakiyi ba ko? Tace hakane, walima ce kawai zamuyi da yan islamiyarmu, yace shikenan idan nabaku dubu 100 yayi ko? Murmushi tayi tace basuyi yawa ba? Harararta yayi yace bansani ba, anfada maki bikin wasa zanyi, wasu ma a party kadai suke kashe abinda yafi haka, seni daza,ayi walima zakice wai sunyi yawa. Tace tonaji maida wukar, Allah yasaka da alkhairi, yace yauwa ko kefa.


Sameer yafadamun duk abinda yafaru jiya, kuma munyi magana da Abbana sede banfada mashi komai ba, kawaide nace ba,a san abinda yasamu Ummi ba, kuma yakira Dadyn ma sunyi magana, yace zeshigo yadubata se Dady yace a,a yabari tunda saura kwana 4 daurin aure seyayi zuwa daya. Kwallan dasuka zubo mata ta goge, tace nagode, bansan dawane baki zanyi maka godiya ba. Yace bakida bakin yimani godiya sbd kinbiyani dakika amince zaki aure ni. Amma inason inrokeki wani abu 1. Wannan yawan kukan da kikeyi yayi yawa, dan Allah kidena, nasan dole ne, amma inaso kiyawaita fadin Innalillahi wa inna ilaihirraji'un aduk lokacin da kikaji wata damuwa tadameki. Tace shikenan nagode.


Haka suka cigaba da jinyar Zarah da Jidda, jikin Zarah kam ana samun cigaba, amma jikin Jidda ba sauki, duk ta rame tayi baki, idan kaganta bazaka ce Jiddar daka sani bace, haryanzu aljanun jikin Zarah basuyi magana ba, sede haukan dasauki, tana samun sauki aduk lokacin da ake mata addu,a amma idan har bakowa agurinta haka zakaga kafarta tana fitar da wani irin ruwa marar kyau, kuma aranar se ansake wani gyaran dan ta kafarta suke cutar da ita, shiyasa har yanzu kafarta kamar sabon ciwo ne.


Hakan yasa Kawu yace ma Alh, dole zeyima wani abokinshi Babban malami ne, kuma yana da sani sosai akan harkar aljanu, Alh, yace to amma abari bayan biki seyazo.


Kasancewar bawani cikin keanciyar hankali ake ba, hakan yasa Jalila bata samu gyara sosai ba, sede duk da haka Falak tana kawo mata wasu abubuwan sha tana sha, Falak takaita gurin saloon akayi mata, takira wata me kunshi tayi mata, duk da ta rame amma tayi kyau sosai, duk wani shiri da za,ayi na Walima wata kawarta yar ajinsu ta mika ma komai Bilkisu, tare da wata Farida, duk ajinsu daya, malamansu da Sameer sune suka shirya komai, kuna anan makarantarsu za,ayi walimar.


Ana gobe daurin aure ranar juma,a kenan wanda kuma aranar da karfe 4 za,ayi walimar, zaune suke adakin Jidda, tana kishingide tana shan kankana, fuskarta har wasu kuraje sun fara fito mata, kadan kadan tana goge kwallar datake fito mata. Falak tace Yaya Jidda dan Allah kidena wannan kukan, babu ranar dazata zo bakiyi kuka ba. Jidda tace Uhm Falak kenan, nikadai nasan menakeji araina, da jikina. Kamata yayi ace hadani akae wannan hidimar bikinta Jalila, amma sbd son zuciya da biyema rudun duniya kalli yanda nadawo, ina nan kwance za,ayi bikin Jalila, wanda gashi de da raina amma banida ikon halartar bikin, wannan kadai ya isheni ishara.


Kalli Ummi, duk yanda taci buri da bikin nan, amma gashinan son zuciya da rudun duniya itama ya kamata ahannu, har garani nasan me akeyi, amma ita batasan meke faruwa ba, kuma hakan bazesa adaga bikin ba. Lallai mun ishi duk wani me hankali zama abun kwatance. Jalila tana kuka tace Yaya Jidda kiyi hkr Allah yana karbar tubar me tuba, insha Allahu zaki kasance daya daga cikinsu.


Baba Mairo da Umman Sameer ce suka shigo sun dawo daga dakin Zarah sunyi mata wanka, Baba Mairo tace Falak kuzo kutafi kishiryata kinga har 3 tayi, kada ayita jiranku kunsan taro za,ayi sosai bekamata ace ku tsaida mutane ba. Kuma idan kingama kisamu guri kizauna kinsan jikinki yayi nauyi, tace to. Kama Jalila tayi wadda take ta kuka, tace muje, Jalila tace tomuje inga Ummi sannan. Baba Mairo tace kuje taganta seku wuce. Kara kallon Jidda tayi, Allah sarki Jidda kifar da kanta saman cinyarta tayi, tana wani irin kuka me ban tausayi, seda tasaka su kuka. Haka Falak tajata suka nufi dakin Zarah.


Kwance take tana bacci, gaba daya tayi bakikkirin fuskarta kamar an shafa mata bakin tukunya, kafarta meciwo takoma siririya tundaga guiwarta har dungulmin da aka yanke, babu kyan gani, gashi duk tarame, kamar ba ita bace me kiba da jiki me kyau, shiru Jalila tayi tana kallonta, tace Allah yabaki lafiya Ummi. Falak ta kalleta, seta tuna Ummanta, lokacin tana cikin rashin lafiya, zuwa tayi ta taba jikin Zarah, taji babu zafi, kai ta girgiza tace ai dasauki ma tunda ita batajin zafin jikinta. Saurin fita tayi sbd kukan daya taho mata. Jalila tagane me Falak take nufi, duk se tausayinta yakamata, tace kingani ko Ummi, mutanen dakika cuta kika maida banzaye yau gashi sune suke maki rana,


Yaugashi Falak da kikaso akashe, itace take amatsayin daya kamata ace kece kikemun abinda takemun. Goge idonta tayi tace Allah yasa kina cikin wadanda Allah ze gafarta ma kura kurensu, sede nasan baze yafe maki laifin bayin dakika cuta ba. Saurin fita tayi tajawo kofar tasamu Falak amota suka tafi.


Jalila tayi kyau sosai tasha hijabinta harkasa, haka tazauna, agefenta Falak ce itama tasha hijabinta da katon cikinta, mutane dayawa sun halarci taron, taro yayi taro sosai aka gayyaci mutane dayawa, kasancewar Jalila tanada kokari amakarantar. Bangaren manyan mutane daban, hatta da Mahaifin Saleem seda yazo shida abokananshi sbd suntaho har daurin aure, Saleem da abokananshi suma sun halarci gurin, Sameer kuwa sune manyan malamai, suna ta hidima da mutane, Alh, da Kawunshi da Mal. Garba dasauran abokananshi daya gayyata duk suna zaune acikin rumfa.


Kanshi yadaga yaga irin mutanen dasuka halarcin gurin kawai seyaji kwalla tacika mashi ido, glass dinshi yaciro yasaka, Kawunshi wanda yana kula dashi yace haba Abba, kayi hkr mana kada kabari mutanen dasuke gurin nan su fahimci halin da kake ciki, nasan kana tunanin babu mahaifiyar Jalila agurin nan, da babu ita akwai wani abu daya ragu? Kalli gefen iyaye mata kagani, ga medakina can da sauran yan uwa waye ze iya cewa babu Zarah agurin? Sede wanda yasanta, kuma kowa ai yasan rashin lafiya ko. Alh, yace shikenan kawu nagode.


Haka aka fara bude taro da addu,a sannan aka gabatar da manyan baki, aka kira Jalila domin ta karanta wata sura daga cikin Qur'ani amatsayinta na wadda akema walima, da kyar tafito, seda Falak ta anshi nikaf din wata tabata tasa, sbd tundazu take kuka. Haka tafara karatu cikin dadin murya, sede dakaji muryarta kasan muryar kuka ce, tana cikin karatun tafara kuka, seda ta burge mutane dayawa, sbd sun dauka karatun ne da murna suka sata kuka, wadanda suka san halin datake cike ne kawai suka san dalilin kukanta. Shikanshi Alh, seda yatashi bada sanin kowa ba yanufi cikin motarshi yazauna yarika kuka kamar karamin yaro, seda yaji dadin zuciyarshi sannan yafito, dayake bakin glass yasa babu wanda yake ganin idonshi. Yana zama Kawunshi yagane meyayi, shima kanshi tausayinshi yakeji.


Ganin Jalila tana kuka yasa Sameer yaje ya amshi lasifikar yayi mata godiya duk da shima jikinshi yayi sanyi. Saleem kuwa seda yayi yan kwalla, har abokananshi suna janshi. Gaba daya tausayin Jalila da Sonta suke kara ratsashi.


Haka aka kira Alh, yazo yayi jawabi, dauriya kawai yayi yafito, yana magana shima muryarshi tana rawa, ahaka yasamu yagama, sannan aka cigaba da. Wa,azi. Se karfe 6:00 dede aka tashi, tare da mika ma Jalila kyaututtuka, haka kuma tasamu kyautar kudi daga gurin bakin dasukazo, aka rarraba kayan ciye ciye kowa ya watse.


Adaran ranar su Baba Mairo sukaje suka bada duk wani abinda za,a girka gobe, ita da Hajiya Fatima matar kawaun Alh, dayake anan gidan yace su sauka, sbd itama tasan komai daya faru, ko kayan gara nasiye suka siya sbd lokaci yakure ba,ayi ba, kuma sunje sunyi mata jerenta, dan dama ansayi kayan dakin, sauran abinda ba,a siya ba, na kitchen suka bari se gobe da safe suje su siyo.


Haka suka tsara komai, da sauran yan uwan Alh, dasukazo, abangaran Zarah kam babu wanda yazo se yan uwan Babanta, shima cewa sukayi sbd Jalila da Alh, sukazo dan ita bata yarda suba, amma ko asibitin babu wanda yaleka. Gida kam yacika ba laifi mutane sun taru.


Adaren ranar jikin Jidda yayi tsanani cikin dare tarika suma, haka Umman Sameer da Baba Mairo suke tsaye akanta da sauran nurse, ganin jikin yaki sauki yasa wata nurse tayi ma Dr, waya acikin daren.


Ur's
NABILA RABI'U ZANGO
(Nabeelert Lady)
08028525263
🙆🏻😭😭🙆🏻 AGOLAH!!! Nah
Marubuciyar Zamani
NABILA RABI'U ZANGO
(Nabeelert Lady)


@ (H,O,N,A)


Part 175.....180


Se da asuba suka samu jikinta ya dedeta, haka aka samata oxygen har seda numfashinta yadawo dede, duk abinda akeyi su Jalila basu sani ba, dan Baba Mairo tace kada afada masu tunda dare yayi.


Da misalin karfe 6 nasafe Alh, ya iso asibitin anan yakejin abinda yafaru, cike da damuwa yace amma Baba Mairo ai da kunsanar dani, ko dare yayi ai zan iya zuwa, tace hakane Alh, yace sannunku Allah yasaka maku da alkhairinsa, Baba Mairo tace Ameen ai ba komai, duk munzama daya.


Fita yayi yadubo jikin Zarah, tana kwance kamar gawa sbd allurar bacci ake mata idan dare yayi dan kada ta farka tajima kanta ciwo, haryanzu bata farka ba, tausayinta yakara kamashi, yace kaiconki Zarah, kalli yanda kika jama kanki bala,i ana bikin diyarki amma kina kwance cikin hauka, juyawa yayi yafita, yabiya gurin Dr, anan yake kara mashi bayani akan ciwon Jidda. Alh, yace Dr, kode afita da ita waje, ciwonta yana bani tsoro?.


Dr, yace E to hakan ma yana da kyau, amma gsky matsalar Jidda bawani abu bane kawai cutar jikinta ce taci karfin jikinta, kuma da karfi tasamu nasarar karya garkuwar jikinta bawai dan takai lokacin ba, da farko tayi sakaci batazo asibiti dawuri ba, na biyu kuma tafara shan magani tabari. Na ukku kuma yanzu kwata kwata maganin baya yimata amfani ajikinta, sbd kotasha amayar dashi takeyi.


Karin ruwan da ake samata ne, kadai yake amfani ajikinta, kuma babbar matsalar bata cin abinci sosai, kotaci ma baya zama. Wadannan sune matsalar Jidda, kuma duk inda kuka kaita, basuda abinda zasu mata. Alh, yace shikenan Dr, nagode. Dr, yace se hkr Alh, Allah ya jarabceka da lalura, amma idan kayi hkr wata rana komai zewuce. Karfe nawa ne daurin auren? Karfe 2 ne, toshikenan Allah ya kaimu. Sallam yayi mashi yafita.


Da misalin karfe 2 dede na rana dubban mutane suka sheda daurin auran Jalila da Saleem, wanda akayi abisa sadaki dubu 50. Adede lokacin su Jalila da Falak suna asibiti, dan Jalila cewa tayi bazata zauna agida ba, tasan anjima babu wanda zebarta tazo asibiti, zaune take agaban Zarah, se kuka takeyi. Zarah kuwa tana kallonta tana dariya tana dariya, Falak tana gefe ta kalli Jalila tace haba Jalila kukan ya isa haka, Jalila tace dole inyi kuka Falak, ace ayau ana daurin aure na, amma Ummina da Yayata suna kwance agadon asibiti, kuma su duka babu me ciwon daza,a fada ta dadi, dukansu su suka jama kansu, yakike so inyi? Kinaji jiya agabanmu wasu suke gulmar Yaya da Ummi, sbd kome kake boyewa dole mutane su sani.


Wlh yafi acema banda Uwa za,ayi bikina hakan zefi mani insan cewar bata raye bazan damu da rashin wanda zemun nasiha ba, amma gata araye kuma cikin halin hauka, wanda zuwa yanzu mutane dayawa sunsan cewar ta hauka ce, kuma qai qayine yakoma kan mashekiya, yakike tunani idan dangin mijina sukaji haka? Nide wlh Ummin kin..... Falak tayi saurin rufe mata baki tace haba Jalila da iliminki, da komai, kinsan fa kome Uwa tazama ba,a canza ta ko? Dan haka inaso kitoshe kunnuwanki da duk wata magana dazakiji daga gurin dangin mijinki, kuma duk wanda yatareki da maganar kiyi banza ki kyaleshi shine kawai abinda ze kwaceki daga gurinsu.


Baba Mairo ce tashigo, cak ta tsaya ganin haryanzu basu tafi ba, tace mezan gani haka Falak? Kinsan fa tundazu aka daura auren yakamata ace kuna gida yanzu tasamu takara wanka sannan taci abinci. Falak tace wlh abinda nake fada mata kenan, tonaji kema ai nace kidena yawo dayawa ko, kinsan fa kinshiga watan haihuwarki, dan likita yace zaki iya kara kwanaki ba lallai bane ace kinsan lokacin, kuma wahala ma tanasa mutum ya haihu babu shiri, nide kutashi kutafi.


Jalila tace Baba Mairo yajikin Yaya Jiddan, munje dakin akace antafi da ita za,ayi mata test. A,a jikinta dasauki nabaro Halima agurin suna can gaba yanzu zasu dawo, Falak tace muje driver yana jiranmu.


Fita sukayi suka nufi dakin da aka kai Jidda test, atare suka jero, tana bisa wheel chair ana turata, wasu mata da miji suka wuce su mijin yana dauke da yaronshi, harsun wuce Jidda tace ma Jalila dan kwalama wancan kira kice Al,amin. Jalila tace kinsanshi ne? Tace inaji kamar shine, amma kirashi mugani. Jalila tace Al,amin. Cak ya tsaya atare suka juyo da matarshi, dawowa sukayi da baya, dan danan matar ta bata fuska.
Al,amin yace sannunku yamejiki? Jalila tace dasauki, kuma itace ma tace amaka magana. Kallon Jidda yayi cike da tausayi yace sannu baiwar Allah yajikin? Kuka Jidda tasa, kowa ya tsaya yana kallonta, Matarshi tace dan Allah honey muje kasanfa akwai inda zamu biya ko.


Jidda tace Al,amin, Ameerah, cike da mamaki matar takara kallonta tace ni kuma? A ina kikasanni? Goge kwallan idonta tayi tace

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login