Showing 57001 words to 60000 words out of 61588 words
Chapter 20 - AGOLA BOOK COMPLETE DOCUMENT BY Nabila Lawan Zango .txt
inzauna mata. Sameer yayi murmushi yace haba Baba yanzu dan Allah so kuke inzama gauron karfi da yaji? Inde haka ne, nima sede indawo nan. Baba Mairo tace nidama ai bance zan hanaka ganin matarka ba, sekaje ka kullo gidan kaima kadawo nan idan sukayi ko wata daya ne, sunyi kwari se ku koma gidanku. Yace shikenan nagode, tace yauwa zanje insamu Alh.
Da misalin karfe , Kawun Sameer suka iso da Malamin dazeyima Zarah karatu, Alokacin shima Sameer ya iso gidan da akwatinshi, dan Alh, yace shima yadawo, a dakin Falak yasauka, su kuma su Baba Mairo suna dakin Hajjo, Alh, shi kadai a part dinsu.
Afalo akayimata shinfida bayan sunyi mata alwala, malamin yazo yafara yi mata karatu, yadade yana karatu amma sunkiyin magana, sbd manyan aljanune, kuma bakake, yasha wahala sosai, kafin suka fara magana.
Wayyo Malam, ya isa zamuyi magana wlh, zufar goshin shi yagoge yace inajinku..... nide sunana Zurkum, kuma nine shugaban bakaken aljanu, wannan matar bata da kirki, sunyi da megidanmu akan duk lokacin da mijinta yagane halin datake ciki, akwai abinda ze sameta, amma haka ta amince, mu kuma dama mune yasa muke mata aiki, kuma dama duk wanda ya kasance yana maka aiki duk ranar daka dena biya mashi bukata, to kanka ze dawo, hakan yasa tundaga ranar da asirinta yatonu muka shiga jikinta.
Mune nan muka fado mata da durowa akafarta, kuma muka shanye jinin jikin kafar da bargon kafar, hakan yasa bazata kara amfani da kafar taba, tabbas wannan mata tayi sa,a tasamu masu yimata addu,a amma munso semun bi duk wani jini dayake jikinta munshanyeshi duka sannan daga karshe mukasheta, amma karfin addu,ar da akeyi mata yasa muka kasa aikata abinda mukayi niya. Amma kusani wannan mata bazata kara ganin haske arywarta ba, sbd tasamu mun cuci mutane, aciki harda karamin yaro wanda besan komai ba.
Dan haka kada ka konamu zamu tafi amma duk lokacin data kara shiga gonarmu tabbas takira ajalinta. Malam yace kuyi mani alkawarin bazaku kara shiga jikinta ba, idan kun fita. E munyi alkawari, amma itama ta gyara rayuwarta, takuma koma ga Allah wanda take bautamawa, hakanne ze kareta daga shrrinmu. To nagode.
Wata irin kara Zarah tasaki tare da atishawa, har so 3 sannan takoma ta kwanta, bacci yadauketa. Malam yace Alhmdllh, insha Allahu data farka zata dawo hankalinta, sede ina tunanin zata iya kaiwa gobe, dan haka zantafi gobe da safe zandawo. Ga wannan asamu wani ya zauna kusa da ita, aduk lokacin data farka abata wannan ruwan addu,ar tasha. Allah yakara sauki, kome kenan sauran bayanin idan nazo gobe zakuji.
Godiya sosai, sukayi mashi, yatashi yatafi. Falak, tana gefe se kuka takeyi, Baba Mairo tace banga amfanin asarar hawayen da kikeyi ba Falak, ace kuka yaki karewa, haba dan Allah, so kike kijama kanki wata cutar. Umman Sameer tace gsky Falak ya isa haka, kin sande kuka baya maganin komai, nasan akwai abubuwa da yawa dakike tunawa, amma kiyi hkr kisama kanki dangana, kinga kinrasa mutane dayawa arayuwarki, kuma duk da haka numfashinki bedena tafiya ba, dan haka kimanta da duk abinda yafaru dake arayuwa, Allah yana tare dake.
Idan kika kalli baiwar da Allah yayi maki ta yara 2 ya isa ki godema Allah, ada kinkasance ke daya, yabaki miji nagari, sannan yazo ya azurtaki da yara, Allah kadai yasan iyakar abinda zaki haifa, kinga wannan ma wata rahama ce daga Allah. Falak tagoge idonta tace nagode, da irin kulawarku gareni, kuma insha Allah, nadena saka damuwa araina. Baba Mairo tace yauwa kokefa, tashi ki kaima mijinki abinci kije daki kidauko yan biyu ki maidasu dakinku.
Bangaren Amarya da Ango kuwa, da kyar Saleem ya lallashi Jalila, taci abinci tayi wanka, yasa sukayi sallah, yajata zuwa gado yacigaba da lallashinta yana kara kwantar mata da hankli, taji dadin irin kalaman dayake fada mata sosai, cikin lokaci kankani taji zuciyarta tayi haske, duk wata damuwa ta gushe, daga lallashi shima ango ya canza tasha, naja masu kofa nace seda safenku.
Washe gari da safe har 8 tayi amma Zarah bata farka ba, mutanen gidan harsun gama karyawa, sunyi wanka, suna jiran tashinta, Baba na Zariya kuwa har yagama shiryawa dan yace shima yau zetafi, jiran tashinta kawai yakeyi da kuma jawabin da malam yace zeyi, se wajen 8:30 sannan ta farka cike da firgici, Baba Mairo tayi saurin riketa tana tofa mata addu,a Umman Sameer tamiko maganin da malam yabasu aka bata, kallonsu kawai takeyi Babanta yace kintsaya kina kalon mutane bazaki bude baki kisha maganin ba? Baki ta daga tasha maganin, sannan tamaida kallonta zuwa cikin Falon, akan Alh, tasauke idonta, suna hada ido yayi saurin dauke kanshi tare da kara daure fuska. Juyawa tayi tana kallon Baba Mairo da Falak, wacce take rike da Ameerah, dan Ameer yana bacci.
Sauke kanta kasa tayi dasauri takara kallon Alh, idanunta suka ciko da hawaye ganin kafarta datayi anyanke, kuma ta koma siririya. Haka falon yayi shiru kowa yana kallonta. Sallamar su Kawu da Malam sukaji, anan Alh, yafita domin ya shigo dasu. Bayan sun shigo aka gaggaisa, suka samu guri kowa yazauna, Sallamar Saleem da Jalila sukaji, dan Alh, yayi ma Saleem waya akan suzo. Falak da tunda taga yanda Jalila ke tafiya tafara dariya ciki ciki, suna hada ido da ita Jalila ta maka mata harara. Sameer ya zunguri Falak ahankali yace kede kincika sa ido. Zama sukayi suka gaida kowa, Jalila se kallon Zarah takeyi wadda kanta yake akasa tana kuka.
Bayan kowa yayi shiru Kawun Alh, wanda shima yana cikin falon, yayi gyaran murya yafara magana...... to Alhmdllh Allah mungode maka da ka kawo mana karshen wannan iftila'i da muke cike, wanda bakowa bane yayi sanadiyar shigarmu cikinshi seke, Zarah, tabbas kincutar da mutane dayawa arayuwarki, ki godema Allah daya barki harzuwa yanzu da ranki, wanda yabaki damar neman gafarar wadanda kika cuta, sauran kuma da kika kashe, sede ince tsakaninki da Allanki ne, kuma ki kara godema tsohon mijinki,,,, saurin dago kai tayi jin abinda Kawu yafada, wai tsohon mijinta.
E tsohon mijinki, dan yanzu haka babu igiyoyin aurenshi akanki, duka ya sauke maki su, kuma duk da irin abinda kika yimashi besa yayi watsi dake ba, ya tsaya akanki ganin baki wulakanta ba, duk da ke burinki kenan inda Allah yabaki dama, kiga kin wulakanta shi, sede ahi azuciyarshi ba haka bane, asali ma, yahanaki fita kije ki gogu da sauran yan'uwanki mahaukata, kuyi yawo aduniya kuna bin bola, yara suna jifarku, wasu marasa imani kuma suna binku suna maku fyade, kuna haihuwa akan titi, duk wadan nan abubuwan babu wanda Abba yabari kikayi, asalima acikin unguwar nan, bakowa yasan halin dakike ciki ba. Sannan wadan da kike da burin ganin bayansu, sune suka zama gatanki, alokacin da kika rasa wadanda zasu zauna dake, Falak, yarinyar da kika tsana, kinso ki lalata mata rayuwa, Allah yatsare abinshi, kin kashe mata Uwa, kaninta ma baki barshi ba, amma duk da haka ta tsaya domin ganin kinsamu lafiya,
Baba Mairo dattijuwa me kirki, wadda ahaife ta haifeki, bake bama, Abba kanshi ta haifeshi amma bata isa ki daraja taba, sbd kawai tana aiki a karkashinki, segashi yau tayi maki abinda Mahaifiyarkice kadai zata iya yi maka shi, tazauna dake acikin halin hauka, na tsawon kwanaki, tayi jinyar diyar cikinki, wadda ayanzu bata duniyar. Harma wata daban wadda baki sani ba, kawai ta dalilin yarinyar da kika tsana itama ta amfaneki, kinga kenan kinci darajar Falak, sirikarta gatanan azaune, sbd ke take zaune gidan nan, kuma ita tayi jinyar Jidda.
Saboda haka yanzu shawara tarage naki, dama ni naroki Abba akan yabarki kizauna agidanshi harki samu sauki sannan sekizabama kanki rayuwar data yimaki, mahaifinki ma nine na tsaidashi, sbd baki daukeshi da muhimmanci ba, bare kuma yan 'uwanki, wadan da tunda sukazo bikin Jalila sukace bazasu dubaki ba, sbd kema kin manta dasu, dan haka yarage naki ki gyara rayuwarki, duk wanda ya yarda zumunci to wata rana seyayi dana sani.
Shiru falon yayi inbanda kukan Zarah bakajin komai, sauran masu tausayi sede hawaye, Jalila, kam idanunta harsun kumbura, azuciyarta tana tirrr da irin halin Umminta, yanzu agaban kowa harda mijinta kalli yanda ake fada mata bakaken maganganu, jitake kamar tabar falon.
Malam yayi gyaran murya yace to Zarah, kinji de da kunnenki irin abubuwan da kika aikata, ace wai musulmi ne, da kanshi ya aikata wannan abun, sbd son zuciya da kuma kwadayin abun duniya, gashi nan ta sanadiyar abinda kikayi kalli irin abinda kika jama kanki, yanzu bakida saura daraja agurin kowa, sede idan har kin tuba kuma kin gyara halinki, abinda nakeso dake, idan har kinyarda zaki canza halinki, to dole sekin koma baya kin gyara rayuwarki daga farko, dan kinada karancin addini, kuma dole sekin gyara ibadarki, sannan zaki samu damar neman gafara agurin ubangijinki, sauran mutanen da kika cutar kuma gaki gasu, zaki iya neman gafararsu, saura kuma sede ince Allah ya gafarta maki,amma tabbas kina da kalubale agabanki, kuma duk wanda yayi niyar tuba, to dole seya bar duk wani abu najin dadin duniya sannan ze iya samun lokacin ibada. Daga karshe kuma ina maki ta,aziyar mutuwar diyarki, tare da fatan alkhairi na auren diyarki Jalila.
Kuka sosai Zarah takeyi, jitake dama Allah yadauki ranta, da irin wannan rana daya gwada mata, jan jiki tayi ta matsa kusa da Babanta, wanda shima kanshi yake kasa yana kuka, kafarshi takama tana kuka tana fadin Baba kaine mutum na farko daya kamata infara neman gafararka, tabbas na cuceka, na wulakantaka, ban baka darajarka ta Uba agareni ba, kai cona, daban zama 'ya tagari ba,nahada kai da makiyiyarka munzalunceka. Dan girman Allah Baba kayi hrk kayafemun, nasan idan baka yafemun ba, raywata bata da amfani, wlh ko haka Allah yabarni naga rayuwa kayafemun ko naga haske arayuwata. Kamota yayi yana kuka yace, ya isa haka Zarah, nayafe maki, duniya da Lahira, idan kina da laifi nima inadashi danayi sakaci da addu,a har wata tasamu galaba akaina, tazo taruguje tarbiyar dana baki afarko, tabbas, yanzu kam naga falalar addu,ar iyaye akan 'ya'yansu. Allah yagafarta mana gaba daya. Kije kinemi gafarar mijinki, shine yafi can canta daya yafe maki.
Matsawa tayi kusa da Alh, wanda shima yake kuka kamar karamin yaro, zata kama kafarshi yayi saurin janyewa, tace nasan banida bakin dazan nemi gafararka, na cutar da kai, na wulakanta ka, naci amanarka, na ha'inceka, nakasa bama yaranmu tarbiya mekyau, amma dan Allah kada kadubi laifukan dana yi maka, ka kalli girman Allah da darajar yaranmu ka yafemun, kaima Allah ze saka maka da mafificin alkhairinsa, kayi hkr da duk abinda nayi maka.
Shiru Alh, yayi yana kuka, Jalila ta matsa kusa dashi tarike kafarshi tana kuka tace, Dady dan Allah kayi hkr ka yafema Umminmu, nasan ta cutar da kai amma idan baka yafe mata ba, zata shiga wata irin rayuwa, dan Allah Dady. Goge idonshi yayi yace shikenan Jalila nayafe mata, ko alahira wani yanacin arzikin wani, haihuwa me rana, kigodema yarki kinci darajarta, nayafe maki.
Komawa gurin Falak tayi tana kuka tama kasa magana, dan muryarta harta dashe, Falak ta tashi ta aje Ameerah, tadawo takama Zarah tana goge mata kwallan idonta, itama tana kuka tace haba Ummi, kintaba ganin inda uwa tadurkusama yarta? Kamar yanda bazaki durkusama Jalila ba, haka nima agurina na daukeki Uwa, kada ki wahalar da bakinki gurin neman gafarata, ni 'yarkice, na dade dayafe maki, kuma har cikin zuciyata nayafe maki, Allah ya yafe mana gaba daya, Zarah jitayi gaba daya kunyar Falak da sauran mutanen falon takama ta, kallon Baba Mairo tayi tace Baba Mairo dan Allah kiyafemun abinda nayi maki, tabbas ke Uwa tagari ce dayakamata ace narikeki amatsayin Uwa, amma sena wulakantaki narike wadda tayi silar shigata wannan rayuwar amatsayin Uwa, gashi ta dalilinki nasamu alkhairi inbadan keba, dayanzu nakarama kaina zunubi me yawa,amma se bakibi son zuciyarki ba, kika kareni daga fadawa halaka. Nagode da irin zaman da kikayi dani da yarana. Baba Mairo tace ai bakomai Hjya. Zarah tace zanso kidena kirana da wannan sunan, dan yanzu nazama diyarki, narasa gatana Uwa, inaso kimayemun wannan gurbin dan Allah.
Kwalla Baba Mairo tagoge tace bakomai Zarah dama can ni amatsayi diya na daukeki, Allah yayi maki albarka,kuma Allah yajikan jidda, kallon Umman Sameer tayi tace Umma duk da bansanki ba, amma kinmun alkhairi, nagode maki sosai, Allah yasaka maki da gidan Aljannah. Tace Kawu kaima nagode kayi sanadiyar samun lafiyata.
Sameer kaima bansan dawane baki zan nemi yafiyarka ba, amma dan Allah kayi hkr da duk abinda namaka, kuma kayafemun, nagode sosai da dawainiyar da kukayi mana kaida Saleem, Allah yabiya ku. Suka ce amin. Zarah tace Allah sarki Jidda Allah yaji kanki, banida rabon neman gafararki, nasan banzamo Uwa tagari agareku ba, amma ina rokon Allah ya yafe maki laifukanki, kema Jalila kiyafemun. Kuka tasaka, kowa seda yatausaya mata.
Malam yace to Alhmdllh naji dadi sosai da kuka zamo mutane masu yafiya ga junanku, kuma dama haka Allah yakeson bayinsa masu saurin yafiya akan laifin da,akayi masu, dan duk mutumin da,aka cuta, yana da ikon daukar mataki amma yayi hkr ya yafe tabbas wannan mutumi Allah zesaka mashi da mafificin alkhairinsa. Allah yakara yafemana laifukanmu, yashiryar damu da iyalanmu, Allah yasa mufi karfin zuciyarmu. Daga karshe Alh, inason inroki wata alfarma agareka, inaso kamar yanda su Baba Mairo zasu zauna agidanka, inaso itama Zarah kayi hkr kabarta tazauna agurinsu, tunda zatafi samun matemaka, akan idan takoma gidansu, tunda shima babanta ba aure gareshi ba, kaga idan Allah yakawo mata miji setayi aure hakan zetemaka mata tasamu saukin damuwar datake ranta.
Kawun Alh, yace tabbas Malam karigani, nima abinda ke raina kenan, kaima Alh, bazeyuwu kazauna haka ba, amma kome kenan, nan da kwana 2 zanzo akwai maganar dazamuyi. Zarah jitayi kamar ta kurma ihu, wai agabanta ake maganar mijinta zeyi aure, ita kuma gata ta nakasa, kilama bazata kara aure ba. Goge idonta tayi aranta tace kaicona. Jalila ma hakanan bataji dadin abinda Kawu yafada ba, taso ace ba saki 3 Dadynta yayi ma Umminta ba, da tasashi ya maidata.
Malam yace to ai semu rufe taro da addu,a ko? Anan yayi masu addu,a yayi masu sallam Alh yabashi kudi masu yawa, yace baze karba ba, Kawu yace a,a ai ba biyanka mukayi ba, kyauta ce yayi maka, anan ya amsa yayi masu godiya yatafi tare da Kawun Sameer. Alh, da Kawu da Mal. Garba suka fito suka nufi part din Alh, Kawu yace kaima Mal. Garba yakama kasamu kayi aure zama babu mata bakaramin matsala bane, sbd akwai lalurar ciwo kuma ga al,amuran rayuwa.
Murmushi yayi yace wlh Alh, ni tsoron ma matan nakeyi, dariya Kawu yayi yace kada kasamu damuwa, idan har kabani dama nizan zaba maka. Yace haba ai yanzu munzama daya, duk wacce kazaba mun nikuma na amince. Yace dama akwai wata diyar kanina da mijnta yarasu yabarta da yara 2 mace da namiji, yanzu haka tana gidana anan take zaune, idan har ka amince zaka aureta, amma kuma da yaranta zata zauna, to? Malam. Garba yace ai babu damuwa, yaro ai nakowa ne, wlh na amince, sede bansani ba ko ita. Kawu yace kamar yanda mukayi maganan nan da kai itama haka tacemun inzaba mata, nikuma gsky nayaba da kai, shiyasa kuma idan bazaka damuba, zanso kabani dama inmaka gyaran gidanka.
Alh, yace a,a kawu kabarni nizanyi wannan aiki, Kawu yace ai ni narigaka, dan haka kaima seka samu wani abun kayi mashi. Har kuka seda mal. Garba yayi, yace babu abinda zance maku se godiya. Alh, yace shikenan nikuma zanbude mashi babban shago wanda zerika kula dashi. Kawu yace yauwa, dan haka bawani daukar lokaci abun zeyi ba. Yace nagode sosai. Kawu yace kaima kashirya kilama tare za,ayi bikinka dashi. Alh, yayi dariya yace haba Kawu niyanzu ai nagama kallon wata mace ince inasonta, inama zan tsaya kallonsu. Kawu yace ato aini harna kallo maka. Dariya suka sa gaba daya.
Baba mairo se lallashin Zarah sukeyi, tace tashi muje kiyi wanka kici abinci, inaso kisaki ranki kada wata cuta tadameki, kidauka kamar ba,ayi komai ba, Jidda kuma addu,a yakamata kirika yimata. Haka suka kamata suka kaita bandaki dan tayi wanka.
Falak taja Jalila daki tana tayi mata tsiya, Jalila tace wlh ke muguwa ce, koma kimun sannu shine daga shigowata ina kallonki kinamun dariya, wai dan Allah ya akayi kika gane? Falak tace yo daga tafiyarki mana. Jalila tace nashiga 3 yanzo kowa yasan abinda yafaru dani, har Dady ko? Falak tana dariya tace ke kwantar da hankalinki ai babu wanda ya kula dake, kinsan hankalin kowa yana gurin Ummi. Jalila tace wash, harnaji dadi, Falak tace to Allah yasa nan da wata 9 musami yan biyu. Jalila ta kaimata duka tace wlh yan biyu su tsaya akanki, Falak tace toshikenan zamu gani ai. Baba Mairo tashigo tace to meza,a dafa ne agidan yau? Jalila tace a,a Baba kibari tunda ina gida indora, tace a,a Jalila daga ganinki bakijin dadi, kawai kibarshi kizauna kihuta. Dariya Falak tayi tace Baba kawai kidafa komai medadi, Jalila tajuya tana gungunai, Baba Mairo tace waini menace ne? Falak tace rabu da ita Baba, Jalila tadauko pillow tana dukanta dashi, baba mairo tayi waje tana dariya.
Bayan kwana 2 komai yafara dedeta, sede haryanzu Zarah takasa sakin jikinta agidan, duk da Baba Mairo tana kokarin ganin tana janta ajiki, gaba daya sunkwaso kayansu sun maido gidan, zamansu gwanin ban sha,awa Umman Sameer da Baba Mairo sune suke girkin gidan, Zarah kuwa ansama mata sanda hartafara amfani da ita, kuma kafarta tana kara samun sauki, sede aje ayi mata dressing, kuma jikinta yafara haske. Kullum tana cikin jan carbi tana istigifari, sallah akai akai takeyinta. Sameer yace ze kawo mata malamin daze rika kara mata karatu.
Bayan kwana 2, Kawun Alh, yazo, kai tsaye gurin Baba Mairo yawuce, waje suka fito, wata magana suka gamayi, sannan nga sunnufi bangaren Alh, Bayan sungama gaisawa Kawu yace dama nace maka zanzo bayan kwana 2 togashi nan nazo, kuma tare muke da Baba mairo dan ina ganin maganar zefi ayita tana nan.
Bawani abu bane akan maganar auren danayi maka ne, akwai wadda nagani kuma na yaba da hankalinta, bakowa bace se sirukarka, Zaro ido Alh, yayi yace bangane ba. Yace E sirukarka nace, wato mahaifiyar Sameer mijin Falak, tabbas tana da halin kirki inaso kayi hkr ka karbi zabin damuka yimaka nasan bazakayi