Showing 42001 words to 45000 words out of 61588 words
Chapter 15 - AGOLA BOOK COMPLETE DOCUMENT BY Nabila Lawan Zango .txt
dan jiya mafarki Baba nayi wai beda lafiya, shine nace gara inje indubashi na dade banje ba. Mamakin kalamanta yayi, dan a iya saninshi Zarah bata taba cewa zataje taduba Babanta ba, sede idan wani uzurinta ya tashi, yace tofa, ai mafarki ba gaskiya bane Zarah, insha Allahu zaki sameshi lfy. Shikenan sekin dawo, amma dan Allah kada kiyi dare kinsan banason tukin dare. Kudi yabata yace tayi mashi siyayya, yakaramata wasu yace idan taje tabashi kuma tace yana gaisheshi. Godiya tayi mashi yatafi itama tayi masu Jalila sallama ta tafi.
Alh, yana zuwa office bayan yagama abinda yakeyi, yaji kiran Sameer, nan yahada kayanshi yafita yasameshi awaje, bayan sun gaisa, Sameer yace ina ganin ka aje motarka semu tafi atawa, haka akayi suka nufi gidan Kawu.
Bayan sungaisa, Kawu yafara magana, agaskiya Alh, ka tsallake rijiya da baya, tun ranar da mukaje neman auran Falak na ganka, nasan akwai abinda yake damunka, gaskiya Alh, kana sakaci da addu,a kasan ita makamin mumunice, duk wanda yariketa, to koda wani abu zesameshi yakan zomashi da sauki. Hakan yasa asirin da akayi maka yayi tasiri akanka. Amma alhamdulillahi yanzu babu komai ajikinka, sede muce Allah yakara karewa, kuma kaima kadage da addu,a.
Alh, yanisa yace tabbas Malam nima naji alamun haka tunbayan da muka hadu da Falak a asibiti, kuma naji labarin da bansan ya akayi ba, adaren jiya sam banyi bacci ba, duk da nace bazan tsananta binciken halin dana shiga ba, amma ajiya nayi nazari sosai, kuma zuciyata tafara zargin wani abu, sede kasan ance zargi beda kyau koda yakasance gaskiya ne, hakan yasa nabar abun kuma nima nayi alkawarin dagewa da addu,a tabbas nasan nayi sakaci abaya, amma yanzu hakan yazamar mani darasi.
Kuma ina baran addu,a awajenka, Malam yace babu damuwa Alh, muna temakon wasu ma, bare kuma nagida, kuma nima shawarar dazan baka kamar yanda kace kana zargin wani abu, to kabarshi ahaka, kada kayawaita bincike, kasan kome mutum yakeyi Allah yana ara mashi rana ne, wata rana dole asirinshi ze tonu.
Abu nafarko dazaka farayi shine karika tashi cikin dare kana sallar dare, kasan Allah yace yana saukowa akowane karshen dare kuma yana amsar addu,ar duk wadanda suka rokeshi a wannan lokacin, ka yawaita karatun alkur,ani, da sadaka suma suna temakon mutum, yawan ambaton Allah safe da yamma, azkar dinka kullum dummin saurin da kakeyi kada kabari suna kubucemaka, koda kana tafiya amota ne, idan ka haddacesu to kasamu kafin ka isa inda zakaje kayisu. Allah shine mafi sani, wannan ruwan addu,a ne danayi maka tunjiya, kashanye yanzu, wannan kuma idan ka koma gida kazubashi aroba kawanke jikinka duka, insha Allah zakaci nasara akan duk wani menemanka da sharri.
Godiya sosai Alh, yayi mashi hada kukanshi, yakawo kudi yace gashi ayi sadaka, daga nan sukayi sallama Sameer yamaidashi office, yana zuwa ya dauki motarshi yanufi gida. Yana zuwa yashiga yayi wanka da ruwan maganin da aka bashi yadauro alwala yazauna yana karatun qur,ani.
Zarah kuwa tana zuwa gidansu taci karo da Babanta yana shirin kulle gida. Tsayawa yayi yana kallonta cike da mamaki, danshi har yamanta rabon daya ganta, tana fitowa daga mota tace Baba ina kwana, yace lfy lau Zarah ashe kina duniyar? Dukar da kanta tayi tana wasa da makullin motar tace wlh kuwa Baba kasan aiyuka ne sukamun yawa. Yace e gsky kam naga alama.
Yanaga kana shirin kulle gidan ina Innar take? To shigo daga ciki tukunna.
Bayan sunzauna, ya kalleta yace Asaben bata fada maki abinda yafaru ba? Saurin kallonshi tayi tace aini rabona da ita tun ranar litinin, kai ya jijjiga yace to ai tundaga ranar nima bankara ganinta ba, dan yanzu bama tare da ita, aranar lahadi tazo tace insaketa zata bar garin, nikuma na sawake mata tundaga nan bankara ganinta ba. Wata irin zufa ce tarika keto mata, tafara fifita tace nashiga 3 yanzu Baba bakasan inda ta tafi ba? Murmurshi yayi yace ai kunfi kusa ni ina zansan inda taje, dama ni asama naganta, bansan kaddarar data kaini aurenta ba, kuma gashi Allah yarabani da kaya, bana fatan musake haduwa da ita.
Shiru tayi tafiddo wayarta tana kara kiranta amma haryanzu shiru. Abinda bata saniba, tun atasha Asabe ta karya sim dinta tace setaje Lagos zata sayi wani. Baba kuma wayarta kullum akashe, dariya yayi yace toni Zarah yakikeso incemaki, kowa yasayi rariya ai yasan zatayi zuba, saboda haka kije gidan kawarta Dije kozata fada maki garinsu. Ai Baba Dije bata nan, kuma bansani ba kota dawo, gashima ni bansan gidanta ba. Kanshi yagirgiza yace waini Zarah me Asabe zatayi maki ne kike nemanta? Babu komai Baba, kawaide ina nemanta ne, kasan banida wata. Uwa data wucemun ita shiyasa hankalina yatashi danaji kace bata nan. Seda yaji kwalla tacika mashi ido jin kalaman Diyarshi, tabbas tausayinta yashigeshi, sede Asabe tayi mata mummunar huduba. Share kwllar datazubo mashi yayi, yace shikenan Zarah, amma de inaso kisani Asabe ba macen kirki bace, kada kicigaba da nemanta babu abinda zaki saku agurinta se halaka, kiyi hkr kamar yanda Allah yarabani da ita kema kidauka rabuwarku alkhairi ce.
Kallonshi tayi cike dajin haushi tace Baba nide kasa wani yarakani gidan Dije sauri nakeyi zankoma. Murmushi yayi yace Zarah kibi duniya ahankali wlh ina tausaya maki duk ranar da duniya zata juya maki baya. Tashi tayi tace nide zantafi, dubu 1 taciro tace ga wannan kayi cefane, yace A,a kirike kudinki zasuyi maki amfani ahanya niyanzu bana bukatar komai, Allah yayima Jalila albarka, tabbas yarinyar nan yar halak ce, tayi mani abinda wadda na haifa takasa.
Tashi muje innuna maki gidan, kudinta tamaida jaka tana gungunai tayi gaba, har kofar gidan Dije yarakata, ya hadu da wani abokinshi makwabcinta, shi yatambay ko tadawo. Yace ai malam Garba Dije da kawarta sunyi hijira bazasu dawo garin nan ba, dan harta saida gidanta da komai nata, nima kiya medakina take fadamun tashiga gida tasamesu suna ta shiri, suke fada mata sukam sunci gaba. Zarah jitayi kafafuwanta suna rawa, zufa kawai take fito mata, da kyar tace to Baba nizan koma, yace to yayi kyau, Allah ya kiyaye kigaishemun da Jikanyata Jalila, haka tanufi mota yana binta da kallon tausayi. Da kyar taja motar ta tafi, ikon Allah ne kawai ya kaita gida, tana zuwa tashige dakinta ta kulle tafara kuka.
Karfe 4 na yamma su Figo kawun Baban Falak suka shigo kaduna, cikin shiga ta mutunci, idan kagansu sekadauka irin manyan yan shiyasa ne, hotel suka nema suka kama daki 2 shi yadauki daya yabasu daya su 3.
Se karfe 6 suka fito shida babban yaronshi Jungle suka tari taxi suka fada mashi inda ze kaisu, suna zuwa unguwar suka sami wani suka tambayeshi gidan Alh, Abba Bala, nan take yanuna masu gidan, godiya sukayi mashi, Figo yaciro wayarshi yasa akunne kamar mekiran waya, can kuma yacire yace wayarshi akashe take kawai muje ma dawo gobe, banason shiga baya gida kasan matarshi bazata barni infito ba, zatace sena jirashi. Kallonshi Jungle yayi Figo yayi mashi signal da driver, murmushi yayi yadaga mashi hannu, suka koma hotel, bayan sun sallami driver Figo yace kasan bana aikina da ka, haka kawai muje guri da driver kuma mu tambayi gidan mutum ana nuna mana kawai mujuya ai kowaye ze iya zargin wani abu. Jungle yace gsky Oga aiki da kai akwai karuwa.
Zaune suke afalo Falak tayi matashi da kafar Sameer, shi kuma yana wasa da cikinta, yace dear idan kika haifa mun mace sunan Ummanki zansa, Idan kuma na kiji ne, sunan Babana zansa, shiru yaji tayi batace komai ba, dukowa yayi yana kallon fuskarta, gani yayi hankalinta baya gurin, girgizata yayi, tayi saurin kallonshi. Meye haka kikeyi Falak, bakisan yanzu bake daya bace, kike irin wannan tunanin, kuma ko ke dayace ma aikinsan banason dogon tunani ko. Murmushi tayi tace kayi hkr wlh ina tunanin Dady ne, ina tausayinshi, nasan Ummi bazata kyaleshi haka ba. Babu abinda zata iya kara yimashi, domin yanzu yafi karfinta, kawai mucigaba dayi mashi addu,a. Shikenan, Allah yakara tsaremu, yace yauwa kokefa, ameen, tashi muje kibani abinci dagata yayi suka nufi daki suna dariya.
Washe gari da misalin karfe 10 nasafe, Jungle da Figo suna daga gefe suka ga motar Alh, tafita. Figo yace yauwa, yatafi muje, suna zuwa suka kwankwasa kofar, megadi yabude, bayan sungaisa, Figo yace ni suna Lado, munzo gurin Alh, ne. Megadi sewashe baki yakeyi yaga manyan kutane, yace yanzu kuwa yatafi office, amma ku kirashi mana. Aa, barshi kawai idan hajiya tana ciki kafada mata zamu bata sako seta aje mashi, yace toshikenan kushigo ga banci nan kuzauna, dasauri yanufi cikin gidan, Karo sukaci da Jalila bayan sungaisa yace tayima Hajiya sallama wasu mutane suna son bata sako ta ajema Alh.
Adaki tasameta kwance tana tunani, tace Ummi wai kizo wasu kutane zasu baki sako ki ajema Dady, tace kash nifa banason yawan damuwa kije kawai subaki, tace a,a Ummi idan kuma sakon kudine fa, ai kinga keyakamata subama, saurin tashi tayi jin ance kudi, gyalenta ta dauka tafita.
Bayan sungaisa Figo ya matsa kusa da ita ahankali yace bagurin Alh, muka zoba gurinki mukazo kuma munzo da magana me mahimmanci amma idan kinasonji zamu iya matsayawa daga nan, harararshi tayi tace nikuma a ina nasanka, murmushi yayi yace amma idan baki sanni ba, kinsan Asabe da Dije ko?
Cike da fargaba tacee kushigo, murmushi yayi yace abokina muje ta matsa semunsha ko ruwane, megadi yace ai gaskiya ne, sekunfito. Bayan sunzauna afalon baki tace dan Allah ina kasan Asabe da Dije? Wayarshi yaciro ya nuna mata hotonsu yace kobasu bane wadannan, jiki narawa ta amshi wayar tafara dubawa, dasauri tace bade sun mutu ba, to ina jakar dasuke tare da ita? Yace tonide bansan wata jaka ba, munshiga mota atare dasu zamuje Lagos, se yan fashi suka tare mu, suka kwace mana kayanmu da kudinmu duka, to ita Dije tana kusa dani, alokacin da aka bude jakarta senaga wasu hotuna sunfado, ina dauka naduba senaga macen jikin hoton nasanta, ita da mamanta, garinmu daya dasu, kuma masu laifine, sunan mamarta Hajjo ko? E ita kuma Falak, haka suke, to bazan boye maki ba, agaskiya mutanen banza ne, mijin Hajjo abokina ne, yanada kudi, shine ita da niyarta suka hada baki suka kashe shi suka gudu.
Nayima yan sanda alkawarin nizan nemosu aduk inda suke, na dade ina nemansu bangansu ba, harna hakura, segashi Allah yakawomun su cikin sauki. Bayan natambayi Dije a ina suke tacemun Hajjo tarasu, ita kuma Falak tayi aure, shine nace tayi mani kwatancen inda zanganta, shine take cemun ai kekika san inda take, kema kinso akasheta kika basu kudi sukaisu gurin boka, shine sukuma ashe karya suka maki guduwa sukaso suyi da kudinki shine yan fashi suka kamamu. Ita ta fadamun sunan mijinki da unguwarku.
To dayake ansamu kudi agurin kowa sune suka boye nasu da kaya, koda yan fashin suka gano kudin suka tambayi masu su, shine suka kashesu, mu kuma suka maida mana kudinmu, nikuma nadaukesu hoto dan innuna maki. Yanzu nazo kitemakeni ki nunamun gidan Falak domin hukuma tayi saurin cafketa.
Bakin ciki tare da farin ciki ne, suka hadema Zarah, jin za,a kashe Falak cikin sauki.
Urs,
NABILA RABI,U ZANGO
(Nabeelert Lady)
08028525263
🙆🏻😭😭🙆🏻 AGOLAH!!!Nah
Marubuciyar Zamani
NABILA RABI,U ZANGO
(Nabeelert Lady)
@ (H,O,N,A)
Part 135.....140
Cike da sauri Jidda tabama me taxi kudinshi tashiga gida, da Zarah suka fara cin karo tace ke lafiyarki naganki kamar arikice? Harzata fada mata, se kuma ta tuna da maganar da Figo yafada mata, akan tabada kudi akai dadynsu gurin boka. Murmushi tayi tace wlh Ummi ba komai ina Jalila? Baki ta tabe tace tana ciki, kinsan yau za,a kawo lefenta amma kika ki tsayawa akarba.
Uhm wlh Ummi wani uziri ne, yataso mun, shine nafita dawuri nadauka bada wuri zasu zo ba. Ai shikenan kishiga ciki sunan ki kalla, Jalilan ma tana falo, yauwa Ummi, da kallon tausayi tabita, aranta tace dole insama maki mijin aure kema, damma Asabe ta munafunceni ai da naje gurin boka asama maki miji medan maiko, ita de Jalila Allah yasota batare dana kashe kudina ba tasamu me kudi.
Jidda tana zuwa falo tasamu Jalila tana kara duba kayanta, cike dasauri takamo hannunta har seda Jalila ta dan tsorata, lfy de Yaya Jidda? Lfy lau kede kawai biyoni muje daki muhimmiyar magana ce bata bukatar bata lokaci, daki suka nufa Jidda ta kulle dakin taja Jalila saman gado.
Ita de Jalila kallonta kawai take cike da mamaki. Inajinki Yaya Jidda Allah de yasa lfy. Uhm Jalila inaso kibani aron hankalinki, ayau inaso infada maki wata magana wadda babu wanda yasan da ita, kuma inaso idan kinjita ki temaka mun domin insamu inyi aiki alkhairi guda daya nima arayuwata. Jalila tace inajinki.
Tun daga farkon shigarta harkar banza harzuwanta London da irin wahalar data sha, har zuwa haduwarta da Viju da irin yanda ya yaudareta, ta cutar datake dauke da ita, harzuwa haduwarta da Figo da abinda yafada mata, seda tafadama Jalila. Kuka sosai sukeyi ba kamar Jalila wadda tausayin yar uwarta yakamata, jin irin abubuwan data aikata. Jidda tace wlh Jalila tun lokacin da Umman Falak tarasu naso intuba, amma rudin duniya tare da irin halin da Ummi take nunamun yasani komawa ruwa. Tabbas Al,amin masoyine nagari, yaso inbar London indawo muyi aure amma nakasa fahimtar abinda yake nufi, seda narigada nakamu da cuta sannan yace baze iya aurena ba, tunda shi beda ita, yanzu haka bansan inda yake ba, ko no shi nakira bata shiga.
Nayi nadamar abinda na aikata, nacuci kaina da kaina, kuma hakan yasamo asaline dalilin Uwa dabamu samu tagari ba. Ko kinsan cewar Ummi dasu Inna Asabe sune silar mutuwar Umman Falak da Ameer, kuma itace ta mallake Dady, yarika yin duk wani abu dayake ma Falak. Gsky nide tsakanina da Ummi sede ince Allah ya....... Saurin rufe mata baki Jalila tayi tana kuka tana girgiza mata kai.
Kada kice haka Yaya Jidda, Uwa Uwace koda kuwa yar mafiyace bamuda wadda tafita, domin itace tayi sanadiyar kawomu duniya, dataso lokacin fitowarmu data kashemu, dataso tun muna jini datayi barinmu. Da jinin jikinta muke rayuwa acikinta, dole mudauki duk wani abu dazata mana, dan bekai rabin rabin wahalar datayi damuba. Ayanzu ko zama mu tsareta na awa 3 tayi bacci bazamu iya ba. Amma ita takan hana kanta bacci domin mu muyi. Saboda haka kada bacin rai yasa kifadi wata mummunar kalma akan Ummi, Allah ze iya kamaki da laifi akan hakan.
Addu,a itace abinda yakamata muyi mata wadda itace nake mata kuma gashi tafara canzawa, yanzu haka neman yafiyar Falak ta aikeni rannan nayo mata. Jidda tace Uhm Jalila ke yarinyace bakison kissa irinta Ummi ba. To wlh yaudararki tayi tayi amfani dake tanunama wadan nan mutana gidan Falak. Dan haka yanzu ba lokacin labari bane, kitashi muje mufada masu halin da ake ciki. Kuma akan labarina dana baki banason kowa yaji, kibarni ni nasan tawa tazo karshe, dan haka zankarbi duk wani hukunci da Allah zemun.
Jalila tace amma Yaya Jidda kinashan maganinki kuwa? Yamutsa fuska tayi tace wannan duk wahalar banza ce, tunda de ba,a iya ciremun ita gaba daya ba, babu amfanin shan wani magani, ada nafara sha daga baya kuma naga beda wani amfani, gara kawai incigaba da rayuwata haka har mutuwa ta tasameni. Jalila tace amma dakin cigaba da shan magani koba komai zaki samu lfiyar dazaki nemi yafiyar Ubangiji. Mikewa Jidda tayi tace kitashi mutafi banason dogon zance.
Adaki suka sami Zarah tabuga tagumi tana tunani, Jalila tace Ummi tunanin me kikeyi kuma? Murmushi tayi tace bakomai kawai ina dan tsare tsare akan bikinki ne, kinga saura sati 2. Hakane Ummi amma banason inga kina tunani. Yauwa Ummi zamuje mukai dinki nida Yaya Jidda.
Zarah tayi murmushi tace amma naji dadi dazaku tafi tare, sekun dawo, driver yana waje kusashi ya kaiku, to Ummi amma sede ya ajemu yadawo dan akwai inda zamu wuce. Tace toshikenan sekun dawo.
Suna zuwa gidan Jalila taga motar Saleem, tsayawa tayi Jidda tace muje mana, tace Motar Saleem nagani. Jidda tace to menene, bazaki shigaba kome? Nifa banason gulma. Jalila tace bahaka bane, inajin kunyar yaji labarinki sede idan bazaki fada masu yanda kikaji za,a dauko Falak daga gurin Figo ba. Murmushi Jidda tayi ta goge kwallan dasuka zubo mata, tace babu sauran jin wata kunya, kuma ni nadaukesu abokana shawarata, kada kidamu kobasu ji labarina ba sun riga da sunsan koni wacece sbd sunsan abinda nake aikatawa. Nasan Saleem yana sonki dan yaji labarina baze taba son dayake maki ba. Kuma dole nasan Sameer yafada mashi halin Ummi, tun kafin asamaku rana, kuma tunda kikaga bedena neman aurenki ba, ai yasan kinada hali me kyau. Kasancewarmu nida Ummi marasa hali me kyau baza,a ce dole kema ki kasance haka ba. Kinsan Allah yana fitar da shiryayye daga wanda ba shiryayye ba. Jalila tagoge kwallan idonta tace shikenan muje.
Kuka kawai Falak takeyi, Sameer kuwa gaba daya zufa ce tarufeshi, hankalinshi bakaramin tashi yayi ba, jin wai wani banza yanason zina da matarshi. Kallon Jidda yayi yace tabbas yanda kika kwatan tamana shi shine kawun Abban Falak, kuma daga gidan nan yake, Lallai biri yayi kama da mutum, tunda yatafi muma bamu yarda dashi ba, kuma aniyarmu gobe da safe zamu tafi gidanmu, sede yanzu dole mubar gidan nan, sbd meson abunka yafika dabara, yana iya canza shawara.
Jidda tace dan Allah Falak kiyafemun da duk irin abinda nayi maki, tabbas rayuwa takoyamun darasi, kuma kwadayi yakaini yabaroni, babu abinda nake nema daga gareku se addu,arku kobayan raina. Sameer yace meyasa kike fadar haka Jidda? Cikin kuka suma tafada masu labarinta.
Duk irin dauriya ta maza seda Sameer da saleem sukayima labarin Jidda kuka. Falon ya dade shiru kukan matan kawai akaji, sukam mazan sede hawaye a ido. Jidda tace narokeka Saleem kada labarina yasa wani abu yashiga zucuyarka na game da auranka ko soyayyara da Jalila. Wlh ko Qur,ani zan iya dafawa akan shedar halin kirki irin na jalila, Allah ya shiryata, duk irin yanda Ummi take nuna mata halin ko inkula lokacin da ina kawo mata kudi hakan besa ko samari Jalila tafara kulawa ba. Duk da bansan rayuwar datayi a makaranta ba, amma zan iya cemaka kaine mutum nafarko da Jalila tafara kulawa.
Dan haka inaso kada jin labarina da kuma halin Ummin mu yasa wata rana ka goranta mata. Saleem ya goge idonshi yayi murmushi yace Yaya Jidda kada kidamu. Allah ne yahadani