Showing 45001 words to 48000 words out of 61588 words
Chapter 16 - AGOLA BOOK COMPLETE DOCUMENT BY Nabila Lawan Zango .txt
da Jalila, bantaba son wata halitta ba kamar yanda nakeson Jalila, bayan Uwata da mahaifina zan iya cemaki Jalila itace mutum ta 3 datakeda muhimmanci arayuwata. Kima dena tunanin zan goranta mata, har abada, kuma wannan labarin naki insha Allahu daga nan yagama zuwa wani guri. Kuma batun maganinki dole zaki cigaba da shan shi, sbd rayuwa da mutuwa agurin Allah suke, idan yaso seyabarki da cutar harzuwa wani lokaci. Kifadamun idan baki shan magani kuma taci karfinki harta kaiki last stage wanda ko likitoci bazasu iya maki komai ba. Gashi Allah yaki yadauki ranki yazakiyi da wahalar dazaki sha? Alokacinne seme kaunarki sosai zeiya zama dake.
Dan haka kimun alkawari daga yau zaki cigaba da shan maganinki. Shikenan Saleem insha Allahu zancigaba dasha, dama na wata 1 aka bani kuma yana nan. Sameer da tundazu seyanzu yayi magana yace insha Allahu kema zakiyi tsawon rai harkisamu lokacin tuba zuwa ga Allah. Jidda tace Falak kinyi shiru bakice komai ba. Dan Allah kiyafemun.
Falak tagoge idonta wanda yayi ja sbd kuka, tace babu komai Yaya Jidda, niban rikeki da komai ba, kecema zanyima godiya, badan keba bansan yanda rayuwata zata kare ba. Saleem yace kutashi mutafi gidan Umma seku kwana acan, kai kuma Sameer daga can seku wuce gurin abokina D,P,O ne dan musan yanda zamu bullomasu, banason gobe tayi haryazo besameku ba, ze iya tunanin wani abu. Kema Yaya Jidda dake zamu tafi dan dole dake zamuyi amfani musamu mu cafkeshi. Tacebabu komai, ashirye nake dabada gudummuwata dama ina da no shi. Sameer yace Allah yadoramu akan sa,a sukace ameen.
Falak tace amma inaso kafin kutafi kusami Dady kuyi mashi bayani dan bazeji dadi yaji abun daga sama ba, dan yafi kowa sanin labarin Kawu. Saleem yace kinyi gsky, idan muka aje ku semu sameshi mutafi tare dashi ma.
Urs.
NABILA RABI,U ZANGO
( Nabeelert Lady)
08028525263
ππ»ππππ» AGOLAH!!! Nah
Marubuciyar Zamani
NABILA RABI,U ZANGO
( Nabeelert Lady)
@ ( H,O,N,A)
Part 140.....145
Kaf suka fadama Alh abinda yafaru, sede sunboye abinda yashiga tsakaninsu da Jidda, sunfada masa saurayinta ne, yarage mata hanya shine taga hoton Falak amotarshi har yake bata labarin abinda zeyi mata. Kuma basu fada mashi abinda Zarah tayi ba.
Sosai Alh, yayi mamkin jin wannan al,amari, yace lallai dole mudauki mataki cikin gaggawa, dan akowane lokaci ze iya aikata abinda yayi niya, dan beda tausayi. Allah sarki Hajjo babu rabon kiga wannan rana, banyi tunanin wannan mutum yana nemansu haryanzu ba.
Abinda zefaru kai Sameer kuyi gaba zuwa gurin abokin shi Saleem kome kenan kuyi mani waya, amma dole ayau za,a je aka mashi, tunda Jidda tanada no shi kutafi da ita nasan zatayi maku rana, nima dana gama abinda nake zanzo.
Kwance Zarah take, hawayene kawai suke zuba a idonta, zumbur tayi saurin tashi lokacin data kara tuna maganar dasukayi da boka ta karshe lokacin dataje karbar maganin mallakar Alh........... πΉ Ina me tambatar maki da duk lokacin da mijinki yasan irin halinki marar kyau, wato asirinki yatonu agurinshi daga ranar zaki haukace. Tace babu damuwa boka bazan taba yarda yasan halin danake ciki ba, inde inada kai ai baxetaba dawowa cikin hankalinshi ba.
π Komawa tayi bisa gado tacigaba da kuka, saboda tarasa yanda zatayi tasamu wata hanya dazata temaketa kada Alh yasan halin datake ciki. Seyanzu take danasanin rashin yin kawaye, dayanzu tasan dole tasamu wadda zata kaita gurin wani bokan. Hannu tadaga sama tace ya Allah katemakeni ka rufamun asiri, kada Alh, yasan halin danake ciki.
Zaune suke aOffice din D,P,O bayan sungama kora mashi bayani. Kallon Jidda yayi yace awane hotel yace maki yake? Tace a Hamdala hotel. Kince kina da no shi ko? E gatanan, good, kirawoshi yanzu kinsan de irin kissar dazakiyi mashi yabaki damar zuwa anjima da dare. Shiru tayi tana wasa da wayarta. Saleem yace Yaya Jidda kidan fita daga waje kuyi wayarku nasan kunya kikeji ko? Murmushi tayi tajuya tafita.
D,P,O yace insha Allahu acikin daren nan zeshigo hannu dashi da yaranshi abunma yazo dasauki ai, tunda mayen mata ne. Wani guri Jidda tasamu sannan takirashi, yana dagawa tace Jidda ce, washe baki yayi yace Jidda kamar kinsan kenake tunani wlh, tundazu nake jiran kiranki, gashi banda no dinki naso inkiraki ince anjima kidawo bazan iya hakurin gobe ba.
Murmushin mugunta tayi tace kamar kasan abinda nakira infada maka kenan, nima tunda nadawo gida nake tunaninka, da na hakura se goben amma naji nakasa shiyasa nace bara inkiraka insheda maka anjima zanzo. Kara washe baki yayi yace kai amma naji dadi, gaskiya kinada kyauta me tsoka sbd wannan albishir din da kikamun. Tace shikenan nagode, karfe nawa zanzo? Yace ni wlh koyanzu ma kitaho dan amatse nake. Tace a,a kaide kawai kayi mana babban tanadi anjima karfe 8 zanzo ana ma zan kwana. Dariya yayi yace kai amma nagode, kinsan dama gobe ina da abokiyar kwana, yau semu kwana tare. Tace yauwa ni namanta room no, ok room 102 dakinzo kawai ki kirani. Sallama tayi mashi tana me hararar wayar.
Tana shiga tafadi masu yanda sukayi dashi, sosai sukayi farin ciki. D,P,O yace yauwa zansa yarana suzama cikin shiri anjima semu tafi. Godiya sukayi mashi. Sannan suka tafi. Ahanya Sameer yakira Alh, yafada mashi duk yanda sukayi, yaji dadi sosai yace Allah yakaimu daren.
Jungle ne yashiga dakin Figo, yana shiga Figo yayi saurin zuge jakar kudin daya daga, yamaidata, Jungle ya washe baki yace Oga ko kudin kake kara kirgawa? Ya daure fuska yace a,a wani abu nadauka abayan jakar. Zama yayi yace wlh Oga dama zuwa nayi infada maka ko cikin kudin nan zaka dan bamu wani abu munaso mudan shiga gari muyo siyayya.
Wani irin kallo Figo yayi mashi, yakara hade rai yace, kaga malam sauraramun, tunda mukazo kaga nadauki kudin nan nayi amfanin kaina dasu? Kuma duk abubuwan da kukeci ai acikin kudin ake maku, shine yanzu zasu turoka, kai me baki kazo ka amsar maku kudi ko? To babu wanda zanba ko sisi harsemun gama abinda yakawomu sannan aduba abinda yayi saura se abama kowa kasonshi. Sbd haka katashi kabani guri, kuma kafada masu gobe, akwai aikin dazan turaku kuzama cikin shiri. Tashi Jungle yayi ranshi abace yafita. Figo yace ashema wahalar danakeyi abanza indauki kudi inbaku.
Baba mairo tace kai duniya, lallai idan baka mutu ba, zakaga abubuwan mamaki dayawa, wai wannan tabewa dame tayi kama ace Kawu mahaifinka yake nemanka, ada yaso yanemi mamanka yanzu kuma yadawo gurin 'Ya. Sameer yace wlh kuwa Baba, nima kaina abun yana damuna, shiyasa ana kamasu baza,a bata lokaci ba, za,a turasu kotu. Saleem yace wlh da za,a barni da dukansu kashe su zanyi. Umman Sameer tace a,a ka kyalesu shari,a ma ta ishesu. Allah de yabaku ikon kamasu.
Kawun Sameer yace duniyace yanzu babu gaskiya, shiyasa komai ya lalace mana, tunda har aka iya samun Uban da yayi zina da yarshi babu abinda baza,a iya samu ba, mude mudage da addu,a akan yayanmu. Allah yakara tsaremu baki daya. Suka ce ameen.
Jungle yace wlh wannan karon hakurina yazo karshe, kutumar....., yama gama raina mana wayau, dazu fa inajinshi zanshiga dakin naji yana tare da mace, sena tsaya kusan dubu 100 yabata, kuma acikin kudinne. Shine muda mukasha wahala baze bamu ba, ti wlh sede kowa yarasa, amma bazan barmashi kudin ba. Suduka sukace ai dama Jungle kaine kake hanamu, da tuni mun gama mashi aiki, dammu munfison kazama Oga da wancan tsohon maci amana ne, mukam babu wanda yataba cin amanar wani nashi, wama yasani ko abinda yayi ma dan yayanshi ne alhakin yake binshi shiyasa kome muka samu baya zama, amma shekarar mu nawa muna fashi ace haryanzu ko yar mota babu wanda ya mallaka.
Kana ganin wadda muka siya akayi hadari da ita, tundaga ita bamu kara samun wata ba, sede musami kudi shikuma yabama mata. Jungle yace ka kyaleshi kawai wlh shima tashi tazo karshe, ayau zamuyi mashi abinda yayima yaron yayanshi. Ayau zesan zafin cin amana, kuma mu dauke kudin muyi tafiyarmu, babu wani gidan dazamuje, dama can rashin tausayi ne irin nashi amma ace wai diyar danka ita zaka nema saboda yana dan akuya. Kuzama cikin shiri, karfe 8 zamu dirar mashi, kuma ayau zamu bar garina nan.
Da misalin karfe 7: 30 D,P,O yagama tara yaranshi yayi masu bayanin komai, su Sameer kawai suke jira, basu dade ba, segasu sunzo hada Alh, da Jidda, bayan sun gama gaisawa yayi masu bayanin yanda suka shirya komai. Alh, yace amma kasan dole semun fara samun Manager na hotel din sbd aka ida bekamata police su shiga gurin mutum babu izininshi ba. D,P,O yace wannan Alh, ba matsala bace, nasan manager din damunje se yaran su tsaya awaje mufara samunshi, nasan baze bamu matsala ba. Tashi sukayi kowa yashiga motarshi suka nufi Hamdala Hotel.
Sede ince Allah yabada sa,a.
Urs.
NABILA RABI'U ZANGO
(Nabeelert Lady)
08028525268
ππ»ππππ» AGOLAH!!! Nah
Marubuciyar Zamani
NABILA RABI'U ZANGO
(Nabeelert Lady)
@ ( H,O,N,A)
Part 145..... 150
Kwance yake daga shi se kajeran wando, wayarshi yadaga yakira Jidda, bugu 2 tadaga, Haba yan matana naga har 8 takusa amma najiki shiru kada de kicemun kinfasa. A'a ban fasa ba, ina hanya. Toshikenan sekinso.
Turo kofar dakin da akayi ne tasashi saurin kallon kofar. Jungle lafiyade zaku shigomun daki haka? Abinci ne, nasa ankawo maku, idan kuma aikin danace zansaku ne, bayau bane se gobe. Wai lafiya inata maku magana amma kun mani shiru? Hahhhh Oga Jungle yimashi bayani. Oga? Waye kuma wani Oga? Akwai Ogan daya wuceni?
Ada ba, amma yanzu Jungle muka sani da Oga. Jungle wai meye haka kamun magana mana. Kafa yasa yataka saman gadon da Figo yake kwance yayi, sannan yaciro sigari daya daga cikinsu yayi saurin kunna mashi ita. Seda yazuketa ya fesa mashi hayakin sannan yamikama na bayanshi hannu, wata sabuwar wuka mesheki yadora mashi ahannu.
Ganin wannan wuka bakaramin tsoratar da Figo yayi ba, lokaci guda yatashi zaune yace haba Jungle kasan fa bama irin wannan wasan, daga magana kuma meyako afito da wuka? Murmushi Jungle yayi yace aikai ba abokin wasa na bane bare inyi wasa da kai, kawai munzo muyi maka abinda kayima dan uwanka ne.
Zufa ce tafara keto mashi tako ina, yace dan Allah kuyi hkr haba jama'a yau shekararmu nawa muna tare amma ace rana daya kuzo mani da wannan magana. Idan ma matsayina kakeso wlh yanzu zan sauka inbaka, Jungle yace a,a kawai mungaji da tafiya da kaine, kuma ashekarunka yakamata ace kaima kana kabarinka yanzu kasamu ka kwanta kahuta.
Dariya suka sa, Jungle yace ina jakar kudinan take? Da hannu yayi mashi nuni, dan bakinsa yakasa magana, daukota yayi ya bude. Lallai kam kaci kudi dayawa, to bara kaji wlh kaci rabonka, mikama nakusa dashi yayi yace aje mana ita, yanzu zamu bar garinma.
Su Sameer suna zuwa bakin hotel din sauran yan sandan suka tsaya daga waje, su D,P,O da Alh, dasu Sameer ne suka shiga ciki, tambaya sukayi ko manager yana nan, akace yana ciki, kaitsaye suka nufi office dinshi. Bayan sungama gaisawa anan D,P,O yayi mashi bayani. Cike da tashin hankali manager yace ikon Allah, wlh bansan dasu a hotel din nan ba. D,P,O yace kada kadamu, kasan ba'a gane mugu afuska, mugodema Allah daya tona asirinsu ma. Manager yace amma gsky naji dadi, kuma nagode. Awane room kukace suke?102, Ok babu damuwa zaku iya zuwa. Godiya sukayi mashi suka fita.
Kafa Jungle yasa yatake cikin Figo, sunsa kyalle sun kulle mashi baki, hawaye kawai suke fita a idonshi. Hannu yahada alamun suyi hakuri. Wani yace Jungle muna bata lokaci fa, kawai aikata mashi shima. Yauwa abokina yama wannan AYAR danaji wani malami yana fadama wasu? Wace kenan? Kaini larabcin ne yakemun wahala, abinda kayi za,ayi maka ko? E e hakane, nima namanta Larabcin. Kuka sosai Figo yakeyi sede babu sauti.
Wuyanshi Jungle yakama babu tausayi yasa wuka yayi mashi yankan rago, jini yafara zuba, dede lokacin wayarshi tafara kara, daukarta Jungle yayi yace Hahhhhh mace ce, kashewa yayi yace kawai muware.
Suna murda kofar suma su Sameer suna tsaye, saurin komawa ciki sukayi, nan D,P,O yayi ma sauran yan sandan waya yace sushigo, Rarraba idanu su Jungle suka fara zarowa. Kwance suka sami Figo acikin jini, nan sukayima manager waya, shima yazo, bed sheet sukasa suka rufeshi.
Jidda kuwa kasa shiga dakin tayi haka tajuya takoma cikin motarsu, se kuka takeyi tana kara danasanin irin rayuwar datayi. Cikin lokaci kankani aka tasa keyarsu aka nufi station dasu, shikuma Figo aka nufi asibiti dashi, gaba daya mutanen Hotel din mamaki sukeyi kowa yana Allah wadai da halinsu.
Gaba dayansu zaune suke a babban falon dayake kusa da office din D,P,O sukuma su Jungle suna tsugunne, D,P,O ya kallesu yace banason mubata lokaci, kunsande munkamaku dumu dumu acikin laifi ko? Dan haka banaso kubama kanku wahala muma kubamu, kai, yanuna Jungle, inaso tsakaninka da Allah kayi mana bayanin abinda yakawo garin nan, da kuma bayani akan wanda kuka kashe.
Jungle yace tabbas yau nasan asirinmu yagama tonuwa, saboda haka bazan tsaya batama kaina lokaci ba, nine nan nakashe shi, kuma tare muke dashi shinema Oganmu............. Anan Jungle yafada masu komai da Figo yayi ma Baban Falak, sannan yafada masu yanda akayi suka san inda Falak take, da kudin dasuka samu, har yanda akayi sukaje gidan Alh, da abinda Zarah tayi. Kuma yasheda masu ita tabada kudi da hotonsu akaisu gurin boka.
Nan take Alh, yaji wata zufa tana fito mashi. Jungle yace muma yaci amanarmu shiyasa muka kashe shi, kuma ashirye muke damu amshi duk wani hukunci daza ayi mana. Kowa agurin seda yayi mamakin irin halin rashin tausayi na Figo. D,P,O yace to Alh, kunje de abinda yafaru, dan haka bazamu bata lokaci ba zamuturasu kotu, wannan kuma tunda yarasu, kawai zamuje ayardashi. Wadannan kudi kuma Alh, Allah ne yamaido maka da abunka, dannasan nakane, babu ta inda matarka zata samesu haka, amma zaka iya kaimata seta fada maka inda tasamesu. Sauran hukunci kuma yana gurinka, sede muce Allah ya kyauta.
Gabadaya Alh, kunya takamashi gashi agaban sirikanshi har 2 duka sunji bakin hali irin na matarshi, nan take yai tsanarta tashiga zuciyarshi, fita yayi batare dayace komai ba, yanufi motarshi yanufi gida zuciyarshi tana zafi.
Sameer da Saleem sukayima D,P,O godiya yabasu jakar kudin sukatafi, amota suka sami Jidda se kuka takeyi, Saleem yace dan Allah yaya Jidda kukan nan ya isa haka, keme yayi zafi maganinshi Allah. Sameer yace zakija ma kanki ciwo, kiyi hakuri hakanan. Tace haba Saleem, yanzu idan Dady yaji abinda na aikata nasan kasheni kawai zeyi, gashi zamu hada mashi zafi 2, dole yanzu yasan abubuwan da Ummi ta aikata, ina zesa kanshi? Wannan tashin hankali dame yayi kama? Kaiconmu, Dady beyi sa'ar mata da diya ba, gashi yarinyar dana raina na tsana yanzu itace zata zama abun alfahari agurin Dadynmu bani ba. Jalila kam taji dadinta dabata bari shedan yayi mata hudubar banza ba. Suduka seda sukaji tausayinta. Sameer yase ya isa haka......
Wayarshi ce tayi kara, yana dubawa yaga Alh, ne yake kiranshi yana dagawa yaji muryarshi tana rawa, yace hello, Alh, yace yauwa Sameer kadauko Falak da Kawunka, kuduka de kutaho gidana inason ganinku, yace to.
Sameer yace Saleem muce gidanmu tunda mota ta tana can se indauketa Alh yace mutaho dasu Umma , Falak da Kawu. Jidda tace innalillahi Wa inna ilaihir raji'un. Shikenan watan tonan asirinmu yakamaπππ.
Urs,
NABILA RABI'U ZANGO
(Nabeelert Lady)
08028525263
ππ»ππππ»AGOLAH!!! Nah
Marubuciyar Zamani
NABILA RABI'U ZANGO
(Nabeelert Lady)
@ ( H,O,N,A)
Page 150.....155
Hannu bibiyu Alh yasa yadafe kanshi, gabadaya jiyake duniyar tamashi zafi, wani abu ya tsaya mashi a makoshi, wanda daze samu yawuce dayafi jin dadi. Kuka yakeso yayi amma sam hawayen sunki zuwa, tabbas kuka ma rahamane.
Zarah data shigo falo tace a,a Alh yaushe kashigo banji shigowarka ba? Shiru yayi bece komai, dan yanda yakeji idan yabude baki komai ze iya fada mata. Zama tayi kusa tashi tace magana fa nakeyi amma kayi shiru ka kyaleni. Ko baka da lfy? Wani ne ya mutu? Duk tambyr datake mashi hakan besa yadaga kai ya kalleta ba. Cike da masifa tace wai Alh, mekake nufi......
Sallamar da akayi ne, yasata hadiye sauran masifarta. Juyawa tayi tana kallon kofa jin sallamar bata mutum daya bace, baki ta saki ganin mutanen dasuke shigowa. Mamakinta be karuba seda taga Baba Mairo tashigo gata tayi kyau cikin shiga me kyau.
Samun guri sukayi gaba dayansu suka zauna, yaran kuma suka zauna akasa, haryanzu kan Alh aduke yake, guri Zarah tasamu tazauna, gaba daya jikinta yayi sanyi. Wata irin zufa tafara keto mata. Baba Mairo tace Alh ina wuni.
Dago kai yayi cike da mamakin ganinta, ahankali yace Baba Mairo. Tace na,am, dama kina garin nan? Murmushi tayi tace wlh kuwa Alh. Gaisawa sukayi dasu Kawu, Alh ya kalli Jidda wadda taketa kuka har idanuwanta sun kumbura saboda kuka. Yace Mamana lafiya kike kuka?
Kara sakin wani kukan tayi ta tashi tamatso kusa dashi tazube bisa guiwowinta, hankalinshi dana Zarah yatashi ganin irin kukan datakeyi. Jalila da Falak suma duk kuka sukeyi dan sun san abinda Jidda takeyima kuka. Dago kai tayi tace Dady dan Allah kayi hakuri kayafemun, tabbas banzamo diya tagari ba, na cuceka na cuci kaina.
Nasan Allah baze taba yafemun ba idan har baka yafemun ba. Nayi dacen Mahaifi nagari amma rashin samun Uwa tagari yasani nima nazama wadda bata gari ba. Alh, yace Mamana wai mekike fada haka ne? Zarah kuwa da cikinta yafara yamutsawa jitake kamar ta nutse dan kunya, agaban sirikinta Jidda take fada mata wannan maganar, jitayi kamar tashakota.
Alh yace ya isa haka mamana, kidena kuka kifadamun wane irin laifi kikamun haka. Zarah tayi saurin fadin a,a Alh, kabarta tashiga ciki tasamu ta kwanta tayi bacci ta huta kasan batada lafiya. Jidda tace, a,a Ummi ya isa haka, kibarni nafadi abinda aka dade ana boyewa agidan nan, garake Ummi kinada lafiyar dazaki iya tuba zuwa ga Allah, nifa? Ina cikin cuta, wadda ko ayanzu Allah ze iya amsar raina.
Tundaga auran Hajjo da fara shigarta cikin halin banza, da abunda Zarah dasu Asabe sukayima Hajjo da Ameer, harsukayi sanadiyar mutuwarsu, dazuwanta London, da irin hudubar da Zarah takeyi mata, zuwa auren datayima Falak da Sameer, da yanda tabama su Asabe kudi, zuwa yanda Zarah ta temaka ma su Figo har cutar datake dauke da ita seda Jidda tafada masu. Gaba daya falon yayi shiru, kukan Jidda, Jalila da Falak kawai akeji.
Zarah kuwa zama tayi kasa kamar meshirin hawa bori, takasa kuka kuma takasa magana, Alh, kawai ta kurama Ido, hatta da Kawun Sameer seda yafitar ma Jidda da hawaye,