Showing 6001 words to 9000 words out of 61588 words

Chapter 3 - AGOLA BOOK COMPLETE DOCUMENT BY Nabila Lawan Zango .txt

sosai, suka yimashi suka tafi. Basune suka koma gida ba se karfe 7 na dare, makulli ya amsa gurin driver suka nufi part dinsu yabude.

Mamaki ne yakama su ganin irin kayan da aka zuba agidan, duk da ba baki bane aganin irin kayan amma sunji dadi sosai. Bayan sunzauna. Hajjo tace Alh, bansan dawane irin. Baki zanmaka godiya ba, kagama mana komai arayuwa sede inroki Allah yabamu ikon saka maka da mafificin alkhairin daka yimana.


Murmushi yayi yace Hajjo basekin godemun ba, domin kingama mun komai tunda kika amsa zaki aureni, nima Allah yabani ikon kamanta gaskiya atsakaninku. Abinda nakeso dake ki kasance me hakuri, banason tashin hankali, kuma nasan baki dashi, kiyi hakuri da duk abinda zaki gani, daga gurin Zarah, nasani sarai bata da son mutane, shiyasa ma na ajeku anan, koda banida wannan part din bazan iya hadaku agida daya ba, dan haka kuyi hakuri dasu.
Kuma insha Allah bayan biki Falak zaki cigaba dazuwa makarantar su Jalila. Nasan aji daya za,a saka ku tunda kince a ss 2 take , itama Jalila haka. Kome kukeso akwaishi akitchen, Falak inaso kidaukeni kamar mahaifinki, kada kiboyemun damuwarki dan Allah, kuma kizauna da yarana kamar yan uwanki. Godiya suka kara mashi sannan yayi masu seda safe yace su kulle kofar,


Adaki yasamu Zarah kwance, kusa da ita yaje yajawota yana fadin haba my luv yau kuma ni ake sharewa haka. Kinsan fa bamuyin haka dake, dan Allah kada kibari shedan yashiga zuciyarki yabata mana zaman lafiyar damukeyi na tsawon shekaru da dama.
Murmushi tayi data tuna shawarar da Karima tabata, dazu fasuka gama waya, tace Zarah maza yan lallashine, idan harkinaso kimallake zuciyar namiji kozakiyi mashi asiri dole sekin hada da biyayya da kuma kissa, idan bahaka ba, kina zaune wata zatazo ta kwace maki miji, kawai ki kwantar da hnklinki ayi biki agama idan yaso da kssa ki koreta, amma idan kina tada hankalinki kome yafaru da ita ke za,a ce.


Kara rungumeshi tayi tasaka kukan kissa, tana fadin dan Allah Alh, kayi hakuri nayi nadamar yimaka abunda bantaba yimaka arayuwata ba se yau, kuma agaban ,ya,yanka da bakinka. Allah yasa haka yazama alkhairi, nide fatana kayi adalci atsakaninmu.


Sosai yaji dadin abinda tafada, dama yasan kishine yasata fadin abinda tfada dazu, goge mata hawayen idonta yayi yace nagode sosai matata, Allah yabiyaki, insha Allahu zaki sameni mecika alkawari, bazan taba juya maki baya ba, kema kinsan aduk duniya kece mace ta farko dana fara so, kece uwar yara na, babu abinda ze rabamu. Tashi sukayi tarakashi zuwa bandaki yyi wanka sannan suka kwanta.


Washe gari bayan yashiga sun gaisa dasu Hajjo yanufi gidan kawunshi, anan yafada mashi abinda ke tafe dashi, sosai kawunshi yaji dadin maganarshi, dan suma sungaji da halin matarshi narashin son mutane, yace bakomai Allah yakaimu asabar din, amma waye ze zama waliyinta? Yace abokina Farouk shine yace ze zama waliyinta. Yace to Allah yakaimu, kuma sekayi kokarin rike amanar marayun Allah daka dauko, yace insha Allahu kawu, anan yayi mashi godiya yatafi.


Ana saura kwana 2 biki komai ya kan kama har dinkunansu ankawo saura wadanda ba,a dinka ba, sosai sukayi kyau acikin kwanakin dasukayi, bakamar Falak, kyawunta yakara fitowa, Jalila kadai take shigowa part dinsu dan ita hakanan takeson Falak, amma Jidda da Zarah tunda sukazo basu kara sakasu aido ba, dan Hajjo macece wadda batason wulakanci shiyasa ta tsorata da irin abinda Zarah tayi masu, hakan yasa bata kara shiga part dinsu ba. Duk yanda Alh, yaso tashiga amma tace itade tsoro takeji yabari bayan biki tashiga.


Sallama aketa kwadawa acikin falon, da kyar Zarah tafito tana yatsina ta amsa sallamar. Ahankali tace tofa yau kuma Inna Asabe ce agidanmu, washe baki tayi tace wlh Babanki ne yace kwana 2 bakizo ba, shine yace inzo inga ko lfy. Zama tayi tace tokema Inna banda abunki tunda kukaji shiru ai kunsan lafiya ko, amma kinwani kwaso kafa kintaho.


Ran Inna yabaci dajin maganar Zarah, amma dayake ita Allah yayita da shegen kwadayi yasa tace ayi hakuri hajiya. Anan tasa Mairo takawo mata abinci da lemu, zama tayi tanata zubi tana zuba surutu.


Zarah tace Inna namanta banfada maku ba, Alh, aure zeyi fa. Cike da mamaki tace haba Hajiya wace irin magana kike fadi haka, kamarki ace wai za,ayi maki kishiya kuma kizauna kina fada ma mutane, aini atunanina mutanen kauye wadanda basu waye ba, sune akema kishiya, yanzu duk cikin kawayenki wakika gani da kishiya? Gaskiya bazata sabuba ayima yata haka.
Matsowa Zarah tayi jin irin maganar da Inna take fada. Asabe tace wlh na dauka tuni kingama da Alh, seyanda kikace yakeyi shiyasa bandamu davkawo maki maganin mallaka ba, kina tunanin duk son dayake maki idan matarshi tafara haifa mashi namiji agida baze manta dake ba. Gaskiya bazata yuwu ba.


Zarah tace yauwa Innata dan Allah kifadamun abinda yakamata inyi, dama neman abunyi nake, segashi Allah yakawoki, wlh konawa zan iya kashewa inde za,a fitarmun da wannan fulanin agida na. Murmushi Asabe tayi aranta tace anzo gurin, tunda baki badawa dan Allah yanzu kam lokacina yayi nima dazanyi arziki, wlh sena ta tseki kamar me.


Asabe tace kada kidamu acan zariya kinsan munada manyan bokaye, dan haka akwai kawata Dije tana da wani hamshakin boka, inaso bayan biki kizo muje gurinshi kome kikeso za,ayi maki. Godiya sosai Zarah tayima Asabe harta manta da irin abunda takeyimata dazu, Zarah tace yauwa Innata ainasan koda nayi rashin Uwa bazanyi kuka ba tunda ina dake, amma de anan zaki kwana zuwa gobe se insa driver yamaida ke ko. Mamaki sosai Asabe tayi jin yau tasamu matsayin kwana agidan Zarah. Anan suka cigaba da firarsu


Urs
NABILA RABI,U ZANGO
( Nabeelert Lady)
08028525
: 🙆🏻😭😭🙆🏻 AGOLAH!!! Nah
Marubuciyar Zamani
NABILA RABI,U ZANGO
(Nabeelert Lady)


@ (H,O,N,A)


Part 25.....30


Ayau asabar aka daura auren Alhaji Abba da Hajara akan sadaki naira dubu 30, mutane dayawa sunsami halartar daurin aure.


Acikin gida kuwa babu wanda yazo ta bangaren Zarah daga Karima se Inna Asabe, dan yanzu sosai Zarah take mutunta ta, sbd zata kawo mata mafita amatsalarta. Tare da kawarta tazo wato Dije, sunci sun sha sunkuma kwashi ganima.


Jidda kuwa alokacin bikin ma bata kwana gida ba, tana can gidan kawarta Ameera bayan sundawo daga party suka wuce gidansu Ameera acan suka kwana.
Jalila ce itada mairo me aikinsu suka shiga bangaren su Falak suka tayasu aiki, matar farouk ma tazo, sekuma yan uwan Alhaji.
Hajjo tayi kyau sosai, idan kaganta bazaka ce Hajjo daga sani bace a wata 5 dasuka wuce, ita kanta tasan rabonta da farinciki irin na yau tunkafin mutuwar mijinta.


Haka akayi biki kowa ya watse aka bar amarya da diyarta agida, Jalila ce ita da Falak zaune adain Falak. Jalila tace wlh Falak nakosa asakaki makaranta nima insamu abokiyar tafiya, musammamma islamiyya, banida kawar tafiya, dan Yaya Jidda tadena zuwa kuma Ummi tahanani infadama Dady. Falak tace ai gara kada kifada mashi, addu,a kawai zaki tayata, kinsan kowa da irin tashi kaddarar. Jalila tace haba Falak, ko kinsan jiya ba,a gida yaya ta kwana ba, wlh ina matukar jin bakincikin halin da yaya tasa kanta, wlh ko sallah ba sosai takeyi ba, idan namata magana karshe zagine zebiyo baya.
Falak tace tabbas Yaya Jidda tana cikin jarabawar ubangiji, sede muyi ta mata addu,a Allah yashiryeta, kuma kada kibari Dady yafara jin maganarta abakinki tunda kinsan abinda Ummi tace. Jalila tace nagode Falak bara intafi kada Ummi tanemeni.


Zaune suke gaba dayansu a falon Alhaji, Zarah tana zaune akusa dashi, bakaramin dauriya tayi ba, wajen boye damuwar dake zuciyarta. Hajjo ko gaba daya tsoro yahanata sakewa ta kosa takoma part dinta.
Alhaji yayi gyaran murya yace, Alhamdulillahi, Allah yanuna mana wannan rana damuke fatan zuwanta.
Zarah takanki zanfara, kece Babba, inaso dan Allah, kamar yanda nasanki bakida fitina acikin gidan nan, haka nakeso kicigaba dazama ayanda nasanki, ku hada kanku, kidauki Hajjo tamkar kanwarki, kuma kirike Falak tamkar Jidda ko Jalila, abanson kubari wasu suzo susamu damar tarwatsa farin cikin damuka gina shekara da shekaru acikin gidan nan. Allah yabaki hakuri akan wanda kikeyi, banyi auren nan dan bana sonki ba, ko kuma da niyar in wulakanta kiba,nayi ne domin ina bukatar hakan, kuma dan inraya sunnar Manzon mu.


Kema Hajjo, inaso ki saki jikinki acikin gidan nan, kidauki Zarah kamar yar uwarki, da yayanta amatsayin naki, banason wata fitina, duk abunda baki ganeba nacikin gidan nan zaki iya samun Zarah ki tambayeta, ko kuma ni kitambayeni.
Maganar girki kuma dama nafada maku, kowa nata zata rikayi, Hajjo idan kina bukatar me aiki Zarah kisa Mairo tasamo mata, ko kuma idan zata iya tarika yimaku ku biyu, ko ya kikace Hajjo? A,a bakomai Alhaji, ai aikin ma bawani meyawa bane, zan iya yi nidaya, tacigaba dayima Umminsu Jalila, idan ina bukatar wani abu zansa mairo tayimun.


Zarah tace haba Alhaji ai base anakara kawo wata me aiki ba, Mairo ma ta ishemu, Fatana Allah yabamu zaman lafiya, kuma Hajjo dan Allah kiyi hakuri da abinda nayi maku farkon zuwanku, sharrin shedan ne. Hajjo tace lah, ai babu komai.
Muemushin jindadi Alhaji yayi yace, to Zarah yakike ganin za,a yi gurin raba girki? Zarah tace bayan kagama kwana 3 ina ganin muyi kwana 2 ko hajjo? E duk yanda kikace yayi hakan. Alhji yace to Allah yabani ikon kwatanta adalci atsakaninku. Bara muje mukwanta naga dare yayi, tashi Hajjo tayi tamata seda safe tawuce, jawo Zarah yayi ya rungume, kwallar data ke boyewa ce tazubo, saurin kifa kanta tayi bisa kirjinshi. Kara rungumeta yayi yana lallashinta, da kyar yasamu tabarshi yatafi.




Haka rayuwa tacigaba datafiya cike da kwanciyar hankali, ansaka Falak makarantar su Jalila,inda aka sata a ajinsu Jalila SS 2, alokacin su Jidda suna shirin gamawa, sosai take gane karatun, dama Falak bade kokari ba, cikin lokaci kadan tazama zakaran ajin, hatta da malamai sun santa. Babu abinda ke hadata da Jidda, dan bakaramin Tsanarta Jidda tayi ba, sbd kyan datake dashi, ko magana tayi mata bata amsawa, amakaranta idan akaje daukarsu tarinka fadama kawayenta ga AGOLAR gidansu nan, abun yana matukar damun Falak, kullum sede Jalila tarika bata hakuri, duk irin cin mutuncin da Jidda takeyi mata bata taba fadama Ummanta ba, sbd tasan Ummanta dasaurin damuwa.


Zaman gidansu Zarah zamane na kissa, domin baka taba gane Zarah batason Hajjo, duk da bawani shiga part din juna suke sosai ba, amma tana nuna mata so.kuma Alh, yana iya kokarinshi akansu, babu abinda suka nema suka rasa, duk irin kudin da yake basu Hajjo bata siyan komai, sbd acewarta babu abinda suke bukata. Hakan yasa taroki Alh, dasuje ta duba account din Falak, tanaso ayi mata ATM, sannan tacigaba da ajiyar kudi aciki.
Tare sukaje akayi mata komai, sannan tasaka dukan kudin datasamu abiki da kuma wanda yake basu,




Bayan wata daya da bikinsu, Hajjo tafara laulayi, zazzabi me zafi takeyi, hakan yasa Alh, yaduketa suka tafi asibiti, suna zuwa awon farko akace tana da shigar ciki na sati 3. Murna agurin Alh, kamar ba,a taba yimashi haihuwa ba, bayan sundawo gida yawuce part din Zarah. Anan yake fada mata cikin Hajjo, Da kyar Zarah ta dedeta kanta sbd wata irin faduwar gaba ce tazo mata jin Hajjo tana da ciki, murmushi tayi tace kai amma naji dadi, ai gara mukara samun yara agidan, amma wadan nan ,yan matan dasunyi aure shikenan gidan ze koma shiru. Alh, yace wlh kuwa, Allah de yasa tahaifa mana aboki. Dif murmushin fuskarta yadauke, shi bema kula da yanayin data shiga ba, haka yayi ta zuba, daga karshe yakoma part din Hajjo.


Wata irin zufa taketo mata, daki tashiga, tarasa abunyi kawai tasaka kuka. Lallai namiji ba abin riko bane, wai yau Alh, dakanshi yake maganar ahaifa mashi yaro, wato sbd yaga niban haifa mashi ba. Wlh dole gobe inje Zariya, nadena kaima Karima kuka na, dan naga idan nabiye mata zata kaini tabaroni, yanzu lokacin kissa da biyayya sunkare dole se boka yashigo cikin al,amarin nan. Allah yakaimu gobe da safe.


Washe gari dasafe ko abinci Zarah kasa ci tayi, haka su Jalila suka gama shiri sukayi mata sallama, tace masu zataje zariya kilama ta kwana. Sukansu sunyi mamakin jin kalmar zuwa zariya abakin umminsu, kuma ma har maganar kwana takeyi, ganin kamar suna yimata wani kallo yasa tace masu Inna ce bata da lafiya. Sukace Allah yabata lafiya, idan kinje kiduba ta.


Segurin karfe 9 Alh, yashigo, alokacin Zarah harta shirya jiranshi kawai takeyi, sanin Alh, bame hana zuwa unguwa bane shiyasa bata damu da seyanzu zata fada mashi ba.


Bayan sungaisa yace waini Zarah ina zuwa naga kinfito da jaka da gyale? Murmushi tayi tace wlh jiya bayan kafita akamun waya daga gida cewar Inna batada lafiya, to ganin dare yayi shiyasa banfada maka yau zanje ba.


Ashsha, meyasa meta? Tace gsky basu fadamun abinda kedamunta ba, amma idan naje zanji,sede gobe nakeso nadawo. Mamaki ne yakama Alh, sede yaboyeshi dan bakaramin dadi yaji ba, dayaji Zata kwana agidansu, acewarshi kila tafara canza halinta ne. Shikenan babu damuwa Allah yakiyaye hanya, kinga akwai inda zanje aida muntafi tare, amma idan nasamu lokaci zanje indubota. Zarah tace ai bakomai idan najema yawadatar, zanhadaku awaya. Yajikin Hajjon? Murmushi yayi yace jikinta dasauki ai tasha magunguna. Daki yashiga yadauko mata kudin naira dubu 100 yace tarikesu ahannunta ko za,anemi wani abu, godiya tayi mashi, yawuce yafita, tace gata nan zuwa ta duba Hajjo. Mairo ta kwala ma kira kasancewar anan take kwana, dan dattijuwa ce. Bayan tazo tafada mata zataje gida se gobe zata dawo. Ita kanta mairo tayi mamaki, duk abinda zasu bukata ta bata sannan tawuce part din Hajjo.


Bayan ta dubata ta tashi zata tafi, Hajjo tashiga daki tadebo sabulan wanka dana wanki masu yawa tace akaima Inna, godiya Zarah tayi mata sannan tafita aranta tana fadin abanza wlh, babu abinda zesa naji tausayinki, haka nan daga zuwanki keda waccan shegiyar AGOLAR taki kunaso ku mallakemun miji.


Murna duk tacika Inna da Baban Zarah ganin yau Zarah ce agidansu kuma harma zata kwana, Inna tace Malan ai yakamata ka koma kasuwa hakanan kazo ka tsaya acikinmu kamar mace, jiki na rawa yace wai da zama zanyi mugaisa da Zarah ta, tunda taxo ai yau babu batun kasuwa kuma. Zarah tace Baba kaje kawai ai anan zan kwana yanzu akwai inda zanje. Inna tace idamma kazauna mezaka bata, yace shikenan to sekun dawo, haka yafita Inna tana binshi da harara aboye, abinda baku sani ba, Asabe tadade da mallake Baban Zarah, dama kuma tahanyar asiri tashigo gidan, dan Asabe muguwar yar tasha ce dan ba,a cikin Zariya take ba,yawon iskancinta ne yakawoya zariya harta hadu da Baban Zarah, Kawarta Dije ta tsaya mata har ta aureshi, kuma tayi sanadiyar mutuwar uwar Zarah ta mallakeshi take zaune agidan, ko Zarah tarasa yanda zatayi da ita ne shiyasa take zaune da ita, dayake ta iya kissa, hakan yasa mutanen gari suke ganinta kamar ta kirki. Ganin Zarah ta auri me kudi yasa ta saduda tamaida kanta sakarai agurinta saboda itama tayagi rabonta
Se gashi Allah yakawo mata hanyar sauki dazata ci kudinta aruwan sanyi.
Bayan Zarah tabata sabulan da Hajjo tabada akawo mata, Asabe tace kinga irin kissar tata ko, ina nan dake idan alh, yazo seta fada mashi abinda tabada aka kawomun,tashi muje gidan Dije, wannan bazesa mukyaleta ba. Alh, baze kara haihuwa da kowa ba, sede ke. Murmushin jindadi Zarah tayi tace shiyasa nake sonki Innata, yauwa ga waya ma nataho maki da ita, nasaka maki layi aciki sbd idan inason wani abu basena nataso nazo ba, banason Alh, yafara zargin wani abu, tunda yasan bazuwa nakeyi sosai ba. Asabe tace dama Hajiya tunda kinada mu agari ai kinwuce kije gurin boka da kanki, aisede kibamu umarni muyi, godiya tayi mata, sannan suka nufi gidan Dije, daga can suka wuce gurin boka, dama Dije ba miji gareta ba.


Abakin bukkar bokan Dije tace sujirata tashiga akwai maganar dazasuyi dashi, kashe ma Asabe ido tayi sannan tashiga, dayake boka natane, anan tayi mashi bayanin abinda takeso yacaji Zarah, dakuma kasanshi idan tabayar, da abinda zasu dauka ita da Asabe.


Fita tayi suka shigo tare. Bayan Zarah tagama yimashi bayani, Boka yayi dariya yace cikin kikeso alalata ko kuma akasheta gaba daya? Fiddo ido tayi, tace boka bazan iya kashe mutum ba, kawai a lalata cikin, idan yaso daga baya da kaina, nasan yanda zanyi inkoreta. Boka yace aikinki yana da tsada, amma sbd wadan nan zanyi maki sauki. Zarah tace boka kudi badamuwata bane, konawa zanbiya inde za,a cire cikin. Boka yace kije can kidaga wancan kwaryar kisaka dubu 150. Tashi tayi jiki na rawa taciro kudin tasaka. Wata diyar roba yadauko hannunshi yasa abisa cikinta yarika wasu surutai, yana murza cikin, wata kara sukaji anyi, Zarah takama Asabe tarike, aje diyar robar yayi yace matso nan ki gani, wata kwarya me ruwa aciki yadauko nan take hoton Hajjo yafito, tana kwance se juyi takeyi akasa, kafafunta kuma jini yana fita. Boka yace cikinne yake fita, angama da wannan matsalar, se nakara ganinki. Tashi sukayi suna mashi godiya.zasu fita boka yace Dije ke kitsaya.
Bayan sunfita, boka yace gaky Dije kun kawomun matar dazan ci kudi kuma kuci, lallai bayanzu zan sallami wannan matar ba, semunci kudinta, sosai, kudin yadauko yadauki dubu yadauki dubu 80 yabasu 70, godiya Dije tayi mashi tace semun sake dawowa.


Urs,
NABILA RABI,U ZANGO
( Nabeelert Lady)
08028525263


[7/8, 4:02 PM] YAYA HAYAT: 🙆🏻😭😭🙆🏻 AGOLAH!!! Nah
Marubuciyar Zamani
NABILA RABI,U ZANGO
( Nabeelert Lady)


@( H,O,N,A)


Part 30..... 35


Falak ce tayi sallama tadawo daga makaranta, kaitsaye dakin Ummanta tanufa, cikin sauri ta ajiye jakarta takarasa gurin Ummanta, ganinta kwance cikin jini tana nishi.
Kiran sunanta tafarayi tana kuka, ganin takasa amsa mata tayi waje da gudu domin kiran driver, fitar ta yayi dede dashigowar Alh, tsaya wa tayi haryayi parking, dasauri ta isa gurinshi, tana kuka.
Fitowa yayi yana tambayarta lfy? Tace Umma ce batada lafiya. Ai bejira ta idasa ba, yayi hanyar part dinsu. Yana zuwa yaga halin datake ciki , hijabinta yasa mata yadauketa, Falak tana biye dasu, mota yasata, Falak na kokarin shiga sega Jalila. Alh, yace yauwa Jalila zamuje asibiti Hajjo ba lfy, ku kula da gidan. Shiga yayi

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login