Showing 21001 words to 24000 words out of 96302 words
Chapter 8 - Aziza da Azima Macizai Ne Part 1 Complete Hausa Novel By Zainab Abdul Mom Ahlan.txt
barota a rafi, Hajja bari na tayaki aikin gida yau" tana gama faɗi ta hau gyara kara a murhu,Hajja har can kasar zuciyarta take jin farin ciki, Baffa ya miƙe yana fadin
"Ba ri naje na gaida Inna Wuro (matar Arɗo) kwana biyu ma tace ba kuje kun gaisheta ba, wai dama Aziza ce yar albarka yar dakinta, ke kam ma Azima ko meyasa jininku bai zo daya ba oho!"
"Ai ni babu wanda jinina ya zo daya da na shi!" Azima ta faɗa tana murmushin gefen baki mai ciki da ma'anoni, Hajja ta ce
"Kinyi magana ne?"
"A'a Hajja ban ce komai ba, bari naje na ɗibo ruwa" ta faɗa tare da daukar tulu ta yi waje.
🍃🍃🍃
Tsaye take a wani jeji suna magana da Inno Fandi, Inno Fandi ta ce
"Aziza jejin lore ba kamar sauran jejin yankin kwana bane! Jeji ne da bai tara komai ba fa ce sai manyan aljanu masu mugun sihiri, babu abunda babu a jejin lore,kina tunanin zaki iya zuwa?"
"Inno Fandi Azima ma taje ta dawo balle ni? Ba ma Azima ba, Baffa da yake mutum ma yaje" murmushin manya Inno Fandi ta yi na yaro-yaro ne ta ce
"Aziza tabbas Baffanku mutum ne amma ba kamar kowa ba"
"Eh ni dai Inno Fandi ko ma miye zanje"
"To shikenan Aziza, dokar tafiya jejin lore, ba a yinta da rana, sai dai ki bari da magriba ki tafi, sannan ki tabbata kafin garin Allah ya waye kin baro jejin! Za ki ta gane-ganen abubuwa amma karki tsorata, dan tsoronki barazana ce ga rayuwarki!"
"To amma Inno Fandi ina ga hakan ai babu amfani tunda ni ba mutum ba ce macijiya ce" sake murmushi Inno Fandi ta yi ta ce
"Sanin kasancewarki ba mutum ba shiyasa nake gaya miki hakan, da ace mutum dan adam ne da ya kama hanyar sunansa gawa! Tun kafin ma ya kai ga shiga" Aziza ta jinjina kai, nan Inno Fandi ta gama gaya mata matakin da zata bi taje jejin ta dawo, godiya sosai Aziza ta mata daga nan Inno Fandi ta b'ace, Aziza ta kamo hanyar gida, tana cikin tafiya har ta kusa isa gida ta haɗu da wasu yan matan yankinsu wanda za a kamasu nan da sati daya wato amare kenan, wanda dukkansu babu wacce ta haura sama da shekara shaɗaya, su hudu suka sha gaban Aziza, dayar mai suna Lantai ta ce
"Ke wacece Azima ce ko Aziza!?" Aziza ta ƙara gyara lullubinta tana rufe gefen idonta da gashinta da ya sauko mata har kirji ta kara dukar da kanta kasa ta ce
"AZIZA" wata mai suna Huwe ta ce
"Yau kwayar idonki muke son gani, da asalin fuskarki!" gaban Aziza ne ya faɗi ta ɗan dago a hankali ta ga rana ya faɗi ga shi dole taje gida ta yi shiri, dan haka ta ce
"Kun ga bana son kalen rigima da jan faɗa ku barni naje gida ni ba sa'arku ba ce!" dariya suka kwashe da shi inda suka hau tureta tana ja da baya, har suna faɗin wai gandamemiya marasa farin jini sun ƙi aure, babu mai sonsu! Gajiya Aziza ta yi inda ta daka musu tsawa sai da suka dare, hannu tasa ta kwashe gashinta na gefen fuskarta farin eyes dinta na mage suka bayyana, da mugun gudu wannan ta yi gabas,daya ta yi kudu,daya arewa,daya kuma ta yi yamma, Aziza ta ce
"Alhamdulillahi! Ni ku ka samu, da ace Azima ce sai dai a aurar da wasu amma ba ku ba" tana gama fadi ta wuce da sauri tana sake rufe gefen fuskarta.
🍃🍃🍃🍃
"Assalamu alaikum" Aziza ta yi sallama Hajja dake kwashe kaya ta amsa ta ce
"Aziza sai yanzu? Tun dazu nake tambayar Azima tace min kina rafi, sawunta yau biyar tana ɗibo ruwa"
"AZIMAR!?" Aziza ta tambaya a mamakince, Hajja ta ce
"Eh wollah, yana ganki haka Aziza ba ki da lafiya ne?"
"E Hajja kaina ke ciwo sosai, shiyasa ma na zabi na zauna a rafin yau, ammm Hajja ga wannan ki sha"
"Inji waye?" Hajja ta tambayi Aziza
"Ba kowa nina haɗa miki sabida ciwon bayan da kike fama da shi"
"Ayye Aziza ai naji sauki tun wanda kika bani kwanakin can"
"E duk da haka ma ki sha wannan Hajja" ba tare da Hajja ta sake magana ba tasha, tana gama sha Aziza zata yi magana taji ana shelan kiran sallar magriba, hakan ne yasa kawai ta rungume Hajja wacce taji komai na kanta ya dauke, sun ɗau lokaci a haka kafin Aziza ta saki Hajja ta yi alwala ta gabatar da sallar magriba ta jima tana addua kafin ta tashi ta canza kaya ta ɗauki abubuwan da zata dauka ta kara da wa inda Inno Fandi ta bata ta fito ta fice a gidan kafin Baffa ya dawo, tana zuwa bayan zanar gidansu ta rufe ido nan ta b'ace b'atttt!!.
🍃🍃🍃🍃
Ko da Azima ta dawo gida ita ma shiri gwabzawa ta yi da Innu Maciji,dan ta lashi takwabin kashesa!.
Hajja kuwa bata tambayi inda Aziza take ba.
Tun tsawon dare Azima ta zama macijiya ta sulale a hankali ta fice a gidan, bata zarce ko ina ba sai tsakanin shigowa yankin kwana da yankin ja'i.
🍃🍃🍃🍃
HAHAH NA HADA MUKU DA PG DIN JIYA DA NA YAU, MUN RABU LAFIYA🏃🏻♀️🏃🏻♀️🏃🏻♀️
COMMENTS AND SHARE by
Mom Ahlan, macijiya🐍😂
[4/13, 10:12 AM] Mom Ahlan: 🍃🍃🍃🍃🍃🍃🍃🍃🍃
💥✨ *AZIMA DA AZIZA*💥✨
(🐍 _Macizai ne_🐍)
MALLAKAR.
*ZAHRA ABDUL(MOMYN AHLAN)*
SAHIBAR KAINUWA.
Littafin kuɗi, naira ɗari kacal dan masoyana, turo da kudinki ta wannan acct din
0096035983 balaraba hassan accees bank, ko kuma hoton kati ta wannan lambar 08165550116, pls ban da vtu.
Sanarwa.
Ga yan niger masu bukatar book din nan su tuntubeni dan sanar dasu yadda zasu biya kar ayi babu ku.
*بسم الله الرحمن الرحيم*
*____________________________________*
*🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻
'''{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}'''
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation
*domin shiga shafin mu na Bakandamiya danna nan*👇🏻
https://bakandamiya.com/group/71/kainuwa-writers-association
*____________________________________*
*MARUBUCIYAR.*
1- _HALITTA DAGA ALLAH NE._
2- _GUDU A JEJI._
3- _SHUHADA._
4- _NIDA ƘANNEN MIJINA._
5- _WA'YA KASHE ZAHRA'U?(#200)._
6- _COLONEL UBAIDULLAH._
7- _ITA CE ZUCIYATA(#200)._
8- _SAMIMA (MACIJIYA CE._
9- _GAWURTACCEN SOJA(#300)._
10- _DA NA SANI NA._
11- _BADAWIYYAH_
12- _DEPUTY SUPERINTENDENT OF POLICE (DSP ALIYU HAIDAR)_
Now
13- _AZIMA DA AZIZA (MACIZAI NE🐍)_
_Follow me on wattpad,@Fateemah'0_
🍃🍃🍃🍃🍃
*IDAN DAI BAKI BIYA KUDIN KARATUNKI YANZU BA LALLAI BANE IDAN NA GAMA KI SAMU CMPLT A #100NAIRA BA, ZA KI SAMU NE A #300 DAN HAKA YAR UWA WANNAN BONUS DIN KAR TA WUCE KI.*
*REMAIND 1 FREE..*
🅿️==2️⃣1️⃣↪️2️⃣2️⃣
"Garkuwa suna can, ya ƙi tahowa wai sai ya musu bayani, da wuya yanzu idan su Garkuwa su na numfashi" Liman ya karasa maganarsa yana zama sharaf a ƙasa yana fifita da hularsa irin na fulanin nan wanda ake saƙa shi, cirko-cirko suka tsaya, yayinda Mai Unguwa Ori ya ce
"Mu ba mu kashe Innu Maciji da gangan ba,akasari ba bamu ne muka kashesa ba! Me yasa zasu kashe mana garkuwa!?" cikin fusata wanda yake nuni da damuwa da ɗimauta Baffa ya ce
"Laifin su waye!? Na ce laifin su waye!? Ga irin abunda nake gaya muku amma kun kasa fahimta, ai shikenan sai mu jira har ta Allah ta kasance damu! Ga bala'in kisan macizai! Ga bala'in yaƙi dame zamu ji ne kam! Ya Rabbi gamu gareka! Babu yadda banyi daku karku aikawa da yankin ja'i wasika ba, yanzu mai hakan ta haifar!? Da ace kun saurareni duk ba za a kai ga haka ba, amma mu da shike fulani Allah ya yi mu da taurin kai bamu jin shawari, wlh da kun bi abunda zan shinfiɗa da mun magance matsalarmu da ikon Allah sabida ina da imanin za a....."
"Ka rufe mana baki Magaji!!Ya isheka haka!!" Jauro ya katse Baffa, Jauro shine mai magani na yankin kwana
"A kan me zamu bi abunda zaka gindaya!? Kana da halin da zaka taimakemu amma kayi hakan ne? Duk wani yaƙin da zai kunno kai kasa a ranka har da sa hannnunka a ciki! Da ace ka taimaki yankinka har za a yi aike a wani yanki mai suna yankin ja'i ne! Dan haka babu abunda zaka gayawa mutanen yankin nan! Sai ka bar mu mutu! Idan an kashe Garkuwa da yan faɗa biyu sai mu ma mu jira mu ga mai zai yi ajalinmu,Macizai ne ko kuma jama'ar ja'i!"
"Haba Jauro miye haka ne kake yi! Bai kamata ka faɗawa Magaji wannan maganar ba! Kwata-kwata ma yanzu ba lokacin musayar yawu bane!" cewar Arɗo, Jauro ya ce
"A kan me ba zan faɗa masa ba! Karya nayi ne! Na ce karya nayi ne!!?" sarki Chubaɗo ya ce
"A gaskiya ban san me zance a wannan lamari ba, amma zan iya bin maganar Jauro! Magana ta domin Allah wannan yanki ya kafu tun kakanni, wanda ya taimaka ya kara tsayawa ma wannan yanki kai ne Magaji! Tun ban san da cewa zan zo na zama sarkin fulanin kwana ba, ni dai roƙonka zanyi da girman Allah ka taimakemu Magaji! Muji da masifa ma daya ta ishemu ba sai an ɗaɗo mana da na yaƙi ba" Sarki Chubaɗo ya faɗa yana haɗa hannunsa alaman roƙo,Baffa ya jinjina kai tare da faɗin
"Naji! Kuma na yarda! Abunda aka binne shekaru ashirin shine zanje haƙosa yau! Shin zaku iya fama da masifu biyar!? E ko a'a? A da masifa daya ce, sannan ku ka kuma janyo mana wata da hannunku, yanzu kuma kun bada dama aje a kara haƙo wata shin zaku iya tayani tareta? Nayi imani a yanzu yankin kwana babu mai iya tayani yaƙi da aljanu babu shi!"
" *AZIZA!* Baffa ya ji an raɗa masa a kunne, da sauri ya dago yana waige amma bai ga kowa ba, "Aziza kuma?" Baffa ya tambayi kansa a zuciyarsa yana shirin faɗawa kogin tunani ya tsinkayo muryan Arɗo da Baffa Mandi suna fadin
"Gaskiya ba zamu yarda a haƙo ba,ta bakinka Magaji babu wanda zan iya wannan yaƙin kawai a bar maganar mu sake neman taimako ku kuma ka faɗa mana hanyar da zamu bi" Sarki Chubaɗo ya ce
"E hakane magaji, ka gaya mana wace hanya ce zamu bi?"
"Inaaaaa! Sam-sam ba zai yu ace Magaji bane zai bamu mafita sam ban lamunta ba! Ni fa wlh ina zargin Magaji, duk yadda aka yi yaransa ne *MACIZAI!*" Jauro ya faɗa yana huci, saurin dagowa Baffa ya yi yana kallon Jauro, dama ya jima da sanin jauro baya sonsa yana baƙin ciki da shi, ya jima yana masa ƙulli amma kawai bai san yadda zai yi da Baffa bane, shuru Baffa ya yi yana kallon Jauro, yayinda Arɗo ya katse Jauro da fadin
"Wai lafiyarka kuwa Jauro? Ko dai akwai wata a kasa ne tsakaninka da Magaji?"
"Miye haɗi na da shi?" Jauro ya faɗa yana yiwa Baffa kallon ƙasƙanci,
"Kawai dai gaskiya abunda na sani ne,meyasa ya ƙi aurar dasu yara duk sun gandare a yanki babu mai rab'arsu, shekarunsu goma sha biyar oh Allah ni Jauro, yara na tafiya jiki na lankwasa ace mutane ne! Taya hakan zata kasance!? Kullum fuskarsu a rufe sabida babu ido mai kyau, sannan duk taron da za ayi na magani basu zuwa, dan Allah a cikinku nan ku gaya min suwaye suka yarda da yaran Magaji mutane ne?" nan wa inda Jauro ya haɗa baki dasu suka amsa da basu yarda da Azima da Aziza ba, sannan Jauro ya matso kusa da Baffa wanda ya koma tamƙar wanda aka dasa bishiya ya ce
"Zan fara sakawa yaranka ido fiye da yadda na saka musu a baya, idan har na gano cewa su ɗin ba mutane bane na maka alkawari da hannuna zan kashesu a gabanka!!" rass!rass!rasss! Gaban Baffa ya bada yana kallon Jauro, shi kuwa Jauro yana gama faɗi ya juya zai bar wajan ya tsinkayi muryar Baffa na faɗin
"Allah ya baka sa'a,ni nan zan baka takwabin da zaka kashe yarana a gabana!" ko uhum Jauro bai ce ba ya bar wajan, Baffa Mandi ya ce
"Wai miye haka ne kam?" murmushin takaici Baffa ya yi ya ce
"Ba komai! Ni na jawowa kaina ai!" shi ma ya juya zai bar wajan sai gasu Garkuwa a muraran! Da sauri aka tarbesu kowa yana furta kalman Innalillahi wa inna ilaihirrajiun! Da sauri aka sauko dasu daga dokin yayinda Garkuwa ana sauko da shi yana sumewa, ba shiri aka ce a kai sa wajan Jauro ya duba sa.
@@@@@@@
A ranar yankin kwana babu wanda ya rintsa, Aziza kuwa ta yi neman Azima ta rasa hakika Aziza idan tace akwai natsuwa da sauran hankali a tare da ita ta yi karya.
Da washe gari Aziza na idar da sallar asuba ta fice, jejin kwana ta nufa, tana zuwa ta kirawo Inno Fandi, Inno Fandi na zuwa Aziza tasa kuka, girgiza kai Inno Fandi ta yi ta ce
"Aziza ba kuka bane mafita, abu mai mahimmanci shine a yanzu ki maido da natsuwarki, rashin natsuwarki shi ya hanaki ganin Azima, zaki iya ganinta amma sai kin samu natsuwa, sannan zaki iya zuwa dan ki gayawa Baffanku gaskiyar su waye ku, dan ba zaku ci gaba da boyewa ba Azima na kashe mutane,idan ba haka ba a duban da nayi kowa na yankin nan ya kusan mutuwa! Abunda Magaji baya so dole karshe shi zai aikata, wato haƙo baiwarsa da ya binne shekaru ashirin, sannan duk yaƙin da zata kama da wuta kece garkuwar mahaifinki Aziza,ki koma gida Magaji ya ba ki asalin tahirin rayuwarsa na abunda ya faru shekara ashirin amma har sai kin gaya masa gaskiyar su waye ku!" Inno Fandi na gama faɗi ta b'ace, Aziza kuka takeyi kamar ranta zai fita,taya zata fara faɗawa Iyayenta su ba mutane bane Macizai ne? Taya!? Ya Hajja da Baffa zasuji? Idan suka gano cewa duk kisan da akayin nan Azima ta yi su?" kuka sosai ta yi ta godewa Allah fuskarta ya yi jajur idonta ya ƙara komawa fari sol, tashi tayi tana ajiyar zuciya tare da tattaro natsuwarta kamar yadda Inno Fandi ta gaya mata sai ta samu natsuwa kafin ta iya sanin ina Azima in ba haka ba yau ma kisan da zatayi sai Allah ne yasan adadi, a hankali ta rintse ido tana karanto adduar samun natsuwa ta hanyar tasbihi ga Ubangijin talikai, sai da taji zuciyarta ya samu natsuwa ta sauke ajiyar zuciya sannan ta rintse ido nan ta ganota kwance a jejin hayi, da sauri ta buɗe idon tana me daukar hanyar jejin hayi ba tare da bata lokaci ba gwanda taje suyi na yau.
@@@@
Maga Isar da Sakon yankin kwana ne yake karantawa fada sakon yankin ja'i kamar haka
" _DAMA MUNYI MAMAKI ACE KUNA DA MUTUM A YANKINKU KAMAR MAGAJI BAWA AMMA ACE KUN ZO YANKINMU NEMAN TAIMAKO DA INNU MACIJI! HAKIKA MUMA MUN ZAMA SHASHASHU DA MUKA YARDA DA KUDIRINKU! BAYAN MUN SAN DA CEWA KU ƊIN ABOKAN GABANMU NE NA TUN TULI-TULI! A KODAYAUSHE KU YANKIN KWANA KUNA SO KU DINGA NUNAWA KUN FI SAURAN YANKUNA! TO MUNA SO KU SANI KU KARA SANI, LOKACI YA YI DA ZAMU MAIDA YANKIN KWANA BABBAR MAƘABARTA! DAN KUWA MUNYI SAƘO YANKIN JIMO MUN ZUGASU NA JARMAN MACIZAI DA KU KA KASHE! TUN KAFIN KUYI AIKE YANKIN TUDU MUN RIGAKU DAN BA ZAMU YARDA DA KASHE MANA INNU MACIJI DA KU KA YI BA, MUN GAYAWA YANKIN TUDU KUN KASHE MANA INNU MACIJI SANNAN BA MAMAKI KU MUSU AIKE A BAKU IRO MAGANIN MACIZAI TO MUN TOSHE WANNAN HANYAR DAN MUN TONOWA SARKIN TUDU TSOHON RAUNIN DA YANKINKU SUKAYI MASA TA HANYAR KASHE MASA GUDAN JININSA, DAN HAKA KU FARA SHIRYAWA TARBAN YAƘI NA YANKUNA GUDA UKU, YANKIN JA'I: YANKIN JIMO: YANKIN TUDU: SAKO DAGA YANKIN FULANIN JA'I._"
Maga Isar da sako yana gama karantawa aka hau kallon-kallo, Mai Unguwa Ori ya ce
"Yaƙi da yanki uku a kan yankin daya?"
"Kuma lokaci daya?" cewar Sarki Chubaɗo,Arɗo ya ce
"Mu dai mun san bamu aikata komai ba, mu sa a ranmu wannan wata jarabawa ce daga Allah, kuma yana sane damu, shi zai kawo mana dauki, kar mu ce zamu yi wani shirin yaƙi, mu zubawa sarautar Allah ido" kowa ya amsa da haka ne sannan kowa ya watse cike da alhini.
🐍🐍🐍🐍🐍
Azima na kwance a kan bishiya rabinta mutum rabinta macijiya, jelarta na lilo a ta saman rashen bishiya fuskarta a haɗe har gefe da gefe ya yi jaa! Idonta kuwa ya kara rikiɗewa ya rine ya koma blue sosai harta fari babu, Aziza tana zuwa jejin hayi jelar Azima ta fara hangowa, saurin karasowa ta yi ta ce
"Azimaa!?" jin muryar Aziza yasa Azima sulalowa tare da komawa mutum, a fusace tayo kan Aziza tana isowa gabanta kafin ta yi mata magana Aziza ta yi saurin dafe goshin Azima nan take taji abu ya shige mata kai sai da ta girgiza.
Ganin yadda Azima ta tsaya yasa Aziza faɗin
"Azima lokaci ya yi da zaki saduda! Ki dakata haka" murmushi Azima ta yi tana yiwa Aziza kallon baki da hankali
"Ni kike cewa na saduda? To naji zan saduda, amma bayan na kashe Baffa!" ta faɗa tana cije baki, Aziza ta ce
"Wai ke wace irin dabbace Azima?" murmushi Azima ta kuma yi ta ce
"MACIJIYA! ina kina tambaya ne wace irin dabba ce ni? To ni Macijiya ce kamar ke amma bambancin shine ni muguwa ce ke akasin haka! Har yanzu ban huce da abunda kika min ba, ki bar ganin kinsa jikina ya yi sanyi kin kafar min da dafina! Ba shi zai dakatar dani ba, na iya yau ne kawai, amma gobe zan haɗa da kisan da banyi yau ba!" Aziza ta jinjina kai ta ce
"Kin sha fadamin idan na isa na dakatar dake! Ni kuma na sha fada miki cewa bazan bar hakan ta faru ba, shine zan kara nanata miki, ba zan bar hakan ta faru ba! Dan haka muje gida, kafin Hajja ta titsiyemu da tambaya!" a hankali Azima ta juya tana dafe kirjinta dan abunda Aziza ta tura mata ya shigeta