Showing 51001 words to 54000 words out of 96302 words
Chapter 18 - Aziza da Azima Macizai Ne Part 1 Complete Hausa Novel By Zainab Abdul Mom Ahlan.txt
ga Brother da sauri ta daga tace
"Assalamu alaikum, Brother ina kwana?"
Daga can ya sauke ajiyar zuciya ya ce
"Lafiya lau Sultana ya kuke? Ina Mom? Na kira wayarta bata ɗaga ba,ki gaya mata yau ina hanya"
"To Brother sai dai nima na kirata a wayar"
"Sabida me? yau ba saturday ba ai ba skull, ko kina skull din ne?"
"A'a Bro ina shagon salon na raka Aziza ne a wanke mata kai" jin sunan da ta kira yasaka shi katse wayar da sauri, dan tun ranar da ya buge yarinyar nan yake mafarkin tana neman taimakonsa,tun abun baya damunsa har ya koma damunsa, da fari ya yi tunanin ko dan ya bugeta ne amma a yanzu ya kasa fahimtar halin da yake ciki, da ya ji Mom tace ta dauketa aiki har cikin ransa bai so ba amma dai bai ce komai ba.
Sultana kuwa mamakin katse wayar ya yi tayi,daga baya kuma ta ce
"Uhum Yaya kenan" wayar Mom ta kira bata ɗaga ba itama, ta kalli mata mai salon din ta ce
"Dan Allah Anty ki gama mata da sauri zamu tafi gida Yayana wai yana hanya"
"Ai gashin nata ne dayawa wlh ga tsayi ga cika tabarkallah Ma sha Allah!" Sultana ta yi murmushi.
Kusan mintuna talatin aka kwashe ana wankewa Aziza kai idonta kuwa yana lumshe ko da wasa bata buɗe ba, bayan an gama ne aka busar mata da kai din aka shafa mata mayuka masu kyau da ƙamshi aka taje mata shi sannan aka sa ribbom aka daure mata shi, Ma sha Allah! shine Abun da Sultana ta faɗa ta ciro wayarta tana daukar Aziza hoton wacce ta yi saurin maida hijabinta tana rufe fuskarta,bayan Sultana ta biya kuɗin mai salon suka mata godiya suka fice tana ta yabon kyawun Aziza da dogon gashinta,ita dai Aziza tana murmushi ne kawai sama-sama, bayan sun shiga mota Sultana ta ce
"Yanzu mu fara biyawa mu karbo kayanki na wajan tela, yawwa dama ina so na tambayeki,kin iya karatu?"
Aziza ta gya ɗa kai ta ce
"Nayi sauƙan al'kur'ani mai girma a kauyenmu, sannan na karanta litattafai da dama,na iya rubutu kamar irinsu ko da wasika idan Baffanmu zai rubuta idan rubutun tayi masa yawa ina tayasa rubutawa amma ba da irin rubutunku ba, da harafin su Alif kamar ajimi haka"
Sultana ta ce
"Ahh Ma sha Allah ki ce malama ce" ta faɗa a mamakince dan kuwa ta sha mamaki ɗin sosai, murmushi Aziza ta yi ta ce
"A'a ina dai kan neman ilmin"
To shikenan zan koya miki karatun hausa da turanci ta yadda zaki iya duka,idan har kina ganewa da wuri zan cewa Yayana ya nema miki skull mafi kusa da saurin ganewa,sannan matsalar idonkin nan ya nema miki medicalglass"
"A'a Anty Sultana karki gaya masa,ki bari kawai idan kika koya mini ma ya isa, idona kuma haka yake haka aka haifeni dan Allah ko wa Mom ne karki ce mata komai" Sultana ta yi murmushi ta ce
"To shikenan"
Bayan sunje sun karbo kayan suka koma gida a daki suka samu Mom, Mom tace "sannunku da dawowa 'yan matana har kun dawo" Aziza ta duka kasa Sultana kuma ta zauna a gefen gadon Mom, ta ce
"E Mom mun dawo barka da gida, dazu muna shagon salon Yaya ya kirani wai yana hanya mun kiraki baki daga ba"
"E munyi waya da shi daga baya,kema na kiraki bai shiga bane, lokacin da ya kirani ashe na tashi na bar wayar a parlour shiyasa, yanzu dai ku tashi kuje ku gyarawa Yayan naku dakinsa, idan kun gama sai ku shiga kitchen" dan mom bata yarda da lalaci ba dan babu irin girkin da Sultana bata yi shiyasa da shike basu da yawa a gidan kuma ba yara garesu ba shiyasa mai aiki daya kawai suke dauka, suka amsa da to, Aziza ce ta fara tashi ta fita, Sultana ta ce "zo muje part din Yayan" tayi gaba Aziza na binta a baya, suna fita sai ga wani ɗan ƙofa madaidaici Sultana ta buɗe suka shiga,parlour a kasa har da step wani sashene mai zaman kansa a wajan tabbas an tsara parlourn ya tsaru, Aziza matowa tayi da kallon parlour,idonta ne ya sauka a wani pic babba a parlourn shi daya da kuma wani a gefe su biyu, dukkansu fuskarsu babu murmushi,tabe baki Aziza ta yi,dan ita bata ga abum gyara a wajan ba,ganin yadda take kallon hoton ne yasa Sultana fadin "wannan shine Babban Aminin Yaya baya da wani sama da shi, a tare suke a america tare suka yi karatu gabaɗayansu kuma likitoci ne, karki ga fuskarsu haka a haɗe barin ma yadda kika ga na Abokin Yaya,to wlh yafi Yaya Nawaz sauƙin kai,kawai dai shi magana ce bai cika yi ba da dariya,amma idan kina neman zafin zuciya kika samu Yaya Nawaz kin gama" jinjina kai Aziza tayi ba tare da tayi magana ba,suka hau sama yadda k'asan ya tsaru haka ma saman ya tsaru haka de ta dinga bin Sultana har suka gama suka saka masa turaren wuta sannan suka wuce kitchen suka hau girki, dama Sultana na koyawa Aziza yanayin girkinsu,duk abunda ta koya mata sau daya kuma cikin ikon Allah ta riƙe kenan babu mantuwa, idan tazo yi kuma sai tayi wanda yafi na Sultana daɗi, haka suka yi girki a tare suka gama duk da ba wani hira sukeyi ba,tunda Sultana ta fahimci Aziza bata son yawan magana yasa itama bata takura ba,ita kuwa ba zata fahimci tashin hankalin da take ciki bane,bata fata su gano cewa ita ba mutum bace macijiya ce har su rabu tinda zama dasu na wucin gadi ne, bayan sun gama girki Sultana ta ce
"Aziza je kiyi wanka ki canza kaya, sai ki kwanta ki huta idan kika huta da dare sai mu fara karatun ko?"
"Dazu fa kafin muje wajan wankin kai nayi wanka"
"E na sani,ai ita tsafta bata yawa sai dai tayi kaɗan, zaki dinga yi ne dai-dai gwargwaɗon iyawarki,kuma gwara ki saba da shi tun daga yanzu dan bamu sani ba watakila Mom ta samu surki a nan garin" wani wawan faduwar gaba ne ya ziyarci Aziza ta sake maimaita kalman sirki a ranta, da kyar tayi murmushin karfin hali ta amsa da to a sanyaye sannan ta wuce daki,itama Sultana sama ta haura, Aziza na shiga daki ta wuce toilet, tana shiga ta maida kofa ta rufe ta rintse idonta ya sake komawa fari, fatar jikinta ma fari yana sab'ulewa, daga ƙasarta ta fara rikiɗewa nan ta zama rabi mutum rabi macijiya sannan ta zauna a gefen bath din wanka ta hau kuka, tunowa da maganar Arɗo da Baffa Mandi, na cewa ba zata warke ba har sai sunyi aure, kuma ita warakanta yana tattare da Azima wacce bata ma san a wani duniya Azima take ba, sai bayan da ta gama shan kukan nata kafin ta yi wankan ta fito.
🍃🍃🍃🍃
Sai huɗu Nawaz ya samu damar isowa, ko da ya iso wajan Mom ya nufa nan take masa sannu da zuwa tare da fadin
"Nawaz sai yanzu?"
"Wlh Mom motata ce ta ɗan samu matsala a hanya sai da aka mata gyara"
"Subhanallahi! Karfen nasara babu tabbas Allah ya kara kiyayewa"
"Amin Mom bari na samu na ɗan watsa ruwa sai na fito na ci abinci,ina Sultana?"
"Ba mamaki tana dakinta,bata ji shigowarka ba ai da ka ganta da gudu" murmushi ya yi kawai ya fice, part dinsa ya shiga ya samu na tashin kamshi bai tsaya wani bata lokaci ba ya yi wanka ya shirya ya fito, ji yayi ba zai iya komawa babban parlour ba dan haka ya kira Sultana ta kawo masa abincin part dinsa.
🍃🍃🍃🍃
MOMYN AHLAN✍🏻
GARKUWAR MACIZAI🐍😂
[4/13, 10:12 AM] Mom Ahlan: 🍃🍃🍃🍃🍃🍃🍃🍃🍃🍃
💥✨ *AZIMA DA AZIZA*💥✨
(🐍 _Macizai ne_🐍)
MALLAKAR.
*ZAHRA ABDUL(MOMYN AHLAN)*
SAHIBAR KAINUWA.
Littafin kuɗi, naira ɗari kacal dan masoyana, turo da kudinki ta wannan acct din
0096035983 balaraba hassan accees bank, ko kuma hoton kati ta wannan lambar 08165550116, pls ban da vtu.
Sanarwa.
Ga yan niger masu bukatar book din nan su tuntubeni dan sanar dasu yadda zasu biya kar ayi babu ku.
*بسم الله الرحمن الرحيم*
*____________________________________*
*🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation
*domin shiga shafin mu na Bakandamiya danna nan*👇🏻
https://bakandamiya.com/group/71/kainuwa-writers-association
*____________________________________*
*MARUBUCIYAR.*
1- _HALITTA DAGA ALLAH NE._
2- _GUDU A JEJI._
3- _SHUHADA._
4- _NIDA ƘANNEN MIJINA._
5- _WA'YA KASHE ZAHRA'U?(#200)._
6- _COLONEL UBAIDULLAH._
7- _ITA CE ZUCIYATA(#200)._
8- _SAMIMA (MACIJIYA CE._
9- _GAWURTACCEN SOJA(#300)._
10- _DA NA SANI NA._
11- _BADAWIYYAH_
12- _DEPUTY SUPERINTENDENT OF POLICE (DSP ALIYU HAIDAR)_
Now
13- _AZIMA DA AZIZA (MACIZAI NE🐍)_
_Follow me on wattpad,@Fateemah'0_
🍃🍃🍃🍃🍃
*PAID.*
🅿️=4️⃣5️⃣↪️4️⃣6️⃣
Hakika wannan mafarki ya tayar masa da hankali, ko da ya farka da washe gari jikinsa a mace, da kyar ya gama shiryawa ya fito ya yiwa Mom sallama da shike driver ne zai kaisa ya dawo, shiyasa zasu yi fitar wuri, bayan sun gama sallama da Mom suka rakasa har bakin mota, sai ware ido yake yi inda zan hangi Aziza amma bai ganta ba, kallon Sultana ya yi ya ce
"Ina Aziza ne?"
"Ina ga tana dakinta bari na dubota"
"Noo leave her" ya faɗa yana jan murfin mota Mom tana kan yi masa addua yana amsawa da amin, Mom da Sultana basu koma cikin gida ba har sai da motar ta fice a gate gabadaya aka ja gate din kafin suka koma,ko da suka shiga Sultana ta wuce dakin Aziza ta sameta zaune tana ninke kayan Mom da ta wanke, Sultana ta ce
"Aziza baki fito kinyiwa Yaya Allah ya kiyaye hanya ba har sai da ya tambayeki wlh"
"Ayye ban san ya fita ba da shike ina nan ina ninke kayan Mom ne" ta faɗa ba tare da ta dago ba, alhali taji sadda suka sauƙo dasu Mom har sadda ya shiga mota duk tana tsaye tana leƙensu ta window, sai da ta ga motar ta fice a gidan kafin ta koma daki, Sultana ta ce
"To ke miye haɗinki da kaya ina Buba yake?"
"Wlh jiya ne yaji ciwo a hannu shiyasa na karba kayan na wanke"
"Subhanallahi! Allah ya kiyaye gaba amma ai sai ki faɗa ba wai ki wankesu da kanki ba da an nemo mai wankewa,yanzu dai ki gama ɗin sai ki zo muje Mom ta aike mu karbo kulolin azumi wanda ake abincin sadaka dasu gidan wata kawarta a nan malali"
"To Anty Sultana bari na karasa gani nan zuwa"
"To kiyi sauri ki shirya, saura kuma wlh ki zunduma hijabin kin nan, dan Allah ki nemi abaya ki saka ki yafa gyale akwai gidan da zaki rakani mu shiga tare Mom ta bamu sako ma a gidan" da to Aziza ta kara amsa Sultana, Sultana tana fita Aziza ta sauke ajiyar zuciya tana fadin "Allah ya kaika lafiya Hamma Nawaz, ba mamaki ba zaka dawo ka sameni ba" ta fada tana mai lumshe ido, saurin kwashe kayan ta yi ta kaisu dakin guga, sannan ta koma ta shirya shap-shap tasa doguwar abaya baƙi ta dauki ash'color din gyale taja gashin kanta ta nannaɗesa ta daure a tsakiyar kanta ta dau hula ta saka kafin ta dauki mayafin ta yi lullubinta kamar kodayaushe,ko da ta fito parlour Mom da Sultana suna parlour Mom tana kara ba wa Sultana saƙo, itama ta yi shigar bakin abaya, tana fitowa Sultana ta ce
"Yawwa ko ke fa" murmushi kawai Mom tayi ta ce
"Ma sha Allah 'yan matana, Allah ya kawo miji na gari,kodayake ma yanzu kam sai dai nayiwa 'yata Aziza dan ita Sultana rana kawai za a saka"
A sanyaye Aziza ta ce
"Lahh Anty Sultana shine baki gaya mini ba? To Allah ya kaimu Allah ya sanya alkhairi" Mom ta amsa da amin Sultana kuwa ta dukar da kai tayi tana murmushi,bayan Mom ta gama basu saƙon ta ce
"Dan Allah karku kai magriba,Sultana karki ga dan Nawaz baya nan ku kai magriba kin san dai ko da wani lokaci kiran waya yake yi,da ya kira kuma zai ce ina kike, dan haka kuyi ku dawo"
"In sha Allahu Mom" suka faɗa suna ficewa, duk inda aka aikesu nan suka je, har gidan surakanan Sultana, a gidan kuwa wani ƙaninsa ya ga Aziza sai kallonta yake yi, har sai da ya biyo Sultana yana faɗin
"Anty dan Allah wannan fa?"
Murmushi Sultana ta yi tana faɗin
"Kanwata ce,kana ciki ne?"
"E wlh Anty ina ciki"
"Lallai kam to sai ka gayawa Yayanka"
"To Anty shi da baya kasar ki kirasa ki fara gaya masa,kinga ma sai a haɗa bikin da naku"
"Ahh lallai Walid baka da kunya, wato ma a haɗa da namu?"
"E mana Anty,kodayake ma ku da ba a saka ranar ba, sai a fara namu kafin Yaya ya dawo ke kuma kin gama skull kafin nan kema kin kara girma Anty" ya faɗa cikin tsokana, Sultana ta ce
"Wlh Walid ka rainani,zan haɗaka da Yayanka kuwa"
"Allah ya baki hakuri Anty,ni dai dan Allah ki fara min kamu" banza da shi Sultana ta yi ta shiga mota ta cewa driver yaja su tafi,basu tsaya ko ina ba sai gida,suna isa Mom ta musu sannu da dawowa tace musu idan sun huta su shiga kitchen suyi girki suka amsa da to.
@@@@
Da washe gari sai dare Mom ta samu damar yin waya da Nawaz ya shaida mata cewa ya isa lafiya, Mom ta ce
"Ma sha Allah haka akeso,Allah ya taimaka ka gaishemin da son"
"Zaiji Mom,ina Sultana?"
"Suna can daki ita da Aziza suna karatu, dama kuwa ni ina son yi maka magana a kan yarinyar inaso zan nema mata makaranta, tana da kaifin basira, wlh basu kai sati da fara karatu ba amma karka ga yadda kanta ke ja,abun mamaki" Shuru Nawaz ya yi na dan wani lokaci har sai da Mom ta kuma cewa
"Nawaz bakaji me nace bane?"
"Naji Mom duk yadda kikayi dai-daine, Allah ya baki lada"
"Amin Nawaz" hira suka ɗan taba kafin suka yi sallama da shi.
🍃🍃🍃🍃
Bayan sati biyu da tafiyar Nawaz abubuwa da yawa sun faru daga ciki kuwa harda fara azumi da aka yi, sosai a wannan wata ta ramadan Aziza ta dage da addua Allah ya takaita mata wahalar neman yar uwarta su samu su koma gida, dan ta ƙosa ta koma ta ga iyayenta,kullum da Hajja take kwana take tashi a ranta har ma da Baffanta, ta maida lamuranta ga Allah.
Ta bangaren Azima kuwa ta kasa gane meke mata dadi, dama duk azumin duniya ita kam ba yinsa take yi ba, to wannan din ma haka ta kasance dan ko daya bata yi ba, sosai kuma take sakawa su Hajjaju ido, duk wani ƙullin da suke yiwa AL'MAZEEN.
Ana azumi lafiya da yardan Allah, tunda Nawaz ya bar nigeria ya kasa samun natsuwa, ga mafarkin Aziza da ya gallazawa rayuwarsa wanda ya rasa ya zaiyi da wannan mafarki, ga shi ya kasa gayawa kowa, wanda hakan har rama ya fara saka shi, wanda da an tambayesa zai ce azumi ne kuma ya haɗa masa da ba a gida yake yi ba shiyasa.
Ana saura kwana uku sallah Sultana ta kai musu dinki wajan telarta inda ya cire musu zuƙa-zuƙan dinkuna na gani na fada, laces kala biyu, atampa kala uku, sai shadda da material kala ɗaɗɗaya, da gyalensu da takalminsu dasu sarƙa da ɗankunne, da komai da komai, hakika Mom ta yi kokari,Sultana kuwa ta yi bajinta wajan zabo musu kaya masu kyau, ita ma Azima anyi mata, amma sam basu gabanta dan bata saka a ranta zata yi wani kwalliyar abu sallah ba.
Ana gobe sallah sai aikin suke yi dukkansu a kitchen har da Mom, Sultana ta ce
"Mom wlh zan yiwa Walid ba dadi, kinga yadda ya takura min wai yana son Aziza?" Mom ta yi murmushi ta ce
"Kai yarinta, duka-duka nawa kike bare kuma Walid? to kuma aje ga maganar Aziza wacce take da 15, Aziza ki maida hankalinki a kan karatunki kinji ko? In sha Allah bayan sallan nan zaki fara zuwa university dinsu Sultana tunda Allah ya baki kwakwalwa karki biyewa shirmen Walid kar ma ki fara kulasa, idan Khalil yaji ma ransa ne zai b'aci" Aziza a ranta ta ce
"Ina kuwa nake da lokacinsa,da yasan wacece ni ba zai so kara yin magana da mai irin sunana ba ma" a fili kuma ta ce
"Ni Mom ina da burika da yawa bana da lokacin kulasa"
"Yawwa Azizata" cewar Mom suka ci gaba da aiki har karfe sha biyun dare kafin suka tattara suka kwanta, da washe gari tunda sukayi sallar asuba basu koma bacci ba, abinci sukayi dukkansu har da Mom, karfe takwas da rabi suka gama, Sultana ta ce
"Aziza kiyi wanka da sauri ki zo muje masallaci" Aziza ta amsa da to.
Wanka sukayi suka saka shaddarsu, sannan suka saka hijabansu mai alkebba da takalmansu, suka fito har da Mom itama da ta dake cikin lace dinta, gabadayansu zasuje masallaci dan Mom tace abu daga shekara sai shekara nan ma sai mai tsawon rai wanda Allah ya nufesa da gani.
Haka akayi idi lafiya, sai fatan Allah ya amshi ibadunmu na alkhairi ya yafe mana kurakurenmu amin.
@@@@@@
Bayan sun dawo gida, nan yan uwa da abokan arziki suka hau zuwa ana yiwa juna barka da sallah, masu kawo abinci suna kawowa wa inda ake kai musu ana kai musu, Mom tana haɗawa tana bayarwa ana miƙawa bayin Allah, dasu lemuka da purewater, da kuɗi haka Mom ta dinga rabo, Sultana kuwa tana cikin yan uwanta ana shan su pics ana gaisawa an dade ba a hadu ba, Mom ce ta shigo babban parlour ta kira sunan Sultana ta ce
"Sultana ina Aziza ne kam?"
"Wlh Mom tun da muka dawo inaji bayan mun gama hada abincin da za a fita da shi ban ƙara ganinta ba, dan tun sadda baki suka fara shigowa ban ganta ba" Mom ta ce
"Kin san Aziza bata son mutane kamar ma kunyarsu takeji yanzu haka to ba mamaki