Showing 48001 words to 51000 words out of 96302 words
Chapter 17 - Aziza da Azima Macizai Ne Part 1 Complete Hausa Novel By Zainab Abdul Mom Ahlan.txt
haka aka haifeni"
"To shikenan,bari na bar ki ki huta sai na shigo anjima,idan kika warke sosai akwai abunda zan dinga koya miki,ina sonki da ƙawa! kinga bana da ƙawa bana shiga hidimar mutane amma ke kin shiga raina" murmushi kawai Aziza ta yi dan ita kadai tasan yaƙin da yake gabanta, tashi Sultana ta yi tana fadin
"Bari naje na kawo miki wasu kayana ki saka yanzu kiyi wanka duk da nasan kayan zasu miki yawa, amma ki canza na jikinkin nan" Aziza ta amsa da to na gode sosai, Sultana tana fita Aziza tayi shuru tana saƙa da warwara, zuwa can ta mike zata shiga bayi har ta manta da ciwon kafarta sai ji ta yi ta takesa, zafi taji ta saki kara sannan ta koma ta zauna tana fadin
"Ba zan iya jurewa ba" hannu tasa ta shafe wajan nan kafarta ya dawo dai-dai sannan ta shiga ta yi wanka kamar yadda Sultana ta nuna mata amma bata wanke kanta ba,tana fitowa Sultana na shigowa ta kalleta ta ce
"Ba ki wanke kanki ba? To ki bari karki wanke,idan kikaji sauki sosai sai muje a wanke miki, wannan gashin naki ai sai wajan masu salon, yanzu ga wa innan kayan ki fara lallabawa da shi Mom ta ce zata siyo miki wasu" godiya sosai Aziza tayi,ta dauki wani dogon abaya ta saka ya mata kyau duk da ya mata yawa tasa ta dau hijabi ta tada sallah,ta jima tana addua Allah ya bata mafita a kan wannan babban lamari nasu, kafin sultana ta shigo ta kirata ta fito taci abinci.
🐍🐍🐍🐍
*KUNTAU.*
wani hamshakin gate Azima ta tsaya tana kallon gate din, ganin tsaruwarsa da haduwarsa zuciyarta ne ya raya mata wannan gida taji gidan ya kwanta mata a rai,kuma dole uwar naki sai ta zauna a wannan gida ko ana ha maza ha mata, da wannan tunani ta yi gate din ta hau kwankwasawa.
🍃🍃🍃🍃
MOMYN AHLAN✍🏻
[4/13, 10:12 AM] Mom Ahlan: 🍃🍃🍃🍃🍃🍃🍃🍃🍃🍃
💥✨ *AZIMA DA AZIZA*💥✨
(🐍 _Macizai ne_🐍)
MALLAKAR.
*ZAHRA ABDUL(MOMYN AHLAN)*
SAHIBAR KAINUWA.
Littafin kuɗi, naira ɗari kacal dan masoyana, turo da kudinki ta wannan acct din
0096035983 balaraba hassan accees bank, ko kuma hoton kati ta wannan lambar 08165550116, pls ban da vtu.
Sanarwa.
Ga yan niger masu bukatar book din nan su tuntubeni dan sanar dasu yadda zasu biya kar ayi babu ku.
*بسم الله الرحمن الرحيم*
*____________________________________*
*🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation
*domin shiga shafin mu na Bakandamiya danna nan*👇🏻
https://bakandamiya.com/group/71/kainuwa-writers-association
*____________________________________*
*MARUBUCIYAR.*
1- _HALITTA DAGA ALLAH NE._
2- _GUDU A JEJI._
3- _SHUHADA._
4- _NIDA ƘANNEN MIJINA._
5- _WA'YA KASHE ZAHRA'U?(#200)._
6- _COLONEL UBAIDULLAH._
7- _ITA CE ZUCIYATA(#200)._
8- _SAMIMA (MACIJIYA CE._
9- _GAWURTACCEN SOJA(#300)._
10- _DA NA SANI NA._
11- _BADAWIYYAH_
12- _DEPUTY SUPERINTENDENT OF POLICE (DSP ALIYU HAIDAR)_
Now
13- _AZIMA DA AZIZA (MACIZAI NE🐍)_
_Follow me on wattpad,@Fateemah'0_
🍃🍃🍃🍃🍃
*ALLAH KA RABANI DA ZUWA GABANKA DA HAKKIN WANI, WANDA KUMA YAJE DA NAWA ALLAH KANA GANI ALFARMAN WANNAN WATAN DA ZAMU SHIGA,WATAN FALALA,WATAN TUBA,WATAN MAI ƊINBUN YAFIYA, A YAU DAI NA YAFE MASA,IDAN KUMA HAR ZUCIYARSA BAI JI TSORONKA BA,YA ALLAH KAI KASAN YADDA ZAKA YI DA SHI, ALLAH KASA MU DACE DUNIYA DA LAHIRA,ALLAH AMIN*
*PAID.*
🅿️=4️⃣3️⃣↪️4️⃣4️⃣
Da sauri Sultana ta fito tana kwalawa Aziza kira, fitowa Aziza ta yi ta ce
"Gani Anty Sultana"
"Yawwa Aziza dan Allah zo ki tayani kwashe tray zan kai wa Yaya abinci ashe ya dawo"
"Oh har ya dawo?"
"Nima wlh ban sani ba sai da ya kirani a waya"
"Ayye" cewar Aziza ta duƙa tana daukar tray din da Sultana ta gama jera su plates, sannan itama ta dau ɗaya tayi gaba Aziza ta rakata a baya.
Da sallama suka shiga Sultana ce a gaba sai Aziza dake binta a baya kanta a duƙe cikin hijabi gabanta na faduwa, yana kwance a dogon kujera yana sanye da jallabiyya, amsa sallamar tasu ya yi yana tashi zaune, da sauri Sultana ta ajiye tray din hannunta ta zauna kusa da shi tana masa sannu da zuwa,kanta ya shafa cikin kulawa yana amsawa, duƙawa kasa Aziza ta yi bakinta na rawa ta ce
"Ina wuni *HAMMA NAWAZ* ya hanya?" rassrassras! gaban Nawaz ya faɗi ya ƙura mata ido amma ta gefen ido yana kallon yadda take rirriƙe yatsun hannunta jikinta na rawa daga nesa yake karantar yanayinta duk da ta boye fuskarta cikin hijabi sai saitin ƙaramin bakinta da yake iya hangowa wanda shi ma ke b'ari,
"HAMMA NAWAZ!" yake ta nanatawa a ransa, Aziza kuwa jin bai amsa mata gaisuwarta ba alhali ya amsa na kanwarsa yasa ta tashi a hankali jiki a sanyaye zata fita, watakila baya amsa gaisuwar masu aiki, har ta kai bakin kofa sai taji Sultana na faɗin Aziza ina kuma zakije?"
"Amm dama Anty Sultana dama akwai kayan da ban....kwa. She...ba...ina...so..ne...naje....na kwashe" ta karasa maganar da in-ina tana fita da sauri, cikin fuskar tausayi Sultana ta juyo ta kalli Yayanta ta ce
"Bro,wlh Aziza bata ji dadi ba, ta gaisheka baka amsa ba fa,kuma kamar ma naga tsoronka takeji"
"Za ki yi serving ɗina ne ko zaki cika min ciki da magana?" ya faɗa ba tare da ya kalleta ba, kasancewar tasan halinsa yasa ta zuba masa abincin ta ajiye masa komai sannan ta fice itama,tana fita ya dauki spoon zai kai abincin bakinsa sai ya tsinci kansa cikin rashin jin dadin amsa gaisuwarta da bai yi ba, HAMMA NAWAZ! ya faɗa a fili ya saki murmushi jin yadda ta kira cike da harshen fullaci kuma sai sunan ya yi daɗi a bakinta, da kyar ya lallaba ya ci abinci dan kuwa yaji dadin abincin sosai yaci yasha zobon da suka haɗa ya yi hamdala, nan ya zauna suna waya da amininsa yana gaya masa ranar thursday In sha Allahu yana hanya zai bi jirgi amma sai ya ƙara komawa ta abuja, Allah ya kawo shi lafiya ya yi masa,yana kan waya har aka kira sallar magriba dan haka yace masa za shi masallaci suka yi sallama akan cewa sai sunyi waya anjima, alwala Nawaz ya yi ya tafi masallaci bai dawo ba sai da ya haɗa da isha'i, ko da ya shigo gida babban parlourn gidansu ya wuce da sallama ya shiga a lokacin Aziza na riƙe da kaskon turaren wuta ita kadai ce ma a parlourn, jin sallamarsa yasa jikinta ya dauki rawa wanda bata san dalilin hakan ba, cikin rawar murya ta amsa sallamar ta shi ta ajiye kaskon hannunta tana shirin shigewa daki da gudu taji muryarsa kamar daga sama
"Ya kike? ya jikin naki? Yanzu babu inda yake miki ciwo ko?" ya faɗa lokaci daya,cak Aziza taja ta tsaya,a iya saninta Sultana da Mom suna sama,to kenan da ita yake yi? take tambayar kanta, bata amsa ba bata juyo ba sai da taji ya sake fadin
"AZIZA baki ji ina miki magana ne?" sai a sannan ta juyo murya na rawa ta ce
"Alhamdulillah na warke" tana gama fadi ta shige daki, shuru ya ɗan yi yana nazartan yarinyar daga baya kuma ya yi tsaki ya hau sama,dakin Mom ya je ya kwanta a gadonta suna hira, Mom ta ce
"Bana ma kenan a kasar waje zaku sake yin Azumi ga Azumi ya ƙarato, meyasa ba zaka sa amininka ya dawo nigeria kuyi azumi a gida ba? Bana dai ace kunyi sallah a kasarku tare damu"
"Mom kema kin san ba zai dawo ba ko da na faɗa masa, azumi kuma In sha Allahu mai zuwa idan rai ya kaimu ai muna nan a gida In sha Allah" Mom ta sauke ajiyar zuciya ta ce
"Ai ya kamata,ni na ƙagu ku dawo dan ku nemo matar aure ku aura,barin ma Son yana da bukatar mata wacce zata kula da shi"
"Ai ya samu Mom"
Mom ta ce
"A'a gwara dai fa ya samo mai tarbiyya da natsuwa da hankali" Nawaz ya tabe baki ya ce
"Humm wanda yake fadin zai aura ni kwata-kwata bata min ba,bamu shiri da ita ko kadan amma shi yace zai aureta,kuma abun takaicin fa Mom shima ba sonta yakeyi ba"
"To ina ruwanka? kai fa matsalarka Nawaz zafin zuciya" Mom ta fada tana kallonsa
"Mom ai ba zan can ina ruwana bane ko zafin zuciya,magana ce ta gaskiya,kuma ai abunda ya shafesa ya shafeni"
"To kawai ka tayasa da addua shine babban soyayyar da zaka ci gaba da nuna masa"
"In sha Allah Mom" daga haka suka ci gaba da hirarsu,bai baro dakin Mom ba kuwa sai sha biyu na dare yana fitowa ya shiga dakin Sultana bata nan,tana can dakin Aziza tana koya mata karatu,cikin ikon Allah Aziza ke ganewa, da bai ganta a dakin ba ya yi tunanin ko tana toilet ne dan haka ya wuce part dinsa ya kwanta, sai sha biyu da rabi Sultana ta miƙe tana fadin
"To Aziza bari mu dakata da karatun haka sai Allah ya kaimu gobe kuma, yanzu akwai wani horror series film din da nake kalla, 12 ake farawa a gama 1:30 ga shi yanzu har sha biyu da rabi sai dai na kalli karashi,ko zaki zo muje ki kalla ne?" Aziza ta ce
"Me hakan ke nufi? shi horror din" sai da Sultana tayi dariya kafin ta ce
"Ina nufin fina-finan dodanni, kamar irinsu abun tsoro haka da film din macizai!" rassssss! gaban Aziza ya buga ta yi sauri dago fuskarta ta kalli Sultana ta tsakiyar gashinta da ya rufe mata fuska,Sultana ta kwashe da dariya ta ce
"Matsoraciya kawai,daga faɗa miki har kin firgita, wlh kuma fa Yaya ya hanani kalla har cewa yake min ranar da na fara ganinsu a zahiri zan sani, yanzun ma inada tabbacin ya tafi part dinsa,kinga sai da safe" tana fadi ta fice ta bar Aziza da zare ido tana tunanin ranar da Sultana zata ganta a macijiya mai zai faru? Saurin kau da tunanin ta yi tana fadin "taya ma hakan zata faru?" ajiye tunanin tayi a gefe ta shiga ta ɗauro alwala ta tada sallah,ta jima tana addua tana kuka tana neman taimakon mahaliccinta.
🍃🍃🍃🍃🍃
Kwana a tashi ba wuya a wajan Allah, Azima duk hankalinta ta karkata shi wajan sakawa su Maman Hanan da Maman Beenah ido ganin manaƙisan da suke kullawa wanda bai ji ba bai gani ba, ta sha jin haushin kanta a kan ƙutse da take yiwa wanda bai san da ita ba kamar yadda itama bata san da shi ba, ga shi duk sadda ta yi yunkurin barin gidan sai taji kamar an ɗaure mata kafafu,wannan gida ya zame mata karfen kafa.
🍃🍃🍃🍃
Ana gobe Nawaz sai tafi abuja jibi kuma zai wuce america ya yi wani mugun mafarkin da ya gigita duniyarsa, Aziza ce ya gani a jejin da yafi na kullum muni tana kuka tana miƙa masa hannu ya taimaketa, kar ya tafi ya taimaka mata,ƙiri-kiri ya ganta a macijiya.
🍃🍃🍃🍃
A Lallaba yau aiki yamin yawa🏃🏻♀️
MOMYN AHLAN✍🏻
[4/13, 10:12 AM] Mom Ahlan: 🍃🍃🍃🍃🍃🍃🍃🍃🍃🍃
💥✨ *AZIMA DA AZIZA*💥✨
(🐍 _Macizai ne_🐍)
MALLAKAR.
*ZAHRA ABDUL(MOMYN AHLAN)*
SAHIBAR KAINUWA.
Littafin kuɗi, naira ɗari kacal dan masoyana, turo da kudinki ta wannan acct din
0096035983 balaraba hassan accees bank, ko kuma hoton kati ta wannan lambar 08165550116, pls ban da vtu.
Sanarwa.
Ga yan niger masu bukatar book din nan su tuntubeni dan sanar dasu yadda zasu biya kar ayi babu ku.
*بسم الله الرحمن الرحيم*
*____________________________________*
*🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation
*domin shiga shafin mu na Bakandamiya danna nan*👇🏻
https://bakandamiya.com/group/71/kainuwa-writers-association
*____________________________________*
*MARUBUCIYAR.*
1- _HALITTA DAGA ALLAH NE._
2- _GUDU A JEJI._
3- _SHUHADA._
4- _NIDA ƘANNEN MIJINA._
5- _WA'YA KASHE ZAHRA'U?(#200)._
6- _COLONEL UBAIDULLAH._
7- _ITA CE ZUCIYATA(#200)._
8- _SAMIMA (MACIJIYA CE._
9- _GAWURTACCEN SOJA(#300)._
10- _DA NA SANI NA._
11- _BADAWIYYAH_
12- _DEPUTY SUPERINTENDENT OF POLICE (DSP ALIYU HAIDAR)_
Now
13- _AZIMA DA AZIZA (MACIZAI NE🐍)_
_Follow me on wattpad,@Fateemah'0_
🍃🍃🍃🍃🍃
*PAID.*
🅿️=4️⃣1️⃣↪️4️⃣2️⃣
Mai gadi ne ya leƙo jin ana kwankwasa kofa ya ga bafulatana tana tsaye kanta a duke,
"Baiwar Allah lafiya kuwa?" cewar Mai gadi,kuka Azima ta saka tana fadin ya taimaka ya yi mata magana da masu gidan,mai gadi ya ce
"Baiwar Allah zan gaya miki gaskiya,me wannan gidan baya ma kasar gabadaya! Ya jima baya nan,iyayensa ne a gidan,idan kuma wani neman taimako kikeyi to wallahi ba zaki samu komai a wajansu ba,dan basu kyauta" Azima ta ce
"Ina da bukatar yi musu aiki ne,don Allah kayi mini magana dasu, ni ba kudinsu nake so ba"
Ganin yadda ta dage yasa Mai gadi fadin "to ɗan shigo daga ta ciki sai nayi miki magana dasu" Azima tana sa kafa a gidan gabanta ya bada dammmm!! Da karfi sai da ta danne saitin zuciyarta,mamakin faduwar gaban nata take yi, a kan benci mai gadi ya nuna mata ta zauna shi kuwa ya nufi babban parlourn gidan da sallama, wata mata ce zaune a hakimce a kujera ta ɗora daya a kan ɗaya tana danna waya,sallamar mai gadi ya sakata ɗagowa tana kallonsa da kyar ta amsa,
"Allah ya taimakeki ranki shi daɗe"
"Lafiya kuwa Ɗan'Bala?"
"Wlh Hajjaju wata 'yar fullo ce a waje take ta faman kuka a taimaka mata tana neman aiki, ina ga irin wa inda 'yan fashi suke kai musu farmaki rugarsu ne, su kashe musu kowa su kwashe shanukansu, wlh Hajjaju abun tausayi" shuru Hajjaju ta yi kafin ta kalli Dan'Bala ta ce
"Je ka shigo da ita" Ɗan'Bala ya amsa da to sannan ya fice da sauri ya zo ya samu Azima dake zaune ya ce
"Zo mu shiga Hajjaju na kira" ba tare da Azima tayi magana ba ta tashi ta bi bayansa, suka shiga parlourn, sosai Hajjaju ta karewa Azima kallo sannan ta kwala kiran wata mai aikinsu
"Hadiza! Hadiza! Hadiza!" wacce aka kira da sunan Hadiza ta amsa da na'am da fito da sauri ta duƙa a gaban Hajjaju, Hajjaju ta ce
"Hadiza je ki yiwa Maman Hanan magana ki ce mata da sauko kasa yanzu" Hadiza ta amsa da to,sannan ta hau da sauri, a tare Hadiza suka sauko da wata dakekkiyar mata wacce ita ma da ka ganta zaka san ta yarda da kanta, tana tafiya a gaba Hadiza na binta a baya,tana saukowa ta ce
"Lafiya kuwa Maman Beenah?"
"E lafiya lau mai aiki ce dama za a dauka shine nace a kiraki tukunna"
"E ya kamata ai, idan yaso sai ta dinga gyara su dakuna tana sharewa da gogewa dan aiki ya masu Hadiza yawa"
"To shikenan sai mu kirasa anjima mu gaya masa mun kara daukar mai aiki dan ya tanadi kudin biyanta ita ma"
"Ah to shine magana ai,idan bai kashe mana kudin ba munyi wadaka yadda muke so ma wa zai yi ma wa? Tunda Uwar da Uban duk sun mutu" Maman Beenah ta yi murmushi ta ce
"Ai muyi kokari da ya dawo mu haɗa masa kannanmu ya aura dan mu ci gaba da tatsarsa"
"Wannan magana taki haka take, Hadiza shiga da wannan ki nunnuna mata abunda ya dace, su dakuna zata dinga gyarawa, dakin su Hanan da Beenah da Hanif sai kuma namu dakunan, sai idan *AL'MAZEEN* ya dawo zata dinga gyara masa nashi dakin dan haka har part din Al'mazeen zaki nuna mata amma ba yanzu ba"
"Tukunna ma ya sunanki?"
"AZIMA BANJU!" cewar Azima kanta a duƙe
"To kin dai ji aikin da zaki dinga yi mana ko? Za a dinga baki dubu goma a wata"
"Na gode sosai" cewar Azima, Maman Hanan ta ce
"Kuje da ita Hadiza"
"To Hajiya,Azima zo muje ki ga dakinmu" da kyar Azima ta miƙe dan tun lokacin da aka kira sunan *Al'mazeen* ta nemi natsuwarta da karfin halinta ta rasa, a zuciyarta take tambayar kanta waye shi Al'Mazeen din? dole ta ga waye shi dan daga kira sunansa sai jikinta ya yi sanyi? anya zata iya zama a gidan kuwa? daga fara saka kafarta a gidan tayi tuntube da faɗuwar gaba,yanzu kuma an kira suna zuciyarta ta tsinke, jin babu kuzari a gangar jikinta yasata b'allan gashin kanta ta sa a baki ta lumshe ido tukunna taji ta dawo dai-dai, Hadiza ce ta nunnuna mata abubuwa dasu dakunan da zata dinga gyarawa a sama da kasa,amma bata haura da ita part din Al'mazeen ba, kasancewar an ce mata ba yanzu za a nuna mata ba,Azima kuwa tace ba zata iya jira ba ko da yaya ne sai ta shiga part din ta gani.
🍃🍃🍃🍃🍃
Yau kwanan Azima biyu a gidan,kuma cikin ikon Allah babu wanda ya shiga hidimarta kamar yadda bata shiga tsabgar kowa, sunan wanda ake kira da AL'MAZEEN shine ya tsaya mata a rai, ga shi bata san part dinsa ba,kuma ba zata iya tambayar su Hadiza ba,dan bata son yawan magana , Beenah har kyautar kaya suka mata,kuma babu wanda ya taba yi mata magana a kan rufe fuskarta da take yi kasancewar ansan kunya gado ce ta fulani, ko Hanif da yake namiji baya shiga hidimar Azima,idan kuma gyaran daki ne tana shiga zata hura iska ta bakinta dakin shi da kansa zai gyara kansa,idan ta shiga daki ko minti goma bata yi zata fito da an shiga za a gansa fesss! shiyasa daga Maman Hanan har Maman Beenah suke jin dadin zama da Azima,ita kuwa Azima yanzu tunanin kisa ya fita a ranta sai son ganin waye AL'MAZEEN.
🍃🍃🍃🍃
A kwana biyu kuwa Aziza ta ɗan sake dasu Mom da Sultana barin ma Sultana da bata nuna mata ƙyama tana janta a jiki, ranar da ta cika kwana biyar a gidan ganin jikin nata da sauki sosai yasa Sultana zuwa wajan Mom tace Mom ta basu kudi zata kai Aziza wajan gyaran gashi, Mom tayi murmushi sannan ta bata kuɗi ta ce driver ya kai su.
Bayan sun je shagon salon din za a buɗewa Aziza fuska ta hanyar kwashe mata gashi tayi saurin saka tafin hannunta a fuskarta dama da kyar ta yarda ta cire hijabinta, dariya Sultana ta sa tana fadin
"Duk rowan da kike mana na ganin fuskarki yau dai dole ki bude" da kyar mai salon ta lallaba Aziza tana kwashe gashin Aziza tayi saurin rufe idonta gam, kan aka hau wanke mata kai ɗin, Sultana na zaune a gefe wayarta ta yi ƙara tana dubawa ta