Showing 66001 words to 69000 words out of 96302 words
Chapter 23 - Aziza da Azima Macizai Ne Part 1 Complete Hausa Novel By Zainab Abdul Mom Ahlan.txt
yan kano din ma, bayan sunyi haka da shi ta gayawa Aziza, Aziza ke tambayarta meyasa bata son kano, Sultana ta ce
"Ni da Hanan yadda kika san kamar wuta da auduga, sannan rashin kirki da mugunta irin na Maman Hanan da Maman Beenah abun ba a magana karki so ki yadda suke yiwa Yaya Almazeen, kuma shine mai kudin fa, gwara ma dai Beenah muna ɗan shiri amma banda Hanan, bana son halinsu ne sabida muzgunawa Yaya Al'mazeen da sukeyi"
"Mutane kam ai sai addua, Allah ya kyauta kawai" Sultana ta amsa da amin.
🐍🐍🐍🐍
Hadiza! Hadiza! Hadiza!.
Da gudu Hadiza ta fito ta zube a gaban Hajiya Lawiza Maman Hanan kenan, cikin yauki ta kalli Hadiza ta ce
"Hadiza, maza ki kirawo Azima ki haura da ita can sama part din Al'mazeen ta fara gani da tattare ƙura, suna nan dawowa nan da sati biyu"
🍃🍃🍃🍃
*BACCI NAKEJI WLH🏃🏻♀️🏃🏻♀️🏃🏻♀️🥱😴🏃🏻♀️*
[4/13, 10:13 AM] Mom Ahlan: 🍃🍃🍃🍃🍃🍃🍃🍃🍃🍃
💥✨ *AZIMA DA AZIZA*💥✨
(🐍 _Macizai ne_🐍)
MALLAKAR.
*ZAHRA ABDUL(MOMYN AHLAN)*
SAHIBAR KAINUWA.
Littafin kuɗi, naira ɗari kacal dan masoyana, turo da kudinki ta wannan acct din
0096035983 balaraba hassan accees bank, ko kuma hoton kati ta wannan lambar 08165550116, pls ban da vtu.
Sanarwa.
Ga yan niger masu bukatar book din nan su tuntubeni dan sanar dasu yadda zasu biya kar ayi babu ku.
*بسم الله الرحمن الرحيم*
*____________________________________*
*🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation
*domin shiga shafin mu na Bakandamiya danna nan*👇🏻
https://bakandamiya.com/group/71/kainuwa-writers-association
*____________________________________*
*MARUBUCIYAR.*
1- _HALITTA DAGA ALLAH NE._
2- _GUDU A JEJI._
3- _SHUHADA._
4- _NIDA ƘANNEN MIJINA._
5- _WA'YA KASHE ZAHRA'U?(#200)._
6- _COLONEL UBAIDULLAH._
7- _ITA CE ZUCIYATA(#200)._
8- _SAMIMA (MACIJIYA CE._
9- _GAWURTACCEN SOJA(#300)._
10- _DA NA SANI NA._
11- _BADAWIYYAH_
12- _DEPUTY SUPERINTENDENT OF POLICE (DSP ALIYU HAIDAR)_
Now
13- _AZIMA DA AZIZA (MACIZAI NE🐍)_
_Follow me on wattpad,@Fateemah'0_
🍃🍃🍃🍃🍃
*PAID.*
🅿️=5️⃣7️⃣↪️5️⃣8️⃣
Damm! Gaban Azima ya buga tayi saurin ware blue eye dinta, ta maimaita
"Azizaa! Aziza dai!?" Maman Beenah ne ta kallesa ta ce
"Al'mazeen kasanta ne dama? Sannan sunanta ba Aziza bane, wannan sunanta Azima ne" girgiza kai Al'mazeen ya hau yi yana ƙarewa Azima kallo,yatsar hannunta ya kalla yaga irin zoben da ya gani a hannun Aziza dazu, sannan ace kuma ba Aziza bane? Ko dai ya yi gamo ne? da sauri ya haura sama, yana shiga part dinsa ya ga sai kyalli yakeyi an gyara sosai bai tsaya karewa ɗakin kallo ba, wayarsa ya ɗaga zai kira Nawaz sai kuma ya fasa ya kira layin mom,ringing uku mom ta daga suka gaisa yace mata ya isa lafiya,mom tayi hamdala ta masa sannu da hanya ta kara da cewa
"Ya ka samu mutanen gidan,su Hajiya Lawiza da Hajiya Luba?da kuma yaran?"
"Lafiyar su lau"
"Ya naji muryarka haka Al'mazeen? Kamar kana cikin tashin hankali ko damuwa, ba dai daga dawowarka suka fara cusa maka baƙin ciki ba?"
"A'a mom basu bane, amm nace ba mom? Aziza fa? Ya jikin nata?"
"Alhamdulillah da sauki, ko ba sauki musulmi ai ba zai ce babu ba sai dai yace alhamdulillah, Sultana tana tare da ita dik da naji tace tana da paper 12 zataje skull ga abokin naka ma shima baida lafiya, bayan tafiyarka da ya shigo idonsa a kumbure wai kansa ke ciwo"
"Subhanallahi! Allah ya basu lafiya, dama tunda na ga yanayinsa na san bai da lafiya dan ina kyautata zaton jiya bai yi bacci ba dan a parlor na samesa zaune da asuba, amma da na tambayesa yace min ba komai,zuwa 12 in sha Allah zan kirasa naji ya jikin nasa maybe yanzu yana bacci, bari na kira sultana naji ya na Aziza yake" nan ya yiwa Mom sallama yana katse wayar, sultana ya kira a lokacin tana magana da wata classmate ɗinta a waya,tana gaya mata ba zata samu zuwa skull ba, Brothern'ta da sistern'ta basu da lafiya, suna cikin magana ta ga wayar Al'mazeen ya shigo dan haka sukayi sallama da kawarta ta daga na Al'mazeen, sai da ta masa an isa lafiya kafin yace mata
"Ya jikin Aziza?" kuka ta sa tana kara masa wayar a saitin fuskar Aziza dake fidda huci tana gurnanin zazzabi,bayan ta kara masa wayar yaji kafin ta maida wayar kunnenta tana ci gaba da kuka tana fadin
"Bro ka ji ta ko? Yadda ka barta haka take sai ma abunda ya ƙaru"
"Subhanallahi! Allah ya bata lafiya kin bata wa innan maganin kuwa?"
"E bai jima ba da na bata,amma kamar bai yi aiki ba"
"Karki damu kinji zai mata a hankali kiyi ta yi mata addua, Allah ya bata lafiya!" daga haka ya katse wayar,ya hau jeka ka dawo a daki yana saƙa da warware, "AZIMAA!?" ya faɗa yana rike kai
"To ko dai yar uwar Aziza ce? Tunda sunansu mai haɗi iri ɗaya ne? Amma kuma Nawaz yace an kashewa Aziza kowa bata da kowa! To ba mamaki kamanni ne" daga haka ya miƙe ya shige toilet abunsa ya watsar da tunanin jin yana shirin saka masa ciwon kai.
A kasa kuwa ba ƙaramin daru aka sha da Azima ba a kan abincin da za a kai wa Al'mazeen, ta dage ta kafe tace wlh ba zai ci wannan abincin ba, Maman Hanan ta ce
"E lallai kam Azima, wato kin samu waje kinyi freesh shiyasa zaki fara murza iskanci son ranki ko! To wlh ki bi a hankali" ba tare da Azima tayi magana ba ta karbi abinci a hannunsu Hadiza tayi wajan kitchen da shi ta ajiye ta hau yiwa Al'mazeen sabo, girki takeyi duk da ba wai ta wani iya sosai bane, amma da taji ance Al'mazeen zai dawo yasa kullum tana kitchen dasu Hadiza tana ganin yadda ake girkin barin ma wanda aka ce mata Al'mazeen ɗin ya fi so.
Tana girki tana tunanin sunan da Al'mazeen ya kirata da shi,hakika hankalinta ya ɗan tashi
"Aziza! Aziza! Ina Al'mazeen ya san Aziza? Shi da baya ma kasar, to ba mamaki wajan kiran sunanta aka samu kuskure zai ce Azima yace Aziza" share zancan tayi ta ci gaba da aikinta dan ta san wan can sakaryan tana can jeji, sai bayan da ta kammala ta jera a tray ta dauka ta haura sama.
A hankali ta tura kofar ba tare da tayi sallama ba, Al'mazeen na zaune a parlour da system a gabansa da alama aiki yake yi, yaji mutum ya shigo ba sallama, haɗe rai ya yi, ita kuwa Azima sallama baya daya daga cikin dabiunta, abunda Al'mazeen ya tsana kenan, dan shi mutum ne mai girmama addininsa fiye da komai a rayuwarsa, Al'mazeen da na riƙo da addini fiye da tunanin mai tunani, murya can kasa yace
"Fita ki min sallama, karki sake ki min magana ba tare da kin min sallama ba" juyawan kuwa tayi ta fita ta sake shigowa tare da fadin
"Salamu alaikum" tana tura bakin, bakintan kawai yake iya hangowa yadda take tura shi tana murguɗa shi tunda fuskarta a rufe yake, abun dariya ya ba sa dan haka ya ɗan murmusa ba tare da ta gani ba, abincin ta ajiye tare da fadin
"Kayi hakuri" bata ma san sadda tace masa ya yi hakurin ba, jinjina kai Al'mazeen ya yi,ya ce
"Kece Azima?" ta gya ɗa kai,
"Daga ina kike?" damm! gabanta ya buga, amma da shike zuciyarta a tsaye yake ƙyam tace
"Daga can cikin kauyen kano a wata rugar fulani"
Al'mazeen a ransa ya ce
"E tabbas to basu da alaƙa da Aziza"
"Ina abincin da aka dafa min?" murguɗa baki Azima tayi tace
"Na ajiye musu a bayan kitchen idan sun ga dama su dauka su ci ko su san yadda zasuyi da shi" tana gama fadi ta mike fuuuu ta fice, girgiza kai Al'mazeen ya yi ya ci gaba da aikinsa, sai wajan sha daya da rabi ya ja tray din da ta ajiye masa ya buɗe yana kan buɗewa sai ga ta ta shigo ta duƙa tunowa da dazu ya koreta akan bata yi sallama ba sai ta kara ficewa da sauri ta shigo tana fadin
"Salamu alaikum! ai saika kirani nazo na zuba maka"
"Kina da waya ne?" girgiza kai Azima ta yi ta ce
"A'a bani da shi,amma idan kace AZIIIMAAAA!!🗣️Ai zanji na taho da sauri!" girgiza kai Al'mazeen ya yi ya tashi zai shiga daki, da sauri ta ce
" *HAMMA MAZEEN* abincin fa?"
Cak Al'mazeen ya tsaya yana nanata sunan "Hamma Mazeen!" kirjinsa ne ke bugawa da sauri-sauri,
"Ina zuwa ki zuba kawai ki tafi" ya faɗa yana shigewa bedroom, Azima haushin kanta ne ya kamata, wai meyasa take masa abu kamar wanda ake sakata ko ana bata umarni ne? Meyasa take jin faduwar gaba a kansa, meyasa take jin makarin gubarta yana tattare da shi? Amma kuma tana ji kamar ita da shi an jona musu kuran karfe, saurin tashi tayi ta fice.
🍃🍃🍃🍃🍃
Sai 1 Nawaz ya farka ya ɗan ji kan nasa da sauki amma kan ya yi masa nauyi, wanka ya yi a nan daki ya yi sallah, sannan ya lallaba a hankali ya shiga cikin gida, ba kowa a parlor dan haka ya fara haurawa sama, sai kuma ya juyo yana kallon kofar dakin Aziza, saukowa ya yi ya nufi dakinta, a hankali ya tura da sallama, mom da sultana ma ashe suna dakin, Aziza na jingine tana sallah a zaune a kan gado, saurin karasowa kusa da mom ya yi ya ce
"Mom jikin nata ya yi tsanani ne haka shine baku tasheni munje asibiti ba?"
"Humm! Nawaz kai ma fa ba lafiyar gareka ba, ka ganta nan jiya bata rintsa ba"
"Bari ta idar da sallar sai a kaita asibiti"
"A'a Nawaz ba sai anje asibiti ba, babu amfani, zaku ƙara huda mata jiki ne kawai, yanzu sai kuce zaku sossoka mata allura a ɗaura mata ruwa aja jini, wanda hakan kuma...!" sai Mom tayi shuru, a lokacin Aziza ta sallame sallarta, Nawaz ya miƙe yana fadin
"Mom dan ta gaya miki bata son allura sai a biye mata dan lafiyar wa akeyi? Ina dan lafiyarta ne!" ya faɗa cikin haɗa fuska, ya nufeta yana faɗi wa Sultana ta tashi taje ta cewa driver ya juya mota.
Aziza kuwa ganin ya nufota yasa ta kwalalo ido waje, dan kuwa jikinta yana fidda farin sab'ar maciji idan ya gani fa? Saurin girgiza masa kai ta hau yi muryarta a shaƙe da baya fitowa sosai ta hau fadin ya kyaleta kar yazo inda take, ko kaɗan bai tsaya ya saurareta ba yasa hannu ya yaye bargon jikinta ya kamo hannunta,ji yayi kamar wani fata ya maqale masa a hannunsa, sake hannun nata ya yi yana kallon tafin hannunsa, wani zare ido Nawaz ya yi sai kace idon zasu faɗo ƙasa,ganin sab'ar fatar maciji fari sol a hannunsa, Aziza kuwa banda kakkarwa babu abinda jikinta ke yi,tana sake boye hannunta a cikin hijabin dake jikinta tana jan bargo tana son rufe kafafunta, saurin fizgar bargon Nawaz yayi jikinsa na kyarma, yasa hannu ya figi hijabinta ganin haka yasa mom cewa da sauri
"Nawaz ka haukace ne!? baka da hankali ne!? mai kake shirin yi!?" ba tare da ya saurari mom ba ya ɗago Aziza tsaye wacce jiri ke kwasarta, hannunta ya riko ya ware nan kuwa ya ga jikinta duk b'awu, a lokacin kuma Aziza ta suma, dagota ya yi yana jijjigata cikin tashin hankali yana tambayarta wacece ita.
Cikin kuka Sultana tasa hannu ta kwace Aziza daga hannun Yayanta ta rungumeta ta ce
"Yaya ta suma fa? Dan Allah Mom kiyi wani abu a kai"
Nawaz yasa hannu zai kara jan Aziza daga jikin sultana, sultana tayi saurin juyawa da ita ta kwantar da ita tana murza tafin hannunta tana kuka
"Zan fa karyaki Sultana ina wasa dake ne!!?"
"Wlh Yaya ko kasheni zakayi ba zan bari ka kasheta ba, dan Allah mom kiyi magana ki gaya masa gaskiya,babu amfanin wannan boye-boyen"
"Nawaz ya isa haka! Aziza Macijiya ce!" Mom ta faɗa a tsawace,
Nawaz ne ya yi baya-baya yayi zaman yan bori sharab, mom ta karaso ta kama hannunsa.
kenan mafarkinsa akan yarinyar macijiya ce gaskiya ne? Kallon Mom ya yi da jan ido ya ce
"Mom da macijiya muke rayuwa kuma ke ma kin sani? Taya hankali zai dauka ace mutum maciji? Da ace sultana ce ta faɗa ba abunda zai hanani ban kaita asibiti an duba min kwakwalwarta ba"
Ajiyar zuciya mom tayi tace
"Zaka iya tsayawa ka saurareni uhum? Nawaz magana nake maka" kifa kansa ya yi a kafadar Mom hawaye suka hau gangaro masa wanda bai san dalili ba.
"Nawaz labarin Azima da Aziza da baffansu da kauyensu abun tausayi ne mai cike da zallar al'ajabi" cikin taushin murya Mom ta hau zayyanawa Nawaz labarin Aziza bata boye masa komai ba kamar yadda Aziza ta ba su haka ta bai wa Nawaz, mom tana gama ba shi labarin ya dago yana fadin
"Wlh mom yawancin abun da kika faɗa min ina ganinsa a mafarkina, tun ranar da na bugeta a mota na kawota kaduna tun daga ranar na daina bacci kirki,mom ina yawan ganinta a siffar macijiya tana kuka tana neman taimakona!" jinjina kai Mom tayi ta ce
"Ba mu san me Ubangiji ya boye tsakaninka da Aziza ba Nawaz, amma inaso muyi wani jahadi wana Allah ya zama silar shigarmu aljanna, Nawaz har zuciyata ina jin Aziza,yarinya ce mai hankali da natsuwa da sanin ya kamata duk da tana da kananun shekaru amma tana da hankalin manya da imani da kaddara ga tawakkali da miƙa wuya,kuma dama abunda akeso kenan ga musulmi mumini ko mumina, Nawaz sultana zata bar gidan nan kwanan nan, dan Allah ina so kayi jahadi ka *AURI AZIZA!!*" dummm!! gaban Nawaz ya bada ya kalli Mom da sauri, Mom ta gya ɗa kai tana fadin
"Tun kana yaro ban taba cewa ina neman alfarma ka kasa min ba, ina so ka taimaka ka auri Aziza, ka zamo silar warkewarta, duk wanda ya zama silar farin cikin mutum daya Allah zai zama silar farincikinsa a ranar da babu wani mai gata sai fiyayyen halitta, Nawaz kana da ilmi duk abunda zan gaya maka ka sani sai dai na kara yi maka tuni, idan ka auri Aziza ka zamo silar warkewarta hakika zaka saka mutane dayawa ne farinciki, zaka fidda UWA da UBA daga ƙunci, da sauran yan uwansu, wlh har zuciyata na aminta" kallo fuskar Aziza Nawaz ya yi, hakika daga fuskarta zaka san cewa tana jin jiki
"NA AMINCE MOM! ZAN AURETA!" da sauri Sultana tazo ta duƙa ta rungumesa cikin murna, "da gaske yaya zaka aureta!? Wayyo dadi wlh nayi farinciki"
"Allah ya maka albarka Nawaz" cewar mom tana shafa kansa.
Nan suka zauna a dakin har sai da aka yi sallar la'asar kafin suka fita da niyyar sallah, nawaz msallaci yaje, bayan sun idar ya jima yana kwararo adduoi a kan wannan lamari da yake gani tamkar a mafarkin da ya saba ne.
Bayan ya dawo part dinsa ya wuce, ya dauki wayarsa ya ga miss calls din amininsa,kiransa ya yi ya daga yana tambayarsa ya jikinsa,Nawaz ya amsa da sauki shima yana masa ya gajiyar hanya, Al'mazeen ya amsa da alhamdulillah ya kara da fadin ya jikin Aziza, alhamdulillah Nawaz ya fada, sun ɗan jima suna magana inda Nawaz yake ji ko ya gayawa Al'mazeen? Daga baya kuma ya fasa har suka gama wayar sukayi sallama.
Sai wajan shidda Aziza ta farka sultana ta taimaka mata tayi alwala tayi sallah a zaune kamar dazu, bayan ta idar tayi addua sultana ke gaya mata sadda ta suma mom ta gayawa Yaya Nawaz komai, a lokacin da sultana ke gayawa Aziza Nawaz sun shigo shi da mom, kuka Aziza ta saka tana fadin
"Shikenan zai koreni! Dan Allah Anty Sultana ki ba shi hakuri kar ya koreni, wlh da na samu Azima zan tafi da kaina,tafiya na har abada ba zai sake ganina ba in sha Allah" rasss! gaban Nawaz ya buga jin tace zata tafi na har abada, a hankali Nawaz ya juya ya fita ganin yadda take kukan duk sai yaji babu dadi yana danasanin abunda ya mata, tayi mugun karya masa zuciya.
Mom tace
"Injiwa yace zai koreki a gidan nan? Bana so na ƙara ji kince zaki bar gidan nan na har abada, dan kuwa kina nan a gidan nan har abada In sha Allah,kinji ko?" Aziza ta gya ɗa kai tana kuka.
@@@@@@@@
Da washe gari tana kwance tana fama da kanta,bata san ta yadda zata samu furen huriri ba, da ace ta samu da tuni an wuce wajan, turo kofar akayi da sallama, jin muryan mai sallaman yasa gaban Aziza bugawa, murya na rawa ta amsa, karasowa yayi a hankali ta dago idonta ta kallesa a tsorace, ta gansa da plate a hannu, mamaki ne ya kamata, zama yayi a gefen bedside'drower fuskar yau da sassauci, murya a can kasa ya ce
"Ya jikin naki?"
"Alhamdulillah, ina kwana?"
"Tashi kici abinci ki sha wannan rubutun, wani babban aminin Daddyna ne malami ne wajansa naje jiya da daddare na masa bayani a kan matsalarki, yace na baki wannan zakiji dama-dama duk da ba lallai bane ya dauke miki abunda kike ji gabadaya ba, amma zaki samu karfin jiki" mamaki ne ya ƙara kamata, amma bata da lokacin tsayawa mamakin, a hankali ya dagata ya jinginata da pillow, ya dau spoon ya ɗibi abincin ya kai mata shi saitin bakinta, tsananin mamaki ya hana Aziza buɗe baki taci dan ji take kamar mafarki takeyi, ganin yadda jikinta ke rawa yasa Nawaz furta kalman
"I'm sorry Aziza" a sanyaye, sake yin ƙasa da kanta Aziza tayi gabanta na ci gaba da bugawa, muryarsa taji yana kara fadin
"Na sani, na cusa miki tsorona a zuciyarki, am sorry once again" kuka ta fashewa da shi, ya ɗan rintse ido ya ce
"Kamar na gaya miki bana son kuka ko?" ta gya ɗa kai
"To meyasa kikeyi?"
"Na...ba...ri" ta fada murya na rawa,
"To kici abincin" ya fada yana bata a baki cike da tausayinta, bata wani ci sosai ba ta ce masa ta koshi, cup