Showing 72001 words to 75000 words out of 96302 words
Chapter 25 - Aziza da Azima Macizai Ne Part 1 Complete Hausa Novel By Zainab Abdul Mom Ahlan.txt
daren yadda Aziza bata rintsa ba,haka ma Nawaz, wanda da ya rufe ido ita yake gani sadda take kuka tana cewa kar ya mata allura, tausayinta ne ya rufe masa zuciya, tashi ya yi ya kalli Almazeen dake bacci, parlor ya fito ya zauna ya riƙe kansa, ji yake kamar yasa kuka, ko yaje ya ganta ko zaiji sauki a ransa, abunda ya shafe wata uku yanaji a ransa bayaso ya tabbata, baya so zuciyarsa ace ta kamu da son wannan jaririyar yarinyar, sannan meyasa yake mafarkinta tun daga ranar da ta shigo rayuwarsa, meyasa yake ganinta a siffar macijiya? Saurin tashi tsaye ya yi, tare da naushin iska, a fili yace
"Kamata ya yi ace na tsaneki, dan kin takurawa rayuwata da yawa! Tsawon dare bana bacci duk sabida dake! Why! Why! Why Azizaaa!!" ya faɗa yana rike kansa da yakeji kamar zai rabe gida biyu, anan ya zauna har asuba, bayan Almazeen ya farka ya shiga bathroom yayi alwala ya fito parlor nan ya ga Nawaz yashe a parlor, kallonsa ya yi ba tare da ya yi magana ba yace
"Nawaz kayi alwala kazo muje sallah" Almazeen na fadi ya fice, shima Nawaz din alwala ya yi ya bi bayan almazeen bayan sun dawo daga masallaci, Al'mazeen ya hau shiri, yana shiri yana tambayar meke damun Nawaz, Nawaz yace masa ba komai, bai takura ba ya kammala shirinsa, takwas ya shiga ya yiwa mom sallama, mom tace dan Allah kafin ya wuce ya shiga ya duba Aziza ya bata magani dan jiya bata rintsa ba jikin ya yi tsanani,da to Al'mazeen ya amsa.
Aziza kwance sai b'ari takeyi jikinta mugun zafi, hannunta Almazeen ya kama ya ga wani zobe a hannunta a ƙaramin yatsarta na karshe, bai damu ba, ya gama dubata ya ajiye mata magunguna sannan yamusu sallama ya tafi.
Har wajen mota Nawaz ya raka amininsa tare fadin sai sunyi waya Allah ya tsare, sai da Al'mazeen suka fice kafin Nawaz ya shiga ya gaida mom idonsa a kumbure shima dan baiyi bacci ba ga kansa dake ciwo,cikin kulawa mom ta ce
"Nawaz lafiya kuwa?"
"Mom kaina ke ciwo jiya banyi bacci ba"
"Subhanallah! Sannu Allah ya baka lafiya, ka sha magani ka kwanta"
"To Mom" ya faɗa yana tashi, yana so ya tambayeta Aziza amma yakasa,dan haka ya koma part dinsa ya sha magani ya kwanta.
bayan ya fice wayar Mom ya dauki ruri, tana dubawa ta ga malamin da tasa ya mata istihara a kan Nawaz da Aziza, da sauri ta daga suka gaisa cikin girmamawa,nan ya shaida mata akwai alkairi mai girma da yardan Allah tsakanin Nawaz da Aziza, shi gwargwadon abunda ya gani kenan, godiya sosai mom ta masa nan ta kara jin karfin guiwa.
Dakin Aziza taje ta samu jikin nata ya kara tsanani, sultana idonta ya zazzago tsananin tashin hankali, Sultana tace
"Mom a gayawa Yaya ko akwai maganin da zai bata, kar ta mutu"
"Sultana shima baya da lafiya idonsa a kumbure da kyar yake budewa shiyasa ban gaya masa na Azizan ba,mu bari nasa ya sauka tukunna" Sultana ta ce
"Mom,anya kaddaran Yaya ba a haɗe yake da na Aziza ba kuwa?" shuru Mom tayi, sai zuwa can tace
"Allah ka bayyana mana Azima cikin sauki Ya Allah, Allah ka jinkirtawa wannan baiwa taka Aziza,duk da tana karama da kananun shekaru amma tana da hakuri da tawakkali da juriya" hawaye Sultana ta goge ta fice a dakin, khalil ta kira a waya tana kuka tana roƙonsa a kan a daga bikin nan kar ayi nan da wata daya, dalili ya fara tambayarta amma ta kasa gaya masa,inda a karshe ya katse wayarsa dan ya kasa gane me Sultana take nufi ko dai ta daina sonsa ne?.
🐍🐍🐍🐍
Yau fa Azima murna tun daga baka har kunne, Al'mazeen na hanya, bayan su Hadiza sun gama shirya masa abinci ita kuma ta gyara masa part dinsa tas, ta zo shiga cikin kitchen ta hangi Maman Hanan akan abincin Al'mazeen tana barbaɗa masa magani, girgiza kai Azima tayi, ta bar wajan ba tare da maman hanan ta ganta ba,amma tayi alkawari ba zata bari al'mazeen yaci abincin nan ba.
Goma da rabi motar Al'mazeen ta yi parking a harabar parker motoci, ya jima a motar yana sauke ajiyar zuciya kafin ya fito, nan ma aikatan gidan suka hau masa sannu da dawowa tare da gaya masa sunyi kewarsa, cikin parlour ya wuce nan Maman Hanan da Maman Beenah suka hau murna suna masa oyoyo, a hankali ya russuna ya basu girmansu ya gaishesu sannan ya fara haurawa samansa, Maman Hanan ta ce
"Fuskar mutum kamar fura a dame kullum, Hadiza! Zo ku kai masa abincinsa sama"
"Ba zai ci wannan abincin ba, wani zan dafa masa!" saurin juyowa Maman Hanan da Maman Beenah sukayi suna kallon Azima da kanta ke duƙe da lullubi, cak Al'mazeen da zai hau sama yaja ya tsaya jin kamar ya san mai irin muryar, Maman Hanan ta ce
"Sabida me ba zai ci ba?"
"Sabida bana da bukatar yaci, a bai wa wasu su ci,ko a ajiyewa su Hanif su ci idan sun dawo!" a daqile Azima ke magana, da sauri Al'mazeen ya dawo da baya,nan kuwa ya ganta sanye da bakin abaya itama fuska a lullube, yatsar hannunta ya kalla ya ce
"AZIZAAAA!?" a mamakin ce.
🍃🍃🍃🍃
MOMYN AHLAN✍🏻
[4/13, 10:13 AM] Mom Ahlan: 🍃🍃🍃🍃🍃🍃🍃🍃🍃🍃
💥✨ *AZIMA DA AZIZA*💥✨
(🐍 _Macizai ne_🐍)
MALLAKAR.
*ZAHRA ABDUL(MOMYN AHLAN)*
SAHIBAR KAINUWA.
Littafin kuɗi, naira ɗari kacal dan masoyana, turo da kudinki ta wannan acct din
0096035983 balaraba hassan accees bank, ko kuma hoton kati ta wannan lambar 08165550116, pls ban da vtu.
Sanarwa.
Ga yan niger masu bukatar book din nan su tuntubeni dan sanar dasu yadda zasu biya kar ayi babu ku.
*بسم الله الرحمن الرحيم*
*____________________________________*
*🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation
*domin shiga shafin mu na Bakandamiya danna nan*👇🏻
https://bakandamiya.com/group/71/kainuwa-writers-association
*____________________________________*
*MARUBUCIYAR.*
1- _HALITTA DAGA ALLAH NE._
2- _GUDU A JEJI._
3- _SHUHADA._
4- _NIDA ƘANNEN MIJINA._
5- _WA'YA KASHE ZAHRA'U?(#200)._
6- _COLONEL UBAIDULLAH._
7- _ITA CE ZUCIYATA(#200)._
8- _SAMIMA (MACIJIYA CE._
9- _GAWURTACCEN SOJA(#300)._
10- _DA NA SANI NA._
11- _BADAWIYYAH_
12- _DEPUTY SUPERINTENDENT OF POLICE (DSP ALIYU HAIDAR)_
Now
13- _AZIMA DA AZIZA (MACIZAI NE🐍)_
_Follow me on wattpad,@Fateemah'0_
🍃🍃🍃🍃🍃
*PAID.*
🅿️=5️⃣9️⃣↪️6️⃣0️⃣
"To yanzu miye mafita? Wani sharrin satan zamuyi mata?" cewar Maman Hanan, Maman Beenah ta ce
"Yanzu ke Maman Hanan idan kikace ta sace miki abu za ace dan ta murɗewa Hanan hannu ne, Al'mazeen ba zai yarda ba, tunda su Sady suna hanya mu jira isowarsa kafin mu yanke shawara" Hanan dake kuka ta ɗago tana kallon hannunta da shati ya fito raɗa-raɗa ta share hawaye tana fadin
"Wlh sai na koya mata hankali, zata gane shayi ruwa ne,ita har ta isa! Wacece ita! Waye ubanta! Tana 'yar aiki!"
"Bar ta ubanta zamu ci dan naga abun nata ya fara wuce gona da iri" Beenah ta ce
"Hummm! Ku ga sadda tazo gidan nan ba ruwanta, amma daga dawowar Al'mazeen sai wani falli take ji da shi, ga shi kullum tana part ɗinsa da yana nan da baya nan, anya kuwa babu wani abunda yake gudana a tsakaninsu?"
"Ai dama ba banza ba! kinga dai yadda Al'mazeen ke shakkarmu..."
"A'a fa Maman Hanan ba dai shakkarmu ba,yana dai kyalemu kasancewarsa mai biyayya yana shanye duk baƙinciki da takaicin da muke ƙunsa masa" Maman Beenah ta katsewa Maman Hanan hanzari ta hanyar faɗin haka.
"To ai ga shi yanzu wannan 'yar banzar mai aikin tana shirin hanamu rawar gaban hantsi 'yan kuɗaɗen da muke karba a wajansa wannan shegiya 'yar banzan tayi ƙyam-ƙyam" Maman beenah zata kuma yin magana suka jiyo sallamarsu Sumy da Sady da karfi sai kace zasu tada gidan, kafin su Maman Hanan su sauko Azima ce ta fara sauƙowa ta fito part din Al'mazeen hannunta dauke da kaskon turaren wuta da alama saka masa tayi, wani kallo Sumy da Sady suka bi Azima da shi har ta gama saukowa tayi hanyar waje ta kofar baya ba tare da tasan Allah ya yi wasu halittu a wajan ba, Sumy ta ce
"Tooo! Ina aka samu balarabiya ko ba india?" yatsine fuska Sady tayi ta ce
"Oho" saukowarsu Maman Hanan ne ya katsewa su Sumy maganar da sukeyi, nan aka hau musu sannu da zuwa, sai amsawa sukeyi a gadarance,Sumy ce mai gajan hakuri ta ce
"Anty (maman Hanan kenan) wacece wata 'yar dogowar yarinya fara ,tasa riga da wando da wani baƙin glass sai kace ba india?" Maman Hanan tayi tsaki tana bin Sumy da Sady da kallo ta ce
"Yoo ai ita ce wacce muke gaya muku Azima"
"Kan Uba! To ma uwarwa ta yiwa wannan shigan a gida tana mai aiki uban wa ya bata wannan damar!?" cewar Sumy, Hanan ta share hawayen da suka gaza tsayuwa dan ji take kamar hannunta zai fita ta ce
"Ba dai yanzu ku ka iso ba? To tunda Al'mazeen ya dawo take ji da iskanci iri da kala"
"son Al'mazeen din take yi ne?" cewar Sady tana tabe baki, Beenah tace
"Kar dai har kin fara kishinsa?"
"Wa? Ni? Allah ya kyauta! Al'mazeen baya raina sam, dan haduwa ya hadu amma ni zan auresa ne dan kudinsa kamar yadda ku ka ce Anty,zamu auresa ne sabida kuɗinsa da mun kwasheshi sai ya sakemu"
"Kai kuyi magana a hankali a ƙasa fa muke, kuma wannan shegiyar tana nan, to ma yanzu kin san me ya faru?" cewar Maman Hanan, nan ta basu labarin tsiyar da Azima ke yi a gidan, ta kara da murɗewa Hanan Hannu da Aziman tayi da safe sadda Al'mazeen zaije aiki, har Hanan na nuna musu hannunta da ya kumbura, haɗa baki Sumy da Sady sukayi suna fadin zasu ci Uban Azima, suna kan meeting din yadda zasu korata a satin nan sai gata ta shigo tana shirin sake wucewa kamar dazu Sumy da ta hangeta tun farkon buɗe kofa ta ce
"Keee ƙidahumar jeji jikar shanuka! Zo nan" wani birki Azima taci ta tsaya cak ba tare da ta dawo ba, Sady ta ce
"Dake ake ballagaza!" cije baki Azima tayi idonta na sake rinewa, rintse ido tayi ta hadiye takaicinta sannan ta dawo da baya ta tako tazo gabansu ta tsaya, Sumy ta ce
"Keee! Cire wannan bakin glass din idon naki!"
"Ke a wa fa!? idan naki cirewa wata uwar zakiyi!?" Azima ta faɗa tana tinkaro Sumy, ja da baya sumy tayi, ganin haka yasa Maman Beenah faɗin
"Kee Azima! ba kya ganin baki ne? Ki dau kayansu ki haura musu da shi sama a wannan dakin da Hadiza ta gyara dazun nan"
"Su ɗin kutare ne? ko basu da hannun dauka ne? idan sun ga dama su da kayan nasu su kwana a nan" Azima na gama faɗi ta juya tana taku jikinta na langwasa harta taka step daya ta juyo ta kalli Sumy ta ce
"Kee kuma! karki kuma kuskuren fadin cewa na cire wannan madubin, dan kuwa kallo daya ake yiwa idanuna! idan kika kallesa baki kara kallon komai a rayuwarki!" Azima na fadi ta hau sama fuuuu! Aka bar su Maman Hanan a daskare.
"Ahaf kun gani da idonku ko?" cewar Maman Beenah, Sumy ta ce
"Na san yadda zanyi da shegiya bari Al'mazeen din ya dawo" ta fadi tana hawa sama, Beenah ta kira su Hadiza suka dauki kayan su Sumy suka haura musu da shi tunda Hajiya Azima Banju tace bata hawa da shi.
@@@@@
Yau kasancewar ya wuni a office yana tunanin Azima yasa bai yi wani aikin komai ba, ga shi yana son magana da ita kuma ba hali tunda ba waya ne a hannunta ba,kuma tin daga ranar da ya dawo ya fahimci babu jituwa a tsakaninta da mutanen gidan balle yace zai kira alfarma su ba shi Azima yayi magana da ita, shawaran da ya yanke shine idan ya tashi a office ya biya ya siya mata waya sai ya koya mata yadda zata dinga amfani da shi.
Bai fara aiki da wuri ba sai wajan hudu ya fara duba marasa lafiya shiyasa yau bai tashi da wuri ba sai wajan takwas da rabi, bayan ya tashi sai da ya biya ya siyawa Azima waya tukunna ya nufi gida.
A lokacin Azima na parlour hankalinta tashe tana ta aikin safa da marwa sabida ganin yau Al'mazeen bai dawo da wuri ba, tana cikin wannan zullumi ya yi sallama ya shigo, wani ajiyar zuciya ta sauke wanda bata san lokacin da ya fita ba, da sauri ta karasa gabansa tana tura baki ya ce
"Yi hakuri 'yar fullo"
"To yau ina ka tsaya kasa duk na damu! Nifa tinda nake a rayuwata ban taba damuwa da damuwar kowa ba sai a kanka na rasa dalili! Ban taba sanin miye tunani ko damuwa ba sai a kanka, abunda na sani a rayiwa shine daukar fansa!"
"Fansa kuma!? To kiyi hakuri yau aiki ne ya min yawa a office,nima wuni nayi ina tunaninki kuma babu ta yadda zanyi magana dake shiyasa na siya miki waya da zan dawo, zancan kuma nuna damuwa a kaina ba mamaki ni ɗin na musamman ne!" gaban Azima ne ya faɗi amma da shike tana zumudin waya yasa bata bada hankalinta a kan fadin da ya yi cewa shi ɗin na musamman bane.
Wayar ya nuna mata amma yace ba zai bata ba har sai ya mata chajinsa, jakar hannunsa ta karba, ya yi gaba tana binsa a baya idonta kyam a kansa,gani take kamar akwai wani mugun haske dake fita ta ƙeyarsa tare da wani farin mutum na mata kwala
"MAGAJI BAWA!" ta faɗa tana shirin kaiwa keyar Al'mazeen duka, juyowar da yayi ne yasa tayi saurin maida hannunta, ya ce
"Mene? Waye kuma Magaji Bawa?" haɗe rai Azima tayi ta ce.
"Tsohon abokin gabana ne"
"Abokin gaba kuma?" Al'mazeen ya faɗa cike da mamaki.
"Karka fiye tambaya" ta fada tana wucewa gabansa ta rigasa hawa, duk abunda sukeyi a kan idonsu Sumy:Sady:Maman Hanan:Maman Beenah:Hanan: Sumy tace
"Muje kasa ku ga yadda zan tsara wasan nayi cilli da shegiya wajen gate a daren nan" suka sauko a tare, suna saukowa, Sumy ta ware murya tana kwalawa Azima kira sai kace gidan ke ci da wuta, a lokacin Azima na tsaye a kan Al'mazeen dake jona mata wayarta a chaji, jin kira kuma Al'mazeen ya gane murya ya ce
"Sumayya? Sun zo ne? To meyasa take kiran Azima haka?" Azima wacce zuciyarta ya tunbatsa jin yadda ake kiran sunanta abun ya bata haushi, a tare suka sauko da Al'mazeen,ya kalli Sumy ya ce
"Sumy, Sady, yaushe ku ka zo? Sannan meya faru kike kiran Azima haka?"
"E mana,mun zo dazu, da muka zo na ba wa Azima kayana ta haura min da shi sama, na zo da sarƙata ta gwal amma yanzu na duba ban gani ba, da na shiga dakin kuma na ga Azima a jikin kayana ta bude min akwati har nake tambayarta me take yi sai ce min tayi babu komai nayi hakuri, ka dai ni ba saninta nayi ba banda yau" Maman Beenah ta ce
"Anjima ana yi mana dauki ɗaɗdai, amma dai bamu taba zarginta ba, kasancewar mun yarda da ita"
"Haka ne kam, nima na nemi sarkata wanda ka siya min ɗin nan ban gani ba" cewar Hanan.
Al'mazeen a rayiwarsa ya tsani mai halin b'era dan haka ya ɗago ido yana kallon Azima wacce jikinta ke rawa idonta sun ƙanƙace sun kara rinewa, harta hannunta ya fara sab'ulewa yana zama blue, cikin wani irin murya Al'mazeen ya ce
"Azima da gaske ne? Kin dauka mata sarƙa?"
Wani ihu da gurnani Azima tayi tasa hannu ɗaya ta damƙi wuyar Sumy, nan Sumy ta hau jijjiga kai jin an shaƙe mata magudanar numfashi, cikin daga murya Azima ta ce
"Faɗi gaskiya ko yanzu ki jiki a kabari! Kikace na sace miki sarƙa! Nayi miki kama da b'arauniya! Da ku ka sakani daukar kayanku na dauka!?" duk maganar da Azima take yi tana rike da makogoron Sumy wacce ke mutsil-mutsil idonta har ya fara zazzagowa, su Maman Hanan sai dambe sukeyi da hannun Azima a kan ta saki wuyar Sumy amma sun kasa koda motsi ne da hannun Azima, harta Al'mazeen ya kasa b'anb'are Azima daga cikin Sumy, cikin in-ina da shaƙewa gami da fitar hayyaci Sumy murya irinta wa inda suka sha azaba ko suke sha ta ce
"Wallahiii.....karya......na.....ke...yi...."
🍃🍃🍃🍃
MOMYN AHLAN✍🏻
[4/13, 10:13 AM] Mom Ahlan: 🍃🍃🍃🍃🍃🍃🍃🍃🍃🍃
💥✨ *AZIMA DA AZIZA*💥✨
(🐍 _Macizai ne_🐍)
MALLAKAR.
*ZAHRA ABDUL(MOMYN AHLAN)*
SAHIBAR KAINUWA.
Littafin kuɗi, naira ɗari kacal dan masoyana, turo da kudinki ta wannan acct din
0096035983 balaraba hassan accees bank, ko kuma hoton kati ta wannan lambar 08165550116, pls ban da vtu.
Sanarwa.
Ga yan niger masu bukatar book din nan su tuntubeni dan sanar dasu yadda zasu biya kar ayi babu ku.
*بسم الله الرحمن الرحيم*
*____________________________________*
*🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation
*domin shiga shafin mu na Bakandamiya danna nan*👇🏻
https://bakandamiya.com/group/71/kainuwa-writers-association
*____________________________________*
*MARUBUCIYAR.*
1- _HALITTA DAGA ALLAH NE._
2- _GUDU A JEJI._
3- _SHUHADA._
4- _NIDA ƘANNEN MIJINA._
5- _WA'YA KASHE ZAHRA'U?(#200)._
6- _COLONEL UBAIDULLAH._
7- _ITA CE ZUCIYATA(#200)._
8- _SAMIMA (MACIJIYA CE._
9- _GAWURTACCEN SOJA(#300)._
10- _DA NA SANI NA._
11- _BADAWIYYAH_
12- _DEPUTY SUPERINTENDENT OF POLICE (DSP ALIYU HAIDAR)_
Now
13- _AZIMA DA AZIZA (MACIZAI NE🐍)_
_Follow me on wattpad,@Fateemah'0_
🍃🍃🍃🍃🍃
*JUMMA'@T MUBARAK*🕋
*PAID.*
🅿️=6️⃣1️⃣↪️6️⃣2️⃣
Sakin wuyarta Azima tayi tana huci,tana sakinta Sumy ta zube kasa a sume, cikin tashin hankali suka ɗagota,Beenah wacce saukowarta kenan daga sama dan dama bata nan akayi wannan show din, Mamanta tace
"Beenah! Hanzarta dauko ruwa a fridge" ganin Sumy a baje yasa beenah kwasa da gudu taje kitchen ta dauko ruwa aka yayyafawa Sumy, da karfi ta fizgi numfashi, ganin ta saki ajiyar zuciya yasa Al'mazeen ya fizgi Azima ya wanka mata mari,