Showing 39001 words to 42000 words out of 96302 words
Chapter 14 - Aziza da Azima Macizai Ne Part 1 Complete Hausa Novel By Zainab Abdul Mom Ahlan.txt
yi cike da jin kansa ya zauna,sannan ya miƙawa Dr din hannu suka gaisawa, Dr din ya ce
"Amma ban gane ka ba daga ina? sannan baka yi kama da marar lafiya ba" murmushi ya ɗan yi na gefen baki, sannan ya miƙa masa ID dinsa,yana dubawa ya kallesa ya ce
"Doctor?" ya yi murmushi yana gya ɗa kai, tashi ya yi da sauri yana fadin
"Allah dai yasa sa'a ce ta sameni har office zaka fara aiki a hospital dina" shi ma tashi ya yi tsayen ya ce
"A'a ko ɗaya wlh,ai ni ba a nan yola nake da zama ba,ina zama a kd ne akwai aikin da ya kawoni ne,tun jiya ma ya kamata ace na bar yola to ashe tsautsayi ne ya tsayar dani dan na buge wata yarinya ne da mota shine na kawota asibitin,inaso nayi treatment dinta sai mu wuce dan bana so na ƙara kwana a garin nan"
"Ya Subhanallah! tana ina yarinyar? muje sai ka dubata ai ba komai" ba tare da ya sake magana ba ya bi bayan Dr har izuwa dakin da aka kwantar da Aziza, suna shiga ya hau dubata ya ga bata mutu ba, kayan aiki yace a ba shi ya fadi abubuwan da za a ba sa aka kawo masa sannan ya hau dubata,ya mata su allurai ya sakawa kanta bandage ya mata komai sannan ya ɗora mata ruwa, ya duba agogon dake daure a hannunsa ya ga sha ɗaya, ya kalli Dr ya ce
"Tnk u so much Dr on my way" ya faɗi tare da kokarin daukar Aziza, Dr ya ce
"Haba Doctor ka bari mana ko zuwa gobe sai ka wuce idan ta farka,ga shi kace baka santa ba,duk yadda akayi inaji irin fulanin rugan nan ne, yanzu idan ka wuce da ita kd alhali ba yar kd ɗin ba ce fa?" shuru ya yi yana nazarin maganarsa kuma gaskiya ne tunda a nan ya sameta miye hujjarsa na tafiya da ita? Kawai ya barta idan ta farka taji sauki sai su sallameta ta koma inda ta fito, da wannan tunanin ya ce Dr ɗin ya ba shi acct number ya masa transfer'n kuɗi ya kula da ita idan ta warke sai su sallameta,haka kuwa aka yi bayan ya masa transfer ɗin nan ya fito da sauri ya shiga mota ya tayar yaja ya bar asibitin, har ya fara tafiya ya ɗan yi nisa sai yaji hankalinsa bai kwanta ya tafi ya barta ba,ko ba komai shi ya bugeta sannan bata farfaɗo ba ya tafi ya barta anya ya kyauta kuwa? Saurin juya kan motar ya yi ya koma asibitin, yana zuwa ya ce a ba shi ita kawai, Dr ya ce
"Haba Doctor baka yarda damu bane?"
"No ba haka bane ba wai ban yarda daku bane,kawai ban yarda da shawaran da zuciyata ta bani bane na in tafi in barta alhali ban san a wani condition zata farka ba that's why, amma yanzu zan tafi da ita,idan ta farka lafiya taji sauki zan sa a maidata gidansu" da haka yasa hannu ya dauketa tare da drip ɗin da ya ɗora mata, har yanzu tana bacci, ya gyara bayan motarsa ya kwantar da ita ya ajiye drip ɗin a gefenta yana duba agogo tare da auna tym din da ruwan zai ƙare" da sauri yaja motar yanayi yana duba tym.
🐍🐍🐍🐍
Horn ta yi a wani madaidaicin gate da sauri gateman ya zo ya buɗe yana zuba mata kirari, hannu ta daga masa sannan ta danna hancin motar cikin gidan,tana parking ta fito tana fitowa ita kam ma ta manta da ta saka mutum a bayan both cikin gida ta wuce tun kafin ta shiga take kwalawa Lantana kira, da gudu wata 'yar dattijuwar mata ta fito ta zube a gabanta ta ce "gani *Hajiya Zubaida*"
"Oh dan iskanci dama kinaji ina ta faman kwala miki kira amma ba zaki iya amsawa ba sai dai ki wani fito da mugun gudu sai kace ana gasan tsaren karnuka, ki fa kiyayeni kiyi hankali!, ina Hajiya?"
"Tana ciki"
"Hajiya! Hajiya! Hajiya!" ta hau kwalawa Hajiyan kira.
An ɗau kusan mintuna uku kafin Hajiyar ta fito tana hamma tana matsa ido alamun bacci take yi kiran Zubaida ne ya tayar da ita
"Zuby me ya faru?"
Zama ta yi tana fadin
"Wlh Hajiya sai na ci uban baban mai aikin nan, kin san wai har da kai karar mu police station wai mun yi 'yarsa duka a bi masa kadi"
"To yanzu ya aka kare?" Hajiya tana tambaya tana zama kusa da inda Zubaidan ta zauna,ta ce
"Na basu kudi nayi gaba abina,kee! Lantana kawo min ruwa mai sanyi" tashi tayi da sauri tana fadin to, sannan Zubaidan itama ta tashi ta shige wani daki wanda yake nuni da nata ne, kaya ta shiga canzawa ta ga ko gyara mata dakin ba a yi ba, da sauri ta cire na jikinta ta watsar dan haka dabi'unta yake, ta saka wani riga iyakarsa guiwarta sannan ta fito tana masifa tana zama
"Haba Hajiya ashe ba a gyara min bedroom dina ba?"
"To Zuby wa zai gyara? Masu aikin duk sun gudu sai Lantana ce kawai ita kuma aiki ya mata yawa" tsaki ta ja tana shirin faɗin yanzu wa zai gyara mata daki sai ta tuno da ta sa mutum a bayan mota, tashi tayi da ɗan sauri tana fadin
"Wayyo na manta da wan can bagidajiyar bafulatanan" a haka ta fita riga iya guiwa kai babu ɗan kwali sai uban attachment, Azima kuwa tana kwance a both a macijiya hankalinta kwance tana bacci, jin kara ne ya sakata buɗe ido tayi saurin komawa mutum,tana zama mutum tana bude both din ta kalleta a wulakance ta ce
"Fito" a hankali Azima ta fito tana gyara mayafinta tana tafiya tana lankwasa kamar yadda take tafiya a yankin kwana.
Shiga parlourn sukayi, Zuby ta ce
"Hajiya naji dama kina neman mai aiki to gata nan, a hanya na tsinceta, sai ta ɗora da aikin da Kuluwa ke yi" Hajiya ta kalleta tana toshe hanci ta ce
"Ya sunanki?"
"AZIMAA!" ta faɗa da kaushin murya dan duk tana kula da yatsine fuska da toshe hancin da Hajiya ke yi.
"To dubu biyar zamu dinga baki a duk wata, zaki dinga share-share da goge-goge,inada yara guda uku, ga Zuby nan akwai Yayarta mai suna Baby sai kuma Babban ɗana namiji yayansu kenan, sunansa Munir dik basu nan sun fita idan suka dawo zaki gansu, ke ce zaki dinga gyara musu bedroom dinsu!" Azima dake duƙe ta ce
"Hajiya miye shi badorom din?" Zuby ta ce
"Hajiya ƙidahuma ce daga jeji take taya zaki mata turanci,keee Bagidajiya ana nufin daki,nasan bukka ku ke kira a can jejinku" cije baki Azima ta sake yi, jin yadda zuciyarta ke tafasa idan bata tashi ba komai zai iya faruwa,hannunta ta kalla ta ga ya fara sab'ulewa yana zama blue saurin ajiyar zuciya ta koma yi dan zuciyarta ta yi sanyi, Zuby ce ta sake kwalawa Lantana kira ta amsa da ta zo tace mata ta tafi da Azima ta nuna mata yadda zata yi wanka ta bata wasu kaya da turare dan Azima na wari,sannan idan ta nuna mata ta taho ta saka musu turaren wuta, Lantana ta amsa tana kamo Hannun Azima suka shige daki, suna shiga Hajiya ta ce
"To ita haka zata dinga rufewa mutane fuska a gida?"
"Hajiya manta da wannan kin san bata taba shigowa birni ba,dan haka bata waye ba"
"Kuma hakane fa" cewar Hajiya, Zuby ta ce
"Wai ina Munir da Baby suka je ne?"
"Wa ya san musu" share zan can suka yi suka kamo wata hirar, da Lantana suka shiga daki ta kalli Azima ta ce
"Baiwar Allah zauna ki jirani kinji bari naje na saka musu tiraren na dawo" ta fita da sauri, buɗe ido Azima tayi tana fadin
"Babu wanda ya isa ya zageni ya tafi a banza ba tare da nayi masa hukunci ba! Babu shi!" ta faɗa tana lankwasa yatsun hannunta, an dauki mintuna sha biyar kafin Lantana ta shigo, ta ce
"Azima ko?" Azima ta sunkuyar da kai tana fadin
"E" a sanyaye kaman wata ta kwarai, Lantana ta kama hannunta suka shiga bayi,ta haɗa mata ruwan wanka ta dauko soso da sabulu da shampoo dan ta ga tana da ga shi mai tsayi, ta ce
"Na wanke miki kan naki naga gashin naki da tsayi sosai" Azima ta gyaɗa kai, Lantana ta bata fallan zani ta ce ta cire na jikinta ta ɗora, ba musu Azima ta cire kayanta ta ɗora fallan zani lantana ta jiƙa mata kayan a ruwa tace zata wanke mata su, sannan ta bata kujera ta zauna, Lantana na fara kwashe gashin Azima tayi saurin lumshe ido dan bata son Lantana ta ga kwayar idonta.
Shampoo sosai Lantana ta zuba a kan Azima amma ta ga idan har ta juye ba isa wanke mata kai zaiyi ba, haka yasa ta dauke ledar omo sai da ta zuba ya kai kwankwani ɗaya da rabi kafin ta fara dirzan kai Azima wanda yake fitar da datti, sun kai mintuna talatin tana wanke mata kai kafin gashin ya fito baƙi da shi ga tsamtsi yayi fess! Lantana ta yi murmushi ta ce
"To kiyi wanka,bari na baki waje" har Lantana ta kai bakin kofa sai ji tayi Azima na faɗin
"Miyatti Inna" karo na farko da ta fara yima wani ɗan adam godiya a rayuwarta, murmushi Lantana ta yi ta fice, sai a lokacin tunanin 'yan yankin kwana ya faɗowa Azima a rai,dariya ta hau yi tana fadin
"Ko ina Macijiya Aziza sarkin tausayi oho! Watakila sakaran tana can an kasheta a jeji! Ko da yake ba zasu iya kasheta ba! Amma nasan shanuwar tana can suna jibgarta" ta karasa maganar tana haɗe rai, wanka ta yi sosai ta dirje jikinta ta fito, sai da jikinta ya bushe ta kuma saukowa da gashin kanta kafin ta fito ta samu Lantana ta ajiye mata fallan zani da t-shart da su mai da turare, kayan ta saka, sannan ta dauki kum ta sharce gashin kanta ta zubo da wanda yake rufe masu gefen fuska sabida kar ana ganin kwayar idonsu, gashin ya sauko har ƙirjinta, kallon kanta ta yi a madubi ta ga ta yi kyau,murmushi ta yi, sai ga Lantana ta shigo
"Wa Subhanallahi bi'ahsanul Khaliƙin!" cewar Lantana Azima ta sunkuyar da kai, Lantana ta ce
"Zo muje na nuna miki ayyukanki" Azima ba ta kuma magana ba ta bi Lantana a baya, nunnuna mata komai Lantana ta yi har da dakin Baby da dakin Munir, Azima ta ce ta gane, sannan Lantana ta ce
"Yanzu ki fara gyara dakin Munir dan bai da mutunci ko kaɗan duk wulakanci Baby da Zuby suna bin bayan Munir ne, idan ya dawo ba a gyara masa daki ba ya ganki ba zaiyi la'akari da cewa ke sabuwar zuwa bace ya yi ta kwallo dake"
"DA KUWA KO ƘASHINSA BA ZAN RAGE BA!" Lantana ta ce
"Iyeeee!!?" sauri saita kanta Azima ta yi ta ce
"Inna je ki kawai zan gyara yanzu" fita Lantana ta yi,Lantana na fita Azima ta bi lafiyar gado ta kwanta dan tayi wanka mai dadin da bata bata yi ba taji bacci takeji.
🍃🍃🍃🍃
Karfe sha daya saura ya shigo kd bai wuce gida ba ya wuce asibitinsa da ita, har yanzu kuma bata farka ba,bai damu ba tunda ya mata alluran bacci mai karfi ne, bayan ya mata komai ya ba wasu nurse mutum biyu kula da ita wanda zasu yi nyt duty, kafin ya wuce gida.
A wani katafaren gate yayi horn da sauri aka zo aka buɗe masa, ya shiga ya yi parking din motarsa, da fari ji ya yi kamar ya shige part dinsa dan ya gaji,amma kuma gwanda ya shiga ya yiwa Mom sai da safe, da wannan tunani ya yi babbar parlon nasu da sallama,kanwarsa Sultana tana zaune wacce ba zata wuce 18 ba tana kallon wani horror seris film tana jin sallama ta miƙe da gudu tana fadin
"Oyoyoo *BROS NAWAZZ!"*
🍃🍃🍃🍃
MOMYN AHLAN✍🏻
[4/13, 10:12 AM] Mom Ahlan: 🍃🍃🍃🍃🍃🍃🍃🍃🍃🍃
💥✨ *AZIMA DA AZIZA*💥✨
(🐍 _Macizai ne_🐍)
MALLAKAR.
*ZAHRA ABDUL(MOMYN AHLAN)*
SAHIBAR KAINUWA.
Littafin kuɗi, naira ɗari kacal dan masoyana, turo da kudinki ta wannan acct din
0096035983 balaraba hassan accees bank, ko kuma hoton kati ta wannan lambar 08165550116, pls ban da vtu.
Sanarwa.
Ga yan niger masu bukatar book din nan su tuntubeni dan sanar dasu yadda zasu biya kar ayi babu ku.
*بسم الله الرحمن الرحيم*
*____________________________________*
*🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation
*domin shiga shafin mu na Bakandamiya danna nan*👇🏻
https://bakandamiya.com/group/71/kainuwa-writers-association
*____________________________________*
*MARUBUCIYAR.*
1- _HALITTA DAGA ALLAH NE._
2- _GUDU A JEJI._
3- _SHUHADA._
4- _NIDA ƘANNEN MIJINA._
5- _WA'YA KASHE ZAHRA'U?(#200)._
6- _COLONEL UBAIDULLAH._
7- _ITA CE ZUCIYATA(#200)._
8- _SAMIMA (MACIJIYA CE._
9- _GAWURTACCEN SOJA(#300)._
10- _DA NA SANI NA._
11- _BADAWIYYAH_
12- _DEPUTY SUPERINTENDENT OF POLICE (DSP ALIYU HAIDAR)_
Now
13- _AZIMA DA AZIZA (MACIZAI NE🐍)_
_Follow me on wattpad,@Fateemah'0_
🍃🍃🍃🍃🍃
*INA GAISHEKU KYAUTA YAN PAID GRP MASOYAN........BAN DAI KARESA BA KU KARASA DA KANKU*
*PAID.*
🅿️==3️⃣3️⃣↪️3️⃣4️⃣
Saurin juyowa Azima ta yi ba tare da ta dago ba
Ya yi murmushi ya CE
"Yan mata magana nakeyi fa" da sauri ta matsa gefe ta hau tafiya tana sake rufe fuskarta, shi kuwa binta ya hauyi yana kan yi mata magana,da ya ga ba zata tsaya ba ya sha gabanta, cije baki Azima ta yi tana hade rai,babu abunda ta tsana kamar a sha gabanta,Cikin murya da yake nuna taji haushin takura mata da yayi tace
"Malam wai lafiya?"
Dariya ya hau yi jin yadda kalar Hausar ta ta ke fita, a ransa yake fadin "wow! Wannan daga ganinta bagidajiya ce daga jeji take,bari nayi mata wayo, ko Allah zai sa na shana da ita daga dawowata!"
"Amm yi hakuri ba nufina na ɓata miki rai ba,naga yadda kika ta kalle-kalle ne kamar baki san kowa ba, shine nake so na taimaka miki" ya karasa maganarsa yana murmushi, itama Azima murmushin ta yi ta ce
"To taimakona da me? ko nazo nace da kai inada bukatar taimako ne iyee!!? Na ce maka ina da bukatar taimako ne?"
"Allah ya huci zuciyarki sarauniyar kyawawa, Kano gari ce mai girman gaske da faɗi kuma ke naga alama kamar baƙuwa ce, dan haka ki yarda na taimaka miki naga ke mace ce,ki zo muje gidanmu" mutuwa da mamaki Azima ta yi ko me ta tuna ta yi murmushi ta ce
"Na gode da taimako muje"
"Ina kayan ki?"
"Wala!"
Ta ba shi amsa hankalinta yana can wajan kalle-kalle, jakarsa da ledarsa ya dauka ya ce
"Muje" ya yi gaba ta bisa a baya, kekenapep ya tare musu suka shiga, wani farin ciki ne ke mamaye zuciyar Azima sai magana yake mata amma ina hankalinta ya yi ƙololuwa wajan ganin girma da faɗi da cikowa irin na NA DABO TUMBIN GIWA, ana cikin tafiya sai ji ta yi kekenapep din ya tsaya sai a lokacin ta maido da dubanta ga wani ƙazamin gida wanda ko bukkarsu na yankin kwana ya fi sa kyawun gani, bata damu ba, yayinda ya ce mata ta fito a keken, ba musu kuwa ta fito tana kallon mutanen da suke zaune a kofar gidan masu caca da masu shan wiwi da sigari har ma da masu shan giya, jin yadda ta hadiyi hayakin sigari da wiwi yasa ta hau tari kadan-kaɗan tana yamutse fuska, mai kekenapep ya biya sannan ya kalleta ya ce
"Mu shiga ciki ko?" ya yi gaba ta bisa a baya mutane sai kallonsu suke yi har suka shiga,suna shigewa a cikin wa inda suke zaune a kofar gidan wata mace tayi shigar riga da wando,duk da babu mai kayan mutunci a cikinsu, tab'o dayar dake kusa da ita ta yi ta ce
"Kee Bariki Dadi, baki ga Hoge ya wuce da wata bafulatana ba?" wacce aka kira da sunan Bariki dadi tana riƙe da sigari a hannunta tana zuga suna buga caca ta ce
"Hoge dai? Yaushe ya dawo?"
"Ba mamaki dawowarsa kenan dan na gansa da kayansa" miƙewa tayi da sauri ta ƙudundumo wani ashar sannan ta yi cikin gidan da sauri wa inda suke zaune a tare suka hau zugata suna fadin "idan kinje kici uwarta da ubanta! Bariki dadi! Baki da kyau baki da dadi!" suna fadi suna ihu,ita kuwa fuuuu tayi ciki,a lokacin Hoge har ya buɗe a kulkin dakinsa ya kalli Azima ya ce
"Shigo mana yar fullo" a hankali Azima ta sa kafa ta shiga, a wani jagalgalalliyar katifa ta zauna tana saƙa abubuwa dayawa a ranta, tana zama sai ga Bariki dadi ta banko kofar kamar zata b'alla shi, Azima bata dago ba illa Hoge dake fadin
"Wannan wani irin iskanci ne haka?"
"Ga ka nan kuwa babban dan iskaci baƙin munafuki! Ka hanani kula ko wani bunsuru, sannan ka dauko wata banziya daga dawowarka ka huce da ita a gabana! To wallahi sai naci Uwarta! Ke kuma munafuka zo nan! Sai wani rufe fuska kikeyi sai kace wata ta Allah kina sunkuyar da kai, to idan baki sani ba ki sani! Kina sa kafarki a nan gidan dukkan wata mutuncinki ya zube kuma saina koya miki hankali!" murmushi Azima ke yi a ranta ta ce
"Inason mutane irin haka! Wa inda basu shiga gonata ba ina kau dasu balle wa inda suka shiga" bata gama maganar zucinta ba Bariki dadi ta shaƙo wuyarta, tashi tsaye Azima tayi,tana tunanin dame zata kasheta! ta sareta ne ko ta watsa mata dafi? Hoge ne ya fizgi Bariki Dadi ya koɗa mata mari sannan ya ingizata waje ya juyo yana ba wa Azima hakuri, bata ce masa ci kanka ba,illa da ya gama rawar bakinsa ya fice wai zai kawo mata abinci, bai jima ba kuwa ya shigo da bakar leda ya ajiye mata, budewa Azima ta yi nan tayi arba da kayan dadi murmushi tayi dan bata taba ganin kalar abincin ba, da sauri ta buɗe ta hau ci tana lumshe ido tana gya ɗa kai, shi kuwa yana zaune a gefe yana kallon gashin kanta da ya rufe mata fuska aransa ya ce
"Hummm! dama ana ganin irin wa innan matan a gaske? Dole na shana wlh,daga