Showing 63001 words to 66000 words out of 96302 words

Chapter 22 - Aziza da Azima Macizai Ne Part 1 Complete Hausa Novel By Zainab Abdul Mom Ahlan.txt

ya gani, Aziza ta kasa gane ita wani hali take ciki, shin murna take yi ne ko akasin haka, ta bangaren Azima ma kullum tana sama part din Al'mazeen zata shiga ta gyara ta zama macijiya ta kwanta tayi baccinta.




@@@@@


*MA SHA ALLAH.*




A jiya ne su Nawaz shi da Amininsa Al'mazeen suka samu damar sauka a kasarsu nigeria, sun sauka ne a airport din abuja, Al'mazeen ya kalli amininsa ya ce
"Dude mu wuce kd kawai"
"No wlh sai na huta, mu wuce hotel kawai mu watsa ruwa mu huta idan yaso gobe da safe tunda driver ya zo 10 ma muna kd in sha Allah, ka ga kaima idan ka so zaka huta kafin ka wuce kano,ko ya kace?"
"As u wish" Al'mazeen ya faɗa yana shiga mota.




A waya Nawaz yake gayawa Mom cewa sun sauka lafiya sai gobe da safe zasu shigo Kd, sannu da gajiyar hanya mom ta musu,sannan ta ce Allah ya kaimu goben lafiya,bayan ta katse take gayawa Sultana sun iso amma Nawaz yace sai gobe zasu shigo, itama dai Allah ya kaimun ta yi, ko da Sultana ta gayawa Aziza sai gobe su Ya Nawaz zasu shigo kd amma sun dawo nigeria suna abuja,itama Allah ya kaimun tace jikinta duk a sanyaye, ta bangaren hajjaju Azima,itama da taji kishin-kishin watakila sai gobe ko jibi Al'mazeen zai shigo kano amma ya dawo nigeria ko kaɗan bata ji dadin hakan ba, amma tace tayi hakurin jiransa na watanni masu tsayi dan dai kwana biyu babu damuwa.






Washe gari tunda sukayi sallar asuba basu koma bacci ba, suka share cikin gidan tass suka goge, Aziza ta ce
"Anty Sulty kije ki k'ara gyara part din Hamma Nawaz, ni zan tsaya a kitchen" Sultana ta amsa da to sannan ta fice ta bar Aziza ta hau aikin haɗa su abinci,ko da Mom ta shigo kitchen Aziza ta ce
"Haba Mom kina damu a raye me zaki zo yi a kitchen, dan Allah kije ki kwanta ki huta" murmushi Mom ta yi ta kalli Aziza ta ce
"Hakika mahaifiyarki tayi farin haihuwa da ta haifeki, na yaba da hankali da natsuwarki, Allah ya miki albarka ƴata" Aziza ta dukar ta kai tana juya white eye dinta ta ce
"Amin Mom ɗinmu" fita Mom tayi tana wasu tunani a ranta, hakika da ace Aziza mutum ce babu abunda zai hana bata yiwa Nawaz kwadayin aurenta ba, duk da Nawaz Allah ya yisa da rainakon mace, yanzu zai iya cewa Aziza tayi masa yarinya,ita kuwa zata so Allah ya bata sirka kamar Aziza wacce zata maye mata gurbin Sultana idan tayi aure, ga shi dai Aziza ta shiga ranta sosai, duk da ita bata taba ganinta a macijiya ba, bata ma fatan ganinta a macijiyan, amma taya zata fahimtar da Nawaz har ya aureta? Dan Nawaz murɗaɗɗan mutum ne, zama tayi a bakin gado tana sauke ajiyar zuciya mai karfi,ta jima tana tunane-tunane sannan ta hau adduar neman zabin Allah wa ɗanta da kuma Aziza wacce bata so ta rabu da ita.






Karfe tara da rabi suka kammala komai suka jera a dinning, sannan suka sakawa gidan turaren wuta ya dauki kamshi, Sultana tace
"Aziza je ki dau wanka nima bari na tafi"
"To Antyna a huta gajiya" Sultana ta hau sama, aziza kuma ta shiga dakinta, toilet ta wuce dan tana da bukatar wankan nan sai kamshin abinci take yi,bayan ta fito ta dan murza mai kaɗan a fatarta wanda yake sheƙi, wani doguwar abaya ta saka, ta shafawa kanta mai,ta daure gashin, bata sa hula ba,illa lullubi da ta yi ta rufe fuskarta wanda ta jima bata rufe ba Mom ta hanata rufewa tace tayi rayuwarta ta daina takurawa kanta tunda sun san gaskiya, amma da shike yau Nawaz zai dawo harda bako yasa tayi lullubin.


Tana nan zaune a dakinta har wajan goma da minti asharin, ihun Sultana ta jiyo tana fadin
"Oyoyooo my 2 Brother's!!" wani wawan faduwar gaba ne ya dira a zuciyar Aziza jikinta ya dauki rawa, tana ji ana oyoyo tare da fadin ya hanya, muryan Sultana ta jiyo tana kwala mata kira, a hankali ta miƙe ta gyara mayafinta ta fito jikinta na rawa, a lokacin Nawaz da Al'mazeen suna rungume da Mom, Sultana na tsaye a gefensu tana dariya bakinta yaki rufuwa dan murna, bayan sun saki mom take kara musu ya hanya suna amsa da lafiya alhamdulillah, nan Mom ta rufesu da addua na nasarar da suka samo,zama sukayi a kujeran cikin parlourn, Sultana ma ta zauna kusa da Yayanta, tana kara gaishesa ya amsa yana tsokanarta amarya-amarya, rufe fuska tayi da tafin hannunta jin Al'mazeen shima ya hau tsokanarta, ganin yadda suke murna da nishaɗi yasa hawaye zubowa a idon Aziza tana kallonsu tana murmushi dan sun burgeta, a hankali ta juya zata koma daki idon Sultana ya sauka a kanta, ta ce
"Aziza kina jina tun dazu nake kiranki Yaya sun dawo amma kika min shuru?" tun sadda Sultana ta kira sunan Aziza hankalin Nawaz ya koma kanta yana kare mata kallo kirjinsa na bugawa, tunda ya bar nigeria mafarkin yarinyar nan ya hanasa kiba, Al'mazeen ya kalleta shima yaji gabansa ya fadi, Mom tace
"Karaso mana ɗiyata" a hankali Aziza ta fara taka kafarta wanda take jinsa tamkar baya jikinta dan kafafun sun mata nauyi, ta karaso ta duka tana gaishesu kanta a duƙe fuskarta kuma a lullube, amsawa Al'mazeen ya yi sabanin Nawaz da yake ji kamar zuciyarsa zata tsaga kirjinsa ta fito waje, bayan ta gaishesu ta mike ta kawo musu abun sha, suka ce ba zasu ci abincin yanzu ba, zasuje su kwanta su ɗan yi bacci zuwa azahar, sai sun farka kafin su ci abinci, a tashi lafiya Mom ta musu suka miƙe a tare, har sun kai kofa Mom ta ce
"Al'mazeen amma ba yau zaka tafi kano ba ko?"
"E Mom sai Allah ya kaimu gobe"
"To Allah ya kaimu lafiya"
"Amin" ya amsa a sanyaye yana bin bayan Nawaz wanda shi bai tsaya ba.




Kwanciya sukayi ba jimawa kuwa bacci ya suresu, karfe daya da rabi suka farka suka yi sallah, Nawaz ne ya fara tashi yana fadin
"Yunwa nakeji yanzu kam, ka zo muje muci abinci"
"Okay muje" Al'mazeen ya faɗi shima yana tashi, wayar Al'mazeen ne ya dauki ruri Nawaz na ganin mai kiran ya yi tsaki yana fita.




A hankali take tafiya Mom ta bata sako ta kai wa driver zai kai wa Hajiya Hauwa, kanta a sunkuye ga shi ta yi lullubi ga tunani,tana tafiya tana tunani, shi kuwa Nawaz hankalinsa na cikin waya yana dannawa, dai-dai wajan kofar shigowa babban parlour sukayi karo nan kafarta daya ya zame yana shirin wucewa ƙananan step guda uku na shigan parlourn ɗin, ganin haka yasa cikin saurin Nawaz yasa hannu ya fizgota, mayafinta ya faɗi kasa, gashinta da bata yi masa daurin kirki ba ya koma baya yana lilo, tsoro yasa ta waro idonta gabadaya waje, caraf sukayi 4 eye da Nawaz, wani mahaukacin bugawa kirjin Nawaz ya yi ganin white eye ɗin Aziza, saurin saketa ya yi ta faɗi ta bugu da duwawu, taji zafi dan haka tace
"Washhh Allah na!" Al'mazeen dake waya ya ga Nawaz ya saki yarinyar mutane a kasa ta bugu dan ya ga sadda sukayi karon zata faɗi ya riƙeta amadadin ya tsaidata da kafarta sai kuma ya saketa?.




"What's wrong with u dude?" Al'mazeen ya faɗa yana shirin sa hannu ya dago Aziza,kafin Al'mazeen ya ɗagata,tuni Nawaz yasa hannu ya sake fizgota ya tsaidata da kafafunta, ya duka ya dauki mayafita ya sa mata a kai, murya a daqile yace mata bar nan, da sauri kuwa Aziza ta bar wajan, Al'mazeen ya kallesa ya girgiza kai ya wuce ya bar sa tsaye, jikin Nawaz ne ya dau rawa yana kara tariyo yadda ya ga idon Aziza, me hakan ke nufi? Ya tsaya yana tambayar kansa.




🍃🍃🍃🍃




MOMYN AHLAN✍🏻[4/13, 10:13 AM] Mom Ahlan: 🍃🍃🍃🍃🍃🍃🍃🍃🍃🍃


💥✨ *AZIMA DA AZIZA*💥✨
(🐍 _Macizai ne_🐍)


MALLAKAR.


*ZAHRA ABDUL(MOMYN AHLAN)*


SAHIBAR KAINUWA.


Littafin kuɗi, naira ɗari kacal dan masoyana, turo da kudinki ta wannan acct din
0096035983 balaraba hassan accees bank, ko kuma hoton kati ta wannan lambar 08165550116, pls ban da vtu.


Sanarwa.
Ga yan niger masu bukatar book din nan su tuntubeni dan sanar dasu yadda zasu biya kar ayi babu ku.


*بسم الله الرحمن الرحيم*
*____________________________________*


*🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation


*domin shiga shafin mu na Bakandamiya danna nan*👇🏻


https://bakandamiya.com/group/71/kainuwa-writers-association


*____________________________________*


*MARUBUCIYAR.*
1- _HALITTA DAGA ALLAH NE._
2- _GUDU A JEJI._
3- _SHUHADA._
4- _NIDA ƘANNEN MIJINA._
5- _WA'YA KASHE ZAHRA'U?(#200)._
6- _COLONEL UBAIDULLAH._
7- _ITA CE ZUCIYATA(#200)._
8- _SAMIMA (MACIJIYA CE._
9- _GAWURTACCEN SOJA(#300)._
10- _DA NA SANI NA._
11- _BADAWIYYAH_
12- _DEPUTY SUPERINTENDENT OF POLICE (DSP ALIYU HAIDAR)_
Now
13- _AZIMA DA AZIZA (MACIZAI NE🐍)_


_Follow me on wattpad,@Fateemah'0_


🍃🍃🍃🍃🍃




TNK U 4 CMMNTS MY PPL'S.




*PAID.*
🅿️=5️⃣1️⃣↪️5️⃣2️⃣






"To meyasa kika ce ba zaki je ba? Ni wlh na zata Hamma Khalil shine Abokin Hamma Nawaz" cewar Aziza,Sultana ta ce
"A'a kinga hoton Khalil" Sultana ta faɗa tana nunawa Aziza hoton Khalil a wayarta, Aziza ta yi murmushi ta ce
"Ma sha Allah,kun dace sosai, Allah ya kaimu musha shagali"
"Amin-Amin"
"To ke yanzu Anty Sulty miye abun damuwa dan za a saka bikinki?"
"Ke Aziza baki da hankali ko? Ke kin san takura irin na Khalil kuwa? Wlh idan ya dawo ba zai bari na dinga motsawa ko nan da can ba,kuma duk abunda ya faɗi Mom zata hau kai ta zauna, taya zamu fara tafiye-tafiye wajan neman Azima? Sannan ma duk ba wannan ba, wannan babban lamari bai kamata ace zamu iya mu biyu ba, Mom tana da fahimta ni a ganina tun a ba kowa mu gaya mata gaskiya, dan kar a zo wata rana ta sani kuma abun ya kwab'e mana" jikin Aziza ne ya dauki rawa ta kalli Sultana ta ce
"Anty Sulty Mom zata koreni!" ture abincin gabansu gefe Sultana ta yi ta kamo hannun Aziza ta ce
"Taya Mom zata koreki Aziza? Babu amfanin boye mata abunda zata sani duk daren daɗewa kamar yadda nima na sani a yanzu, dan haka gwara mu gaya mata a san abun yi tun a yanzu, ga shi ana maganar tsaida bikina kwanan nan, tsammaninki yanzu Khalil zai dawo a cikin sati, su Yaya Nawaz zasu dawo nan da wata daya,ina mai tabbatar miki za a iya aurar dani nan da wata biyu, dan haka gwara muyi da gaske, yanzu ki tashi muje mu samu Mom mu gaya mata gaskiya, dan hausawa na cewa da zafi-zafi ake dukan karfe"
"Wani gaskiya zaku gaya min?" suka ji magana daga bayansu, ba iyakar Aziza ba, har ta Sultana sai da ta kwalalo ido waje, Mom ta ce
"tambayarku nake yi, sai zazzare idanu kukeyi ku min magana mana, dan wannan idon naku baku da gaskiya" Sultana ta kalli Aziza wacce take girgiza mata kai alaman kar ta faɗa, Sultana ta hau in-ina tama kasa magana,idan ta kalli Mom, Mom zata ce ta gaya mata me suke boyewa,idan ta kalli Aziza zata girgiza mata kai kar ta faɗi, dan haka Sultana ta kasa magana banda in-inar da takeyi dan an sakata a tsakiya, ganin ta ruɗe har zufa take yi, ga Aziza da ka kalleta kaga tashin hankali a fuskarta ganin haka yasa Mom kamo hannun Sultana ta ce
"A iya sanina ban yi miki tarbiyyar k'arya ba,ba halinki bane, sannan baki boye min abu, duk da ban san Aziza sosai ba amma zan iya tsayawa na bugi kirji na faɗi halin Aziza, dan haka karku fara min karya daga yau, karku boyemin komai, tun dawowarku nake ganin damuwa a fuskarku, ku gaya min meke faruwa" kuka Aziza ta fashe da shi tana duƙawa ta rufe fuskarta da tafin hannunta, Sultana tace
"Aziza ki kwantar da hankalinki, Mom zan gaya miki" Sultana ta zaunar da Mom tace
"Ban san taya zaki fara daukar maganar ba, watakila da ace ni daya ce zakice nayi gamo da aljanu" Sultana bata fara cewa Mom Aziza macijiya bace,tun daga tushen labarin ta dauko mata tana bata tiryan-tiryan har ta kawo mata shi karshe ta dasa aya, wani ware ido Mom tayi tana bin Aziza da kallo wacce ta haɗa kai da guiwa tana kuka, hakika hankalin Mom ya tashi, Sultana kuwa ta gaya mata ta ga Aziza a macijiya kuma ita ce ma ta taimaketa daga hannun su dan gidan Alhaji wanda da badin Aziza ba da sunyi mata fyaɗe, jikin Mom banda kyarma babu abunda yakeyi, ta jima tana karanto kalman
"Innalillahi wa inna ilaihirrajiun!" kafin ta fara jin tana samun natsuwa, sai da ta ware tukunna ta yi kan Aziza ta duka duk da zuciyarta na dukan tara-tara ta kama Aziza ta rungumeta tana rarrashinta, cikin kuka Aziza tace
"Mom dan Allah karki tsaneni! Dan Allah karki koreni! Dan Allah karki ji tsorona!" girgiza mata kai Mom ta yi ta ce
"Ko daya ba zanji ba, kamar yadda kike a da haka kike a yanzu, ai ba laifinku bane, a gaskiya Banju ba karamin mugu azzalumi bane marar imani, Allah sai ya saka muku, Allah ya bayyana mana Azima lafiya, Allah kuma ya kare bayinsa wanda Banju yake shirin tarwatsawa" suka amsa da amin,bayan sun gama yan koke-kokensu da jajinta lamarin Mom ta miƙe ta fice zuciyarta cike da zullumi, abu sai kace a film, bata fata ta ga Aziza a macijiya a labarin ma ya isa, Mom na fita Sultana da Aziza suka sauke ajiyar zuciya, Sultana ta ce
"Alhamdulillahi! Mom ta rage mana aiki"
"Kamar ya?"
"Da taji mana, da yanzu muna nan muna wallahi tallahi dake" murmushi Aziza ta yi tace
"Duk da haka ku zuciyarku daban yake, mutane irinku kaɗan ne"
"Humm! Yanzu ke kuma kenan dole kafin ki koma mutum sai kunyi aure?"
"Ai babban damuwar yana jikin Azima, idan har ta warke nima na warke In sha Allah, amma da kamar wuya a samu wanda zai auremu har ya taimaka mana mu dawo mutane kamar kowa"
"In sha Allahu, Allah zai kawosa,kuma zaki gani,muddun kunyi tawakkali Allah zai dubi hakurin da kukayi na cinye wannan babban jarabawan, sannan ya saka muku ta yadda baku tunani"
"Haka ne kam" Aziza ta faɗa tana gyara zama, sun jima suna hira.




🍃🍃🍃🍃🍃🍃


Bayan kwana biyu komai ya dawo dai-dai, kamar yadda Khalil ya faɗa zai dawo cikin sati to hakan ne ta kasance,dan kuwa shirye-shiryen dawowarsa akeyi,dan da ya dawo biki kawai za a sha, yace ayi biki a ba shi matarsa.






Ranar lahadi da da daddare ya iso gari, bayan da ya huta maganar biki Hajiyarsa ta hau masa, yace tunda yau ya dawo a bari nan da kwana hudu ko biyar sai aje dan a saka rana, duk da shima Nawaz ɗin yace zasu dawo su ma kwanan nan, da haka suka ajiye maganar.




Washe gari da misali karfe goma na safe yasha wankansa yasa manyan kaya na mutunci ya shiga ya gaida hajiyarsa, ta ce
"Khalil ina zuwa ne haka? Ko dai za a je ganin ɗiyata Sultana ne?"
"E wlh Mom, zanje dai gaishe da Mom ne"
"Ah ba wani nan kar ma ka wani fara fakewa da Mom Ah to ,a gaishe min da su Sultanan" tashi ya yi yana dariya yace zasuji sannan ya fice.


@@@@@


Bai gayawa Sultana a kan cewa zai zo da safe ba, ya dai gaya mata ya shigo kaduna da daddare da misalin takwas da rabi, ko da ya isa gidan kasancewar mai gadi ya san shi ya hau masa sannu da dawowa, Khalil ya amsa yana dariya, da shike gidan ba baƙonsa bane, nan ya shige kansa tsaye yana buga sallama, Aziza ce kawai ta farka a lokacin ta gana mopping kenan, ta ga mutum,tana ganinsa ta ganesa ta ce
"Lahh Hamma Khalil marabalale" ta fada tana hawa sama da gudu ya yi murmushi ya ce.
"Kanwarmu kenan" ya nemi waje ya zauna, da gudu Aziza ta shiga dakin Sultana ta haye gadon ta janyeta, Sultana ta bude ido cikin haushi ta ce
"Dan Allah miye haka Aziza!?"
"Kai Anty Sultana kin san da cewa Hamma Khalil zai zo shine kike bacci har yanzu baki masa girki ba, ba kiyi wanka ba haba dan Allah" ai Sultana tana jin an ambaci sunan Khalil yazo ta miƙe zunbur, ta ce
"Ke Aziza da gaske Khalil yazo?"
"Wlh yazo yana parlourn kasa" da sauri Sultana ta miƙe da kayan bacci ta ɗiro a gadon ta fita ta shiga dakin Mom ta ce
"Mom wai Khalil yazo"
"E na sani"
"Shine Mom ni ban sani ba, bai fa gaya min zaizo ba, ga shi ban shirya masa komai ba, ban yi wanka ba" Mom ta dauki mayafinta tana fadin
"Too idan kin gama mitan saiki haɗa masa komai ɗin sannan kiyi wanka" ta fice, fita itama Sultana ta yi, ta samu Aziza na kwashe kaya a parlourn sama,ta ce
"Aziza yanzu ya zanyi?"
"Karki damu Antyna,yanzu kedai kawai kije ki cakare wanka, zan kula da saura"
"Thats my lil'sis" Sultana ta fada tana shiga daki da sauri, kasa Aziza ta sauko ta shiga kitchen, a cikin mintuna qalilan ta jera tray ta haɗa abubuwa a kai na burgewa da ban sha'awa tazo ta ajiye a gaban Khalil wanda yake duƙe a gaban Mom suna magana, sun jima suna magana da Mom kafin Mom ta tashi ta koma sama, ba jimawa gimbiyar tasa ta sauko, nan aka hau hiran soyayya na yaushe gamo, sannan ta kara gabatar masa da Aziza.






Kamar yadda Khalil ya fada bayan sati daya da dawowarsa aka zo aka tsaida ranar aurensa da Sultana wanda za ayi nan da wata daya da sati uku,wanda Nawaz shi da Khalil ɗinne suka yanke wannan shawara.




Tunda aka saka wannan rana Khalil ya hana Sultana sakat, tayi-tayi ya bari suje kano amma ya ƙi, yace ta bari ba yanzu ba,ita da basu shiri da

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login