Showing 69001 words to 72000 words out of 79094 words

Chapter 24 - YAR SHUGABAN KASA COMPLETE DOCUMENT BY Rahma Kabir .txt

29 Nov 2024

4650

yayi yace
"Saboda ba kada lafiya, ba zata zauna ba domin tabbas matsalan ka zai iya shafanta" yaya Ahmad ya fad'i hakan ne domin ya tunzura Aryan dan ya tabbatar da ciwon nasa. Aiko Aryan ransa ya k'ara baci.


Basma sai gata ta fito tana ta kuka, Yaya Aryan ya tare mata hanya ya kama hannunta gam, kansa ne yayi mugun sarawa sai ya rik'e Kan da d'ayan hannunsa, Basma tace


"Yaya Aryan ka barni na tafi ko zaka ji sauk'in abinda ke damunka"


Yaya Ahmad ne ya matso wurin ya fintsike hannun Basma, ya kama Aryan ya zaunar dashi tare da kama kansa da k'arfi, Addu'a ya fara tofa masa nan take ya ture Yaya Ahmad suka fara dambe. Basma ihu ta soma security da suke gidan suka fad'o falon a sukwane suka kama Yaya Aryan yana cijewa.


Yaya Ahmad ya fad'a kitchen d'in Basma ya d'ibo ruwa a cup ya soma karanta Addu'o'i yana tofawa a ciki, bayan ya gama ya soma watsawa Aryan a jiki, wani k'ara ya saki yana gunji, haka yayi ta watsa masa har sai da yayi shuru yana gunji.


Da sauri Yaya Ahmad ya kira Naufal yace
"Naufal kana ina ne? ina so kaje gidan Malam Hashim ku tawo tare dashi gidan Aryan Akwai Matsala ne" bai jira mai zai ce ba ya kashe wayan.


Cikin tashin hankali Naufal ya mik'e ya fito, gidan Malam Hashim ya wuce ya d'auke shi suka nufi gidan Aryan.


Sun isa gidan cikin sauri suka fad'a falon, Aryan yana jin shigowar su ya saki k'ara, Malam Hashim ya kunna karwashin wuta ya sanya wasu Magani a ciki ya soma turara d'akin, Malam Hashim ya fara karanto wasu Addu'a yana tofa masa, Aryan yana gunji ya fara magana


"Zan fita, Zan fita, Zan fita, karku k'ona ni"


Malam yace
Bama buk'atar kiyi magana ki tafi kawai"


"Ni bazan tafi ba saboda ina son Basma"


Ai Basma sai cikinta ya d'uri ruwa.


Malam yace
"Meyasa kike son ta sannan baki shiga jikinta ba saiki shiga jikin mijinta?"


"Saboda tana burgeni, tun tana k'arama nake bibiyarta don na shiga jikinta amma ban samu hanya ba, saboda a jikinta banida mazauni dan Kakansu Bukar ya shayar da jikokinsa magun guna na tsarin jiki gaba d'aya babu wani jinnu da zai iya cutar dasu"


"To meyasa kika Shiga jikinsa bacin Basma kike so?"


"Soyayyan Basma yasa na shiga jikinsa, shima na jima ina son shiga jikinsa, ran nan ya kwanta ba tare da yayi Addu'a ba har barci ya d'auke shi. shine na samu hanyar shiga jikinsa, kuma bana so ya kusanci Basma saboda son da nake mata banson kowa ya rab'eta"


"Kina mace maye da son shiga jikinsa, wannan ai ba soyayya bace, tunda kina cutar da shi, dan haka zan konaki da Ayar Allah"


"Kar ku kona ni zan tafi har Abada bazan dawo ba"


Malam ya watsa masa wani ruwan Magani, k'ara ya saki yana birgima nan take yayi shuru kamar ruwa ya d'auke. Aka sanya karatun Al'Qur'ani Suratul Bak'ara, nan take barci ya kwashe shi.


*Hmmm duk abinda wasunku ke zargi akan Sihiri akaiwa Aryan kunata zaigin su Mami, to ba Sihiri ke damunsa ba, ba ruwan Mami, Yaya Shureym, balle kuma Jidda.* 🤪


Bayan komai ya lafa Yaya Ahmad ya kira su Ammi ya shaida musu abinda ya faru. Cikin tashin hankali suka zo gidan su Aryan. Sun zauna jugum-jugum suna jiran Aryan ya farka, cikin ikwan Allah kuwa sai gashi ya farka yana mai Ambaton Allah, zama yayi yana kallon Mutanen falon d'aya bayan d'aya, yana kai kallonsa ga Basma da take kuka sai ya yun k'ura da k'arfi yace


"My Basma me ya same ki kike min asaran hawayenka"


Haka ya isa wurin ta ya kama hannunta ya mik'ar ya zaunar da ita a bisa cinyarsa, sam ya manta da Mutanan dake falon, Momy cikin jin kunya ta mik'e ta fita daga falon, Ammi ma fita tayi tabi bayan Momy, Yaya Ahmad yace


"To Love Birds hala ka manta da mutanan dake d'akin ne?"


Dariya yayi yace
"ba dole na manta daku ba, Pretty na tana kuka"


Duk sai suka sanya dariya, nan Malam Hashim ya bashi wasu Magani da zai yi amfani dasu wanka da sha sai hayak'i, sannan kuma ya bashi shawarwari akan ya kula da ibadansa da kuma yawai ta karatun Al'Qur'ani da Azkar, Yaya Aryan yayi masa Godiya, nan suka yi musu sallama gaba d'aya suka tafi Gida.


Yaya Aryan ya zauna gefen Basma yace
"Babyna Allah yasa na samu lafiya kenan, kin ga yanzu bana jin komai in ina zauna gefenki"


Hawaye ta share ta d'aura kanta bisa ciyarsa tace
"Myn wallahi na firgita da lamarinka sosai, insha Allah ka warke hakan bazai sake faruwa ba".


Nan dai suka samu suka karya, suka sake wanka, Aryan yayi amfani da magun-gunansa, sai suka dawo falo suka zauna suna hira suna soyewa abin gwanin sha'awa.


*Bayan Kwana Biyu*
Aryan ya warware sosai babu sauran wani damuwa, da dare ya siyowa Basma kayan ciye-ciye, suka baje a falo suka ci abinsu, bayan sun kammala ko wanne ya wuce d'aki domin yin shirin barci.


Wani Rigan barci Basma ta d'auko, ta d'aga sama tana kallon rigan, jin-jina rigar take yi tana ayyana wa a ranta
'Anya zan iya sanyata kuwa?'


Aryan daya jima da shigowa yana kallonta, yace
"Dama kin mai data kin aje, dan kar ta bani wahala wajen cirewa, ki bari gobe in Allah ya kaimu sai ki sanya ki min kwanliya da ita da dare kafin mu kwanta"


Da sauri ta juyo dan harta tsora ta, kunya ce ta rufeta akan maganan daya fad'a, maida rigan tayi ta ajiye.
Arya yazo bayanta ya tsaya, d'aukarta yayi tsak ya ajeta bisa gado.


*Nima daga nan nayo waje, na basu guri tare da yi musu saida safe.*


*Washe Gari*
Da misalin k'arfe shida na safe, Basma ce kwance bisa jikin Yaya Aryan yana lallashinta akan tayi barci, sai shagwab'a take zuba masa. Da kyar ya samu tayi barcin, sai ya gyara mata kwanciya ya ja mata bargo, ya sauka ya zauna gefen gado, dafe kansa yayi cike da mamakin yanda ya samu Basma a cikakken Budurwa, tambayan kansa yake


"Dama Basma bata tara da Shureym ba kenan, lallai Allah kaine Mai cikakken iko, hak'ik'a babu wani Sarki sai Kai, kuma Kaine Majib'icin dukkan Al'amuranmu, Alhamdulillah da wannan babban kyauta daka bani, nasan ba wayauna bane ba kuma dubara na bane".


Hawayen farin ciki ne ya sauka kuncinsa, ya shiga jero Addu'a tare da yiwa Allah kirari, saida ya karanto sunayen Allah D'ari ba d'aya, ya cika da salatin Annabi s.a.w, sai ya shafa.


Basma ta bud'e ido tana kallonsa, ashe barcin nata bai yi nisa ba, ta taso a hankali ta rugumeshi ta baya tace


"uhum, uhum, Myn yunwa nake ji ka bani abinci inci"


Jawota yayi ya birkito ta akan jikinsa suna kallon juna, hura mata ido yayi yace


"kina kallo na kamar zaki had'iye ni, ko d'an kunyan nan ma" runtse ido tayi yana dariya tace
"kai Yaya Aryan ka daina cewa haka mana ba ina sonka bane, Ni dai ka bani abinci zanci"


"tom bud'e ido muyi magana, me kike so in miki wanda zai saki farin ciki sosai, Hasken Rayuwata kin bani kyauta mafi girman kyauta wanda yazo min a bazata, Basma nayi mamakin samunki a cikakkiyar..."


Bai k'arasa ba Basma ta had'e bakinsu guru d'aya saida suka yi tsayin minti biyar, kana ta zaro bakinta a nashi ta kalleshi ido cikin ido, tace


"Myn Kai ne kad'ai nake so, kuma kaine Allah ya zub'a da zaka mallakeni, Yaya Aryan so nake muje Asibitoci, Gidan Marayu, da Gidan Kurkuku mu basu taimako da abinda Allah ya bamu, in kamin wannan kad'ai, zanyi farin ciki sosai mara yankewa".


Rungumeta tayi tsam a jinshi tamkar zai maidata cikinsa, wani sabon So da K'aunarta ke k'ara ratsa zuciyarsa yana yad'uwa a duk sassan jikinsa.


_*To Readers nasan yau dai na saku farin ciki*_☺


*Rahma Ce*
[8/15, 8:45 AM] Rahma Kabir🌺: *'YAR SHUGABA👑*


_page_ *36.*


_Na_
*_Rahma Kabir✍🏾_*


*Bayan Mako D'aya*


Aryan da Basma sun murmure sunyi kyau sun fara kumari, kwance suke bisa gado Aryan yace


"My Queen nan da Mako guda Insha Allah zamu je Makkah muyi Umara tare da Honey Moon, amma fa na yin Ibada, sannan Gobe Insha Allah zamuje Asibitoci domin in cika miki alkwarinki"


Kallonsa take cike da So da K'auna tace
"Myn Godiya nake Allah ya k'ara maka Bud'i na Alkhairi yasa kafi haka"


"Ameen My Pretty" sai ya rungumeta tare tayi mata sumba a goshinta. Daga nan kuma suka yi Addu'an barci, cikin minti goma Basma barci ya d'auketa. Shima ba dad'ewa barci ya kwashe shi.


Saura kwana Uku su tafi Makkah, suka zagaye dangi tare da yi musu Sallama, har Kano sunje sun kwana d'aya, suka je Kaduna ma suka kwana washe gari suka dawo Abuja, a gidan Abba suka yini kowa na farin ciki da sauyawan su, sunyi kyau da k'iba gwanin sha'awa, sai dare suka koma Gida.


Ranar da zasu tafi, harda su Momy suka yi musu rakiya, Basma har kuka tayi saboda kewar 'Yan uwanta. A cikin Jirgi Aryan ya rungumeta a jikinsa yana lalla shinta har barci ya d'auketa.


*MAKKAH*
Sun samu masauki a hotel d'in kusa da Harami, suka yi wanka a tare sannan suka ci Abinci, Basma ta shirya cikin jallabiya Brown mai ratsin fari a jiki babu kwalliya fuskarta amma tayi kyau, sannan ta shirya Aryan cikin doguwar jallabiya fara da farar hula, ta sanya masa turare, tana murmushi tace


"My Aryan ina kishi ka fita domin gaskiya Mata karsu kallen min kai, dan ba k'aramin kyau kayi ba"


Murmushi ya sakar mata yace
"ai kema kinyi kyau sosai, ji yadda Jallabiyar ta amshi jikinki, nima gaskiya ina kishi dan haka Nik'af zaki sanya"


Dariya ta sanya tace
"Nik'af? bazan iya numfashi a ciki ba Allah kuwa, ban tab'a d'aurawa ba, Ni koda nayi Islamiyya bana sayawa sai dai ina sanya Hijab har k'asa da safa, amma bana iya sanya Nik'af, kuma ai fuskata ba kwalliya"


Dariya shima yayi yace
"Ai fuskarki ko ba kwalliya kyanki na nan, amma naji baza ki saka ba, sai dai zaki rik'a d'aure fuska kina bonewa"


Dariya ta kyalkyale da shi ta fad'a jikinsa, rungumeta yayi kamar bazai sake ta ba sai da suka yi minti biyu a haka kana suka saki ajiyar zuciya a tare yace


"kin ga tashi mu wuce masallaci" Ba musu ta mik'e suka wuce masallaci.


Sun duk'ufa wajen yin Ibada da yiwa Allah Godiya bisa Ni'imomin da ya basu, sannan kuma da Addu'an Allah ya k'ara musu zaman lafiya acikin zamansu ya barsu tare har a Aljanna, ya saka wa iyayensu da gidansu Aljanna. Sun rokawa dukka nin Al'umma Musulmi da kuma samuwar zaman lafiya a K'asar mu Nigeria da dukkan Duniya gaba d'aya. Nima dai na taya su da "Ameen Ya Rabbi"


*Bayan Mako Guda*


Suka wuce *MADINAH* dan ziyaran Masallaci Monzon Allah S.A.W. Basma ta kira Hajiya Kaltum ta sanar mata da zuwansu, cikin farin ciki tace su tawo gidan ta. Anan suka samu masauki da kyakkyawan tarba.


Bayan sun natsa, Basma ta kwashe labatinta tas ta bata Hajiya Kaltum, ba k'aramin mamaki tayi ba da labarinta, tace


"Ashe Basma ke *YAR SHUGABA* Ce, lallai rauyuwa kenan, da ace da farko na rik'e ki da wulakanci da baza ki Ni meni ba, Naji dad'i sosai kuma Nagode" Nan dai suka cigaba da hira.


A masallaci suke kwana danyin Ibada. Satin su biyu a Madinah suka shirya dawowa Makkah, Basma Check d'in kud'i ta rubutawa Hajiya Kaltum masu yawa wanda ni kaina ban san yawansu ba, ta bata ta ciresu a bank, dan cigaba da kasuwancin ta, Hajiya Kaltum tayi mata Godiya harda kuka, kaya ta had'a ma Basma na gyaran jiki, ta kuma had'a mata da guzirin wasu kayan. Cikin farin ciki da kewar juna suka baro Madinah, shima Aryan ya yaba sosai da Mutuncin Hajiya Kaltum.


*MAKKAH*
Sati guda suka k'ara a Makkah suka shirya dawowa k'asarmu Nigeria. Watan su guda kenan a K'asa Mai Tsarki, Basma sunyi Ibada sosai sunyi kuma Honey moon cikin Soyayya da K'aunar Juna. Haka suka tarkato zuwa K'asarmu Nigeria.


*Nace "Allah yasa Basma ta kwaso guziri mai Albarka a Makkah".* Lol☺


*NIGERIA*
Jirginsu k'arfe Biyar na yamma ya sauka, su Yaya Ahmad, Yaya Naufal, Meena, Deeja, Na'im da Anwar sune suka je tarbansu.


Gidan Abba suka wuce gaba d'aya da kayansu, gida ya hautsine da murnan dawowarsu, a falon Abba duk suka zaune, Abba ya sauko suka gaishe shi, yayi musu barka da dawowa. Nan hira ta b'arke a tsakaninnsu sai gab da Sallan Magrib kowa ya watse, su Basma suka shiga d'aya daga cikin d'akin dake Falon Abba suka yi wanka suka sauya kaya.


Bayan Sallan Isha'i a part d'in Abba suka ci Abinci duka mutanan gidan, Yaya Ahmad yace


"In kun kimtsa zan mai daku gida"


Yaya Aryan yace
"Ai ni na kammala, dan na gaji ina buk'atar in kwanta da wuri"


Yaya Ahmad yace
"Basma ke fa?"


Itama tace
"Na gama" Yaya Aryan yace
"Kayan tsaraban nan a barsu anan washe bari zamu zo, kowa a bashi tsarabansa".


Sun shiga Mota sai suka fita gate, Yaya Ahmad ya wuce dasu k'ofar wani Gida dake kusa da gidan Abba, Aryan ya juyo da sauri yace


"ina zaka kaimu kuma? Don Allah ka kaimu gida mana, muna buk'atar mu huta, ka bari Gobe in Allah ya kaimu in munzo sai mu shiga nan d'in"


Dariya Yaya Ahmad yayi yace
"mai kake ci na baka na zub, Ni dai ku zuba min ido kurum"


Basma da Aryan suka had'a ido sai basu ce komai ba. Hon yayi Mai Gadi ya bud'e wangameman Gate, shiga yayi tare d'ayin kwana ya d'anyi tafiya kad'an, Manyan flat guda Uku ne a cikin Gidan, ko wanne da gab a tsakanin su, da kuma k'ofar shiga. Parking yayi a flat na tsakiya ya fito, key ya ciro a aljuhunsa ya bud'e k'ofar da zai sa dasu da cikin gidan yace


"Ku fito mu shiga mana"


Ba musu suka shiga, tafiya suka yi kad'an ya sadasu da k'ofar babban falon, ya bud'e k'ofar da key kamshin turaren wuta mai dad'i ya daki hancinsu, Yaya Ahmad ya shiga suma suka bishi a baya, kujerun Falon su na wancen gidan suka yi arba dashi, cikin mamaki Yaya Aryan yace


"Ya naga kayanmu a nan kuma?"


Yaya Ahmad ya zauna yana murmushi yace
"nan kuka dawo, gaba d'aya kayanku dake wancen gidan mun dawo muku dashi nan, muma nan mu ka dawo, flat na farko na Naufal ne, na biyu naku ne, na uku kuma nawa ne, munk'i tarewa munce sai kun dawo kun fara shiga kafin mu dawo, Abba ya gida mana shi"


Cikin farin ciki Basma ta mik'e ta shiga bin d'aku nan tana kallo, murna fal cikinta dan tsarin gidan yayi mata, katon falo ne sosai mai d'auke da d'akuna guda hud'u, ko wanne da toilet a ciki, an kuma sanya Furnitures a ciki, ga katon kitchen a falon da extra toilet. Daga cikin kitchen d'in akwai wani d'aki shine store d'insu, shak'e yake da kayan abinci da masarufi. A takaice gida ya tsaru yayi kyau sosai dan yaji kayan Alatu da more rayuwa.


Yaya Aryan ya soma Godiya, Yaya Ahmad yace
"Ka rik'e Godiyan ka, in ka bad'u da Abba kayi masa" ya mik'e yana Dariya, Yaya Aryan yayi masa rakiya, suna gabda barin falon Yaya Ahmad ya juyo yace


"Basma akwai swimming pool ta baya, akwai kuma Lanbu in kin za gaya ta bayan gidan, za kiga k'aramar k'ofa da zai sadaki da lanbun" Yana gama fad'a bai jira mai zata ce ba ya fita.


*Washe Gari*
Sun had'u gaba d'aya a gidan Abba, suka yi masa Godiya da gidan da ya sauya musu tare dayi masa Addu'a sosai, sun raba tsaraba gaba d'aya, harda na Mutanan Kano da Kaduna sun ware musu. A ranar su Yaya Ahmad da Yaya Naufal suma suka tare a Gida jensu.


*Da dare*
Basma da Yaya Aryan suna zaune a falo, Basma tayi pillow da cinyansa yace mata


"My Queen akwai wani shawara dana yanke, nasan kema zai miki dad'i in kika ji"


Basma ta tattaro natauwarta tace
"Ina jinka Myn"


"Yauwa Babyna, dama so nake ki had'u dasu Meena ku bud'e wata organization na taimakon Al'umma, Nak'asassu, Almajirai, masu k'ara min k'arfi, marasa lafiya da dai tallafawa Talakan K'asarmu baki d'aya, ta wannan hanyar ne za muyi amfani da dukiyar da Allah ya bamu domin mu nima Lahiranmu da shi, kinga Ni dasu Yaya Ahmad sai mu rik'a jagorantar ku akan abin, amma me kika gani?"


Wani farin ciki ne ya rufe ta, sai ta mik'e ta zauna tare da sumbatarshi a kumatu ta gyara zama tace


"Yaya Aryan ka sani farin ciki sosai Wallahi, na dad'e ina tunanin wani hanya zanbi dan taimakon Al'umma A matsayina na *'YAR SHUGABA* dan haka wannan shawaran naka yayi, Gobe Insha Allah zan tattauna dasu Meena".


" Masha Allah da kika amshi shawara ta, yanzu ki bari kar kiyi magana dasu, zan shirya Meeting a tsakaninmu gaba d'aya, sai mu had'u a anan don mu tattauna, amma kan lokacin zanyi magana da Yaya Ahmad, kuma sunan organization d'in *_QUEEN BASMA ('YAR SHUGABA) FOUNDATION_*.


tsalle tayi ta fad'a jikinsa ta fara sumbatarshi ta ko ina, nan ta rikita shi gaba d'aya, d'aukarta yayi tana wucil-wucil da k'afa tare da kyalkyata Dariya, suka shiga cikin bed room d'in su.


*_Ni Rahma nayi musu fatan Alkhairi, sai na nufi gidan Yaya Ahmad don naga wainar da suke toyawa._*


*Rahma Ce*
[8/15, 8:46 AM] Rahma Kabir🌺: *'YAR SHUGABA👑*


_page_ *37.*


_Na_
*_Rahma Kabir✍🏾_*


Yaya Ahmad yana zaune a bakin gado Deeja na zaune nesa dashi tana kuka sosai, cikin damuwa yace


"Haba Deeja don Allah ki daina kukan nan haka, Allah ya bamu kyauta banga dalilin da zaisa ki zubar min da ciki ba, Plss Babyna kiyi hak'uri ki daina zancen cire cikin nan"


D'agowa tayi ido jajir, cikin kuka tace
"Yaya Ahmad yanzu fa Walid bai wuce wata biyar zuwa wata shida da haihuwa, ya zaka ce in bar cikin nan a jikina na, Walid fa zai walaha nima haka"


"Ni banga wani illa a shayarwan Walid ba, muddun yana cin abinci, kuma cikin nan watan shi guda ne kinga da sauran lokacin har zai sha na kusan wata biyar fa, in kin yaye shi zan kaiwa Momy shi"


Kuka take sosai tace
"Nifa Allah zai an cire cikin nan"


Cikin b'acin rai yace
"Wallahi Khadija in kika kuskura kika cire min cikin nan sai nayi mugun sab'a miki" yana gama fad'an haka ya gyara kwanciyarsa ya kwanta ransa na masa zafi. Kuka take sosai, ganin kuka bazai fissheta ba ta mik'e ta Shiga bayi ta wanke fuska, ta dawo tayi shirin barci, ta kwanta da niyyar

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login