Showing 39001 words to 42000 words out of 79094 words

Chapter 14 - YAR SHUGABAN KASA COMPLETE DOCUMENT BY Rahma Kabir .txt

29 Nov 2024

4661

zuciya tace
"Abba kun cuceni, da gatana na zama baiwa, Ina *'YAR SHUGABA* na zama mara galihu" saida tayi kuka mai isarta, kana ta mik'e ta fita falo, kud'in da Abba ya bata ta d'auko su a inda ta bari, d'aki ta koma ta rufe, ta aje kud'in a inda take adana kud'inta, murmushi kawai tayi ita kad'ai tasan matakin da zata d'auka akan Shureym.


Safeena bata dawo ba sai cikin dare, ta shiga d'akinta, wanka tayi ta fito tana tsaki, zama yai tace


"gaskiya Shureym na gaji da wannan auren boyen, ya kamata a fito da zancen nan kowa ya sani, Ni da Mijina auren halal, amma ina guje-guje sai kace auren tsiya mukayi, to wlh da sake, ka kira Maminka ka sanar mata na gaji da wannan wasan kuran da nake da danginka"


Sassauta murya Shureym yayi cikin lallashi yace
"Haba my baby love, meye na damuwa? da zaran kin haihu magana zai bayyana a dangi, ran nan nayi magana da Mami ita tace haka, dan haka ki kwantar da hankalinki, yanzu cikinki ba wata hud'u ba, nan da 5month in kin haihu komai zaiyi dai-dai"
Ajiyar zuciya tayi tace
"to shikenan baby wlh d'azun naji haushi sosai, kawai an sani yini a gidan mutane" murmushi yayi ya kamota, nan ya shiga jefa mata zazzafar soyayyansa, tuni ya mantar da ita damuwa.


*Rahma Ce*
[8/8, 5:41 PM] Rahma Kabir🌺: *'YAR SHUGABA*👑


_page_ *19.*


_Na_
_*Rahma Kabir*_✍🏾


*Nigeria*


Abba sun sauka lafiya cikin dare, ya shaida ma su Momy Basma na gaishesu ba wata Matsala. Yaya Naufal ya labaratawa Yaya Ahmad duk abinda ya faru, damuwa ne ya ziyarceshi yace
"anya kuwa Shureym na kula da Basma?" Yaya Naufal yace
"yana kula da ita a yanda muka gani, kuma ai in da da matsala zata gayawa Abba" murmushi kawai Yaya Ahmad yayi a ransa yace
"ban yarda ba dole zanyi bincike akai, dan Basma tana da zurfin ciki, ni kad'ai take gayawa damuwanta ko Momy" a fili kuma yace
"hakane, to Allah ya bata lafiya ya k'ara musu zaman lafiya"
"Ameen" Yaya Naufal yace, kana ya wuce part d'inshi.


*Kasar Monaco*


Aryan yayi nisa cikin karatunsa, a yanzu hankalinsa ya kwanta, sai dai har yanzu bai maida jikinsa ba, yana waya dasu Umma da Khadija sai Yaya Ahmad, yanzu ya daina kashe wayansa kullun tana kunne, har yanzu bai dawo cikin walwala ba, baya dariya sai dai yak'e kuma shima saiya d'auro, murmushi ne kawai ya kanyi time to time.


Wata rana yana makaranta ya fito daga aji yana tafiya, karo yaci da wata ta tawo a guje bata lura dashi ba, d'agowa tayi cike da tsoro, cikin harshen turanci tace
"yi hak'uri wlh ban kula bane" gyad'a mata kai kawai yayi sai ya rab'eta ya wuce, binsa tayi da kallo cike da tunani barkatai,


"iya had'uwa wannan guy d'in ya had'u, ko dan wani kasa ne oho? Gaskiya bazan bari ya kub'ucemin ba, dan na kamu da sonsa, kuma shine dai-dai tsarina"


Abinda take fad'a a ranta kenan, da gudu ta bi bayanshi, bata san sunanshi ba gashi ya tsere mata, duk da haka bata hak'uri ba, ta cigaba da bin bayansa da gudu ta cimmasa, gabansa ta sha, sai ta tsaya cike da yin nishi tace


"Yi hak'uri na tsaidaka, sunana Jidda Bukar, ni 'yar Nigeria ce katsina state, muna zama a Abuja, nazo nan karatu ne, in ba zaka damu ba ko zan san daga ina kake? dan kayi min zubin d'an k'asar India"


Murmushi yayi a takaice yace cikin harshen turanci
"sunana Aryan Aliyu, Dan k'asar Nigeria" ido ta zaro tace
"wow ashe k'asarmu d'aya, wlh gani nayi ba kayi kama da 'yan Nigeria ba, amma nayi murna sosai, cewa nayi bari na biyo ka saboda naga Kana da sauk'in kai, in ba damuwa ko zamu kulla abota" ransa ne ya b'aci, amma saiya dake cikin rashin sakin fuska yace
"nagode, amma ba zai yuwu ba kawai, in dai mun had'u sai mu rik'a gaisawa" yana gama fad'an haka ya wuce, binsa ta cigaba da yi tare da yi masa magayi akan suyi exchangen number, tsayawa yayi zuciyansa na tafasa cikin masifa yace
"ya isa dan Allah, kiyi hak'uri ina da mata, pls ki fita a harkata, sai wani bina kike kamar naci miki bashi" jikinta ne yayi sanyi bata k'ara furta komai ba sai ta juya ta fara tafiya, tausayi ta bashi sai ya dakatar da ita yace
"Jidda kiyi hak'uri ban cika son ana takura min ba" juyowa tayi idonta ya cika da kwalla tace
"ba komai na fahimceka" Numbern shi ya karanta mata, kana suka yi sallama.


Ta wuce cike da murna shi kuma ya tafi cike da tunanin Basma, ji yake kamar yaci amananta, wani b'angare na zuciyansa yace
"bakaci amana ba, itama ai tanacan tare da mijinta" runtse idonsa yayi hawaye mai zafi ya fito masa, ji yayi komai ya dawo mishi sabo, zazzab'i ne ya rufeshi, sai ya tafi gida cike da matsananciyar damuwa.


Tun daga wannan ranar Jidda ta mak'alewa Aryan, Sam baya son abinda take masa, yana k'ok'arin janye mata amma sai k'ara shige masa take, ita burinta bai wuce ta samu zuciyar Aryan, ko bazai aureta ba tunda yace yana da mata, zata amince masa su tab'a rayuwa ko kad'an ne, domin tana fama da sha'awansa.


Aryan yana gida a kwance da yamma, sai yaji anyi masa knocking, tashi yayi ya tafi ya bud'e, mamaki me ya rufe shi ganin Jidda ce, murmushi tayi masa sai tabi gefensa ta shige d'akin, binta yayi da kallon yana mamakin yanda akayi tasan gidansa, cikin nuna ko rashin damuwa Jidda ta cire mayafinta ta zauna a kan kujera mai mazaunin mutum d'aya, komawa yayi ya zauna kujeran dayake fuskantarta tace


"Nasan kayi mamakin yanda akayi na gano gidanka, kasan ance mai son d'an tsuntsun shike binsa da jifa, Aryan wlh ina sonka amma kak'i bani gurbi a zuciyanta"


Aryan d'aure fuska yayi yace
"Jidda nafiso ki bar alak'anmu da abota kawai, domin bana tunanin zaki samu gurbi a raina, dan na riga na bada soyayyata ga wata"


Hawaye ne ya cika mata ido tace
"pls Aryan, ni wlh ko kaina kace in baka a shirye nake" mik'ewa tayi ta juya a gabansa ta cigaba da cewa
"Kalli surata da kyau, ina da duk abinda mace take dashi a jikinta wanda namiji zai mora, dan Allah ka yarda dani in zama mai d'ebe maka kewa, koda baka sona in har ka yarda min da haka zanyi murna"


Aryan cikin b'acin rai ya mik'e nuna mata hanyar waje yace
"Jidda natsaki na tsani mata masu irin halinki, ki sani har ki mutu ba zaka samu yanda kike so ba domin nafi k'arfin iskancinki, kuma ki sani Ni ba kalar ki bane, ki gaugauta cireni a cikin jinsin mutanan da kikasani" jiki na rawa ta mik'e zata bashi hak'uri, cikin tsawa ya dakatar da ita
"Na ce ki fita" da sauri ta kwashi kayanta ta fita tana mai jin haushin kanta, rufe k'ofarsa yayi tare da sauke ajiyan zuciya, Addua yayi da k'ara niman tsari ga irin wannan matan.


Tunanin Basma ya shiga yi,
"Yarinya ce mai natsuwa, duk wayewarta a kame take, ga kud'i da jin dad'i na rayuwa amma akwai tarbiyya mai kyau, har abada yanajin ba zai samu mace kamarta ba" hawaye ne ya zubo mashi yace a fili


"Basma har abada ina sonki, babun macen da zan aura ta kai matsayinki, nasan haduwata dake wani jarabawa ne a rayuwana, Allah ya rabamu ina tsananin sonki, Allah ka bani wacce zata share min hawaye na".


*_Aryan nima na tayaka da cewa "Ameen". Masu karatun bari mu koma k'asar America mu ga wainar da Suke toyawa._*


*Bayan wata guda*


Basma ta warware, zamansu kuma yana nan zaman doya da manja, da dad'i ba dad'i, kadaran kadahan, Basma yau tasha Riga da wando English wears, saita d'auko gyale tayi rolin iya kyau tayi, jaka ta d'auka ta fito falo, Safeena ta tarar tana shan fruit, Safeena tace cikin tsokanar fad'a


"Ayawo yau kuma shigan yan iska kike ji?" Basma bata tanka mata ba, illa tsaki taja ta fice, Safeena ta ce
" 'yar rainin wayo, zaki had'u da Shureym shine dai dai da iskamcin ki".


Basma na fita taxi ta shiga ta wuce inda suke had'uwa da Bilal, ta sameshi yana jiranta, kallonta yake cike da soyayya yace
"Basma kinyi kyau sosai" murmushi tayi tace
"nagode muje ko" wurin shak'atawa suka wuce, suna tafe suna hira, Bilal yace


"Basma yaushe zaki kaini gidan ku na gaida da Iyayenki, nifa da gaske sonki nake kuma aurenki zanyi, dan har na fara magana da Ammi na" Murmushi tayi tace


"ni iyaye na suna Nigeria, yanzu da Yaya na muke a nan k'asar, kuma ina so ka sani gaskiya ina da aure" ai bata k'arasa maganar ba ya juyo a zabure yace
"pls my Basma ki daina fad'an wannan maganar imma wasa kike" murmushi tayi tace
"Bilal da gaske nake, Mijina dai baya tare dani yana k'asarmu" tab'oye masa hakan saboda bata son yasan komai nata, cike da damuwa ya samu guri yayi parking yace


"meyasa kike wasa da aure, Basma na tabbata ke mace ce mai ilimin addini, meyasa bakya amfani dashi, yanzu kusan 1month da had'uwarmu, sauk'in abin ma tun farko kink'i Amincewa dani muyi soyayya, kin ce ke kin d'ukeni brother d'inki ne, dama nike kid'ana da rawa, da tun farko kin gaya min kina da aure da alak'anmu batayi nisa ba, ko kuma dana nasan yanda zan fuskance ki, amma ba damuwa naji dad'i da kika gayamin gaskiya, zan koyawa kaina hak'uri da soyayanki, sai mu cigaba da zumunci"


Murmushi tayi tace
"nagode da tunatarwa, insha Allah zan gyara muje ko"


"yanzu ina muka nifa?" murmushi tayi tace
"muje wurin wasa da mota ko?" dariya yayi yace
"OK my Friend" dariya tayi tace
"abotan harya fara aiki kenan" murmushi kawai yayi ya tada mota suka cigaba da tafiya.


Sai k'arfe bakwai na dare Basma ta dawo daga wurin kallonta wasan mota, Bilal ya sauketa a k'ofar gida, hakan yayi dai-dai da cillowar motan Yaya Shureym, ita kuma tana d'aga ma Bilal hannu harya wuce, sannan ta shiga gida.


Ta samu Safeena zaune sai d'irkan abinci take, tsaki Basma taja tace
"Mutum baida aikin yi sai ya zauna yaita d'irkan abinci kamar jaka, wai dole ita mai ciki" Murmushi Safeena tayi bata ce komai ba domin ta riga ta had'a mata bomb mai kwacenta yau a gun shureym sai Allah.


Safeena ta gayawa Shureym daya dawo, k'arya da gaskiya akan fitan da Basma take yawan yi da kuma mummunar shiga, ransa yayi matuk'ar b'aci, fita yayi nimanta wuraren shak'atawa ko zai ganta a can, amma haka ya karad'e yawan nimanta bai ganta ba, dawowansa kenan yanzu daya hangota tana d'agawa wani hannu, ransa ya k'ara b'aci sosai kishi ya rufe masa ido, da sauri ya shiga gidan yayi parking.


Falo ya shiga da sauri ya soma kwalawa Basma kira, da sauri ta fito tana fad'in
"dan Allah karka fasa min kunne, sai wani kwala min kira kake, sai kace tsohon makawo" a zuciye ya bud'e baki zaiyi magana, sai ga Bilal ya kwad'a sallama ya shigo falon, Basma saida gabanta ya tad'i, amma saita dake tace cikin Fara'a
"Friend hala nayi mantuwa ko?" murmushi yayi yace
"kin manta da ice cream d'inki kina sauri"
"ayya wlh ban kula ba, nagode kuwa sosai"


Shureym ai sakin bakin yayi yana kallon ikwan Allah, cikin harshen turanci Bilal yace masa
"ina yini big brother" Shureym ya amsa a tak'aice, sai ya fice da sauri.


Yaya Shureym zama yayi akan kushim yana cizon leb'ensa, gaba d'aya kishi ya rufe masa ido. Har wani d'aci bakinsa yake masa saboda b'acin rai, Basma tana ganin ya zauna bai ce mata komai ba, sai kawai ta shige d'aki.


Shureym ya d'aga wayarsa ya kira Dadyn Kaduna, Gobna Ibrahim, suka gaisa Dady yace
"Shureym ya Basma da fatan kuna lafiya?" cikin k'unan rai yace
"Dady Basma tana cin Amanta, fita take yi tana hurd'a da wasu maza a waje, yau tun rana ta fita sai yanzu ta dawo, kuma Dady wani saurayinta ne ya kawota gida, yanzu yabar falon mu" a razane Dady ya mik'e yana fad'in


"Inalillahi wa inna ilai hir raji'un, Basman ce ta zama haka, to maza ku shirya gobe-goben nan ku tawo Nigeria, zan kira family meeting gaba d'aya zamu had'u a Abuja duka, kayi hak'uri kaji Shureym karka ce mata komai" sai suka yi sallama.


Dady ya fara kai koma a falo sai salati yake, Ummin Meena dake zaune itama ta mik'e a tsorace tana tambayarsa
"Alhaji lafiya?" kallonta yayi bai ce komai ba, ya shiga niman number Mai Martarba Sarkin Kano, suka gaisa, sai ya shaida masa akwai family meeting a Abuja gobe in Allah ya kaimu, nan suka yi sallama. ya d'aga waya ya kira President, shima haka ya shaida masa kamar yanda suka yi da Mai Martaba, President cikin mamaki yace
"Ibrahim lafiya dai ko?" cikin murmushi yak'e yace
"Lafiya Kalau sai in munzo zaka ji komai insha Allah" da haka suka yi sallama.


Dady ya koma ya zauna, itama Ummi ta zauna, ya shiga gaya mata Abinda Shureym yace masa, cikin salati Ummi tace


"wlh k'arya yake yi, ba dai Basman mu ba, sai dai in sharri zai mata, dan ba haka muka tarbiyyantar da ita ba"


Cikin b'acin rai Dady yace
"karki shaideta domin d'an yau ba a iya masa, kuma ai ba tare dasu muke zama ba, hasali ma ba gari d'aya muke ba, Basma zata iya komai tunda dama bason Shureym take ba" sai jikin Ummi yayi sanyi ta shiga nazarin maganar Dady...


*Rahma Ce*
[8/9, 5:47 PM] Rahma Kabir🌺: *'YAR SHUGABA*👑


_page_ *20.*


_Na_
_*Rahma Kabir*_✍🏾


Safeena cike da damuwa tace
"amma Shureym anya baka jawo tonuwar asirinmu ba, domin in dai Basma taji cewa ka kai karanta ne, tofa zata gaya duk abinda ya faruwa, da kuma dukanta da kake yi"


Runtse idonsa yayi ya bud'e, cike da damuwa yace
"wlh Safeena raina ne ya b'aci, idona ya rufe sam ban kawo haka ba, sai yanzu da kika tunatar da ni, yanzu ya kike ganin za'ayi" cikin damuwa ta rafka tagumi tace
"ina ganin karka gaya mata, kace kawai ana nimanku ne, inya so inta je can taji komai, kuma na fison dama kowa yasan dani a family d'inku dan nagaji da b'oye-b'oye" cike da damuwa Shureym yace
"haba safeena bai kamata ace abinnan ya fasu yanzu ba, kawai ki tayani da Addu'a kar asirinmu ya tonu" yana gama fad'an haka sai ya mik'e ya shige d'aki, Safeena ta bi bayansa da kallo, ta yatsine baki tace
"ba Addu'an da zanyi, in maganar ta fito karshe dai ace an raba aurenka da Basma, kuma abinda nake so kenan".


Shureym yana shiga d'aki ya kira Maminsa ya sanar mata duk abinda ke faruwa, hankalinta ya tsahi ta shiga yi masa fad'a, tace
"yanzu kazo kaja asirina zai tonu, a gaskiya ba yanzu naso ace maganar nan ya fito ba, domin hakan zai iyi barazana ga aure na, kuma kaima za ka fuskanci fushin Mahaifinka, gaskiya zan San abinyi" tana gama fad'a ta kashe wayar.


Kai komo ta shiga yi a d'akinta tana tunanin hanyar da zata bullowa lamarin, zama tayi tayi dogon nazari, murmushi naga tayi sai ta ce
"Allah ya kaimu goben, na samo mafita".


Da dare Shureym ya kira Basma a waya, yasan in yaje d'akinta ba zata bud'e ba, yace
"ki shirya gobe in Allah ya kaimu zamu tafi Nigeria, Dady ya kirani yace muje akwai Family miteeng, dan haka ki shirya da wuri da sassafe mamu tafi" cike da murna tace
"Allah ya kaimu" saita kashe wayar.


Mikewa tayi, tayi rawa da tsalle, tana murnan zata ga family d'inta, kaya ta shiga had'awa kamar wacce zata bar garin duka ba dawowa. Zan iyace cewa barci b'arawo shine ya saceta, amma sam ta kasa sukuni, kosawa tayi gari ya waye.


*Washe gari*
Yau Basma harda yiwa Safeena sallama sai fara'a take mata, Safeena tace
"hoo su Basma za'a tafi min da miji sai dariya kike, to Allah yasa in kin tafi karki dawo" harara Yaya Shureym ya galla mata, saita gimtse sauran maganarta tana dariya k'asa-k'asa, Basma kuwa cike da dariya tace
"Ameen ya rabb, nima bana fata na dawo, kuma mijinki gaki ga shi, babu abinda zan miki dashi, ni dai na barki lafiya" saita fice tare da jan trolley kayanta.


Safeena ta bisu har mota tare da musu Addu'a, haka suka wuce airport, Shureym yana cike da damuwa, Basma kuma cike take da murmushi.


*Nigeria*


Gidan President ya cika da dangi, sunzo sunata zumunci, da yake ya kama yau rana ce ta Juma'a, mazan gidan duka suka taru suka tafi babban masallacin Juma'a na Abuja.


Bayan sun dawo gida, iyayen maza da mata suka had'u a babban falon bak'i na shugaban k'asa, anan aka shirya musu abinci a tsakiyar falon kan babban dadduma daya mamaye falon, yara kuma suka baje nasu liyafar a part d'in Ammi, can suke hidimarsu.


Bayan sun gama cin abinci suka shiga hiran zumunci, Abba (President) ya kalli Dady (Gobno Ibrahim) yace
"Ibrahim yanzu gamu duk mun had'u gaba d'ayanmu, ina so ka sanar mana musabbabin had'uwarmu anan daka buk'aci muyi"


Dady ya nisa ya d'ago ya kalli Abba yace
"naso ace Shureym da Basma sun zo tukunna sai kuji bayani a bakinsu, dan dama mun had'u anan ne domin su, na tabbatar suna gab da shigowa" Mai martaba yace
"A'a Ibrahim ka fara sanar mana da komai kafin zuwansu" Mami (Hajiya sa'a) tace
"kwarai kuwa, ya kamata mu ji komai, domin ni hankali na ya ya shi" Hajiya Fatima (Ammi) tace
"gwara ka fad'a kawai domin mu fara tattaunawa akai" ita dai Momyn Basma bata iya furta komai ba saboda nuna kawaici, Hajiya Murja Mahaifiyar Leema ita ma bata furta komai ba, Ummin Meena kuwa shuru tayi cike da damuwa a fuskanta.


Dady yayi gyaran murya ya gaya musu duk abinda Shureym ya fad'a masa jiya, ai duka falon sai suka d'auki salati, Momy kuwa wani irin fad'uwa gabanta yayi, idonta ne ya kawo kwalla zuciyarta na mata suya, Abba sun kuyar da kai yayi ya kasa yin magana, duk falon ya d'auki shuru sai k'aran fanka da kukan AC ke tashi, Mami ce tace


"hmmm nasan za'a rina saboda Shureym ya sanar min cewa tsawan watannin bikinsu da suka yi, Basma tak'i bashi had'in kai suyi rayuwar aure, akwai ranar da har

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login