Showing 75001 words to 78000 words out of 92879 words

Chapter 26 - DEEN MARSHALL COMPLETE DOCUMENT .txt

27 Nov 2024

6152

natse ta qurawa numbern wayarsa ido..


Basarwa tayi tana shigar da wayar key ta aje gefenta tana dauke idonta daga kansa tana Dan kame kamen fatan Kar yayi mgn ko wani tunani akan hakan,
Ta bayanta ya ranqwafo da fuskarsa ya zuro kansa ta cikin wuyanta ya Dora bakinsa Kan kunnenta cikin wani irin sauti me tsananin taushi da son qara Mata kunya sbd kunyarta na kashe dukkanin nutsuwarsa yace"


Basai kin saka kiranba gani nazo.


Kasa dagowa tayi ta kallesa tana kokarin miqewa tabar gurin sbd tafara fahimtan koyaushe da gayya yake Mata wasu maganganun.


Hannunta ya riqo yadawo da ita Yana zaunawa ya zaunar da ita Kan qafafunsa Yana kallon fuskarta dake cikeda kunyar datake basarwa har lokacin ya riqe hannunta Yana sauke numfashi me sanyi na samun nutsuwar dayayi bayan zuwansa gurinta ahankali ya kwantar da kanta kan kafadarsa ta lafe tana sauke ajiyar zuciya boyayya itama
Bude bakinsa yayi cikin nutsuwa har lokacin hannunta na sarqe da nasa yace"


Yaya yarona ko yarinyata?
Lafiya kalau right?


Wani yanayi na mutuwar jiki tambayarsa ta sakata aciki sbd wannan shine Karo na farko da maganar cikin nasu take shiga tsakaninsu bayan wancan tashin hankalin dasukai a asibiti,
Ta Kai hannunta kan cikin ahankali ta Dora tana qaunar cikin naqara mamayeta ta dago ta kallesa daidai lokacinda ya Dora hannunsa akan nata hannun Dake Kan cikin yasake cewa"


Kin shirya zama uwar babyn?


Zame hannunta tayi tana barin nasa hannun akai ta dauke idonta daga kansa ahankali ta furta"


Meyasa Jake tambayan hakan yanzu?


Kwantar da kansa yayi a jikinta cikin nutsuwa yace"


Ina tsananin son cikin ne bayan yakushi da dukan danasha gurin Samar dashi...


Bata taba sanin yakai hakaba a gurin iya magana me nauyiba sai yanzu taqara tabbatarwa takasa danne girman kunyar maganar tasa ta miqe tsaye tana barin gurin ta nufi bakin gadonta tana kokarin hayewa ta kwanta ta shige bargo ko ta rage Jin girman kunyar zancen
Yabi dogayen cinyoyinta Dake fili bayyane sbd gajeran wandon kayan baccin Dake jikinta da wani mayen sanyin kallo Yana tasowa ya riqota Kai tsaye ya juyo da ita Yana kamo fuskarta ya hade bakinsu guri daya Yana sakar Mata qamshin mint mouth wash dinsa kafin ta sauke Kai tuni ya dauketa Yana hayewa gadon da ita hannuwansa na cire dukkanin botiran rigar baccinta ya jefar qasa Yana binta da zafafan romance dinsa data kasa qwatan kanta.


Asubar fari da kansa ya taimaka Mata tayi wanka sbd sabon yanayin data Kuma shiga ko ayau din daya Kuma kusantar tata taji jiki matuqa
Bayan tayi wankan Kaya masu Dan kauri ya dauko Mata tasaka sbd sanyin asuba yakuma kashe AC na dakin yakoma yayo nasa wankan yafito daureda towel dinta a qugunsa qaqqarfan jikinsa a bayyane ruwa na diga ta sauke Kai ahankali tana daukewa daga gefensa ta tayarda sallah dan dama akan dadduma take.
Bayan fitarsa sallar asuban tanata fatan kada yadawo sbd karsu hajjo su fahimci kwanansa anan din tana Gama sallah tayi adduointa ta miqe ahankali ta nufa gado ta Haye ta kwanta tana sauke numfashin wahala kafin ta rufe idanu ahankali tanajin baccin na zuwar mata.


Bacci Sosai tayi har batasan lokaci yajaba sosai sai qarfe goma Sha daya da mintuna arbain ta tashi jikinta duk ba qwari ko kadan
Kasalar data tashi da ita tasa Hanifa da hajjo daketa yawon duba lafiyar wannan baccin datake sukai tunanin batada lafiya Dan Haka tana saukowa gado wanka tafara Yi Dan tasamu qarfin jikinta yadawo,
Tashirya cikin riga da skirt na atampa me coffee brown ta fito Palo
Ruqayyat ta kawo Mata Cocoa Krispies dayaji madarar ruwa data gari sosai Babu sugar sbd batason zaqi cikin farin glass bowl ta karba tana gefen hajjo data damu da yanayinta da tunanin batada lafiyane akwai wani matsalar Kuma.


Ki kawo Mata samosas dinda anty Amina ta Aiko mata dazu" Hanifa dake zaune tafada tana kallon yanda Naj din ke Shan Cocoa Krispies din ahankali kamar baya Mata Dadi bayan itace tace akawo Mata shi zatasha.
Samosas din aka kawo cikin plate manya manya da ita tacika da nama Amma batajin cinta taci gaba Shan abinda takesha tana amsa tambayoyin hajjo ahankali na cewan lafiyanta kalau...


Shigowarsa palon ne yasata tsarguwa taqi dagowa duk da tanajinsa gefenta ya zauna Yana kallon hajjo da itama shi din take kallo ganin fuskarsa na wani sheqin annuri duk da fuskarsa yawanci koyaushe a kame take yau dinma a kame take saidai tana iya hango nutsuwar da zuciyarsa ke ciki a fusakarsa cikin tambaya tace"


Ka fitane yau kaima baka fito da wuriba ko breakfast baka samu zuwaba kaci?


Kafin yabata Hanifa ya kalla da hankalinta Yana Kan qawarta yace mata"


Zanci wannan yanzu da normal drink Mara gas.


Maida hankalinsa Kan hajjo yayi yana cewa"


Bansamu bacci bane da wuri jiyan shiyasa yau da safen na kwanta nasamu hutawa.


Tissue Hanifa taje ta dauko Masa tareda orange juice dinda Babu abinda matarsa Kesha a drink bayanshi takawo Masa ya karba Yana cewa"
Thank you.


Zama tayi tana cewa"


Anjima Zan shiga gurin umma na dubo anty Amina ta kone a hannu Amma inaga ba sosai bane tunda itacema da kanta take fadamun.


Cikin mamaki da 'yar damuwa Naj ta kalli Hanifa din da muryarta me sanyi tace"


Yaushe ne ta kone?


Dazu da safe tace,taface ba wani sosai bane Dan konewa ne a yatsanta ahaka gurin aikin snacks dinta.


Zanje Nima na dubata nagani....


Kallon Marshal hahifa tayi Dake cin samosas dinsa tayi Yana jinsu Yana Kuma kallon yanda take juya abincin Bata wani ci Hanifa zatai mgn ya katseta a cikin Isa da nutsuwa da cewan"


She's not going anywhere until she finish all the Krispies Dake cikin abindake gabanta.


Tsit tayi tana son satar kallon yanayinsa Amma kunyar hajjo ta hanata ta share tana cigaba da sha tabatareda tasan umarninsane take cikawaba,
Hajjo kuwa cewa Tai"


Idan kunje Ina gaisheta anjima zanjira Dr sa'id yazo ya duba Mata hannun tunda konewa ce ba'a Wasa da ita.


Babu Wanda yayi tunanin zata iya shanye bowl din duka sbd yanayin cin abincinta dasuka sani Amma saigashi ta shanye hajjo batasan lokacin mamakinta yasata cewa"


Sannu Najma,yasaki Dole kin...


Girgiza Kai tayi ahankali tana cewa"


Dama adadin Wanda Zan iya shanyewa ne.


Sabon mamakine yakuma Kama hajjo dama shi kansa uban gayyar Hanifa kuwa qaramar dariya tasaki tana cewa"


To yanzu zamu iya zuwa tunda kace idan ta shanye Kuma ta shanye din.


Kamar jira Naj din keyi Yana cewa suje din ta miqe ta nufi dakinta tashige.
Saidata zauna abincin ya Dan fada cikinta dakyau sbd yawan dayayi Mata taji cikinta yamata daidai kuma jikinta ya Dan sake ta miqe ta dauko mayafi ta fito riqeda wayarta Hanifa Daman a jallabiyace ajikinta da qaramin mayafinta.


Hajjo saimun dawo tafada tana nufar kofa ahankali ta riga Hanifa ficewa Yana bin tafiyarta da wani irin kallon dayasa hajjo sauke ajiyar zuciyan kada kawaicinsu yaqare aringa abun kunya agabanta wata rana shiyasa zataso su tafi taren sugama zazzage Amarcinsu acan Dan taga alamar tunda aka samu ciki a sashenta batada labari komaiba zai iya biyowa baya.
Suna fita ta Dan sauke boyayyan numfashin da ajiyar zuciyanda Hanifama Dake kusada ita batajiba suka nufa gidansu Kai tsaye.


Suna shiga Dattijo zai fito Yana sauri yana sanyeda farar shadda da babbar riga da hula cikin girmamawa Naj ta gaidatasa tana basa hanya ya kalleta har Cikin ransa Yana Jin dadin ganinta da albarkar aure data samu saidai Bai Gama saukowa dukaba akan laifinta ya amasa gaisuwar Yana kallon Hanifa ma Dake gaishesa ya tambaya hajjo Yana cewa a gaida Masa ita ya wuce sbd jiransa ake
Naj tabisa da kallo bayan sun wuce tana tunanin gurin neman neman aure kokuma saurin auren zashi Dan kullum Dattijo agurin harkar aure hidimarsa tafi yawa.


Suna Shiga sashen umma habiba suka fara leqata Naj ta gaidata ta fito Asmau na biyeda ita suna mgana Hanifa na gabansu.
Suna Shiga sashensu Dadah dake zaune zainaba na Danna Mata qafafu ta kallesu bayan ta amsa gaisuwar hanifa tana kallon Naj dake qarasowa gurin fuska hade sbd Kar Tai Mata maganganun datake Mata akan cikin tace"


Wani borin kikazo gidan Yi bakyason auren da mijin kike hade mun fuska?
Tun wuri ki saki fuskarki zai fi Miki Dan Ni kingama cin Amanata da sakani koke koken wahala akan ki hkr tunda dai dama ihu muke bayan Hari,
Na are na yafe akan baza'a takurakiba lallabaki za'ai Ashema naquda nake bayan haihuwa,Kika kasa ko Jin Dan tausayin tsufana da kukan danake ki fadan na daina kingama daidaitawa.....


Anty Amina ce ta katse Dadahn da cewa"


Dan Allah Dadah kibar Naj akan maganar Nan tunda ta wuce,
Kiyi hkr ansan taci Amanarki yanda kike cewa.


Naj data rasa ina zata saka kanta sbd takaici da kunya ga qanwarta Asmau a gurin ga zainab din Anty Amina harda ma umma na gurin
Dakin ummanta ta wuce Kai tsaye tana Jin dadar na kwabe Anty Amina tanaci gaba dayi ummansu duk da Bata wani sakarwa Naj fuska haryanzu Saida zancen yasata dariya ta girgiza Kai tana Yi sbd Dadah Bata dagawa kowa kafa basuba da jikokin ba.
##MAMUH#




################################


*DATA!!DATA!!DATA!! PROMOπŸ˜πŸ˜‡πŸ€—πŸ’ƒπŸ’ƒ*
*Assalamu Alaikum*
*Batools Net.S
*muna sayarda DATA bundle akan farashi mae sauki, tuntubemu dumin yin subcription dinku*
*πŸ’ƒπŸ’ƒ
*πŸ“ΆMTN DATAπŸŒ•*
*500MB πŸ‘‰β‚¦140
*1GB πŸ‘‰β‚¦ 240
*1.5GB πŸ‘‰β‚¦ 400*
*2GB πŸ‘‰ ₦500*
*2.5GB πŸ‘‰ ₦650*
*3GB πŸ‘‰ ₦750*
*3.5GB πŸ‘‰ ₦900*
*4GB. πŸ‘‰N1000*
*5GB πŸ‘‰β‚¦1250*
*6GB πŸ‘‰β‚¦1500*
*10GB. πŸ‘‰N2500*
*15GB. πŸ‘‰ N3800*
*20GB. πŸ‘‰ N5000*
*30GB. πŸ‘‰N7500*
*(Valid for 30days)*
Balance, *461*4#* OR
*131*4#*
πŸ’ƒ
Airtel data plan
1gbβ€”550
1.5gbβ€”750
2gbβ€”1100
2.5gbβ€”1350
3gbβ€”1550
4gbβ€”2100
5gbβ€”2400
6gbβ€”2750
10gbβ€”3300
Balance*140#


Glo Data price
1.gbβ€”550
2.9gbβ€”1000
4gbβ€”1500
5.8gbβ€”2000
7.7gbβ€”2300
10gbβ€”3000
Balance *127*0#


9mobile Data price


1.5gbβ€”1000
2gbβ€”1250
3gbβ€”1550
4.5gbβ€”2250
11gbβ€”4750
15gbβ€”5500
Balance *228#
(All valid for 30days)
*CALL/SMS/WHATSAPP -* *08034450108
πŸ‘‡πŸ‘‡πŸ‘‡
*MTN 1GB @ 240


*Ana biyan kudi taβœ”Bank*
*ACCOUNT NUMBER:*
1130713591
*ACCOUNT NAME : Fatima Abubakar Ibrahim,
*BANK NAME :Polaris BANKπŸ‘‡*
*








*_ZAFAFA BIYAR 2022πŸ”₯_*




*_NANA HAFSAT(MISS XOXO)_*
_SO DA ZUCIYA_


*_SAFIYYA HUGUMA_*
_DABI'AR ZUCIYA_


*_MAMUH GEE_*
_DEEN MARSHALL_


*_HAFSAT RANO_*
_HALIN GIRMA_


*_BILLYN ABDULL_*
_TAKUN SAKA_


*_Zaku biya kudin wainnan daddadan labaran Kamar haka_*πŸ‘‡πŸ‘‡
D’aya 300
Biyu 400
Uku 500
Hudu 700
Biyar 1k


*_Zaku tura kudin a_*


6019473875
*MUSAA ABDULLAHI SAFIYA*
*keystone bank*


*Sai shedar payment dinki a*πŸ‘‡πŸ‘‡πŸ‘‡


08184017082


*Kokuma katin waya na MTN anan*πŸ‘‡πŸ‘‡


09134848107








*_DM 48_*
Tana Shiga dakin umma ta zauna kan kujera tana Dan rintse ido ta bude tareda sauke boyayyan numfashin damuwa da takaici me girma na Dana sanin zuwanta yanzu data sani a waya takira anty Aminar sbd Dadah tasamu ta daina Mata wannan mugun gorin kafin tasamu ta manta abar tada maganar tukuna tazo cikin rufin asirinta.
Shigowar umma tareda anty Amina da Hanifa ne yasata Dan dagowa kadan batareda ta kalla ummanba sosai sbd girman kunyar zancen Dadah da har lokacin tana tsakar gidan tana jeho zancen Bata Bari ba,
A natse cikin sanyi tace"


Umma ya gida?
Ina wuni?


Zama umman tayi Kan kujerarta datafi zama a palon tana cewa"


Lfy kalau,ya hajjo?


Wata sabuwar ajiyar zuciya ta sauke ranta na samun sauki da sanyi me yawa Jin umman ta amsa Mata cikin yanayi me Dadi batareda bacin raiba acikin zancen
Sbd wautarta saita kasa yin shiru ta kalla umman da farin ciki bayyane a fuskarta tace"


Umma kin yafemun?
Kin daina fushi Dani?


Wani kallon sakarya umman Tai Mata tana cewa"


Albarkanci mijinki kikaci daya kasa sukuni sai daya nema Miki gafara agurinmu,
Mutuncinsa yasa muka yafe Miki yanzu Amma gaba Kika Kuma makamancin Haka wlh Najma Ni kadai nasan hukuncin dazan Miki,
Yanzu meye amfanin wannan tonan bankada asirin na Dadah duk Dan sbd kinki yiwa kanki fada ki yadda da qaddara ki runguma aurenki Kuma umarnin iyayenki ko nace zabin iyayenki,Kika ringa borin bakyaso anata tashin hankula gshi Nan Dadah tanata Miki bankada Kuma wlh idan ba Allah Kika roqaba yasamata rikicin mantuwar wannan alamariba har tsufa taringa Miki fadensa,
Dan Haka kiyi wa kanki fada ki runguma aurenki sbd kinsamu mijin Dake tsananin sonki da qaunarki Sam bayason damuwarki,
Haka ya ringa zarya a gidan Nan Saida Dattijo ya sauko tas akan fushinsa Dake badan hakaba da yanzu dagake harni muna cikin bacin ransa da fadansa a kullum.


Cikin son bawa umman hakuri da kawar da damuwar zancen Dake neman dawowa sabuwa Hanifa ta kalla umma tana cewa"


Umma ai ta tuba tuni wannan ya wuce yanzu hakama binsa zatai tare zasu koma inasa ran sai takusa haihuwa zata dawo.


Anty Amina Yar dariya ta sake tana cewa"


Naj Wai binsa Zakiyi??


Shareta Naj din Tai kamar bataji me tafada ba ta basar da zancen tana kokarin yiwa umma mgn anty Amina takuma cewa"


Umma Dan Allah kiyi Mana gyaranta na amare masu ciki....


Wani kallo umman Taiwa anti Aminar tana cewa"


Amina kin Gama rainani ko?sbd Kinga muna goga kafada acikin gidan nan.


Dariya Hanifa da Anty Aminar sukai anty Amina na cewa"


Yi hkr umma Amma Allah gskia nake fada ayi Mana Dan gyara......


Jefa Mata sabuwar tissue din hannunta datake kokarin budewa Tai tana cewa"


Yaushe nafara Wasa dake.


Hanifa ce tace"


Dan Allah umma kiyi Mata,
Itama fa Kinga Amarya ce wancan na farko da akai na auren Abbas ne yanzu na auren 'danki Zakiyi umma.


Hanifa kema zama da Aminar kwana biyun Nan yasa kin lalace da rashin kunya ko??


Naj dataga zasu kasheta da sauran ranta da zantukansu ta miqe zata bar dakin umma tace"


Gwara Miki kunyar nan da wadda Dadah zata ringa sakar Miki a tsakar gidan.


Fasawa tayi tadawo ta zauna tana hadewa Hanifa da Anty Aminar fuska ko zasu bar zancen umman tasu ma dayake dama ba ruwanta akwai sakewa sosai a tsakaninsu Banda matsalolin rashin auren Naj din dasukaita shigowa rayuwarsu.


Fira suka hau sunayi suna jeho maganar tafiyarsu Naj din Wanda duk kusan sanarwace suke Mata tareda gargadi akan saken datake dashi akan girman banza data dauka ta sakawa kanta bayan itama Hannah din bawai girmanta Marshal din yayiba kusan shekarunta daya dashi idanma itama Bata girmensa ba sbd kamar shekarunta daya da Hanifa Kamar yanda Hanifa ta taba ji agurin hajjon Amma dai ba maganar shigarsu bace Dan Haka koma dai yayane ta aje abinda takeji ta Kama mijinta da aurenta idan ba uwargida takeson zama da wuri wuri ba,
Cikin neman mgn Anty Amina tace"


To ai bawai fasa auren akaiba nashi da Hannah din kamar ji nai hajjo tace idan sun dawo za'ai Auren.


Murmushi Hanifa tayi tana kallon Naj tace"
Eh to kusan hakanne Amma ganin nake sukai tafiyar Nan Naj kafin kudawo ki sauya ra'ayinsa akan auren Nan kawai.


Umma dataga rainin wayon dasukewa Naj din tace"


Kyalesu Naj,
Kawai dai kiyi kokari ki kafa zamanki a gidansa da zuciyarsa maganar aure Kuma ai basai kin hanaba shi da kansa yace.........


Umma kibari ta tashi tsaye akan mijinta da kanta Mana basai kin Bata kwarin gwiwan zama da kishiya ba."" Anty Amina ce ta katse umman da hanata fadawa Naj ba maganar aurensa da Hannah,
Umma ta sake kallon fuskar Naj datai wani irin kalar tausayi duk jikinta yayi sanyi da maganar
Take tausayin Naj din yakama umman ta dafata cikin kulawa tana murmushin farin ciki tace"


Inshallah Zaki zauna gidanki ki Mori rayuwar aurenki ke daya ba takurawa,
Kishiya idan ba alkhairi bace agareki Allah ya nesanta mijinki da Miki ita,
Karki saka damuwar wainnan biyun Dake zugaki aranki kibi mijinki kawai ki Masa biyayyar data kamata ahakanma saiki riqesa,
ALLAH yayiwa auren Albarka ya saukeki lafiya.


Amin suka amsa gabaki daya Banda Naj da zuciyarta ce ta amsa da Amin din Amma Bakinsa yakasa furtawa.
Kunun gyada da Madara Umma tayi masu sbd Naj
Kuma tashasa sosai sai bayan sallar magriba suka fito gidan bayan umma ta hadawa Marshal lafiyayyan Macaroni salad da kunun gyadar shima aka jerasu a basket ta miqawa Naj wadda ta karba daqyar tana Jin kamar ta kwanta agurin tayita ihu ko zataji saukin halin kunya da takaicin datake ciki sbd Dadah data Kuma bude Mata wani babin data karba basket din harsaida takasa jurewa ta miqawa Hanifa kwandon tana dan dauke fuska.
Hanifa taqi karba tana cewa"


Ba nauyi Zaki iya riqewa ai.


Gaba ta wuce bayan tayiwa umma Saida safe sbd masifar Dadah duk da hakan tanayin gaban Dadah tace"


Eh ai Zakiyi sauri ki koma sbd duk ranarda Kika Kuma kawo zancen banza akan rashin yarda da auren wlh zagewa zanyi na kwada Miki Mari,
Ana tareki akan kiyi hkr kina zuba rashin arziki kala kala akan bazakiyi auren qanin kawarkiba gashi Nan Zaki haifawa kawar Taki 'da a bakyason, za'a gida kina wucewa kece a gaba,jibi idan shegen haukarki ya motsa kidawo kice bakyaso mijin da auren to anshani na warke fes nake kallonki keda Fatiman Dan itama ban yarda dabatasan da cikin ba kuka barmu nida Dattijo bawan Allah muna gwara Kai gurin tunanin mafitar ki hakura ki zauna da auren.


Naj dai gaba tayi Bata waiwayoba tanajin su Anty Amina na shiga maganar suna tausar Dadahr da bakinta yaqi shiru Hanifa ma Saida safe Tai musu ta wuce Tani bayan Naj din suka fito tana 'yar dariya tace"


Naj kin shiga Tara da goma gurin Dadah.


Bude Baki tayi tana cewa"


Dadah ai dama yanzu tasamu abin fada kenan,dama kwana biyu Bata samu Wanda ta maqalewaba duk yashigo ayita Jan riqe magana anayi yanzu tasamu ta maqale mun.


Kofar gate aka bude musu tun kafin su qaraso suka Shige securities din na gaidasu cikin girmamawa musamman Naj din datake Matar ogansu Kuma sunsan yanzu yashige Yana harabar gidan.


Hankalinta na Kan gabanta tana sauraren zancenda Hanifa ke Mata fuskarta daukeda Dan qaramin murmushin zancen me neman auren anty Amina da Hanifa ke fada Mata yanda akai jiya shida Dattijo kaca kaca Wai tsohon class mate dinsane.


Wani sabon murmushi tasake dayayi Kama da 'yar dariyarta me burgewa har tana Dan dagowa sbd sosai labarin ke Bata dariya Dan anty Amina da Hanifa sukai zancen ita Bata samu sunyi zancenba.


Akansa idanuwanta suka sauka dagowar datai,
Yana sanyeda farar jallabiya data qara Masa kamala da kwarjini
Idanuwansa akanta sbd yaune Karo na farko dayake ganin murmushinta harma da dariyarta tun bayan lokaci me tsayi daya Santa,
Waya yakeyi Amma gabaki daya hankalinsa yakoma kanta tunda suka shigo harabar gidan,
Hannah dake gefensa tsaye cikin riga da skirt na atampa itama ba dankwali akanta sai wani Dan siririn mayafi data yafa akan tana ganinsu ta Dan dauke Kai tana saka Kiran qarya a wayarta tafara wayar itama Dan batason su tsaya ko da nufin gaisawa da ita gwara su wuce ciki tasamu yau zata dage saisunyi fira da Marshal din da Allah yasa tagansa yanzu tana dawowa daga anguwa shima Yana dawowa.


Dan sauke Kai Naj tayi daga kallon dayake Mata,
Tana ganin Hannah gefensa ta Dan sake kawar da Kai tana tafiyarta cikin nutsuwa batada Niya ko tunanin tsayawa Dan Babu dalilin yin hakan Dan Haka

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login