Showing 48001 words to 51000 words out of 92879 words
iska yayi yawa Zaki kwasa sanyi tafi gurin ummanku nasan dama can kikai gulmar na sanmiki goron ne yasa za'ai zaman Shan hantsi Dani.
Miqa Mata qaramin farin goro tayi tana cewa"
Allah ya nunamun NAJMA tazo tambayar goron Nan ranar nayi kwanan niyar azumin godiya ga Allah.
Najma dake qarasowa taji abinda Dadahn tace ta kame fuska matuqa rashin Jin dadin zancen da qyamarsa na bayyana fili a fuskarta tafasa zama gefen Dadahn ta gaidata kawai ta wuce dakin ummanta
Dadah tabita da fadin"
Duk mugun halinki sai Naga 'yayanki da yardar Allah,
Mara godiyar Allah.
Daka tawa tayi ahankali ta waiwayo zatai magana gabaki daya ranta ba Dadi Anty Amina data fito daga dakinta ta riqo hannunta tana girgiza Mata alamar kada tafada koma menene tayi niyar fada.
Juyawa sukai suka nufa dakin ummansu dake zaune dakinta tana hada khumras masu shegen qamshi da kame jiki Kamar na _*YERWA INCENSE*_ tana jinsu takuma San da Amina Bata Hana Naj din mgn ba zata iya fadar abinda Dadah yau zata Hana uban kowa bacci a gidan sbd zaunarda Dattijo zatayi ta hada masu gurminda zai fatattaki kowa da bacin Rai.
Naj tareda Aminar ne suka shigo kafin Hanifa dake bayansu suka zauna Naj na cewa"
Umma barka da aiki,
Ina wuni?ya gidan?
Amsawa umman tayi batareda ta kalletaba sbd A qule take da ita akan wannan taurin Kan da muguwar zuciyar sbd Hanifa kawai ta kyaleta Dan batason tayi Mata fadan rashin son datake nunawa auren jalal a gaban Hanifa Dan kuwa tasan ko Dadah sbd Hanifan na gidan ta taqaita tata masifar.
Kusada umman Hanifa ta zauna tana daukar kwalban khumrah daya tana shinshinawa tace"
Umma wannan khumrahn wankane ko?
Eh Hanifa,Yaya jiki jikin?
Ankai Miki wainarki Kan lokaci kuwa?
Eh umma naci kafin mufita anjima alalan manja nakeso umma ko gobe da safe ruqayyat Basu iyaba idan sunyi qarfi yake.
Anjima Inshallah Zainab zata kawo Miki yanda kikesonta.
Yawwa Ngd ummana.
Ganin yanda umman fuskarta ba asakeba da alama ranta bace yake akan Naj hakama anty Amina ma Babu wani dogon magana ita kanta Naj din duk tayi wani iri ranta ba Dadi itama kowa sai kame kamen yaqen Dole yake Kuma duk tasan sbd itane ba'ason tada maganar Dan kada asa taji ba Dadi saidai ita Bata damu sosai da duk qin auren da Naj keyina sbd tasan Dole bazata iya karban aure irin wannan lokaci daya ba tunda har bata fitina ko fada akan auren ko ahakan ai ba laifi tasan wata Rana zata Aminta da auren.
Kallon umma da anty Amina tayi cikin nutsuwa da sanyin murya tace"
Umma kuyi hakuri ku sake bawa Naj lokaci Inshallah komai zai daidaita tunda na tabbatarda itama kasa amsar abin ne Kai tsaye yasa takejin bazata iyaba Amma ai komai lokaci yakeso.
Da kallon takaici umma tabi Naj din hakurinta na qarewa tace"
Kinji abin datake fada ko?
Fahimtarki takeso ayi abaki lokaci akan abinda kece aka rufawa asiri da kuwa da Bai aurekinba da yanzu kinanan kina zaman wulaqanci da matsuwa agidan wani,
Shine namiji shine yakeda damar cewa bayaso sbd shine me riqe auren Amma kece kike rainin wayon da kikaga dama sbd sun nuna suna sonki.
Dagowa Naj tayi da idanuwanta dasukai jajir suna neman cikowa da hawaye tace"
Umma.....
Katseta anty Amina tayi da cewa"
Naj bakida gskia ko kadan
Kuma wallahi kunya kike bani da wannan dabi'ar Taki sbd banyi tunanin ko Dan su hajjo ba ki nunawa wannan auren tsana haka,
Menene matsalarki?
Kukan baqin cikin datake dannewane tsawon lokaci ya kufce Mata tana cewa"
Wallahi bazan iyaba,
Nakasa,
Shin meyasa da aka tashi taimakon nawaba Amin taimakon da akasan Zan iya dauka,
Zuciyata zafi take,
Ciwo take,radadin hakan nakeji Dan Allah Araba wannan auren koba komai Ni bazan iya da Wanda yakeda wadda yakeso ba.....
Au bayan girman da kike ganin kinmasa yanzu Kuma hadda wadda yakeso tazama dalili kenan?
Sake fashewa tayi da wani kukan tana cewa"
Ni koma menene Dan Allah Araba auren Nan.....
Wani irin salatin Dadah sukaji data shigo tana kallon Najman bakinta na rawa gurin magana saikuma kawai ta fashe da kuka tana cewa"
Innalillahi-wainna ilaihirrajiun
Wace masifar ce zata kunno Kai rayuwarki Najma,
Wace tsanace kikewa wannan auren dako shekara daya baiyiba za'a kidawo zawarci,
Najma Dan Allah ki duba tsufana da mutuncin Dattijo ki hakura ki cirewa ranki masifa ki runguma aurenki....
Irin kukan da Najma da Dadah keyi yasa umman sake Shiga wata mummunar damuwa da baqin ciki ta tashi cikin tsananin fushi tayi Kan Naj din Hanifa da duk hankalinta itama ya tashi ta tashi da sauri ta janye Naj din tana kasa mgna sbd ganin cikin qanqanin lokaci Abu yazama tashin hankali.
Ba shiri Dadah tasa aka Kira Mata Dattijo tun kafin ya qaraso sashen yake jiyo fadan umma da ranta yayi mummunan baci qololuwa dakuma kukan dadah daya Gama daga hankalin kowa.
Anty Amina ce tayi Masa bayanin abin Dake faruwa tana dasa Aya ya kalli Naj cikin tsananin bacin Rai da baqin cikin daya rasa abin dazai Mata
Tana durqushe gefe har lokacin kuka takeyi me qarfi na rashin sanin mafitar abindayake cin ranta.
Kallon umma yayi cikin fushi da bacin Rai me tsanani yace"
Najma dai takai matakinda tafi qarfin umarnina Dan Haka ke dakika haifeta bakifi qarfin umarnin nawaba saiki shirya kayanki dan wallahi tallahi tana dawowa gidan Nan da sunan aurenta ya mutu bazata zaunaba tare zaku bar gidan nan.
Kallonsa umman tayi cikin baqin cikin koyaushe yayanta sukai laifi aurentane yake barazanar rawa,
Ta maida kallonta kan Najma tace"
Kinji ai saikije ki hado kayan naki mubi duniya tunda shine sakamakon dazaki bani.
Dadah cikin kula tace"
Najma Dan Allah ki dubi girman Allah kiyi hkr ki dangana wlh na zubarda makaman yaqina na yarda anmiki ba daidaiba ki dangana ki runguma aurenki wlh gaba Zakiyi farin ciki da yardar Allah.
Cikin fushi Dattijo yace"
Ki daina rarrashinta Dadah wlh ko ta tashi ta fice Kona nema mugun ice nai Mata dukan da bazata iya komawa da qafafuwantaba.
##MAMUH#
*_ZAFAFA BIYAR 2022🔥_*
*_NANA HAFSAT(MISS XOXO)_*
_SO DA ZUCIYA_
*_SAFIYYA HUGUMA_*
_DABI'AR ZUCIYA_
*_MAMUH GEE_*
_DEEN MARSHALL_
*_HAFSAT RANO_*
_HALIN GIRMA_
*_BILLYN ABDULL_*
_TAKUN SAKA_
*_Zaku biya kudin wainnan daddadan labaran Kamar haka_*👇👇
D’aya 300
Biyu 400
Uku 500
Hudu 700
Biyar 1k
*_Zaku tura kudin a_*
6019473875
*MUSAA ABDULLAHI SAFIYA*
*keystone bank*
*Sai shedar payment dinki a*👇👇👇
08184017082
*Kokuma katin waya na MTN anan*👇👇
09134848107
*_DM 33_*
Janyeta anty Amina da Hanifa sukayi ta suna sake bawa su dattijon da Umma hakuri Dadah kuwa kamata tayi tayi dakinta da ita ta zaunar tana kallonta tace"
Ki dauka dangana 'yar Nan kibi umarnin mahaifinki da mahaifiyarki tunda dai kinsan bazamu zabar Miki mugun abu ba,
Banda abinki Najma kinyi aurenki kina cikin kwanciyar hankali da nutsuwa meyafi hakan,
Dan shekarun da Kika basa waye yasani tunda idan aka kalleku ma sai adauka sa'an babban yayanki ne,
Shin menene illar auren qaninka tunda?
Shin kin manta Nana Khadija ko data aura Manzon Allah ya girmesa da shekarun dasukafi Wanda kikaiwa naki mijin ita datafi daraja ma ko farin ciki da wannan koyin bazakiyiba ki faranta Mana?
Mu idan bakya Yi danmu munada fada da takura to kiyi Dan hajjo da Alfa Mana,ga Hanifa Nan haryanxu Bata ganin laifinki tana bayanki sbd irin qaunar datake miki
Dan Allah kiyi hkr kiyi zamanki gidan aurenki tunda har daga mijin harsu hajjon sun amincew zamanki ba takura sai kinji kin samu nutsuwa da auren.
Haka Dadah ta ringa Bata rarrashi da maganganu sbd ganin fadan ba inda zai kaisu saiga tone tone har Azo abata goma biyar Bata gyaru Dan ita da wannan aure ya mutu gwara aje ahakan tana zaune gurin hajjo indai da auren yafi musu zasui jira har Allah yasa auren yazama Kamar kowanne auren.
A dakin Dadah tayi zamanta saidata nutsu kafin Dadahn da kanta ta rakasu har palon hajjo suka Kuma taruwa suka rarrasheta kafin Dadah ta tafi
Har dare hajjo da hanifa na tarairayarta Dan tasake Haka suka Kwana
Ko Dad Alfa da kansa Saida yakirata suka sake zama da hajjo suka ringa rarrashinta cikin kulawa hartazo tanajin kunyar abin qarshe Dole ta sake Dan ganin yanda duk suketa sake lallabata shiyasa ta sake sosai ta koma bakin aikinta,
Hannah da mum Malika Koda sukaji abindaya faru Dadi Kamar me musamman suka sake maida himma gurin ganin auren Hannah da MARSHAL din ya tabbata,
Duk yanda Hannah taso fadawa marshal din rigimar Bata samu damaba sbd baida lokacinta busy yake sosai gashi yanata tafiye tafiye acan din Dole ta hakura harta samu lokacinda zata fada Masa.
Umma da Dattijo Basu duk da zancen yayi kwanaki sosai Basu daina fushi da itaba sama sama suke amsa gaisuwarta idan tashigo gidan Dadah ce dai take lallabata dataga fushin ba yayi sai anty Amina daketa aikin dawainiya da duk abinda Hanifa keso sbd cikinta daya fito sosai yanzu.
Takoma aikinta gadan gadan sai yamma take dawowa musamman da ayyuka sukai Mata yawa na 'yar rigimar da ake wadda ta tarar Marshal ya fige Abbas daga ALFAs Amma sauran shareholders din Basu yardaba shikuma sbd yafi kowa hannun jari aciki yace hukuncinsa kenan.
Rigimar tasa ayyuka sun Mata yawa sbd dukkanin ayyukan office din president na companyn yadawo office dinta tunda Abbas an dakatar dashi say angama rikicin gashi Marshal din yatafiyarsa saiya dawo Kuma.
Da mamakin wannan qarfin halin nasa take aikin office din kullum sbd ayyukan sun Mata yawa ko yawon meetings yasa har wata Yar rama ta taso mata.
Saidatai wata daya da sati biyu tana fama da ayyuka kafin ayyukan suka Dan daidaita tafara samun kanta har tana dawowa gida da wuri.
Yau tunda tazo office din batai komaiba sbd jiri datake gani tun jiyan tafara jinsa yanayi Yana tafiya.
Dafe kanta tayi tana Dan rufe ido ta bude ahankali ta dago tana kallon Sarah data shigo office din ta bude Baki ahankali tace"
Sarah please bani ruwa me sanyi nasha.
Kallonta Sarah tayi da mamaki tace"
Me sanyi ko me Dan sanyi kadan?
Batareda ta dagoba tace"
Me sanyi sosai.
Da mamakin Sarah takuma kallonta sanin Bata Shan ruwan sanyi zatai mgn saikuma ta fasa ta nufa fridge ta bude ta dauko Mata ruwan roba masu sanyi sosai ta kawo Mata ta miqa Mata.
Karba tayi ta bude Kai tsaye takai bakinta tana Sha Sarah na kallonta da mamaki.
Ajiyar zuciya kadan ta sauke bayan tagama sha ta ajiye sauran ruwan tana cewa"
Sarah zanje gida yanzu kaina na ciwo Ina buqatan hutawa ko zai sake.
Tare suka fito da Sarah din itace take tuqin takaita gida suka nufa cikin gidan tare.
A Palo suka tararda Hanifa zaune tareda anty Amina data kawo Mata sabuwar Awarar da Umma ta Aiko Mata wadda akaiwa sauce din kayan miya dasu carrots da kwai.
Kallo daya Naj tayiwa Awarar taji tana son ci abinda Bata taba yiba shine ko dakinta Bata shigaba ta qaraso gefen Hanifan ta zauna ahankali tana cewa"
Yunwa nakeji sosai har kaina Yana ciwo.
Ta dauka plate tana miqawa Hanifan tana cewa"
Samun zanci.
Zuba Mata Hanifa tayi tana cewa"
Lallai yau 'yar gaban goshin hajjo yunwa takeji tunda ko daki bazaki iya qarasawaba.
Batace kalaba saidataci Awarar a bakinta taji kanta dake sarawa ya daina ta dago ta kalli Hanifan ahankali tace"
Thanks.
Sai alokacin ta kalla anty Amina tana cigaba daci suna gaisawa anty Amina na kallonta dakyau cikin nazari tace"
Naj bakida lafiyane Naga kamar kin fada.
Kallonta Hanifa tayi tana cewa"
Ramar aikice Amma duk da hakan Ni Banga ramarba haske dai Naga tayi sosai kodai bakida jini ne Naj?" Taqarasa fada tana Dan zare ido.
Batareda ta dagoba tace"
Lafiyata kalau stress ne kawai amma zanshiga hutu sbd komai yakoma yanda yake a office din Inshallah.
Saidata qoshi kafin ta qarasa dakinta tabarsu a palon ta tube ta shiga toilet wanka.
Sai datai wankan taji jikinta ya sake sosai ta fito daureda towel ta nufa jikin mirror kenan taji wayarta na ringing ta juyo ta nufa wayar dake Kan gado ta dauka sai kawai taga No din qasar waje destination id dinta ya nuna Mata United States of America.
Kai tsaye ta dauka batareda ta tsaye tantance kiranba Wanda yake Vidcall sai ganin mutum tayi ya bayyana kan screen din wayarta Yana zaune cikin lafiyayyan palonsa sanyeda uniform dinsa na sojojin America dasukai Masa wani irin kyau uwa uba hutu da nutsuwar daya samu ta bayyana ataredashi Ya zuba Mata fararen idanuwansa har zuwa kirjinta dake daureda towel Tsananin hasken data qara yasashi sake zuba Mata idanuwansa,
wannan ne Karo na farko data gansa cikin uniform ta dauke kainta ganin irin kallon dayake Mata sai alokacin ta tuna da towel ne jikinta ta kashe wayar tana jefarwa Kan gado ta tafi tahau shirinta.
Baccin maraice yayi sai magriba ta tashi ta fito bayan tayi sallar magriba sbd yunwa me tsanani datake ji.
Kicin ta nufa sbd sanin lokacin cin abincin Daren baiyiba tasan Hanifa na kicin sbd Bata jimawa bataci ba shiyasa take zuwa kicin taci ta koshi Kuma ahau dining aci da ita.
Tana Shiga kicin din ba kowa sai ruqayyat dake qarasa aikin abincin Daren ta nufa fridge ta bude ta dauko milk drink tasha sosai ta dauko cake guda hudu ta cinye ta qara da apple biyu kafin taji ta dan samu nutsuwa ta fito suna hadewa da Hanifa dazata Shiga kicin din neman abinda zataci itama tace"
Naj yunwa nakeji cake zanci da Madara tunda kin cunyemun awarar da Umma takawo min dazu.
Batace komaiba Takoma Palo ta zauna tana duba wayarta tana jiran agama abincin akawo dining.
Sallar ishai taje tayi tana fitowa hajjo na fitowa suka dunguma dining Hanifa tuni ta riga kowa Isa.
Naj din ita tazubawa hajjo abinci takawo Mata ruwa da komai ta kalli Hanifa da Bata harta zuba abincinta tafara kaiwa Baki.
Zama tayi itama tareda zubawa ta zauna suna binta da ido ta dago ta kallesu ganin irin kallon dasukewa abincinta yasata kallon abincin sai alokacin taga ta zuba da yawa ba kamar yanda ta Saba ba dama kwanakin gabaki daya cin abincinta ya sauya ta Dan fuske tana cewa"
Yunwa nakeji sosai duk yau banci wani abincin kirkiba.
##MAMUH#
*_ZAFAFA BIYAR 2022🔥_*
*_NANA HAFSAT(MISS XOXO)_*
_SO DA ZUCIYA_
*_SAFIYYA HUGUMA_*
_DABI'AR ZUCIYA_
*_MAMUH GEE_*
_DEEN MARSHALL_
*_HAFSAT RANO_*
_HALIN GIRMA_
*_BILLYN ABDULL_*
_TAKUN SAKA_
*_Zaku biya kudin wainnan daddadan labaran Kamar haka_*👇👇
D’aya 300
Biyu 400
Uku 500
Hudu 700
Biyar 1k
*_Zaku tura kudin a_*
6019473875
*MUSAA ABDULLAHI SAFIYA*
*keystone bank*
*Sai shedar payment dinki a*👇👇👇
08184017082
*Kokuma katin waya na MTN anan*👇👇
09134848107
*_DM 34_*
Hajjo kallon abincin takuma Yi kafin ta kalli Naj din cikin kulawa da nutsuwa tace"
Najma ki daina zama da yunwa Haka sbd zata iya Miki illa yanzu wannan abincin zai iya qulle Miki ciki,Kisha tea kafin ki ci abincin cikinki ya sake tukuna.
Kallon Hanifa tayi tana cewa"
Miqa Mata tea din ta zuba ta Sha.
Qaramin flask din dake cikeda black tea dinda yaji kayan qamshi da hadinsu lemon da Zuma wanda koyaushe dashi ake jere abincin safe Rana da dare Wanda qaidar hajjo ne wadda ta Saba da Shansa Kuma al'ada da dabi'ar Shan nasa ya Kama duk Wanda yake gidan ko baqi akai idan za'a kawo musu ruwa sai an tambayesa ko akawo Masa tea din.
Miqawa Naj Hanifa tayi tana cewa"
Kin riga kinfara cin abincin kinsha tea din daga baya" ta aje tana daukan spoon tafara cin nata abincin.
Kamar yanda tasaba cin abinci a natse ta cinye abincin tas tasha ruwa kadan ta zuba tea din Wanda kurba daya Tai Masa ta ajiye tana cewa Alhmdlh ahankali.
Kallonta hajjo tayi tana sake cewa"
Idan Zaki ringa zama da yunwa irin Haka Zaki sa ciwofa ya kamaki karki sake hakan daga yau.
Guntun murmushi tasaki ahankali tana kallon Hanifa da har lokacin abincin takeci tace"
Yaune kawai hakan bazai Kara faruwa Inshallah hajjo.
Barin gurin tayi ahankali tanajin nutsuwarta ta dawo ta dawo palo ta zauna sai alokacin ta dauka wayarta tana dubawa har Hanifa da hajjon suka Gama suka baro dining din hajjo tayi dakinta sbd qafafunta da ruqayyat zata gasa Mata da ruwan dumi.
Hanifa Kuma gefenta ta zauna tana daukan tata wayar itama tace"
Naj gobe umma zata faramun sabon gyara Isma'eel zai dawo next week fa.
Juyowa Naj din tayi ta kalleta tana sake maida hankali kan abinda take dubawa a wayar tace"
Shine kike Zillo Haka?
Cemasa zanyi yayi zamansa sai zaki haihu yadawo muga qarshen gyaran.
Dariya Hanifan tasake tana cewa"
Zillo ma ai kadan ne zille zille zanyi ma idan ya dawo tunda bansan kalar zille zillen da matan duniya ke can suna Masa ba tunda bana kusa Dana Haka idan yazo nawa lokacin ne nayi haukama idan Zan iya,
Hannah kina ganin duk ranarda tasamu auren Marshal wannan rawar kan datake ai uwar ubansa zamu gani akan wannan datakeyi Yan.......
Hade sauran maganar tayi tana rufe bakinta Jin Naj din tayi shiru sbd gabaki daya ta manta da Naj take maganar,ta Dan kalli fuskar Naj din data juyo itama ta kalleta tareda sake wani irin guntun murmushi tana basarwa da cewa"
Ashe kinada qarfin yiwa miji zille zillen Kike makure Mana fuska ki nade muna dawainiya da matarsa.
Haba sirikita idan bakiyi hidima daniba waye zaiyi....
Dan kame fuska Naj din tayi Hanifan tasaki dariya tana cewa"
Sorry my Naj.
Wayar Hanifan ce tayi ringing ta waiwayo tana kallon wayar ta maida kallonta kan Naj da kallo daya tayiwa wayar taga sunan me Kira ta dauke tana maida hankali akan tata wayar.
Dauka Hanifa tayi cikin murmushin ganin video call ne ta dauka Kai tsaye tana cewa"
Hey Deen Marshal,ya kake?
Kallonta yayi Yana Dan gyara crossing qafafunsa da yayi wayar na ajiye saiti dashi a gabansa Yana zaune acikin office dinsa sbd sun safiyace har hantsi ma yafara,
Ya bude Baki ahankali yace"
Lafiya kalau,ya baby?
Kinje scanning din kuwa?
Nayi mgna da Dr sa'id,ki turamun scanning din I want to see it.
Ok,ok,Baby is fine,and iam fine also" satar kallon Naj tayi tana cewa"
And Naj ma tana Lafiya.
Jingina yayi baya Yana folding hannuwansa fararen idanuwansa akan wayar cikin muryarsa data Gama Isa cikin kunnuwanta yace"
Bata wayan.
Kallonsa Hanifa tayi tana Dan kame fuska da murmushi akan fuskarta tace"
JALAL karka damu qawata da wannan kamewan naka,
Wani irin kallo yayi Maya Wanda yasata harararsa tana cewa"
Kome ka zama karka manta dai Ni yayarkace.
Dan rufe idanuwansa yayi ya bude da wata muryar yace"
Matan auren dake gefenki Zaki bawa wayar.
Naj dake zaune duk takasa ma qarasa abinda take a waya sbd zancen a bayyane yake fita ta miqe zata bar gurin lokacinda Hanifa ke kokarin miqa Mata wayar Kai tsaye taji muryarsa ba Wasa aciki yace"
Kika bar gurin Zakiyi mamakin hukuncin hakan.
Dakatawa tayi tareda waiwayowa ta kallesa ta cikin wayar zatai magana saita kasa ta fuske tana kokarin wucewa tabar Hanifa ta riqota tareda maidata zaune tana cewa"
Dawo ki zauna Bari Ni natashi kicin zanima.
Miqewa tayi tabar gurin bayan ta aje wayar saiti da Naj din.
Dauke Kai Naj din tayi tana cigaba da duba wayarta tanajin idanuwansa na yawo akanta duk sai hakan yasata kasa nutsuwa ta dago ahankali fuskarta a hade suka hada idanuwa ta dauke Kai kafin tayi