Showing 3001 words to 6000 words out of 86122 words

Chapter 2 - BUDURWAR QAUYE Complete-by miss Deejarh-.txt

26 Nov 2024

4809

kawai zaka fahimci hutu atare dashi, kyansa yadad'a fitowa, Daddy suka qaraso ya rugumeta Daddy yana cewa I missed u Daddy, Daddy yace muma munyi missing naka sosai son"


"sake Daddy yayi ya rungume momcy, momcy nayi qewarki dayawa, nima haka papa amma yanzun ai kadawo Komai ya wuce, yes momcy barin sake nisa dakuba "


" har side nasa suka rakashi, Daddy yace son kayi, momcy tace kana tayyar ho (ga abinci yayi gamu) ko bazakaci girkin momcy ba? Waw momcy thanks nafayi missing girkin kifa "


" ok saika fito suka fice, halliru mai wanki ne ya shigo, yana jaye da jakan kayansa, dasauri yace hey what ar u doing here yana nuna sa da hannu, shiru yayi alamun bai fahimce shiba, tsaki yaja cikin tsawa yace mekake mun adaki "


" adiririce yace hajiya ce tace na kawo maka kayanka, sai kawuce falo kashigo mun har daki so kada kasake, next time dik abinda kazo dashi katsaya daga qofar falo kayi knorcking samje (kagane)


Ayi Haquri yallabai bazaa sakeba, kana iya tafiya yace dashi, qarema dakin kallo yake, dan yanayin dakin yamasa"


"wanka yayi ya shirya tsaf, afalo yasami su Daddy suka wuce dinning, bayan sun gama cin abuncin suna hira papa yace momcy awani unguwa didi niima takene, tana federal lowcost tacema gobe data zo, ok bamatsala barina dan huta "


Da yamma lis ya fito shikin wasu black troser da red shirt mai dogon hannu, hannunsa riqe da wayoyi, momcy tace ina zuwa haka, momcy inason fita akwai abinda dan sayo, to kaida bakasan gariba sai dai driver ya kaika"


"Bayan magriba yana zaune adakinsa layin TJ ya kira yana dayawa yace ya akayine man, dariya yayi taya kasan nine, TJ yace inafa tajiran call naka so ina ganin baqon layi nasan kaine, ok to ya kasamu mutan gida, lfy lau sai dai ina missing abarfa


Papa yace ina ai sai da nafita na nemo ta, TJ yace shege mutumina ainan dad yakasa ya tsare haka na haqura, amma gobe zan shigo, ok sai naganka"


Ranan haka papa yayi tatil abinsa, nan yahau bacci kamar ba gobe, momcy tashigo yanayin data gashi ya bata tsoro dan gefensa kwalabaine na syrup da giya ga wasu drugs agefe, Daddy ta kira yazo ya gani takaici yahanashi magana kawai ya juya ya fita "


" dasafe momcy ta tuhumeshi akan abinda tagani, yace haba momcy mene aciki kawai fa ina dan wartsake gajiya, ganin yaqi sauraran ta yasa tace Allah ya shiryeka "


" satin papa 1 da dawowa Daddy yace ya shirya suje dambam weekend, ana gobe dasu tafine suna zaune a afalon Daddy, Daddy yace Alamin mene zaka kaiwa fauziyyah tsaraba? "


" fauziyyah ya maimaita sunan kafin yace, konhe fauziyyah (waye fauziyyah) dan shi harga Allah yama manta da labarinta "


Daddy yace tumare dulhan (amaryarka), dulhan, dulhan ya maimaita sunan, momcy tace yar gidan uncle Usman mana papa kake kamar kamanta ta"


"nan take ya tuno aiko ya bone fiska, yace pls Daddy kabar maganan nan nibani da abinda dan bata, yana fadin haka yayi hanyar waje, Daddy yana kiransa ko ya juyo ya fice abinsa"


"Daddy yace hajiya kihada mata kayan kwalliya, kuma dole yakai rabudashi, momcy tace ai papa rigimace dashi, badamuwa zaa hada"


"ranan da sukaje dambam Daddy yabawa papa kayan kwalliya da momcy ta hada yace yaje yagaida mama ya kuma bawa fauziyyah, inba hakaba ransa dai baci, haka ya karba bada san ransa ba ya tafi "


" atsakar gida yasami mama tana tsefe ma fauziyyah kanta sai kuka take wai zafi, da faraa mama ta karbeshi suka gaisa, mama tace bazaki gaida yayankibane "


" fiska shabe2 da kuka ta dago, aiko kallo daya ya mata ya kau da kansa, ina yini tafada tana goge hawayen fiskanta, lfy kawai yace, miqewa yayi yace mama zan tafi ana jirana awaje, ajiye ledn hannunsa yayi yace agaida abba gobe zanzo bagaidashi"


"mama tace angode Allah yasa ka, madalla agaidasu hajiyn, y amsa da dayaji"


"yana tafe a mota yana saqa da warwara, dan gaskiya zanje nasami Daddy ya ma warwara wannan alqawarin, haba wata qazamar yarinyan, toh shi inma aure zaiyi yayi me da ita, wlh bazai yiyuba sam dasake "


✍🏻Faty Mmn Faty
[10:37PM, 8/6/2017] β€ͺ+234 703 448 8635‬: 🌾🌾🌾🌾🌾🌾




🌾🌾🌾🌾




🌾🌾🌾




Budurwar Qauye πŸ€·πŸΌβ€β™€πŸ€·πŸΌβ€β™€πŸ€·πŸΌβ€β™€


Written by Faty Mmn Faty


July, 2017




*Gaisuwa mai d'inbin yawa gareku masoyan Budurwar Qauye, Mmn Faty tana gaidaku a dik inda kuke, dama su turo mun saqonni, harma da masu kirana awaya, da wad'andama basu da hanyar mun magana Mmn Faty luvs u all wannan shafin nakune nagode Allah ya bar qauna πŸ’•πŸ’•πŸ˜˜πŸ˜*


0⃣4⃣
β€œYana isowa gida falon Daddy ya nufa amma ganinsa da baqi yasa ya juya, room nasa ya wuce rai b'ace, zuciyarsa kamar tafashe haka yakeji


Syrup ya d'akko ya balle murfin yakai bakinsa, sai daya shanye tass sannan ya ajiye, ahankali yafara jin b'acin ran yana raguwa dan tafara tafiya dashi duniyar sama "


" yana nan kwance shiba bacci ba haka ba idonsa biyu ba, har akayi sallan magriba bai tashiba


Daddy ne ya shigo, Matsowa daf dashi yayi yaja yatsun qafarsa ya kira sunansa Alamin, jin bai amsaba yasa ya tunanin ko bacci yake


Alamin yasake kiransa, sai anan ya motsa tare da fad'in uhumm


Daddy yace au kana jina dama ka yi shiru har akayi sallah baka fitoba


Naji ai zanyi, to is better katashi kasan lokacin magriba dawure yake qurewa, da kyar ya miqe zaune dan dik jikinsa ciwo yake masa


Daddy ya juya zaifita ya ga kwarbar Syrup a jife, hannu yasa ya d'ago, rai b'ace ya dubi papa, yace yeh sab kyahe? (mene ne wannan) yana nuna masa Kwalban
Shiru yayi baice komaiba saima b'ata fiska da yayi


Daddy yace yanzun Alamin abinda kake kana kyautama kanka kenan, ka dubi irin abinda kake sha kamar baka san illansaba


Haba Daddy dawanne danji ne da irin kashemun rayuwa da kuke qoqarinyi ko kuma da wadannann sarautan naka


Wanne irin kashe maka rayuwa kuma?
Ah waccar qazamiyan yarinyan da na kusa haifata ma dakuke wani cewa wai ita zan aura, to wlh ni dana auri wannan yarinyan gara na mutu ba aure dan ni mata basa gabana


Daddy yace kashe rayuwa ya fice wanda kake ma kanka, ka sha wannan kasha wancan kamar ba Dr ba, ko so kake kace bakasan illansaba, toh wlh kashiga hankalinsa da wannan shaye2n naka, inba haka ba ranka zai mummunan baci kodan kaga na zura maka idanu ina kallonka shiyasa kullum kake qoqarin zubarmun da mutunci


Daddy nifa banfa nemi dogon maganaba kawai kasan abinyi, inkuma ka matsa wlh sai kunji dama baku somaba dan bata yanda zan fara rayuwa da wannan jsririyar


To idan naqifa sai yaya ko zagina zakayi tinda ka girma


No, nifa gaskiyace kawai fa I can't marry that villager atow


Toh tinda ka girma har ka iya sa insa dani zangani nida kai waya haifi wani, ka kuma bud'e kunnenka da kyau kaji wlh kaji na rantse aure babu fashi, saanka 1 fauziyyah har yanzu yarinyace da acikin satinnan zaa daura auren inyaso idan aka kawo ta ka ratayeta, kuma ko Bayan raina banyafe makaba matuqar baka auri fauziyyah ba shashasha yana fad'in haka ya juya ya fita ransa a b'ace
Daddy yana fita papa ya kira momcy awaya, aiko tana dagawa ya fashe da kuka


Momcy hankali tashe tace papa lfy mene yafaru? Da kyar yayi shiru yafada mata yadda sukayi da Daddy


Rarrashinsa tayi tace kayi Haquri zuwa kudawo ba gobe daku dawoba, yace eh


Toh kaje kabawa Daddy Haquri inyaso idan kundawo dansan abinyi tunda baka so aiba dole


Yawwa momcy pls help me out, kada kadamu son ammafa kaje kabasa Haquri


Gaskiya nifa momcy bawani Haquri dazan basa kawai rabu dashi, ganin zai tsiyar mata rikici yasa tace shikenan sai kundawo din




Washegarin dawowarsu momcy tasamu Daddy akan maganar fauziyyah, nan yamata ba Daddy yace kuma kada tasake sa bakinta aciki tinda goyon bayan danta take


******
Watanni papa uku da dawowa Daddy yace toh papa ya shirya next week zai fara fita office


Ransa dai bai soba haka ya amince


Watan papa biyu da fara fita aiki amma har ansanshi acikin asibitin dan kwarewansa akan aikisa dik wata lalura indai yashafi harkan qashi, da ikon Allah bata gagararsa


Hakan yasa kowa Dr Alamin, sai dai miskilanci yasa bai kula kowa, cleaners kuwa basa barin ya kamasu da laifi dan yanzun yaci mutuncin mutum baqaramin aikinsa bane


Ahakanma yanzun sai ya gadama yake fita aikin, acewarsa baison stress, Daddy dai ya zuba masa idanu tsakaninsu sai adduar shiriya






Pls ku managy da wannan, battery na yayi low




✍🏻Faty Mmn Faty
[10:39PM, 8/6/2017] β€ͺ+234 703 448 8635‬: 🌾🌾🌾🌾🌾🌾




🌾🌾🌾🌾




🌾🌾🌾






Budurwar Qauye πŸ€·πŸΌβ€β™€πŸ€·πŸΌβ€β™€πŸ€·πŸΌβ€β™€


Written by Faty Mmn Faty


July, 2017






0⃣5⃣
Haka rayuwa take tafiya, inda kullum alamarin papa qarauwa yake, tun su momcy suna damuwa har sun dawo yimasa addu'a kawai


Afannin aikinsa da kyar Daddy ya shawo kansa ya amince yana fita kullum, gashi teaching hospital ma sun nemeshi yazo ya masu aiki


Yacema Daddy shifa barai iyaba, aiki dai masa yawa, Daddy yace masa ai hakan ba laifi bane inkuma bazaiyiba shiya sani


Ganin ran Daddy ya baci yasa ya amince
Kafin wani lokaci, kamar wasa sunan Dr Alamin yabazu


Sannan hanyar shigan kudi ya qaru masa, sai iskancinsa ya fi nada


Wani gida flat mai kyau sosai yasaya a sokoto road, wanda ko su Daddy basu san yasayaba


inya taso daga wajen aiki can yake wucewa ya sha shagalinsa


Amma dik abinda zaiyi da mace sai dai ya romancing d'inta ya barta dan baqaramun kyankyami yake da ba


Sau da dama TJ kan ce masa anya kuwa Ameen kana da lfy


Yace me kagani, haba abokina dik irin lokacin da kake b'atawa da mace amma baka iya....


Dariya kawai yayi yace umm kawai banson qazanta da jaqwali shiyasa tinda mutum baisan suwane suka.......


TJ ya jinjina ma abokinsa yace tab wlh nikam sai naci kudina tsaf dana bari


Papa yace kadafa watarana kaci wahala


TJ yace ina nimahaukacine da zanyi ba condom


Papa yace kabi dai ahankali


Yanzu gidama bai komawa sai 12 wani tym har 1pm, idan yadawo da wuri kuma to irin 11pm ne


Yanzun hankalinsa akwance yake ganin lokaci yana tafiya bai kuma jin Daddy ya sake maganar waccar *BUDURWAR QAUYE* ba


Inda shikuma har yau baiga macen data burgesa amatsayin matar aureba






************
*Bayan wasu Shekaru*


Yan makarantar secondary ne sun taso amakaranta misalin 12:30pm


Wata kyakykyawar yarinya, yar matashiyar budurwa wadda shekarunta bazasu fice 15 ba


Tana da dogon fiska mai dauke da dara2n idanuwa, dogon hanci had'i da d'an mitsi2n bakinta, Allah ya mata yalwar gashin gira


Fara ce tass wadda idan kaganta zaka fahimci ba algus acikin farin ta


Fauziyyah Usman, daga bayanta wata ta kwala mata kira


Juyawa tayi ba tare da ta amsa ba, ganin mai kiranta yasa ta gyara tsayuwarta dan jiran isowarta


Tana isowa tace, ashe kinfito inatakan dubaki bangankiba sai Aisha salman tacemun kintafi


Fauziyyah tace wlh saurinake yau suna zamuje da mama


Kai Fauziyyah ba kya girma bikin suna kuma


Tsaki tayi gami d juya manyan idanuwanta amasifance tace eh d'in, ni kina b'atamun lokaci mene yasa kika tsaidani


Sanin halin Fauziyyah na fad'a yasa tace haba qawata ba nufina kiyi fushiba amma Allah ya baki haquri, dama note d'in Basic science nakeso ki aramun


Tabd'ijam, kinajifa abinda uncle bala ya fad'a d'azu, kada kowa yayi wasa da note d'insa saura mana term 1 daga wannan mu fara JSSCE
Kuma dik sai antambayemu abinda aka mana tin daga first term


Marairaice murya tayi haba qawata gobefa zan dawo maki dashi


Toh indai kinyi alqawari shikenan, barin nabaki


Yawwa nagode


Bud'e jakarta tayi ta lalimo mata, gashi ta miqa mata saura kuma kibari qannenki su shafamin miya


Uwar masifa ta fad'a aranta, amma afili sai tace haba dai yadda kika bani haka zandawo maki da kayanki


Sallama sukayi kowa ya wuce, tanashan kwana taji horn d'in mota abayanta


Juyawa tayi ganin wadda ke cikin motar yasa ta murmushi da yaqawata fiskanta


Parking yayi ya fito, dogon saurayi choculate colour, kyakykyawa dashi


Da murmushi ya qaraso wajenta, shine kika tafi abinki ko beauty na, abinda ya fad'a kenan


Sunkuyar da kanta qasa tayi, kayi haquri uncle yasir sauri nake kada mama ta tafi ta barni


Yar mama kenan kinfa girma yanzun kam, kibar mama take zuwa unguwa ita kad'anta


Shagwab'e fiska tayi, bikin sunafa damuje a can gongola


Toh shikenan kada na tsaidaki amma amshi wannan nagaji da rashin jin muryarki ko yaushe


Duban tsaleliyar wayar daya miqo mata tayi, shiru tayi bata amsa ba


Amshi mana beauty yace da ita


Gaskiya ina tsoron mama tamun fad'a


Haba my fauzee pls ki amsa kinji inyaso kada kibari mama ta gani


Amsa tayi tace nagode


Aa nine da godia


Ahuta gajiya ko baby na saina kiraki


Toh amsa sannan ta wuce


Juyawa yayi ya koma mota, wanda yasan koda yamata tayin zai maida ta gida bayadda datayiba


*Wanene Yasir?*
Yasir Mukhtar shine ainahin sunansa, asalinsa haifaffen garin Gombe ne, shine d'an fari a gidansu, iyayensa suna zaune a unguwar Buba Shango, kuma balaifi suna da hali


Bautar qasa ya kaishi dambam, inda aka turashi makarantar su Fauziyyah, shine malaminsu na Mathematics


Tin lokacin da yaga Fauziyyah yaji yana tsananin sonta, kuma da aure yake sonta


Da kyar ya shawo kan Fauziyyah har takarbi tayin soyauyarsa, inda yanzu suke tsananin son junansu


Kuma Fauziyyah ta amince masa da zarar sungama JSSCE shima dai dai da gama service d'insa zai turo magabatansa maganar aure


Inyaso taci gaba agidansa, dan jiyake bazai iya haqura har ta qare secondary ba, wannan kenan




✍🏻Faty Mmn Faty
[10:39PM, 8/6/2017] β€ͺ+234 703 448 8635‬: 🌾🌾🌾🌾🌾🌾




🌾🌾🌾🌾




🌾🌾🌾






Budurwar Qauye πŸ€·πŸΌβ€β™€πŸ€·πŸΌβ€β™€πŸ€·πŸΌβ€β™€


Written by Faty Mmn Faty


July, 2017






0⃣6⃣
Tana shigowa gida, sallama tayi tana mai cire hijabin wuyanta


Daga cikin d'aki mama ta amsa mata


Wurgar da hijab da d'ankwalinta tayi atsakar d'aki, jakarma firo tayi da ita sannan tayi super kan gado tana cewa wash Allah na


Mama ta miqe tana tsintar kayan data watsar tana fad'a


Aifa kindawo kenan, Komai haka zaki watsar mun kamar haka kikaga nakeyi


Haba mama zafifa na d'ebo wlh nagaji


Bawani nan dama haka kike kullum, aiko a ruwan sama kika dawo haka zaki hejjefar da kayanki


To mama nabari shikenan


Aikam daya fi maki, inkuma haka zaki keyi ad'akin mijinki to kinada aiki ja


Wuwwurga qafafu tafara haba mama nikuma nawa ma nake, kullum kice gidan mijina


Sai kiyi kuma mama tace tana fita waje


Yanda tabarta haka tasameta akwance, toh kitashi kici abinci gashinnan, kishirya mutafi inkuma bazaki ba toh kada kibata mun lokaci


Tashi tayi zaune ta bude plate din, lafiyayyar shinkafa da miya da maccaroni, yaji naman rago


Nan tafara ci hankali kwance dan mama badai iya girki ba


Nan da nan taci ta shirya suka tafi gidan suna


Gafda magriba suka dawo, basu jimaba Abba yadawo


Bayan sallan ishai, suka hadu sukaci abincin dare atare kamar yadda suka saba ko yaushe


Fauziyyah ta miqe tamasu saida safe, ta wuce d'akinta, sai data kulle qofarta tayi adduan kwanciya sannan ta jawo wayar da yasir ya bata


Nan ta kunna aiko ba tafi 2mins sai call ya shigo


Assalamu alaikum ta fada lokacin data daga wayar


Lumshe idanunsa yayi, yace waalaikumussalam beauty na


Dftn ka yini lfy


Lfy lau my baby n u


Tace umm nima haka lfy lau


That's good, dayaushe kuka dawo?


Umm tin kafin sallan magriba


Ayyah ina ta trying wayarki bai shigaba sai yanzun


Umm yanzun na kunna dftn habiby baiyi fushi ba


Haba dai waneni, nifa yanzun burina bai fice kuyi JSSCE nanba, su dad suzo kodan sami natsuwa


Kai uncle yasir yan....
Katseta yayi nifa banson uncle dinnan, gaskiya


Dariya tayi toh habiby naji barin sakeba


Yawwa ko kefa, nan suka sha hiransu sosai na masoya daga bisani sukayi sallama akan sai sun hadu gobe a school


Rayuwa tana tafiya ma Fauziyyah da yasir yadda suke so, ana haka suka fara exams na second term, kuma idan anyi hutu yasir zai tafi gombe shima


Ranan da suka gama exams, aranan yasir ya tafi amma da kyar suka rabu da Fauziyyah, tasha kuka kam shima ba qaramun daure zuciyarsa yayi ba


Bayan tafiyan yasir Fauziyyah tayi kewarsa shima haka amma saukin suna waya


Ana gobe hutunsu zai qare yasir ya dawo, Allah Allah yake gari ya waye yaga abin qaunarsa


Haka Fauziyyah itama dokin wayewar gari take dan yanzun ta tabbatar yasir yazama wani bangare na rayuwarta


Wanda batajin akwai abinda zai iya rabasu (toh fa lalle akwai chakwakiya inji Mmn Faty)






*********
Daddy ne zaune da Abba wanda ya kawo masa ziyara


Suna harabar gidan Daddy sai hira suke kasancewar saturday ne


Papa ne ya fito cikin shiga ta alfarma kamar kada ya yaushe, rigace navy blue da ash troser, yasha wasu bufolino shoes, gashin kansa sai kyalli yake alamun yasha gyara kuma ankashe kudi


Qarasowa yayi wajensu, da faraa yagaida Abba, Abba ya amsa cikin sakin fiska




Miqewa yayi Daddy barinje wajen TJ


Toh saika dawo yace dashi, wajen motarsa ya nufa wadda tasha wanki sai kyalli take


Mai gadi na ganin haka dasauri ya bude qofa gudun yin laifi


Sai daya fice sannan Abba ya dubi Daddy yace Alhaji inaga lokaci yayi Da zamuyi Wa yaranna aure, badan mamana ba aa sabida Alamin, bazaiyiwu muna kallonsa har fice munzalin aure ba gaskiya sabida wani dalili nadaban


Daddy yayi shiru yana sauraronsa, sai daya qare sannan Daddy yaja dogon numfashi yace


Gaskiyane Alhaji amma tin bayauba nakeson muyi maganar nan sai dai bansan ta inda zan somo makaba, nayi shiru ne danaga Fauziyyah ma yanzun take kan karatunta


Abba yace ai karatu bazai hana aureba, tinda yanzun nan da watanni uku masu zuwa zasu zana jarabarsu ta JSSCE to ya isa haka agidana, sai kuma ta ci gaba agidan mijinta, kuma ko Alamin yace bai aminta da ci gaba ba to balaifi matarsace, baranma shima ai yasan dadin karatun


Daddy cikin damuwa yace aiko da idan hakan ya faru danafi kowa farin ciki, sai dai hakan bazaiyiwu ba




Abba yace bazai yiwuba kuma, yana kallon Daddy

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login