Showing 42001 words to 45000 words out of 86122 words

Chapter 15 - BUDURWAR QAUYE Complete-by miss Deejarh-.txt

26 Nov 2024

4816

abinsa ya farru




Juhaina sosai takeson munnir dan araayinta idan ta tashiyin aure shidata aura haka shima ya amince da batun aurenta tinda shikam ya samu tana masa komai


Bayan ta qare karatunta ta dawo nan suka dora daga inda suka tsaya itada munnir


Lokacin da papa yazo mata da maganar aure bata boyewa munnir ba


Amma shi saiya ce sam baisan zancen ba kuma ba auren da zatayi ta barshi


Nan tace masa wane shi harya isa ya hanata aure dama itace tace data aureshi kuma tafasa sai yaya


Duban bakida wayo yamata yace wlh intayi aure sai da yardarsa dan zaije ya samu saurayin nata yafada masa gaskiyar abinda ke takaninsu inyaso yaga yanda zatayi


Sanin munnir zai iya bin diddigi ya samu inda papa yake yasa ta lallaba shi dan tana matuqar son papa sosai


Dakyar tashawo kan munnir ya amince amma da sharadin suna tare koda tayi aure


Haka ta amince akan bayan bikinta zata sama masa koda gidane inda zai zauna saiya dawo bh da zama harma ya fara karatu
Wannan kenan


*****
Bayan sallar magribah papa da juhaina suka fita basu jimaba suka dawo dama abinci sukaje sayowa


Bayan sunyi parking Abdu yazo dasauri ko da akwai abinda zai shiga dashi ciki


Cikin girmamawa yace barka da dawowa oga


Aha Abdu shine abinda yafada yana miqo masa abincinsu adaqike yace gashi na hutar dakai fita


Juhaina ta fito da leda guda uku ahannunta yayinda uban gayyar shima ya fito


Har zata wuce sai papa yace my queen


Juyowa tayi ta amsa da yess my king


Inaga mu miqama munnir abincinsa idan munshiga ciki basai munfitoba ko


Ok muje to tashi dashi


Munnir kuwa tunda suka shigo yake tsaye ajikin window yana kallonsu cikin baqin ciki


Dan wani haushin papa yakeji cos y rage masa jin dadi ganin sun nufo wajensa yasa cikin sauri yasauqe curtain ya koma kan cussion ya zauna yana latsa wayarsa


Norcking suka masa


Daga ciki yace yess come in


Suna shigowa dasauri ya tashi cikin murmushin dole yace barkanku da shigowa


Papa yace yawwa amma yana tsaye cos baxama zaiyiba


Miqomasa take away nasa tayi tace bross ga abincinka sai da safe


Allah ya kaimu yafada yana bin bayanta da kallo


Nace sai kayi ai matar wani ceπŸ™„


Bayan sun ci abinci papa ya dubi juhaina amma bada wasa ba yace my queen yakamata kifara dafa mana abinci tunda kinga yanzu ga munnir ma bai dace kullum muriqa bashi abincin wajeba


Ganin yadda yayi maganar bada wasa ba ya kuma sha murr yasa tace shikenan Allah ya kaimu


Washegari da safe ta dafa masu indomie


Sai dai satisfactory haka sukaci dan bai wani test ba


Da rana kuma haka aka kwaba white rice da stew dikda kajin dake ciki amma sam kasa ci sukayi dagashi har ita


Sauran mutanen gidan kuwa banbi takansuba


Ai daga kan dinning yace mata kada tamasu dinner tabari kawai dan yafahimci bata iya girkiba


Haka sukaci gaba da zama ahaka inda azuwa yanzu yafara gajiya da halayenta sam


Gashi bata kunyar idan yace tamasa abu tace bayanzuba


Satin bikinsu biyu TJ ya kwanta rashin lfy fever mai tsanani har saida papa yaje ya saka masa ruwa agida da allurai


Amma abinda ya birgeshi da gidan TJ shine tsaftar matarsa ko ina kyalkyal kamar baa takawa sai qamshi kawai dake tashi ta ko ina


Gashi ya lura da tana son TJ sosai ba irin sonda juhaina kemasa ba tinda dik abinda yakeso shi take masa


Agidan ya wuni ranan bayan tagama abinci ta kawo masu amma TJ sai ya gagara ci


Papa kuwa haka yaci yaqoshi yana santi aransa har yana inama ace matarsa haka take


Ganin yakasa cin abinci dik ta damu sai tambayarsa take mezaici adafa masa


Yace tamasa faten irish potatoe da hanta da alayyahu


Nan da nan ta daho ta kawo masa balaifi yadanci kuwa sai anan hankalinta ya kwanta


Sai gab da magriba ya tafi yana fitowa wayar juhaina ta shigowa


Doguwar tsuka yaja kafin yadau wayar dan


Tun bayan laasar juhaina take kiransa awaya yaushe zai dawo


Cikin jin haushi yace wai meyene kika dameni aidai zandawo ko ko ancemaki bata zanyi yana fadin haka ya kashe wayar dan wani haushinta yakeji yanzu dayaga yarinya qarama yadda ta iya komai da kula da miji


Ita kuwa banda abiya mata buqta batada aiki


Yana tafiya yana tunanin gaskiya dole dasake inma makarantar koyan girki da gyaran gida zata shiga sai dai tashiga dan zamansu ahaka bazai yiyuba


Itakuwa tasamu dama suna sheqe ayarsu da munnir shiyasa ajima kadan ta kira taji koya kusa dawowa kada ya dawo yasamesu atare




Amurtuqe ya shigo gida direct room nasa ya shige sai bayan yayi wanka sannan ya fito


Juhaina ta dubeshi tana zaune afalo tana kallo tace wai lfy kuwa hooney kaketa bata rai


Nakira ka awaya kana wasu magana gashi kadawo kuma ranka abace


Yace eh kawai zamanmu ne yakamata mu gyara


Gyara zama tayi tace toh kamar me kenan


Yace yanxu ace ko girki baza ki iya yimana ba komai idan inason nagani da kyau sai dai inni nayi haba


Kawai nayanke shawara zan maki register a school na koyan girki da kula da gida


Dubansa tayi nan taji ranta ya baci wato raini ne yasa zai zo yana fada mata haka


So kawai gobe zanje na mak........




Hannu ta daga masa tace heeyheey ya isa haka Alamin kul karkasoma wannan maganar


Da mamaki ya dubeta yace ni kikecema hey har kina dagamun hannu


Tace anfada maka din so what


Kuma ko cemaka akayi mai aikice ni da zaka fara tsiro da wani abu aidai ciyar dani dolenkane


Ko ance maka agidanmu inayin girkine har zakazo kanamun wasu surutai da shouting


Cikin bacin rai ya dubeta yace lalle juhaina nikike fadama haka ba kunya


Tace nice ma kai kajiko


Hannu ya daga zai mareta sai yafasa


Wata dariya ta sheqe dashi tace ya kafasa lalle da kamari mai tsada dan wlh ramawa zanyi tsaf ni banza bazata shani ba


Ko ashaye kazo kada ka taba kwatanta dukana dan ni bazan tolarating nonsense ba




Dubanta yatsaya yi dan baitaba tunanin tasan yana shan wani abu ba tunda boye mata yake


Itama dubansa tayi ido cikin ido tace yess ko ka dauka bansan kana shayeshaye bane kawai kallonka nake so kada kafara abinda zai dameka kaji nafada maka tana fadin haka ta wuce shi tabarshi awajen


Tsabar mamaki da bacin rai yakasa koda motsi kamar wadda aka dasa......




Wai ina labarin mutan Abujane kamπŸ€”


Kubiyoni a next page domin jin labarin *Swt Fauzy*






✍🏻Faty Mmn Faty












🌾🌾🌾🌾🌾🌾




🌾🌾🌾🌾




🌾🌾🌾






Budurwar QauyeπŸ€·πŸΌβ€β™€πŸ€·πŸΌβ€β™€πŸ€·πŸΌβ€β™€


Written by Faty Mmn Faty


August, 2017






4⃣4⃣
Ahankali ya wuce ya nufi room nasa yama rasa wanne irin tunani zaiyi guda daya


Tun daga ranan ya shareta ya fita aharkarta shi atunaninsa zatazo ta basa haquri


Amma har sukayi 5days ahaka itama bata kulashi kamar yadda bai kulata


Abincima sai dai ta tura asayo mata


Papa kuwa abin ya masa yawa wai suna yana da mata amma babu abu daya dayake amfanuwa dashi ata bangarenta


Dan abinda yake samunma yanzu baisamu tunda sun kancake


Gajiya yayi yaje yasameta ya lallaba ta suka shirya


2weeks later
Yanzu hutun daya dauka awajen aiki ya qare hakan yasa juhaina ta bude sabon babin walawanta


Sassafe kafin papa ya tafi aiki munnir yake fita amma yana fita zata kirashi awaya ya dawo


Ta back door yake shiga wajenta yadda bawanda yake sanin shigarsa


Kullum suna shan shagalinsu da munnir hakan yasa yanzu ko papa bako yaushe yake samun biyan buqatarsa


Dan taringa masa hanya2 kenan aa daga tace batajin dadi sai tace bacci takeji


Idan ya matsa mata sai tace toh bata cikin mood din wannan abin


Gashi yanzu tamaidashi kamar ATM mashen sabida kullum acikin ya bata kudi take


Ga yawon tsiya da koyaushe sai dai ta dauki motarta ta shiga gari


Sau da dama haka zai dawo bai sameta ba


Yau dama tun bai fita ba yamata kashedin kada ta fita ko ina idan yadawo office zasuje gida sugaida daddy baiji daddy ba


Bayan ya dawo suka shirya sukaje basu jima ba ta dameshi da sutafi sabida yadda bata samu fuska awajen momcy ba haka aunty niima bata sake mata ba


Bayan sun tafi aunty niima ta dibi momcy tace momcy wlh matar papa ashe bayarinya bace yanzu naqare mata kallo da kyau


Cikin takaici momcy tace wannan ai idan bata girme masa ba toh saidai suzo saanni dan bai isah ya girmetaba


Aunty niima tace wai ya labarin fauziyya ne kam nakai 3days banyi waya dasuba


Momcy lfyrta qalau dazunma munyi waya da mabarukha tacemun tatafi makaranta


Aunty niima tace Allah sarki Allah ya bata miji nagari yarinya mai haquri


Momcy tace insha Allahu Allah zai canza mata da mutumin kirki


Haka sukayita hiransu suna jajanta abinda ya wuce


*****
Juhaina ce tsaye gaban papa ta riqe qugu ranta abace


Fiska a tsuke tace wai Alamin maeke damunka ne dannace kabani kudi shikenan sai kafaramun kididdiga kuma kana dashi bawai baka dashiba


Shima cikin fada yace ai banace bazan bakiba but i just want to know mezakiyi da kudinne ke kullum cikin abaki kudi kuma banga me kikeyi dasuba


Ahasale tace idan bazaka bani bane kawai kafadamum bawai kana wani kwana ba


Kallonta yayi dakyau sannan yace toh bazan bayarba ki kwata


Ok is that what u said tace dashi tana wani turo qirji


Yeah haka nace kin wani tsareni kamar wani danki kina turomun tsumma


Kutt qirjinawa ne tsumma ta fada cike da bacin rai


Adaqile yace toh meye acikin ido banda ruwa ni bani hanya kiga ina da abinyi


Naqi nabaka hanyan marar mutunchi kawai kuma ahakan kake kwantar da kwadayinka ba


Ya tsina fiska yayi yace eh arashin uwa ba


Nan sukayi tsiya tsiya kamar zasu daki junansu


Da kyar yasamu ya shige dakinsa ya kulle dan shakkar juhaina yake kuma ya tabbata idan ya daketa zata iya ramawa shiyasa bayi attempting dukanta


Kwanaki na tafiya, watanni sun shude


Haka rayuwa yaci gaba da tafiya tsakanin papa da juhaina


Zaman lfy da kwanciyar hankali sun qauracem papa kullum yana yawon wajen cin abinci kuma itama dole ya kawo mata nata inba haka ba bayi da kwanciyar hankali


Kudi kuwa ko yaso ko yaqi dolensa ya bata


Abunda yafi daminsa yanzu yawo da ta qara couse akai yakuma rasa inda take zuwa tunda bata da yan uwa bauchi amma kusan kullum bata yini agida


Munnir kuwa yanzu yayi sabuwar budurwa


Dazaran juhaina ta bashi kudi ita yaje zuwa ya kashewa shiyasa kullum acikin tambayarta kudi yake


Time to time kuwa yana zuwa kd yayi two weeks harma fiye da haka


Yanzu haka mota juhaina tamasa alqawarin zata canza masa


Itama can wajen yawonta tayi sabon kwarto shiyasa yanzu bata damu da mumnir ba


Ita yanzu hanyar da zata samu ta koreshi take nema shiyasa takeson tacanza masa mota ta lallaba shi ya koma kd


Wasa gaske yanzu aurensu ya doshi shekara amma shiru ko batan wata bata tabayiba sabida kwayoyin hana daukar ciki datakesha


Dan bata shirya haihuwa yanzuba acewarta zata tsufa da wuri kuma ma ita bata shaawar yara dan wai takura garesu


Ya zuwa yanzu dik wadda yake tare da papa zai fahimci akwai abinda ke daminsa kawai dai bai fito ya fada bane


Amma acikin zuciyarsa yafara danasanin auren juhaina tunda bai qareshi d komaiba


*****
Aunty mabarukha nagani tsaye ajikin mota da alamu fita zatayi unguwa sai dai kamar jiran wani abu take


Fauziyyah ce ta fito cikin shiga ta alfarma wadda sai danayi da gaske naganeta


Taqara haske taqara girma


Wata arabian gown ce pusher pink wacce ta matuqar shan adon duwarwatsu masu kyallin gaske


Ta rolling veil din rigan akanta hannunta riqe da wata waya mai dan banzan kyau


Cikin sauri ta qaraso wajen aunty
Tana cewa am sorry aunty nabarki kina jirana


Aunty tayi murmushi tace no badai kin gamaba muje bazama mujima ba zamu dawo sabida kada su daddy sudawo daga islamiyya


Ok ta fada tana shiga mota


Gidan wata qawar aunty sukaje suka karbo wasu kaya tadawo daga dubai


Bayan sundawo yara ma sundawo daga islamiyya suna hira afalo


Aunty ta dubi fauziyyah tace Fauziyyah inaga tinda yanzu kina SS2 kawai kizana SSCE inyaso bazaki fasa zuwa school ba


Idan paper yayi kyau sai munemi admission kawai


Fauziyyah tace toh Allah ya kaimu


Aunty tace inyaso idan anyi hutu bazuwa dambam sabida kisamu kiyi karatu sosai


Cikin ikon Allah fauziyyah tana cikin shekaranta na biyu da komawa makaranta ta zana SSCE


Kuma da ikon Allah papers nata sukayi kyau dan fauziyyah dagaske take karatu idan kuna magana da ita zaka dauka tagama university sabida yadda takware a turanci


Kuma tana daukar shawara da nasihar da aunty take mata akan karatu


Takan cemata kiqara maida hankali akan karatunki sabida kizama wani abu kema arayuwa kinga dai abinda namiji yamaki akan rashin karatu


Hakan yasa ita kuma tayi alwashin sai tayi karatu mai zurfi


Lokacin da paper suka fito dikkansu suka taho bh


Daddy yayi murna sosai


Sannan yace meye shawarin aunty


Aunty tace yanzu dama sun sayi jamb form sun kuma sayi form na gwagwalada university


Daddu yayi shiru yace jiya sunyi magana da mr khan wani friend nasa dake india


Kuma yamasa magana akan asamawa fauziyyah gurbin karatu a jami'ar new delhi


Kuma ya tabbatar masa wannan badamuwa zai trying best nasa yace atura masa takardunta


Sosai sunji dadin shawaran da daddy ya yanke


Kwanansu daya ta wuce dambam abinta dan bata kaunar abinda zai hada ta da papa


Cikin watanni uku komai ya kankama na tafiyar fauziyya dan tasamu admission kuma agidan mr khan zata zauna dan abokin daddy ne sosai


Ranan talata su daddy suka kaita airport dake lagos dan tacan zasu tashi


Qarfe uku na rana jirgin su fauziyyah ya bar nigeria ya nufi india...[truncated by WhatsApp]










[7:12PM, 8/26/2017] β€ͺ+234 803 082 4581‬: 🌾🌾🌾🌾🌾🌾



🌾🌾🌾🌾




🌾🌾🌾




Budurwar QauyeπŸ€·πŸΌβ€β™€πŸ€·πŸΌβ€β™€πŸ€·πŸΌβ€β™€


Written by Faty Mmn Faty


August, 2017






*I dedicated this page to Zainab Abdulmumini(Mmn Samha) n My Swt Sis Fauzy, Allahu ya barni daku Mmn Faty 😍😘*




4⃣5⃣
Dawuri ya dawo gida cos yana da sugery da yamma a asibitin daddy


Akwai wani mutum da zaamasa aiki a spinal cord nasa


Yana shigowa tin daga parking space ya gane juhaina bata nan sabida he did not see her car


Key nasa ya bude qofa ya shiga ciki dan inda sabo ya saba da hakan


Dik randa ya kuskure ya bar key nasa kuwa to zai zauna a gate jiranta


Sabida rana daddaya ne zai dawo yasameta agida


Room nasa ya shiga ya kwanta nan bacci ya kwasheshi sai pass 3 ya tashi


Cikin dauri ya shirya ya fito sabida 4:30pm zai shiga aikin


Fitowa yayi ya kulle dakinsa dan ya kuskura ya bari abude sai tamasa barna


Amma ga mamakinsa bata dawoba ficewarsa yayi kawai abinsa


Bashi ya fitoba sai wajen 7 sallah yayi sannan ya nufi gida amma sai daya tsaya a resturant yaci abincinsa sannan ya wuce gida


Dagangan yaqi saya mata yace taci yawon taqoshi yau bazai saya ba


Har lokacin daya koma gida nanma bata dawoba


Tabe bakinsa yayi yaje yayi wankansa yayi sallah sannan ya fito ya kunna press tv yana kallon wani program da sukeyi


Har wajen 9 sannan yaji shigowarta


Gyalenta a hannu ta shigo falo


Ganinsa azaune sai tayi kamar bata ganshiba zata wuce
Keh daga ina kike da wannan daran yafada yana kallonta


Ko cikanka bata ce dashiba zata wuce ta gefensa


Cikin sauri ya riqo hannunta yace bada ke nake maganaba nace daga ina kike


Hannunta zata fisge yayi saurin sake riqeta sosai sannan ya miqe tsaye


Yace juhaina wai me kika maidanine dan iskanci ina maki magana sai kiqikulani toh inkinga kinbar wajennan sai kinfada mun daga gidan ubanwa kike at this time


Wani walaqantaccen kallo ta wurga masa sannan tace daga gidan uban mai tambayar nake


Nan take yaji xuciya ta debeshi watoma harshi zata zaga


Aiko nan take ya daga hannu ya wanka mata mari mai kyau


Yana sauqe hannunsa itama ta daga hannunta ta zabga masa mari tana huci tace kai har ka isa kadakeni to ko ubana bai dukana baran kai banza a banza ta fisge hannunta ta wucectabarshi


Shikuwa mamaki ne da baqinci suka hanashi cewa komai ko ya tanka mata


Wani zafi ne kawai yakeji yana taso masa daga kasan zuciyarsa kamarshi ace matarsa har tadaga hannu ta mareshi


Tsabar bakin ciki nan take idanunsa suka caza launi suka qanqance


Dakinsa ya nufa ya bude fridge ya dakko wine nasa ko takan cup baibi ba


Ya dannan bakin kwalbar amma maimakon tamasa dadin sha sai yaji wani daci sabida yadda zucitarsa ke tafasa


Nan take sai tunanin fauziyyah ya fado masa


Yaune rana tafarko daya fara tunota tinda ya saketa


Tunanin yadda yake nada mata duka yakeyi amma koda wasa bata taba tunanin fada masa magana mai muniba baran tarama


Ya walaqanqanta ta son ransa amma yarinyar nan haka zata haqura sai dai tayi kukanta tayi shiru bata taba fada ma waniba


Anya kuwa yamata adalci kuwa nan yaji xuciyarsa tasake quntata


Kotana ina yanzu ko wani hali ta shiga lokacin daya saketa bada haqqinta ba


Nan take zuciyarsa tafara bugawa da sauri sauri


Nan yafara tuno irin yanayinta kyan fuskarta yanayin jikinta


Tuno rananda yafara ganin qirjinta yayi nan take yaji wani kewanta marar misaltuwa yana shigansa


Zuciyarsa take raya masa inama har yanzun itace matarsa ba juhainaba daya rungumeta tsakani da Allah da bai cutar da ita ba


Nan ya tuno qamshin girkinta idan tana dafa abinci amma zuciyarsa ta cuceshi ta hanshi aminta da ita


Cikin qunan rai yake zargin kansa da mai yasa tunda baiga wannan abubuwanba sai yanxu da bai masan inda takeba


Nan wata zuciyar tace wataqilanma tayi aure abinta


Damm yaji zuciysrsa ta buga wani zafi yasakejin yana mamayeshi har yana zufa dikda sanyin AC dake bugawa


Haka ya ajiye kwalbar giyar dan bazai iyama shaba


Yadda yaga rana haka yaga dare sabida tunani daya addabeshi ya kuma tabbatar ma kansa zuciya takaishi tabaro tunda gashi yau yarasa tudun dafawa




Tundaga wannan ranan tsanan juhaina ya dasu a azuciyarsa amma haka yake zaune da ita ya kuma kasa saketa


Hakadai suke zama marar dadi


Sai abinda yafi daminsa wato yadda tunanin fauziyyah ya addabi rayuwarsa ba dare ba rana


Wani matsanancin son kasancewa tare da ita yakeji


At last ya tabbatar ma kansa sonta yakeyi


Rasa mafita yayi yaje yasami TJ ya fada masa abinda ke faruwa


TJ yaso yayi masa dariya amma ganin halin dayake ciki sai ya danne


Yace toh wai bakada labarinta ne


Papa yace banma san inda takeba ko agidan momcy ban sake ganintaba


TJ ya nisa yace toh yanzu shawarn da zan baka kadage da addu a idan rabon kace tadawo gareka


Nikuma zan tambayi khairy tunda yar uwartace dole nasan tana da labarinta inma aure tayi inma ko me nene zamuji


Godia yayi ma TJ sosai dan

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login